jikinsa ta fada qeyarta ta samu masauki a tsintsiyar hannunshi fuskarta na facing tashi fuskar,yabi oily eyes and golden eyes dinta da kallo wadanda suka dada sheqi saboda hasken farin qwai daya mamaye falon ya haska cikinsu,ya kalli dan qaramin bakinta da yake motsi yana tattara kalmomin kayi haquri cikin rudewa
Ranshi ya baci,wai me yarinyar ta maida shi ne?,dan iska?,haka wancan karon tayi masa fa?,tana so tace masa a age dinta bata taba ganin romance tsakanin mutum biyu ba saboda tsabar rainin hankali?idan ma hakanne yau zai koya mata hankali,a hankali ya soma kusantar da bakinsa zuwa nata,numfashinsu ya soma gauraya,tsoro da rawar jikin maryam ya dadu,don tuni zuciyarta ta gama ayyana mata abinda abdallahn ke shirin yi
karon farko tattausan lips dinsa suka taba haduwa da na wata diya mace kamad yadda yake haka a gurinta,baisan yadda akayi ya tsinci kanshi da tsotson lausasan lebunan nata ba cikin rashin sani
''hasbunallahu wani'imal wakeel''kadai take ambata cikin zuciyarta,gudun zuciyarta ya dadu har numfashinta na qoqarin janyewa,hawayen dake malala kan fuskarta ne ya soma taba fuskarshi da sajen bakinsa na quater millon
''abdallah!,meye haka kake yi?''salma ta fada cikin qaraji da wani irin yanayin baqin kishi da bata taba shiga irinshi ba,a nutse ya saki bakin maryamun ya juya yana kallon salmar wanda hakn ne ya bawa maryam qwarin gwiwar hada ragowar qarfinta don ta tsere masa,saidai tana tashi taji ya cafko dantsenta idanunsa na kan salma,kallon 'yan sakanni ya mata ya maida idonsa ga maryam
cikin fada da tsawa yaso yi mata maganar amma sai ya gaza,kasala ce ta saukar masa lokaci guda tamkar mai jin tsananin barci
''gobe ma idan kinganni tsaye da wata kimin kallon dan isaka,zaki ga yadda ake iskanci ra'ayil ain''ya fada yana kallo tsakiyar qwayar idonta da hawaye ya cika yake zuba kana ya cikata,da gudu kuwa ta bar gurin sai ya bita da kallo yayin da salma ita kuma ta tsare shi da idanunta wadanda suma tuni suka kawo qwalla
''haba,haba abdallah,irin wannna cin fuska haka da me yayi kama?cook dinka?''ta fada tana nuna hanyar da maryam din tabi da yatsa ''abdallah ka rasa bakin da zaka tsotsa sai nata,ni me na gaza da shi?just hugging dina kawai nace kayai ka kasa sai gashi ka buge da kissing house girl''
''hey!stop''ya tsaidata cikin hade girar sama data qasa,ya qara taku biyu ya iso gareta ya tsaya agabanta
''kada ki sake ambatar nayi kissing yarinyar can,kaifi tayimin nayi punishing dinta,ina fata kun fahimta''
murmushin takaici ta saki sannan takama qugunta da hannu daya tana girgiza kai
''kada ka maidani jahila mana abdallah,sau nawa ina maka laifi ka taba punishing dina ta wannan hanyar''
har ya juya vaya taba dauke briefcase dinsa sai ya waiwayo
''ita tana showing kanta a matsayin kanta a matsayin mai nutsuwa tana min kallon abinda ban taba aiwatar da shi ba,kinga gwara nayi mai dalili ko?''
girgiza kanta ta sake
''ko jikina kunne ne bazan yadda ba,kayi ne da manufar wulaqantani da nunama duniya iyakata''
''well,idan hakan kika zaba shikenan daidai ne''ya fadi yana kewayeta ya fice daga sashen bayan yasa key dinshi ya kullesu ta baya kamar yadda yazo ya tarar da su,dama abincinshi ya shigo yaci ya sameta zaune ita daya afalon
kamar ta dora hannu aka tayita rusa ihu haka ta ji,hawaye shabe shabe ta shige dakibta bayan ta qudiri abinda zata aiwatar musu a gobe
Qarfe goma ta gama breakfaat di gidan ta shiryashi a dining,Allah Allah take ta kammala komai ta shige dakinta don bata son haduwa da kowa uwa uba abdallah da take masifar jin haushi tsoro da tsanarsa,ta yanke ma zuciyarta abdallan yana layin 'yan iskan maza ne kawai,tuni ta bashi wannan sunan
tana gefan gadobta tana shafa mai bayan sanya doguwar rigar atamfa da tayi mai dogon hannu taji wayarta na b'urari,sunan mami ya soma yawo saman screen din,haka kawai gabanta ya fadi,cikin rashin kuzari ta sanya robar lotion din dake hannunta a gefanta kana ta daga wayar,tana qoqarin gaidata taji tace
''ki sameni yanzun a sama''
''to mami''ta fada cikin rawar murya,kasa ci gaba da shiryawar tayi sai ta zaro blueblack din hijabibta ta ware shi daga gugarsa ta sanya ta miqe ta fice a dakin
kallo daya ta yiwa mamin gabanta ya fadi don zata iya cewa a iya saninta da ita bata taba ganin yanayin fuskarta haka ba,gefanta salma ce zaune fuskarta jazur idonta a tashe,a salube ta qaraso,qasa ta zauna daga can gefe tana fadin
''barka da safiya mami''
''matsonan''tace da ita tana nuna mata gabanta ba tare da ta amsa gaisuwar tata ba
''maryam,me ya faru jiya da misalin daya da wani abu na dare tsakaninki da abdallah?''wata mummunar faduwar gaba ta ziyarce,tsoro da fargaba suka mamayeta ,bata raba dayan biyu wani abun salman ta gayawa mami mai muni a kanta
kimanin minti uku mamin na saurarenta babu amsa,don bata da bunda zata ce din
ta fadi gaskiya?,bazata iya ba,tasan mamin mai yarda ce da gaskiyar abunda ta fada din amma bata burin shiga tsakanin soyayyar da da mahaifiyarsa don ta dan dana hakan ba lamari ne mai dadi ba kona second guda
ta musanta kuma ya zamo mata zunubin qarya,idanun mamin na kanta tana jin babu dadi cikin zuciyarta,don har ga Allah 'yar cikinta take kallib maryam,dan yanzu ba'a shaidarsa duk da ta shqida da nagartattun halayen abdallah,amma yaran zamani koda yaushe yana iya sauya halayyarsa,tsoronta daya kada ya yaudari maryam din ya bata rayuwarta,hakan idan ta tuna shike qara hasalata da sa mata suya cikin zuciya
''dake nake magana kinhi shiru''
shirunne ya sake biyo baya,tuni hawaye ya soma ambaliya cikin idanunta tana sa gefan hijabinta tana sharewa
''to tunda kinqi magana bari na kira ahi shi mai gayya mai aikin yayi bayani''
''a'ah mami,tun farki na gaya miki ba laifinshi bane''
salma ta fada da sauri har tana kamar zata dafe hannun mamin da ya dauko waya don kiran abdallah
wani kallo mamin tayi mata
''bana hukunci da ji daga bakin bangare daya ba tare da dayan ba,koma mene da nashi laifin kuma tilas ya bayyana nan,''
mami ta qare maganar tana kara wayar a kunnenta
shiru ne ya biyo baya har ahigowar abdallah,sanye yake da kayan training ajikinsgi wanda da alama yana filin motsa jiki ne,hannunahi daya handkhercief ne yana tsane gumin suma da fuskarshi,daya hannun kuma gorar ruwan swan ce dake fidda gumin sanyi bisa dukkan alamu a falon qasa ya daukota
da zolayar mamin ya shigo falon saidai yanayin fuskarta kawai ya bayyana mishi ba lafiya,shi sam bai kula da su ba cikin falon ba sai da mami ta jeho masa irib tambayar data yiwa maryam sannan ya kuka da salma
cikin ko in kula yace
''nothing happened,nasan dai sha biyu da rabi na dawo gida,so ina jin yunwa sai na bude nan na shigo naci abincina,sai waccan da na hadu da ita zaune a falo tana game''
''ita kuma maryamu a ina kuka hadu da ita?''ta fada tana nuna masa ita wadda kanta ke duqe
yatsan bata yabi da kallo har zuwa gun maryam,sai ya yamutse fuska
''wace kuma maryamu?''ya fada yana shanye ragiwar ruwanshi,sai ran mamin ya baci,ita zai bunne,tasan waskewar abdallah sarai tunda ita ta haifeahi,kadan daga aikinshi ma yace bai tabajin sunan ba sai yau
''ni zaka ninke a baibai?,ko ka manta cewa ni na haifeka na raineka?, a hannuna kayi wayo?,naci kashinka da fitsarinka?,yaushe abdallah ka sauya hali?,ita da na tambayeta ai tasan baku da gaskiya shi ya sanya tayi shiru bata ce komai ba,amma kai da yake madainiyar wayonka ta tambayeta sai ka nemi raina mata wayo ko?''
ya danyi qasa da ido dob sam kalaman mamin basu yimishi dadi ba,bazai iya yaushene na qarshe da rayi masa irin wanna fadan ba
muryarshi a sanyaye yace
''idan ita ta gayamiki ai sai ta bude baki mami ta fadi abunda na mata ko?''
''ta gaya min ne tunda tare kuka aiwatar,mai kishina binda ya faru ne ta fada salma,har yaushe ka farq neman yaran jama'a,ko kunyar ina cikib gidan bakayi ba?,kasan illar da girman zunubin abinda kuka so aikatawa badan Allah ya kawota ta hana afkuwar lamarin ba,mai makon kuma ka gode mata sai cin mutunci ya biyo baya?''
sumewa ne kadai maryam bata yi ba a zaune kukan da take aboye sai ya koma na fili,ran 'yan maza yq baci take idanunshi suka sauya kala,ya zubawa salma ido wadda runi dana sanin abinda ta aikata ya mamayeta,ita so tayi aci mutuncin maryam ita kadai a kuma koreta ta bar gidan,kasa daukar irin kallon da yake matq tqyi tqyi qasa da idanunta
muryarsa a kausaahe cike da sautin fushi yace''wanne la'a nannen Allahn ne ya mana wanna qazafin,ko da yake mami kince salma ce,amma nayi mamki mami,kin san halina ciki da bai,kinsan abunda zan iya aikatawa da wanda bazan iya ba,me yasa lokaci guda wata can zato ta rushe kyakkyawar fahimtar da mukayi shekara da shekaru da gina ta,kai cina da har yau,ban kubuta daga zarin zan aikata zina ba daga gun mahaifiyata''ya fada yqnq girgiza kai jijiyoyin kansa na tashi,sai jikin mqminyayi sanyi,tabbas babu kyau gaggawar yarda da abunda baka da yaqini,balle abdallah da maryam,babu wana bata san halinsa ba,dukkansu tasan ne zasu aikata da wanda,ba zasu aikata din ba
ganin da salma tayi mami na shirin yarda da abdallan ita ta tashi a tutar kunya ya sanyata sake,zaqalqalewa
''ni ba la'a nanniyar Allah bace,kuma na gani din ne da ban gqni ba ai da bazan......''
bata qaraahe maganar ba taji quma abakinta,abdallah ya jefeta da ruwan robar dake hanjunahi wanda ko rabi bai sha ba,aka kuma yi sa'a ya sauka a bakin nata,ta dafe lebunan nata wani azabar zugi na ratsata,take lebunan suka fashe,bayan sun kumbura sunyi suntum cikin daqiqar da bata wuce talatin ba
hakan baiwa Abdalla ba ciki fushi ya yo gunta,da sauri mami ta shiga tsakaninsu tasa hannunta tana tokare qirjinsa don iya inda tsawonta yake kenan tana turashi da baya
''ki barni mami na lalata shashan bakin da bai iya komai ba face sharri da qazafi wa mutane''
''ka dakata abdallah,nutsu don Alla banason shashanci''mamin ke cewa,tasan halinshi sarai,bai fiya sairin fuahi ba amma idan ya fusata din komawa yake kamar mahaukacin zaki
kusan minti biyar mamin na artabu da shi
''na nutsu mami,amma na bata minti goma ta tattara dukkan wani abu nata tabar gidan nan,wallahi wallahi ta sake muka sake haduwa da ita sai na nakasta ta,banza shasha sha kawai,don ina rufa asirinki,sau nawa nake kamaki da syrup da capsule cikin jaka,shine har kike da bakin yiwa wani qazafin zina,to idan baki bar gidan nan ba nan da minti goma ba nine zan zamo mutum na qarahe da zaki tiwa qazafi a rayuwarki,bindigata zansa na harbeki ki mutu kowa ya huta''
cikin huci ya juya a sukwane ya fice,da sauri maryam tayi gaggawar jaye qafafunta badon tayi hakan ba kadan ya rage ya take mata dogayen yatsunta
bibbiyu ya dinga hada matattakalar har ya gama sauka daga benan,abida ce da saddiqa tsaye kowacce cikin sleeping dress tayi tsuru tana sauraron abinda ke wakana a saman,zuciyar kowaccensu tayi fari jin an kori salma suna ganin tamkar aiki aka rage musu
wani banzan kallo ya bisu da shi ba tare da ya furta komai ba ma suka watse
cikin mintina qasa da goma salma ta hada komatsanta tana kuka wiwi mami na lalkabrta ta shiga motarta ta fice agidan,ranar sai gidan ya wuni shiru kowa na dakinsa,mamin ma haqura tayi da fita asibitin ranar don tsoron kada ta tafi wata fitinar ta taso,jin shirun yayi yawa abdallah bai sake shigowa ba ya sanyata tattaki da kanta zuwa bangatenshi,don ta san cewa ba lafiya,don komqi akayi bazai iya fita bai gqyq mtq ba,to tabbas yana cikin dakinshi ne
A qurya ta sameahi kwance daidai yayi rigingine kan gadonshi,shigowartaya sanya shi miqewa ya zauna
''me kake haka har yanzu baka fito ba ko karyawa baka yi ba ga azahar ta gota biyu da rabi fa yanzu''
''bana jin yunwa mami''ya fada cikin rashin walwala,sai kuna ya dago ya dubeta
''mami ina fatan bakiyi fushi da ni ba,na kasa sukuni tun dazun''
dama ta sani a runa,yanzun haka bacin ran da ya gqni kan fuskarta ne ya sashi kasa fita,tun yana qarami haka yake,baya juriyar ganin bacin ranta
''zan iya yin fushin da kai dai na haqiqa matuqar baka gayan gaskiyar abunda ke faruwa ba''
''zan gaya miki mana mami,mami kiss ne kawai,wallahi bayan haka babu komai,kuma ko shi din ma haushi ta bani,kallon dan iska take min''ya fada bayan ya riqe hannayen ta cikin marairaicewa
dariya yaso bawa mamin amma sai ta gimtse don ba muhallinta bane
''don tana maka wanna kallon idan banda rashin dabara da wayo ta hakan zaka wanke kanka ta fahimci na gari ne kai?''
''am sorry may mami,nayi kuskure''
a nutse ta dinga masa fada sanna ta rufe da fadin
''idan irin hakan ta sake faruwa raina zai baci fiye da bacin ran daka gani yanzu,don ban yarda asabi Allah ba,duk son da nake maka zan iya ajjiyeshi gefe na hukuntaka hukunci mai tsanani,kada makamancin hakan ya sake faruwa akan ko wace ma indai ba matarka bace''sai maganarta ta qarshe ta bashi kunya ya dan sunne kai
dariya ta danyi
''da nema yau kuma nice akejin kunya''dariyar shima ya tayata
sai kuma ta hade cikin seriouse tone
''sannan abdallah,lallai lallai ya kamata kayi aure indai kana son hankali na ya kwanta yadda ya kamata,ka fidda mata cikin masu qaunarka''
qasaitaccen murmushin nan nashi ya saki
''relax mami na,insha Allahu kwanan nan zan sanyaki farincikin da kika dade kina fata,zan kawo miki mata ta har gida nan kusa,amma fa abida da saddiqa kowacce ta wuce gidansu,don wlh mami bazan iya auran kowaccansu ba''
''naji,saddiqa dama gobe tace zata tafi,abida kuwa dole ayi haquri sai an samu visa,zata sake ko sati uku ne tare da mu''
''shikenan mami,zan wa abokina magana harkarsu ce''
qememe yaqi fita yace zai je ko ina ba sai ya tabbatar ta gama hucewa haka suka wuni a gida gaba dayansu
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:53 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣2⃣
*Allahumma ya imada man la imada lahu,ya sanada man la sanada lahu,ya giyasa man la giyasa lah,ya karimal afwu,ya hasanat tajawuz,ya khaahifal bala'a,ya azimar raja'a,ya aunaddu'afa'ah,ya munqizal garqa,ya munjiyal halka,ya muhsin,ya mujmil ya mun'im,ya mifdil,antal lazi sajada laka sawadul laili wa nurun nahaar,wa dau'ul qamar wa shu'a ushshams,wa da wiyyul ma'i wa hafifushshajar,ya Allahu la sharika lak,ya rabbi ya rabbi ya rabbi,Allah ka shiga lamarin mutanen qasar burma,Allah ka shiga lamarin jama'ar musulmin duniya baki daya don sayyadis saqalain*👏🏽👏🏽😔😔
Qarfe goma saura na dare mami ta shiga dakin nata,har ta gama shirin bacci tana kwance tana jiran wayar abdur rahim da yace ta jirashi kada tayi bacci zai kira ta,da sauri ta miqe tana maida hularta da santsin gashinta ya sa ta sabule,mamin ta dan bita da kallo qauna da tausat
yinta suka lullubeta ganin ta takure ta kasa hada ido da ita
gefan gadon ta qaraso ta zauna kusa damaryam don ta dafa gadon bayanta
'.dago ki kalleni maryamu,mamanki ce fa''sai taji qwalla na shirin zubo mata nauyi da kunyar mamin takeji,gefe daya hauhi da tsanar abdallah na takura zuciyarta
''ki kwantar da hankalinki abdallah ya yimin bayanin gaskiya,ba laifinki bane laifinsa ne,kuma nayi masa gargadi insha Allah bazai sake faruwa ba kinji,ki i gaba da kame kanki maryam kamar yadda kike,daraja mace da mutuncinta yana tqfin hannunta,ruwanta ne ta riqesu su zame mata abun alfahar ruwanta ne ta wargaza,bazan so wani abu ya shafi mutuncinki ba maryamu don tamkar amana kike a hannu na,ko bayan haka ma unajinki har cikin zuciyata,haka za bazan iya yafewa abdallah ba idan ya maki wani abu da ya sabawa shari'a da mutuncinki,duk abinda kuma nayi nayi ne saboda kare martabarki,ina fata kin fahimce ni?''
gayada kai tayi tana share hawaye
''na gane mami,na kuma gode Allah ya qyara girma da lafiya''
wayar abdur rahim ta katse 'yar hirar da mamin ta fara janta da shi don ta saki jikinta,ganin maryam din taqi dauka yasa mamin ta dago wanda ke kiran
''bari in abku waje kinga ma shikenan ya fanshe ni sai ya qarasa lallashin,ki gaisheshi sai da safe''ta fadi tana miqewa cikin dariyar zolaya,kasa amsawa tayi ta sunne kanta saboda kunya mamin na dariya ta fice
hira suke abinsu sosai irn ta masoya kamar sun shekara da sanin juna
''maryam ya kukayi da abban,nasan dai an bani dama ko?''
ta dan zaro ido tana fadin
''wa ya gaya maka,abdul irin wannan zumudi haka''ya marairaice murya
''maryam bani so in rasaki ne inaso a bani dama koda kudine a kawo''
ajiyar zuciya ta saki
''abdul dole dai ai mu danyi haquri ko,tunda yanzun dai kaga azumi saura kwana bakwai,mu bari bayan sallah idan Allah ya kaimu sai ayi dukka abinda za'ayi''
''wa ya gaya miki azumi na hana kai kudi,akwai cousing dina safiyya hudu ga azumi aka kai kudin aurenta,so pls maryam ki barni na kawo kudin idan yaso bayan azumi asa mana ranar aure na qagu ki zama tawa,baki san ya nake ji ba duk lokacin da na kalleki ko naga kin fita a matsayin budurwa ba mata ta ba,bani da wani iko a kanki''
dariya ta saka
''yaushe ma kake ganin nawa ne abdul''
''ina iya ganinki mana da idon zuciya''
''shikenan yanzu mu bari zan sanar da mami na,duk yadda ta kama zaka ji''
da qyar abdur rahim ya barta bayan ya cikata da dad'ad'an kalmomin qauna
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Su hudu ne cikin lafiyayyar motar da idan ka shiga ba zakayi tsammani tafiya akeyi ba sai idan kaga kuna wulga gurare,mami ce da maryam a baya sai Abdallah da driver a gaba
mami cikin shigar leshi dinkin buba orange wanda yasha adon lemin hreen,takalmi jaka da mayafi dukka toomatch masu dan karen tsada da kyau,ba qarya mami gwanar iya ado ce,ko cikin mata masu shekarunta da wuya ka samu irinta goma,shi yasa sam sai ka rantse bata haifi abdallah ba,zakayi tsammani yayarsa ce kawai
maryam ma cikin cikin kwalliyar take amma zamu iya cea kwalliyar jiki don babu wani make up a fuskarta,material ne pich da kwalliyar sea green,tayi adon takalmi mayafi da fashion na dan kunne duka kalan sea green,ba gwanar jaka bace hakan ya sa wayarta ce kawai riqe a hannunta,abdallah dake gaban mota yake ta faman zuba mitar shi kam da an barshi bazaya je ba,ba gun zuwanshi bane idan ba kamawa tayi ba,sanye yake da shadda light blue dinkin tazarce da yaji aikin hannu na maza dan ubansu da baqar hula,takalmi sau ciki baqi da agogo,kallo daya zaka masa ka tabbatar kudin da jikin nashi ya lanqwame ya ishi mai qaramin qarfi jari
''ayita aure gab da azimi barna tayi ta afkuwa''ya fada yana yarfar da hannunshi wanda ke daure da agogon ruwan gold''nikam dai wallahi kam duk wanda yamin aure a irin wannan lokacin alhakin a kansa''
''baka da kunya ka maidani kakarka,yaro duka ka gama mitarka,dinner ce dai si kaje,minti nawa anyi an gama,hajiya mai gado idan da halacci ba zaka mata haka ba,ita tayi yayenka abdallah,ba qaramib sonka take ba''
ya dan waigo yq dubi mamin
''ayyah mami me ya kawo maganar yaye na''ta dago shi qwarai wai shi baya son raini,dariya ta saka
''to meye kowa ma an masa yaye har ni kaina''kadan kadan take bashi labarin quriciyarsa gidan hajiya mai gadon,yana son ji amma baiso wani ya ji masa ya raina shi don haka ya canza topic din
''mami,cikin kwankin nan nake son kawo miki dear ta gaidaki,so kuma bata nan sunje umarar azumi,ni kuma na qagu mami in yi wani motsi''
murmushi ne ya subucewa mami
''ummm,abdallahhh......,yaushe ka zama haka?yaushe sonta ya maka irin wannan kamun?kai har naji ina sonta data iya sato zuciyar birkitaccen yarona haka ta farat daya''
murmushi yayi hadi da lumshe idonsa,ya jinginar da kansa jikin seat din motar yana tunata yana jin wani yanayi na shigarsa,mami ta sosa masa inda yake masa qaiqayi
''dis luv inside of me is strong mami,there ar no boundaries that it can hide''
Kasa daurewa mamin tayi har sai da ta dan daki kafadanshi ta baya dariya ta kamata,ringin din wayar maryam ya katsesu,abdur rahim ne,kamar ko yausheta kasa dagawa saboda kunyar mami shi kuma bai fasa kira
tsaki abdallah yaja yana fadin
''du Alla a kaahe wannan culculator din ya damemu haka nan''
mami ta kalli maryam
''daga kiranki maryam,ba mai jinki hirar mu muke''
tsaki ya kuma j''idan ba zata daga ba asauketa ta kammala wayar ta biyo mu daga baya kota koma gida''
''shut ur mouth,oya ina jinka,muyi maganar dake gaban mu''cewar mami
Minti ashirin tsakani suk iso gun dinner din,ita dai maryam rava idanu kawai take don bata saba zuwa ire iren guraren ba,bata da wannan rawar qafar sam,da dai su jamila ne su lubabatu tof babu na biyunsu
uwar taron dakanta ta fito ta taresu
''masha Allah hajja bintu ina kika samu kyakkyawar diya haka,ko surukar taki ce''
murmushi tayi ta wauwaya ta kalli maryam da abdallah dake bayanta,sai taga sun mata kyau din kuwa tamkar wasu couples,abinda bata taba kawowa a ranta ba ta jishi lokacin,sai taji tana fadi cikin zuciyarta ina ma da gaske ne haka dinne,ya waiwaya ya danqarawa maryam harara sai akayi sa'a suka hada ido,ya dan matso gab da ita har tana sheqar qamshinsa kana yayi qasa da murya kamar mai fada mata abun arziqi
''yi gaba mamalama,kin wani jera da muta ne kamar sa'anninki,salon 'yan jarida su ganmu tare ki samu daukaka ni kuna ki bani kunya'',itakam tsoronshi take don neman tsari take da shi hakan ya sanya batare ce masa komai ba tadan ja da baya da yake ya fita sauri tuni ya dan zar tata
mami ta kalli hajiya mai gado
''diyata ce ita din ma,amma surukar naku na zuwa insha Allahu,don shekaran jiya yaron naki ya min albishir,ya gama ruwan idon nashi da bani kunyar gun iyayen yara''
''a'ah,a qyale yaro na,ai lokacinshi ne a barshi ya zaba ya darje,ai ya cancanci yin hakan''
''um um kada ka ki fasa masa kai''
''ba zancan fasa kai sai tsabar gaskiya''da daddan hirarsu irinta qawaye suka iso gurin da ka tanada don baqi na musamman irinsu
anyi kiran iyayen amarya suzo su nuna tasu karar don haka mami ta miqe,ta dubi abdallah dake ta faman shan qamshi idanunshi na kan waya tunda sukazo
''bari muje nida martmyam liqi yanzun zamu dawo,kaima ya kamata ka qarasa ku gaisa da amaryar''
''ina zan iya tashi an cika guri da sakarkarun 'yammata marasa kamun kai,duk inda ka motsa suna kallinka kamar wasu mayu''
''kaji da shi dai,kallo kuma kayi abun kallin ne dole a kalleka,dukka abokan ango na gun stage suna liqi kaja ka zauna bayan kaima abokinka ne''mamaki ya cika maryam,yadda taji ana tababa da shi kan bazai je ba tayi zaton ma bai sanshi bane
''mami ni bazanje in kalli matar wani ba don nima babu mai kallarmin tawa''
''haka za'ayi naka bikin kenan kana nufin''
''ko za'ayi mami ba zata zo min da irin shigar da amaren yanzun suke ba,sai babballata in zubar''
hade rai mami tayi
''to ni kuwa bazaka balla 'yar muta ne ba ka barmu da jidali ba ka canza tunani''
murmushi ya subuce masa ganin yadda mamin ta hade rai kamr ma ya riga da ya aikata
miqewa yayi ya karbi jakar hannunta yana dariya
''Allah ya barmin ke mamata ni daya,muje in rakaki,Allah ya huci zuciyar hajiyata''
''hutsu ne abdallah''maryama ta fada cikin zuciyarta,suna hada ido ya daka mata harara ya kuma hade rai qyam tamkar bashi yake murmushi yanzun ba
a baya suke binta har suka isa atge din,ya miqawa mami jakar yana fadin
''gashi mami,ayi liqi a hankali''
''haba handsome,girman mami ne ai ta liqa ko nawa take so,babu ji tunda tana da kai''maryam da abdallah suka kalleta lokaci guda don mami bata ji ba tuni da kutsa ciki,wani sakaran kallo yayi mata gami da jan tsaki,ita dai maryam gaba tayi tana qoqarin bin sahun mami tana fadin cikin zuciyarta
''kin debo ruwan dafa kanki''
ji tayi an riqo tsintsiyar hannunta gam ana janta,babu shiri ta waiwayo abdallah ne tuni har ya fara tafiya,tilas ta saita wa kanta hanya ta bishi a baya tamkar raqumi da kala,don idan tayi tirjiyar bin nasa zata iya zubewa a qasa don da sauri yake jan nata
bai saketa ba sai da suka iao teburin na su kana ya sakar mata hannu hadi da yi mata nuni da kujerar data tashi dazu a kai,tsareta yayi da idanunshin nan masu kaifi
''sit,dake aka hada kutingwilar zuwa na nan,shine kuma duka zaku fashe ku barni zaune ji daya kamar yaron mayu,ki zauna ki kula da ni har mamin ta dawo ta karbeki,daga nan ma idan club zaki wuce ke ya shafa''
Tuni hawaye sun cika idanunta,bata ce masa komi ba ta zame ta zauna,shi kuma yayi tsaye hannayenshi harde bisa qirjinsa yana qarewa gun kallo tamkar mai neman wani
matashin saurayi ne yake dosowa gurin,kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewa ya gogu cikin duniyanci,sannu a hankali yake qarasowa har inda maryam din take,shigowarsa gurin kenan idanunahi sukayi tozali da ita,totally ta gama yi masa fatanshi daya 'yar hannu ce,zai iya kashe mata ko nawa ne matuqar zai samu hadin kanta,ta bayan kujerarta ya zagayo yasa dukka hannayenshi ya dafe makarin kujerar
''hello babe...''
gabanta ne ya yanke ya fadi,har ta kasa jiyowa taga ko waye,ga zatonshi bata ji ba don haka ya ranqwafo bayan nata yana shirin sanya hannunshi ya dafa kafadunta
cafkar da yaji an yiwa hannunshi yasan bata wasa bace,tamkar tarko ya kama bera haka abdallah ya riqe hanun nashi tsam,bai gama qarewa abdallan kallo ba yaji saukar lafiyayyun mari guda biyu da suka gigita shi,
hannu abdallah yasa ya yaye dogon hannun rigar t shirt din dake jikin saurayin,take wasu yan qanan rubutu da suka fi kama da na 'yan china suka bayyana a saman tsintsiyar hannunshi,a tare suka kakki juna ahi da mataahin tashin farko tsoro qarar ya bayyana idanun matashin,motsin da matashin ya fara yi da daya hannun nasa da abdallan bai riqe ba yana qoqarin cusa hannunshi aljihun bayan wandonshi ya ankarar da abdallan,cikin hanzari ya dunqule hannunshi ya daki hannun matashin take ya sagar masa da duk wata jijiya da zata taimaka masa ya iya motsa hannun,ya zura hannunshi aljihun matashin ya ciro 'yar qaramar bindiga ya cillata cikin nashi aljihun,qarar da ya saki ita ta janyo,hankalin mutanen dake kurkusa da su,cikin zafin nama da qwarewa da hannu daya ya tsinke duk wani maballi dake jikin t shirt din matashin ya finciketa daga jikinsa hade da juyo da bayan matashin ya kalla,zane ne kala kala a jiki wanda ba lallai kai ka iya ganewa ba
''anaconda isnt it?um?yaron alhj hamza mai qusa''
Abdallah ya fada bayan ya zagayo gaban matashin sunyi face to face,hannunshi daya ya sanya a aljihub rigarshi ya ciro qaramar wayarahi keypad qirar samsung,cikin qanqanin lokaci ya bada order turo ma'aikata inda suke din kana ya maida wayar aljihunsa,idanunshi qyar cikin na matashin yake tambayarsa
''ku nawa ne agurin nan?''shiru ya masa babu alamun zai amsa masa,hakan ya bawa abdallah damar yin tsai yana karantarshi,ba tare da matashin ya masa nuni ba ya karanci tabbas akwai abokin tafiyarsa ahannun daman abdallah,sai kuwa akayi dace shima ya yunquro da niyyar kubutar da dan uwanshi,duka daya abdallah ya waiwaya ya masa a dokin wuyanahi ya zube a qasa yana malelekuwa.
minti goma kyawawa basu cika ba jami'an ss suka iso gurin ya damqa musu su yace su kira jamal hussain ya fara aiki a kansu kafin gobe ya iso office din,mutanen dake gurin kam kowa godiya yake ma Allah suna fadin Allah ne kadai yasan me zai faru badon zuwanshi ba,sai da koma cikin mota ya kira mami yace suzo su taci don baya son,jama'suci gaba da shaida fuskarshi
ko cikin motar tamkar kace ket maryam ta zura a guje take ji,tsoron abdallah ya kuma cikata,ya dubeta da madubin motar lokacin da yake goge hannunshi da handkherchief suka hada ido,hade rai yayi yaja tsaki
''mutum sai shegen tsoro,komai ma tsorataka yake''mami tayi zaton da jama'ar inda suka baro yake
''a'ah wannan lamari fa da tsoro,wannan aikin ai saiku,kawai dai Allah ya tsare mana ku daga dukkan sharri''
murmushi ya saki
''haba mami na,kema fa jaruma ce,kin manta ke ke fede mutum ki ciro abun cirowa ki,mai da na mai dawa ki hadeshi ki dinke ya tashi tsaf yaci gaba da rayuwa cikin ikon ubangiji'
''um um,wannna daban da naku abdallah,a'uzubika bi kalmaatillahit taammaat min kullu ainin lammah wamin kulli shaidanin wa hamma''ta mishi irin addu'ar neman tsari da annabi s a w kewa hassan da usaini r.a
''ameen mami''ya fada don kusan a bakinta ya haddace wanna addu'ar tsabar yi masan da take yi,kuma yasha ganin riba da fa'idar ta
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
ana jibi za'a dauki azumi ta tafi gidan raliya don su tattauna,ba qaramin dadi raliyan taji ba dq jin fitowar abdur rahim da dukkan qarfinshi neman auren aminiyar tata,ta jira har nasir ya dawo tayi mishi bayanin abdurrahim da kwantancan anguwarsu,ya dauka mata alqawarin xaiyi tattaki da kanshi har unguwar ta qoqi don ya mata bincike a kanshi,sosai taji dadin kara da karamcin da hayi mata,sun rabu kan duk yadda ake ciki nan da sati zaya sanar mata,ta mishi godiya sosai,yace babu komai ai an zama daya ya zolayeta da don ma ta qishi ne,dukkansu dariya suka saka da tuno baya da sukayi
kwanki shida kacal ba'a cika na bakwai din ba nasir ya kirata ya mata bayanin abdur rahim bashi da matsala,dukkan abunda ya fadi din haka yake,saidai abu guda bayan kasuwanci da yakeyi din yana da damara wato ma'aikacin tsaro ne,ta masa godiya mai qima sannan suka rabu,data tambayi abdur rahim din dariya kawai yayi yace yana tsammanin bata son auren mai unifoarm ne ya boye mata,bata dauki abun wani seriousd ba duk da ta nuna masa rashin jin dadinta ya kuma nemi afuwarta maganar ta wuce
azumi na da kwana goma ta sanar da abdur rahim ya shirya yazo ya gaida mami,bai musa ba ya amince,ta shirya masa girki na musamman,cikin wani dan kebantaccen gu dake harabar gidan ta ahirya komai,guri ne mai kyau davtsari cike da shuke shuke tamkar qaramin lamvu,duk da cewa daga can bayan gida akwai lambun amma wanna hakanan aka yishi darumfar bunu qwaya daya,qasanta shirye da fararen kujerun roba
mintina goma sha hudu ya rage akira magariba ta shiga wanka,ta ahirya tsaf cikin baqar doguwar riga mai sulbi data wadatu da dutsuna masu sheqi saqar qasar oman,mai kawavta shafa hoda ta zizara kwalli da man lebe,ta taje gashinta tayi acuci da shi daidai lokacin da masallatan garin kano suka soma kwarar kiran sallar magariba dabinonta dan madina dake cikin qaramin fridge din dakin ta ciro ta ciri uku taci ta ciro ruwa tasha sanna tayi add'ar buda baki,bandakinta ta koma tayi brush hadi da alwala ta yi sallar magaribar,kusan tunda aka fara azumi tare suke yin buda baki gaba dayansu,don haka bakwai na qarasa cika ta sauko qasan
tuni har mami da abida sun hallara don haka ta gaida mamin da yi mata sannu da shan ruwa ta soma sarving dinsu,ta kammala ta ja nata ta zauan,bata kai ga fara ci ba abdallah ya shigo ya ja kujera kusa da mamin yana fadin
''mami ke daya zaki ci ki bar autan naki''
''hmmm su auta manya''abida ta cafe zancan,harararta ya danyi
''kinga bansa da ke ba,wanna magana ce tsakanin d'a da mahaifiya''
hannu yasa cikin plate din chips dinta ya soma kaiwa baki dadin na ratsashi,bai ko kalli farantinsa guda biyu da cup da maryam ta shirya masa ba
sai teburin yayi shiru kowa na harkar gabanshi,cakula kawai maryam keyi don bata qaunar zaman cin abincin nan tare,sam bata sakewa
mami ta dubeta tana goge hannunta da ya dan baci da maiqo da tissue
''amma dai maryam ba wanna ce shigar fita zancan ba ko''
tayi murmushi har dimple dinta na lobawa kanta aduqe
''itace''ta fada kanta asunkuye,kallonta abida tayi ta sheqe da dariya kana tace tab,kallonta take kwaia wadda kanta yake cikin tukunya
''ban me yasa baki wa fuskarki makeup ba ko don kinsan ke din mai kyau ce,kyanki yana qara......''
bata iya qarasa zancan ba sakamon ciko pork da abdallah yayi da chips ya cusa ma mamin a baki
tilas ta karba sai davta fara taunawa ta dubeshi
''meye haka abdallah,dure zaka min''
ya marairaice
''mami baki qoshi ba fa,kuma idan ana cin abinci ba'a magana,ki qyale koma mene sai kin qoshi''
dauke kanta tayo ta dubi maryam
''ki duba kan mirrow dina akwai makevup kit ki dauko min yau da kaina zan miki kwalliyar
raka'a shida kacal ta samuyi sallar tarawih a maimakon raka'a goma sha uku davtakeyi,cikin awa daya saiga fuskar maryam din ta canza,zama mamin tayi sosai ta mata make up,abida kanta mamaki ta dinga yi,haka mami ta iya make up mai ma'ana?haka maryam ke da kyau,tun usuli ita din ba maison cika tarkace bace ta makevup a fuska,wannan kaye kayen sai hindatu,kyan da ta yiwa mamin yasa ta ta gaza barinta sai data mata hotuna,ta yi azabqr fita kuwa ahoton
aka gama kuwa a daidai,don gamawar tasu bai wuce da minti uku ba abdur rahim ya kirata gashi a compound din gidan ya samu shigowa bayan tarin tambayoyi da waya da mami ta yiwa securities din kan su barshi ya shigo
''jeki maza diyata ki shigo da shi''mami ta fada tana maida hijabinta data idar da sallar asham
tana qoqarin fita saqo ya shigo wayarta ta zaro tana dubawa,number din abdur rahim ta gani wanda hakan ya sanyata sakin murmushi ta soma qoqarin duba abinda ya turo mata
''ya subhanallah''taji ance bayan taga inuwar mutum a gabanta,da sauri ta daga kanta kana ta duba abinda taji ta taka
qafafan abdallah ne,taja baya kadan da sauri a tsorace,dawowarshi kenan daga sallar asham,sanye da jallabiya fara sol mai gajeran hannu wadda hakan ya sanya dukka gargasar hannunshi bayyana da hular tashi ka fiya naci itama fara,sai ya koma tamkar wani balarabe,kallonta yake kawai wanda har hakan ya bata tsoro,sexy eyes dinshi ya lumshe bisa fuskarta na aecond biyu ya bude
murya qasa qasa yace
''wacce iriyar makauniya ce ke,ki hau qafafun mutum ki taka saboda rashin kunya,idan baki wasa ba zan targada qafafun''tuni idanunta suka kawo qwalla
''kayi haquri ban kula bane''
ya janye shanyayyun idanunshi ya motsa zai wuce,har ta gifta shi yace
''wannan wane irin sakarci ne kwalliya cikin ramadan a irin wannan time din''cak ta tsaya zuciyarta na bugu
''ina zaki?''
''waje zanje.....baqo......''
bai bata damar qarasawa ba ya daka mata tsawa
''oya,wuce ki koma wannan iskancin ba'a gidan nan ba,idan zaki tara mazan ki bari sai a naku gidan''
jikinta na rawa ta wuce ya take mata baya
mami data hangota tace
''a'ah,ina baqon?''kasa cewa komai tayi sai satar kallon abdallah da yayi kicin kicin da fuska ya kuma basar kamar bashi ya korota ba,ya samu gefan mamin yayi zamanshi yana shan ruwan bunun da yasha kayan qamshi wanda mamin ta zuba tana jira ya huce ta sha
''kai abdallah,kai ka dawo da ita ko?''
''eh mami dare yayi me zata fita waje tayi taje ta dauko mana magana?''
''kaga malam baqo tayi yana nan compound ba wani gu zata ba''
''ok,wannan stupid din ita yake jira?,to ki fita mu gani,mami baza a ja mana magana ba agia,ta kwatanta mishi gidansu suje can su hadu''
''kai dakata!banason iskancin banza iskancin wofi,uwarta ne kai ko ubanta da zaka hanata fita ga mutumin da zai aureta,ina cewa jiya kasa bacci kayi sai da ka tasheni ka gayamin rana ita yau akai maka kudin aure?shine zaka hana wasu saboda tsabar son kai,to wallhi ahir dinka ka fita daga sabgar maryamu indai kanason zaman lpy''
saukowa yayi qasa ya sanya gwiwoyinshi a qasa ya kama hannayen mamin
''kiyi haquri mami,wannna ne karo na qarshe insha Allahu da zaki sake samuna da irin wannan laifin,ki yafe min banason shiga fushinki,cikin wata muke mai alfarma''
Sai da ta juya tace da maryam taje ta ahigo da baqon sannan ta kalleshi
''idan kana haka abdallah sai ta dinga jinta daban acikin mu,yin hakan tamkar takura ne agareta,ka gyra pls my son''
''insha Allahu mami''ya fada sannan yayi kissing bayan hannunta
shigowar abdur rahim ya sanya abdallah fita,a nutse suka gaisa da mamin,sosai ta yaba da hankalinshi,shi yake sanar mata maryam tace ita zata fadi ranar da za'a kai kudin aurenta gidansu,ya zabi kwana bakwai tace yayi kusa
murmushi mamin tayi
''maryam manya,kwana bakwai din yayi,Allah ya nuna mana''cikin farinciki walwala da mutuntuna juna suka rabu da mamin ya nufi inda maryam tayi masa masauki
''me yasa abdul kaqi cin komai ne''murmushi ya saki kana ya miqe tsaye yana duba agogon hannunshi,ya dauke idonshi daga agogon ya dan kalli bayanta kadan yasake dauke idonsa
''zan wuce ne maryam,lokaci yayi sai wani jiqon''ya fada agaggauce,a hankali ta waiwaya ta maida idanunta inda taga yana kalla din,abdallah ne tsaye saidai sam ba sashen da suke yake kallo,tuni har abdur rahim ya soma tattakin barin gurin,ta bishi a baya don masa rakiya,ya tsaya cak kana yace
''na gide,bana buqatar ki wahalar min da kanki ki koma ciki,sai haduwa ta gaba?''ya fada cikin sigar tambaya yana daga gira,kafadarta itama ta daga sukayi sallama ta juya don komawa mazauninsu na dazu ta kwashe kayan data shirya masa duk da bai taba komai ba face ruwan,duk da ya bata uzirin cikinshi a cushe yake baya iya cin komai sai da sahur amma bata ji dadi ba
abdallah ta taras yayi daidai yana kwasar garar abinshi,bata ce komai ba ta juya ta bar gurin ta shige bangaren mamin
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣3⃣
💞😍💞😍💞😍
*_godiya ga masoya na_*🙏🏽👩❤👩
*_masu qaunar rubutuna_*💞✍🏽
*_qaunar da kuke min bazaiyu na manta da ku ba,na yaba qwarai da gaske_*😃😍
*_gaisuwa ban girma da jinjina mai qima ga_*
*huguma novels room and huguma conversation room*
*maman aysha novels group*
*hausa novel group by umar dalha 1&2*
*zama na amana group facebook*
*khafinga group 2012 class*
*gaisuwa kai tsaye zuwa ga GARKUWAR ABADAN SISTER RABI'ATU HARUNA*😄😄
*Allah ya barmu tare ya samu cikin masu son juna saboda shi da zuciya guda ameen*
*_rabbanag fir lana wa li ikwaninallazina sabaquna bil eman wala taj'al fi qulubina gillal lil lazina amanu rabbana innaka ra'ufur rahim_*🙏🏽
Sau biyi tana zuwa dubawa taga ko ya kammala sai tazo ta tarar bai gama ba,sai a zuwa na ukun ya sameshi ya ture kwanonin gefe alamun ya kammala kenan,bata ce da shi komai ba ta soma hada plates din guri guda tq zuba cikin kwandon
''ji mana''taji yace da ita,a hankali ta dago kai suka jada ido,ya kafeta da zaratan idanunshi sai ta kau da kanta gefe
''idan kin koma kuma ki sake hada ni da mami na kice ni naci abincin,ko da yake ko kin fada din dama ai aikina aka dauko ki yi ba wai ki dafawa wani qato ba,a qa'ida ma idan kika kuma gigin yiwa wani girki ba da izini na ba ma a albashinki''
ya ture kujerar da yake kai baya ya miqe ya kewayeta ya wuce,ta biahi da kallo tsanarsa da tsanar halyenhi na takura matsi da girman kai na addabar zuciyarta,sai da ta tabbatar ya ahige bangarenshi sannan ta shiga nasu bangaren
🎄🌲🎄🌲🎄🌲
da yake azumi ne qarfe tara ta shirya taje gida,ita da hindatu suka tattauna abinda za'a shirya don 'yan kawo kudi da zasu zo jibi da safe,ruwan roba ta siya carton biyar na lemo ma haka,sai maltina itama carton uku,kujerun da aka fidda dakin mama su aka maida sitroom dinsu wanda rashin wadata yasa yake fanko babu komai a ciki,babu abinda kujerun sukayi tunda ba'a dade da yi musu kwaskwarima ba ta qarin katifa da canza yadin kujerar kuma ba yara gareta ba balke su lala ce da wuri,ko dama can ita mamsn mai tsumi tattaku da tanadi ce,ta siyi leda da labulaye duka aka sanya,sai sitroom din yayi kyau daidai talaka,tuni dama kayan gadon maman aka shiryashi bedroom din baban sun zama nashi
muqullin ta danqa hannun hindatu don tana jin su kula na rawar kan yau a ciki zasuyi zance don duka babu wanda yasan me za'ayi da dakin aka gyara shi haka,wannan rufewa fa da tayi sai taso zama dan zani sukayi dafifi a tsakar gidan suna basu amince ba ai gida dai na ubansu ne babu wanda ya isa ya musu shamakivda wani bangare na gidan,shigowar baban ya tambayi ba'asi wannan karon hindatu ce tayi uwa tayi makarbiya ta masa bayani
to shi din ma wannan karon bai basu goyon baya ba yadda suka saba samu,hakab ba qaramin qullacinsu maryam ya sake sa musu ba,da azahar sukayi sallama don tana so ta leqa raliya,mama ta dakatar da ita tana fiddo da dararen borikan fenti uku daga uwar dakanta
''me wannan a ciki mama?''ta fada tana budewa
botikin farko alkaki ne a ciki
na biyu dubulan
na uku nakiya ce
ta dago ta dubi maman
''duka na meye wannan?''
''saboda 'yan kawo kudin nsn nasa akayi,kinga za'a kuma fita kunya ko''qauna da tausayin mamanta ya sake shigarta,Allah sarki mama,farincikin dake zuciyarta Allah kadai ne ya sani,a haka ma tana alkunya tana danne farincikin nata sabida kara irin ta dan fari
''Allah ya saka da alkhairi mama sunyi,Allah ta qara arziqi,amma mama banason ki dinga tatse kudin hannunki haka,yanzu wannan kayan ai sunci kudi da yawa''
''ai aikina ne maryamu,idan da da akwai cikakkiyar wadata ma baki cancanci ki kiyi komai ba''
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
qarfe biyu da rqbi suna falon raliyan su biyu sai fadil dake kwance kujerar geansu yana baccinshi hankali kwance,cikin farinciki raliyan take tamkar ma itace maryam din
''wani hanin ga Allah baiwa ne maryam,yau gashi Allah ya musanya miki da jabir,sun sanya bawan Allah a tsaka mai wuya har yau yana cikin damuwa,shekaran jiya yazo gidan nan yake tambayar abban fadil ke,yana son ya nemeki amma wai kunyarki yake ji,shegiyar yarinya marasa tsoron Allah itavda uwarta,duk jabir ya fita hayyacinshi kmar bashi ba,roqon Allah ne masa ya dawo cikin tuna ninshi cikin lokaci qanqani haka''
ajiyar zuciya ta saki
''duk wanda ya debo da zafi ai bakinsa raliya,nikam wanna ya riga ya wuce tamkar wani mafarki na daukeshi''
ta zura hannunta cikin jaka ta soma laluben wayarta dake ringing hade vibration ta cirota,kiran abdur rahim ne tasan shi dinne tun kafin ta ciro saboda special tune da ta sa masa
''ranki ya dade duka yau ban jiki ba ko cigiya ta baki yi anya kuwa''ya fada cikin salin zolaya bayan sun gama gaisawa
murmushi ta saki
''yau na tashi ne cikin sabgogi amin afuwa''
''ayyah,da kinyi magana ai da nazo na tayaki,ina fata basu wahalmin da ke ba''
''alhmdlh tunda tuni na kammala yanzun nake shirin in koma gida''
sai ya danyi duf kana yace
''me yasa baki tambayeni ba da zaki fita,saiki dinga fita kanki tsaye maryam ana ganemin ke''
murmushi ta saki
''mantuwa nayi ashe fa yanzun ina da miji,baza'a sake ba''
''matsalar ban iya fushi dake maryam,yanzun dai sgikenan kimin kwatancen gidan da kike zanzo yanzun nan na maidake gida,naga hadari na haduwa kada ruwa ya dakarmin ke ya barni da zazzabi''
ba qaramin nishadi maganar ta saka ta ba ,take ta masa kwatancen inda take din sukayi sallama ta ajjiye wayar
suka hada ido da raliya tare suka saki murmushi
''gaskiya na fuskanci ba qaramin ji dake abdul din nan yake yi ba,Allah ka nuna mana wannan rana''
dariya tayi gami da dukan gefan cinyar raliyan tace
''har ya kama qafar nasir abban fadil''suka sake sa wata dariyar raliyan na fadin haba wane mutum
minti goma wayar ta sake kadawa,abdur rahim tayi tsammani shi dinne kuwa
''kiyi min afuwa maryam zuwa na bazai samu ba wani aiki ne na gaggawa yanzu aka turamu dole kuma na kasance aciki idan ba haka ba akwai matsala,amma kiyi sauri don Allah ki koma gida hadari ne sosai a garin kada ruwa ya tabaki''
macace mai sauqin kai da fahimta don haka tace masa
''babu damuwa Allah ya bada sa'a''
ya saki ajiyar zuciya
''na gode da kika fahimceni sai munyi waya''
ta dubi raliya bayan ta miqe tana hada jakarta,ta tavbata hadarin ne don tuni garin ya lumshe har ta soma jin quginsa
''wucewa zanyi raliya an samu matsala abdul bazai samu zuwa ba aikin gaggawa nebya taso muau yanzu a office''
''a'ah,yanzu da uban hadarin nan zaki tafi?ki jira abban fadil ya dawo sai ya kaiki''kama baki tayi bayan ta gama rolling mayafinta
''girkin kuma na barwa wa?,so kike kenan yau abdallah ya samu nayi ko,cikin watan nan ya tairi wani abu ko kunu ne idan bani nayiba sai ya gane,yanzun sai yace a salary dina''
ta dage girarta sama
''haka ne fa,muje in taka miki,amma jirani in shiga in fito''cewar raliyan tana shigewa bedroom dinta na qasa
kwalbar turare ta fito da shi hade da baqar leda qarama ta miqa mata
''turaren da kike ce min kina son irinsa nasa abbn fadil ya aiyo manaamma kiriqe da kyau saboda yana leeking,sai bra din nan qualitative one da mukayi maganarta jiua da muka fita na siyo mana''
''kai qawata,bani da bakin magana,Allah ya raya mana fadil ya bar mana zumuncinmu,ya tsone idon maqiya''
''ameen raliyan ta fada tana bin bayanta,haduwar jadarin ya sake rudata har ta kasa saka kayan cikin jaka,a bakin get suka rabu ta soma sauri gashi ita ba gwanar saurin bace
har ta kai bakin titin su raliyan bata ga abun hawa na haya ba,kusan dama haka yanayin unguwar tasu yake ko jama'a baka fiya gani ba,bare yanzu yanayi na azumi kowa yayi likimo cikin gida,hankalinta bai daga ba sai data tsaya atitin,taga motoci dake karakaina ma baifi ka irga au ba,adaidaita uku ne suka wuce biyu daga cikinsu duk cike take da mata dayarkuma maza ne cike har gaba kusa da mai tuqin,a hankali iska ta soma kadawa mai qura alamun dake nuna hadarin ya gama nuna a sama sauka kawai yake da buqatar yi,addu'a kawai takeyi cikin zuciyarta a haka ruwan saman ya soma sauka
tsamo tsamo tayi don ya fara jiqata ta soma hade jikinta guri daya,motoci uku ne qirar land cruisser baqaqe wul hatta da glass dinsu suka tsaya a gabanta,gabanta yayi mummunan faduwa,tuni ta somacwaige waigen neman inda zata fake idan gudun ceton rai ya kama
glasan motar farko nagaba mazaunin mai tuqi suka sauka qasa,hassan ta gani daya daga cikin direbobin abdallah,sai a likacin taji ta samu nutsuwa,murmush yayi nata itama ta maida masa
''madam yi sauri ki shigo kina ta jiqewa''
taji dadi sosai kuwa,da saurinta ta qaraso ta bude mazaunin gaba ta shiga tana fadin
''na gode qwarai,amma ba tare kuke da og.....''
''me muka tsaya yine hassan?''
muryar data fito daga sit din baya ta katsse mata sauran magan
''nun dauko madam ne''ya fadi yana qoqarin tayar da motar
''waya baka izini ko tsabar iya sayawa mutum raini ne?''
''sorry sir,naga gida zamu ne,kuma itama gidan zata.....''
''ni na gaya maka haka?''ya tambaya murya a kaurare
''am sorry sir naga madam nada kirk.......''
abdallah ya katseshi ta hanyar fadin
''mtswee,shutup malam sauka ka barmin mota ka koma motarsu auwal''
da saur maryam ta kuma riqe jakarta wadda garin saurin ledar hannun ta har ta subuce ta fadi qasan motar bata sani ba
''kayi haquri,ni ya kamata na fita ba hassan b.....''
''hey,bana son iyayi shi nace ya fita din bake ba''
tuni hassan ya bude motar ya fice ganin hakan ya sanya itama ude na bangarenta tana qoqarin fita
''idan kija sake kika fita sai na karya sillar qafar taki inga ta rashin kunya''
tilas tana ji tana gani ta koma ta zauna
''rufemin mota malama don idan ruwa ya jiqata sai kin busar da ita tas a yanzu yanzu''taja qofar garam ta rufe cikin haushi,tana iya gano ragowar motocin suka zagayesu suka wuce
mujallar da yake research kanta tun dazun ya sake janyowa ya bude yaci gabavda karuntunshi hankalinshi kwance tamkar yana cikin dakinshi ne,sanyin a c din motar ya soma takurata gashi tayi mata kusa da yawa,tuni kanta ya fara sarawa ta qudunduna gu guda tarw da jingina jikin makarin motar ta lumshe idanunta tana ci gaba da jin yadda ciwon kan ke dada yin gaba
'yar qaramar qara taji tamkar ta waya ''siiit''a hankali sai dumi ya maye gurbin sanyin ac din,bata tantama maidashi akayi banaren dake bada dumi,duk da taji dadin hakan amma babu abinda ya rage mata daga ciwon kanta
mintina kusan arba'in basu tafi ba kamar yadda ruwan bai tsagaita ba,ta bude idanunta a hankali ta miqe ta zauna daidai,a karo na biyu ta kuma sanya hannunta kan mabudin qofar don ta qudiri aniyar ficewarta zatayi kome zaiyi mata saidai yayi,saidai taqi buduwa da alamu an saka lock,ya ajjiye mujallar hanun nashi ya jawo baqin space ya mannawa idanunshi sannan ya bude 'yar qaramar kyakkyawar baqar lemar dake kusa dasji ya fito ya dawo mazaunin driver
amadadin ysyi hanyar gida sai taga sun csnza titi,batason kulashi amma ya zama mata dole
''ina cewa gida zammu ko''
banza yayi da ita,ta qufula amma bata fasa sake fadin
''girki fa na can na jira na gashi yanzu hudu harda rabi''
''karki cika ni da hayaniya,baki da zance sai na girki kamar dinshi aka halicceki,ai bake daya kika iya girku cikin gian ba ko''
ya fada udanunshi na bisa kwalta,bata sake tofawa ba ta maida kanta gefe daya
cikin wata unguwar taga sun shiga wadda take kama da tasu mamun wajen kyau da tsari,qofar wani katafaren gida taga ya tsaya,ita kanta sai da ta bi gidan da kallo,duk kyau na gidansu mamin wanna ya dokeshi,bude motar yayi yay ficewarsa ba tare da da yace mata komai ba
zaman kusan awa guda da rabi tayi kafin ta sake ganin fitowarsa,a dan bakin qofar ya tsaya kafin ya qaraso tana iya hango jikin wanda suke magana tare,da alama macece don ga gefan mayafi nan,ba qaramar qufula tayi,ba cikin zuciyarta
''zance yazo kenan ya barni a mota ko yaya?''ranta sai ta kuma ji ya baci,ya bude motar ya shigo
''zance da ranar Allah cikin watan azimi,wanne wane irin tsari ne''ta ja tsaki,saidai cikin subutar baki tsakin ya fito
juyowa yayi kalleta
''wa kike ma tsaki?''sai ta juyo tana kallonshi itama
''idan kika sakemin tsaki sai kin fita min a mota tunda bada kudinki aka siya ba''sai idanunta suka wal
''daina kallona''ya fada bayan ya dauke kanshi da sauri daga cikin idanunta
''kada ki cuceni''ya fadi can qasa yana lumshe idanu tarw da yiwa motar key,bata kawo komai cikin ran ta ba ta dauke idonta cike da jin haushinsa
🎄🌲🎄🌲🎄🌲
Ashirin ga azumi mami ta bata kayan sallarta,a dinke suke dinki ne na gayu wadanda suka mata cif a jiki,atamfofi uku lace daya material daya,sai codelace shima daya,duka atamfofin dogayeb riguna aka mata don mamin ta fuskanci tana sonsu,jaka biyu takalmi biyu sai mayafi biyu hijabi daya,sannan tace ashirin da biyar ga azumi zasu fita sai ta zabi fashion da zatayi amfani da su,bata fasa yiwa mami gidiya ba duk da ta gaya mata diyarta ta yiwa no need tace sai ta gode mata,godiya kuwa ai tamkat wajibi ne tayi mata don ko daga gurin mahaifinta bata taba samun makamancin irin wannan gatan ba
abida kam akwati guda medium abdallan ya hada mata bayan takurawar da mami tayi masa kan ya hada matan,don shi totally baiyi niyyar mata komai ba
cikin irin kyautar da mamin ke yawan yi mata ta fidda atamfa biyu ta baiwa tela ya dinkawa mamanta,ta siya mata mayafi takalmi da jaka,albashinta na watan ciki ta cira ta baiwa hibdatu tayi siyayyar salkarta babanra ma shadda ta siya masa kala biyu ta hada mishi da kudin dinki da takalmi da hula daidai,kai kada ksso kaga baqinciki,ina wuta a saka maman da iyalsnta,godiya kam gun baban ba'a magana
''sai yanzu nasan na haifa,yanzu ne na fara cin albarkar haihuwa''baban ya fada lokacin da yake gwada hular da ta kawo masan
''oho dai,wlh malsm ka guji ranar da zaka karbi shegen jika cikin gidan nan,ka gama cin dadin dai wuyar na tafe,shi yasa gata nan har yau babu mashinshini yo kowa yasan aikin tsiyar da take aikatawa''
inji baba hadizar don daga ita har huwailsn babu wanda yasan da zancan kawo kudinta,ranar kamar Allah ya kadasu duk suka fice unguwa suda qananun 'ya'yansu,huwaila tayi gurin boksn boginta ita da uwale hadiza ma ta bazama ga nata bokan,sunacan yawon asara har yan kawowar suka tafi,'yammatan da zawarawan kuma na nade a gado suna bacci don wadan nan sukan kai sha biyu da rabi zuwa daya basu tashi ba
huwaila kuwa cewa tayi''mu namu ai shegensu mukayi muka shigo dasu gidan ko,ko ince tsinannu ne''shidai babu wadda ya kula cikinsu ya kwashe kayanshi ya shige dakinsa
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Qarfe goma suka dawo daga siyan kayan kwalliya da suka fita harda mami da abida,tayi sallama da mamin ta shige dakinta don da wuri take son yin bacci ta tashi akan lokaci sallar dare saboda yau an kai azimi ashirin da shida zuwa anjima daren ashirin da bakwai zai shi daren da akesa ran dacewa acikinsa
zuwa sha daya na dare takammala komai ta haye gado bayan ta gama addu'o'in kwanciya ta karanta saqon abdur rahim fuskarta fal da murmushi,kusan cikin watn gaba daya wayarsu bata fi aqirga ba sai tex akai akai,yace shikam bazai iya jurar jin muryarta ba,tana shirin kashe wayar kira ya shigo,ta zubawa lambobin ido tana kallonsu,tana tunanin inda ta taba saninsu
tabbas ta taba sanin numbers din,har wayar ta tsinke ta kasa dagawa,second biyar tsakani wani kiran ya kuma shigowa,jiki babu qwari ta sanya hannunta ta daga ta kara akunnenta
''assalamu alaikum wa rahmatullah''itace abinda yavdaki sodon kunnenta,mummunar faduwa gabanta yayi,babu inda zata ji muryar ta kasa ganeta,amma tan tama take kiran nata ne ko batan kaine,ta sake cire wayar akunnen ta tayi ta kuma duba screen din wayar mai kiran dai na bisa layi kuma ita din aka kirar
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣4⃣
*_daga abu hurairah Allah ya qara yarda da shi yace:an tambayi manzan Allah s a w wanne musulmi ne yafi falala?,sai yace:wanda musulmi suka kubuta daga sharrin harshensa da sharrin hannunshi(ma'ana bai cutar da kowa da harshensa ta hanyar magana,ko kuma da hannunshi ta hanyar ayyukansa,daure ka/ki zama daga cikin musulmin da suka fi falala,abun ba wuya 👌🏽matuqar ka jajirce kafi qarfin zuciyarka,Allah ta bamu iko ameen)_*
''wa alaikumus salam''ta fada asanyaye
shiru ya dan ratsa tsakani kadan
''da alamu baki ji dadin jina da kika yi ba ko maryamu?,hala ma kin manta da ni?''
''ko daya,ban kuma mance da kai ba''
''da fari kafin nace momai maryam,nasan bani da kalmomin da zasu gamsar da ke gurin ban haquri,amma duk da haka ina roqarki don Allah don annabi ki yafemin,ba da gangan abinda ya faru tsakaninmu ya faru ba,bada sani na bane maryam,ki yafewa jabir masoyinki''
tausayinshi ya kamata ta dan kumshe idonta kadan ta bude
''kada ka bata bakinka gurin bani haquri jabir,tuntuni gaskiya ta dade da yin halinta,anyi walqiya komai ya bayyana''
yaja dogin numfashi kana ya sauke ajiyar zuciya
''alhamdulillahi rabbil aalamin,dukkan godiya ta tabbata ga Allah,babu shakka ke din jaruma kuma nagartacciyar masoyiya ce,bana tantama zaki zama mace ta gari uwa ta gari gurin 'ya'yanta,bazanyi nauyin baki ba ba kuma zanyi qauro ba maryam inason ki bani damar fitowa neman aurenki karo na biyu,tare da cikakken fatsn babu wani da ya sha gabana''
sai da gabanta ya fadi,tayi shiru tana son daidaita bugun zuciyarta sannan daga bisani tace
''qaddara ta riga fata jabir,Allah ya qaddara run da dama ni ba matarka bace,hakaza matar mutum kabarinsa,bai wuce sati biyu da kawo kudin aure na da wani ba''
''la haula wala quwwata illah billah''ita ya dinga maimaitawa tsawon mintina biyar
''yanzu kina nufi maryam na rasa ki kenan,zaki auri wani na?,ki bani dama maryam mai rabo shi zaya samu tunda har yanzu ba'a daura aurenku ba balle kice kin haramta a waje na''
''kai mai sani ne jabir bakin gwargwado,ka sani cewa nema akan nema haramunne,baya ga haka ma daga ni har kai babu wanda aka bawa qudirar rubuta kundin qaddararsa da kansa,kuma buwayin sarkin dake rubuta msna din mai dumbin adalci ne,babu yadda za'ayi ya rubuta mana abinda zai zama zalunci ne a garemu''
''haka ne maryam,alhndlh Ala kulli hal,na gode maryam,na gode matuqa da gaske,bazan taba iya mantawa dake cikin kundin rayuwata ba,na barki lafiya''
tafi minti biyar riqe da wayar ra kasa ajjiyeta,tausayin jabir dinne kadai ke dawainiya da ita,babu shakka bazata iya manta dumbin alkhairansa gareta ba,koda ta tashi sallar dare bata mantashi cikin addu'o'inta ba,ta roqa masa alkhairi mai yawa kamar yadda a baya yayi nufinta da shi
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Washegari mai lalle tazo yi musu,babu yadda mami batayi da abida ba amma qememe taqiya,tabe baki tayi
''nifa mami ba za'a batan hannu ba hakakawai da wannan abun''
''banda abinki ai shi jan lalle ga mace sunna ce baya ga haka ma ado ne''inji mami
ta sake ya mutsa fuska
''um um,a muku dai,mukam a turkey bamu irin wannan abun''ba wanda ya kuma tanka mata cikinsu nanta kwanta tun tana kallin qunshin har bacci yayi awon gaba da ita
kamar ko yaushe suna table don cin abincin buda baki u ukun maryam mami da abdallah,ta zubawa mami da abida ta soma zuba na abdallah,ya dago da sauri don yaga iya wanda zata zuba din don vaiso ta cika masa plate kamar na jiya,idanunshi suka sauka kan zara zaran fararen yatsunta da qunshin yayi kwanciyarshi kai ya sake fidda kyawun hannunta,farar fatarta ta sake shar
Zanen ya burgeshi duk da ya saba gani lokaci lokaci gun maminshi,duk kuwa sanda tayi din tun yana yaro ya dinga cewa tayi kyau kenan,maryam ta janye hannunta bayan ta ajjiye nasa plate din ta koma mazauninta,sam babu wanda ta lura sai abida,kishi ya cikata har taji kamar ta guntike hannun maryam din,ya janye idanunshi daga kan lalken suka hada udanu da abidan
''ke ina naki kwalliyar?''
''abida kam ai ta manta gargajiyar al'adarta,tace bataso bata mata hannu za'ayi,bayan shi kanshi ma ganine''
caraf abidan tace
''naga kamar ya burgeka ko,ba damuwa sai amun gobe''
tabe baki yayi ta daga kafadarshi hade da ware ya tsunshi
''no,idan ta nine kada ki sauya ra'ayinki ki bata hannunki''ya qarashe zancan yana jan plate dinshi ta soma cin abincin
zahariyya ce tayi sallama hannunta duka biyun dauke da foodflask masu azabar kyau da tsada,fuskarta a washe da faea'ar data qiqirarwa kanta ta qaraso gun,ta fara da dora flask din duka saman teburin wadanda tunda aka shigo dasu maryam take jin matsananciyar faduwar gaba ta kuma kasa daina kallonsu,mami ta gaida kana abdallah,tsakanin ita da abida kuwa babu wanda ya kula wani kowa na ji da danbanzan girman kanshi rawanin tsiya
''favourite food na ya abdallah nene ra tashemu sai da mukayi masa wai yadda ta saba sanda alhj baaba(alh abdulkareem mai nasara kenan mahaifin abdallah)yana raye wai yanzun ma ba zata fasa ba''
murmushi mami tayi tana janyosu gabanta tare da fadin
''kai kice mata kam mun gode qwarai,kamar kuwa tasan yau bamuyi girki ba nace maryan ta bari sai sahur aikin yayi yawa''inji mami sanda take hude flask din,rake kuwa qamshi ya cika gurin
''ki mata godiya''inji mami sanda zahariyyan ke nufin fita
''zata ji kam''ta amsa mata lokacin da take qoqarin sanya qwayar idanunta cikin ta maryam a fakaice,cikin sa'a kuwa suka hada idon,wanu mummuna kallo mai cike da gargadi da jan kunne tayi mata kana ta fice
Gaba daya ta saki cin abincin ta zurfafa cikin tunanin yadda zata salwantar da abincin ba tare da tabar kowa ya dandana ba,tayi imani komai zasu mata ba zata iya bari tana gani gaban idonta wannan ahli su salwanta ba,qarshen butulcin da zata musu kenan wanda ba zata iya yafewa kanta ba har abada,cikin haka taga mami na kiciniyar bude food flask din zata zuba,da sauri ta miqe tana fadin
''mami barshi in zuba miki mana ''tuni har ta isa gabanta ta karba don kada ta yanke mata hanzari tace ta barshi,ta jawo flask din miyar gaban table din sosai ya zama rabi kan tebur din yake zaune rabi kuma free ba matokari,sai ta jawo na abinci ta bude,da plate a gabanta amma sau tayi dabarar miqa hannunta tavdauko na can sashen da abida ke zaune
Tana daukar plate din ta sakeshi kan flask din miyar take nautin tangaran din ya rinjayeshi sukayi qasan table din suka tarwatse kan tiles,tangaran din ya koma piece,taja baya da sauri tana salati tate da kallon gun da abincin suka kife
''subhanallahi ya haka maryam?''
''for god sake mami yanzu wannan wane irin kidahumanci,ita din qaraman yarinyace da zata kifar da abinci flask biyu,kayi magana kuma yanzun mami ta ji haushinka ta saka a black list''ya qarashe maganar cikin bacin rai yana yayyarfa hannu da jujjuyawa hagu da dama kan kujerar da yake zaune
harara ta balla masa sannan ta kalli maryam
''ina fata baki ji ciwo ba maryamu''
kai ta gyada zuciyanta na wani irin gudu gefe daya kuma tana hamdala ga madaukakin sarki da ya bata nasara a sauqaqe ta rabasu da abinda zaya hallakasu,ita ta tsaya ta gyara gurin duk da momi tace ta bari sai ta huta tukyn amma sam ta qiya,bazata iya ba don ko quda bata fata ya dandana abincin,balle ma ta tabbata ban da awa biyu ko uku indai da gubar abincin zai fara ratattakewa
ta gyara gurin tsaf ta kwashe bayan ta rage kadan ta samu yar roba ta zuba hade da miyarshi ta shige da shi dakin gadonta ta tura ahi qasan gado,sai da ta gama komai kafin ta kwanta ta jawo robar don dubawa,cikin awa uku abincin ya fita kamanninsa kamar wancan,batasan lokacin da hawaye suka soma zuba daga idonta ba
mutum abun tsoro Allah abun tsoro
yanzu dan uwanka bil'adama kake da buri yaci wannan abun?
waishin wanne rin laifi ne abdallqh ya yiwa mutanen nan ne haka da zafi da suke da burin rabashi da soron duniya?
sai kace mudin an mana wahayin tabbata acikinta?
kwana nawa ne kaima ka hada ya naka ya naka ka qara gaba?
koda shekara miliyan zakayi wataran dai sai sun qare din ka tafi.
itakam ko kadan batq ga abun morewa ba wajen cutar da wani bayan ka san cewa Allah bazai taba qyaleka ba sai yabi kadi,duk wanda yaci nanin nanin dole ta cishi
cike da kasala da mutuwar jiki ta shige toilet dinta tayi plushing din duka abincin ta wanke robar ta wullar a dust bin
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Sallah bikin daya rana,cike da walwala farinciki bikin sallah ya soma gudana cikin duniyar musulmi baki dayanta,sai a lomacin mayama ta dinga ganin dangin su mami da na mahaifin Abdallah,don kusan kullum ne sai sunyi baqi,saboda haka bata samun zama aosai,damuwarta daya ma kada abdur rahim yace zaya zo ya samu bata da lokaci sai gashi bai ma nemi zuwanba iyakaci waya sai saqon,barka da sallah daya turo mata na credit din dubu goma yace kuma ta jirayi kayan salarta duk ranar da zaya zo
Ta fuskanci ba kadan bane maso sun abdallah cikin danginsa daga na mamin har na abbaanshi,kishi ke hana abida zama ciin gidan tayi ficewarta yawo sai dare
''rashin sani yafi dare duhu''maryam kan fadi hakan cikin zuciyarta ko kuma tace
''bonono rufin qofa da barawo''a duk sanda taga abida na wannna haukar kishin nata don bata da masaniyar kai kudi abdallah daga ita har zubaidan bare salma da saddiqa da bama ganinsu ake ba,har ga Allah tausayinta takeji kan fadawa son botsatstsen mutum irin abdallah,wanda koda yana sonki zaki sha wuya da shi bare kuma baiyi da ke a ganinta
hudu ga salla suka fara samun sararawar baqin duk da ana cikin dai hidimar sallah da shagulgulanta
da la'asar ne babu dadewa da gama salla wayarta ta fara ringing,tana kan cinyarta din haka ba jinkiri ta daga,muryar jabir ta tsinta yana mata sallama,ta amsa masa kana suka gaisa amutunce
''mai yayi zafi haka ido zaici wuta maryam,a qalla dai ai ko barka da salla a kirani ayimin''
ta dan saki murmushi
''kayi haquri,na ahiga sabgogi ne da yawa,ayyuka sun kacame min kusan yaune ma kadai na dan samu kaina''
''gaskiya ne,ai manya dama sai da uziri''dariyar zolayan da yayi mata tayi,kafin tace komai ya dora da fadin
''ko zan iya ganinki,maryam?''tavdan fiddo ido waje kamar yana ganinta
''yanzu?''
''eh idan da zan samu yau din da nace miki na gode,amma da zakimin alfarma da sai mace miki mu hadu gobe''
tunaninta daya ina zata ce mishi su hadun?,sam bata da sha'awar kawoshi nan gidan kamar yadda ko kusa ba zata yarda su hadu gidansu ba
ajiyar zuciya ta saki
''babu damuwa,muna iya haduwa gobe kamar hudu na yamma a gidan zoo ko?''
''kin ko san a itin kwanakin nan cika yake,anya zamuyi magana anutse kuwa?''
''eh nafison gurin jama'a din ai,kuma akwai bangaren da zamu iya zama da babu cikowar''
''shikenan babu damuwa na gode,amma baki tambayeni,mai yasa nake da buqatar mu hadun ba''
murmushin ta kuma yi
''a tun sani na da kai da alkhairi,na sanka,don haka yanzu bazan canza in maka zaton sharri ba,kaga kenan ina tsammatar jin alkhairi ne daga bakinka''sosai yaji dadin irin shaidar da tayi masa,har yau bai fasa yaba kyawawan halayen maryamu ba,kowa tana masa kallon mutumin krki ne kamarta,hakanan tana kowa kallin mai kyakkyawar zuciya kamar yadda ita din take
🎄🌲🎄🌲🎄🌲
Qarfe hudu suka fita daga gidan zuwa gidan zoo din ita da hindatu,dukkaninsu cikin kwalliyar atamfa suke riga da skert,sunyi kyau kam masha Allah
a can suka taddashi har yana zolayarsu sai yaci tararsu sun mishi african time,yayi kyau abinshi cikin dinkin kufta ya dswo jabir dinshi na ainihi,kyakkyawan matashin saurayin nan mai yawan ado da fara'a jabiru
gurine kebantacce dake can cikin ainihin gidan ajiyar namun dajin na garin kano,tamkar lambune ska yishi na musamman kudin shigarshi ma daban yske kusan ba kowa ne ma yasan da gurin ba,kujera ce irin ta siminti suka zauna a dayan shima ya zauna a dayan,sabuwar gaisuwa suka sake,maryam ta dubi jindatu tace dan bamu guri kadan to tace kana ta miqe,jabir din yace
''ai da kin qyaleta ma don maganan ya shafeta''ta yi gaba amma ta jiyo abinda yace din sai gabanta ya fadi hakanan
''maryam,haqiqanin gaskiya na yaba da kyakkyawar tarbiyyar da kuka samu,sannan nayi baqinciki qwarai da gaske da rasa ki da nayi duk da nasan cewa komai qaddara ce daga ubangiji,saidai ina kwadayin hada iri da ku maryam,ina neman wata alfarma guda daya,Allah yasa wannan karon bazanyi failing ba''
cikin tattara dukkan hankalinta a kanshi tace
''babu wata alfarma da bazan iya maka ba indai ina da iko kima bata keta haddin shari'a''
''be keta ba maryam''ya fada yana murmushi wanda ya qara masa kyau da kamala
''so nake ku bani hindatu''
idanu ta zazzaro tamkar taga wani abun tsoro idanunta kan jabir din
''jabir........shin ka manta alaqar dake tsakanin hindtu da jamila ne?,ya da qanwa ne fa?''
''koda na taba sanin jamila a matsayin diya mace hindatu bata haramta gareni ba tunda igiyar saki ta raba tsakaninmu balle babu abinda ya taba shiga tsakanina da ita na auratayya,yadda aka kaimin ita haka na dawo musu da ita,so kika babu maganar janamin auren hindatu kenan''
kai ta girgiza''haba jabir,yau ko maqota muke mu da su jamila ai duniya ta zagemu balle iba daya''
''ya kamata kiyi amfani da ilimin da Allah ya huwace miki,ki dinga saka addininki gaba da al'adarki,babu wani abu da ya jaramta min auren hindatu koda kuwa ke na aura matuqar mun riga da mun rabu''
cikin girgiza kai tace
''haba jabir,amma dai ai ana barin halas don kunya''
take yanayin fuskarsa ta sauya
''gwara maryamu ki fito kanki tsaye kice min ba kyason tarayyata da hindatu,gwara ki cemin jabir ba zamu baka hindatu na tafi qarfinka
wace iriyar kunya kike magan akanta ne maryam?
su waye kima wadan da za'aji kunyar?
ko kin manta jin kunyar mara kunya asara ce?
har kin manta da abunda suka miki ne,shin a lokacin da suka aikata din ba'a halicci kunya ba ne ko kiwa akwaita sune basu da ita?''ya qarashe maganar cikin bacin rai,ta bude bakinta zata yi magana ya dakatar da ita da hannunshi kana yace
''dakata maryam,bana buqatar kice komai,tun yanzun na cireki daga batun nan,ban neman kimin komai,zan yiwa kaina yaqin samun hindatu,naki kawai ido addu'a da fatan alkhairi''bai bata damar cewa komai ba ya tashi ya nar gin yabi hanyar da hindati tayi
kimanin minti talatin ta gaza tashi a gun,wani bangaren na zuciyarka na gaya mata bata kgautawa jabir ba,mai son naka ai ya gama maka komai,yayin da wani,bangaren kuma ke ganin dai dai tayi,don rigima ce zata riri ba qarama ba cikin gidan,daya barin uace mata,to sai me?,da ba naki bane jabir din suka aikata abinda suka aikata suka maidashi nasu?to ai dama idan mai guri yazo mai tabarma nade kayarshi yake
shiru shiru hindatun ma bata dawo ba,ta ciro wayarta tayi kiranta,abun mamaki sai taji jabir ne ya daga,kafin tace wani abu ya rigata
''kada ki cikata da fada gamu nan zuwa''hangame baki tayi tana kallon wayar,bata qarasa daskarewa ba sai da ta jangosu sun jero suna tafe suna qyalqyala dariya hannun jabir din riqe da fararen ledoji masu dauke da tambarin sahad store
duban hindatun tayi saivtaga yarinyar ta waske mata tamkar babu wani abu da tayi,kabir me ya katse kallon da take mata ta hanyar ajjiye mata leda daya kusa da ita
''kada ki cinye min gimbiyata ki barta hala,s
duka sauran tuhumarki ki hadiyeta na karbi tutar hindatu''
bata data cewa kallinsu kawai take,haqiqa ta san cewa indai hindatu tayo,nasarar auren jabir bata da sauran matsalar rayuwa,miji na gari kam ta gama samunshi,suka qaraci mata shaqiyancinsu suka miqe don tafiya,nan ma ya kasa ya tsare kan shi zai kaisu,hindatu ta takura tolas suka bishin ya ajjiyau har qofar gida
suna shiga soron gidan maryam tayi saurin janyo hindatu da har tayi gaba
''hindatu ashe baki da tunani?''
ta zumburo baki
''me kuma nayi adda?''
''kin manta waye jabir tsohon mijin yayarki jamila?''
sai ta kwashe da dariya har maryam na toshe mata baki kada ta dauko hankalin mutanen gidan
''nice ta biyu wajen sanin waye jabir bayan ke ta farko,to wai ma anty don autukina yaje aikin hajji sai in kasa zuwa in sauke farali nima saboda kunya?,jabir yayi min adda don na tabbatar yana da nagarta tunda har kika amince da shi a baya''
sai ta kuma yin qasa da murya
''baya ga haka adda wannan wata qatotuwar dama ce garemu ta rama duka cin kashin da aka mana,wallahi sai na dauki fansar duk baqincikin da suka cusa mana''
ta fuskanci da gaske hindatun take
''Allah ya taimaka''ta fada kana ta shigeta cikin zuciyarta tana musu addu'ar tabbatar lamarin cikin nasara da farinciki
🎄🌲🎄🌲🎄
Batasan ya akayi ba itadai taji an kawo kudin hindatun har da kudin sa rana jimillar naira dubu dubu dari uku dubu dari kudin aure dubu dari biyu kuma kudin sa rana,hakan ya sanya baba yace ta shaidawa abdur rahim ya turo a saka rana,su din ma kudin sa ranar suka bada naira dubu dari biyar,kudin sun bawa maryam din mamaki,murmushi abdur rahim din yayo yace
''ko nawa na bada kudin aurenki yayi kadan maryam,kinfi qarfin haka,me din mai tsada ce''murmishi kawai tayi tana sake ganin qima da darajar son da yake mata
duk abin nan da ake jama'ar gidan basu da masaniya,kusan duk ranar da za'azo din basu gidan suna yawon asara yawon bidar asiri,asara goma da ashirin babu kudinsu ba imani
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣5⃣
👇🏾 *wannan page naku ne*
👉🏾 *_haske writers asso_*
👉🏾 *huguma conversation and novels rooms_*
👇🏾 *da kuma*
👉🏾 *Zauren biebie isah*
*Allah ya bar qauna*👍🏽❤🤘🏽
*_Ankarbo daga imam bukhari r.a,manzan Allah s.a.w yace_*
*_(qarami ya yiwa babba sallama,matafiyi ya yiwa wanda ya taras,jama'a 'yan kadan su za suyi yawa masu yawa)_*
*_a wani hadisin da imamu muslim ya rawaito daga annabin rahama s a w yace(wanda a zuciyarshi akwai girman kai daidai da qwayar zarra bazai shiga aljanna ba)_*
*Allah kayi mana tsari kada ka haramta mana aljannarka,ka hanamu dukkan wata baiwa ko ni'ima taka da zata yi sanadin zamowa masu girman kai*
Fadar irin farincikin da mama da iyalinta ke ciki ma bata baki ne,sunyi amanna cewa wannan ce shekarar farincikinsu,addu'o'in da suka dade suna qwanqwasawa qofa yau kam an bude musu dukkan qofofin,duk wani tsohuwar ajiya ta mama data jibanci kadara ta daga ta saida,ta yiwa bikin shiri matuqa da gaske,ga dangi masu zuciyar yi mata da Allah ya hadata da su
takanas suka ziyarci gaya ta saida manyan gonakinta na gado guda biyu,ba qaramin kudi ta samu da su ba kasancewar yadda a yanzu kowa ya koma noma gonakin daraja suke,tuni ta fidda kudin kayan gado kayan kitchen da sauran tarkace na hindatu,maryam kam dama da yan kudadenta da take sa ka ran zasu isheta sayan kayan gado,ga mamakinsu saiga kudade baban su ya damqa masu a boye yace sukaje su zabi kayan gadon da suke so,shi din ma gonakinsa biyu ya siyar dake gayan,dama bashi yake amfana da su ba yan uwansa ne,cikin rufin aairi, Allah sai gasu sun tashi da kayan gado na kere sa'a masu kyau tsada da aminci
bata sake shiga farinciki matsananci ba sai da mami ta damqa mata passport dauke da visa ta qasashe biyu saudiyya da china
''maryam,inason inje siyayyar lefen abdallah ne,sannan ke kanki ina son in miki siyayya irin wadda uwa take wa diyarta,naso 'ya mace amma Allah bai bani ba,to a yanzun kuma sai Allah ya bani ke,naso ace lokacin bikinki da abdallah bai hade ba da ina mai tabbatar miki anan gidan zaki zauna har akammala taro a miqa ki gidanki,saidai duk da haka bikin magaji ai bazai hana na magajiya ba,zamu fara zuwa china muyi siyayya sanan mu dawo saudiyya muyi umara,kuyi addu'a kowannanku ya roqawa kanshi alkhairi kan sabuwar rayuwar da zaya shiga,ni da ke ne da abdallah''
rasa bakin da zata gode mata tayi saidai ta tsinci kanta cikin zubda qwallar farinciki,tabbas uwa ce,mami uwa ce wadda tasan ciwo da darajar 'ya'ya,babu shakka ko ita ta tsugunna ta haifeta iyakacina binda zata mata kenan,haduwars ta tabbatar daga Allah yake,bata manta yadda taqi taji batason aikin gidan mamin ashe alkhairi ne Allah yake nufinta da shi,gaskiya ne maganar Allah haka take da yake cewa cikin alqur'a ninshi mai girma
(zaku iya qin abu kuma alkhairi ne agareku,sannan zaku iya son abu kuma sharri ne a gareku,Allah shine ya sani ku baku sani ba)
mama kam rasa mai zata fada tayi,babu shakka duk yadda kaga Allah yayi da rayuwarka baiyi don zalunci a gareka ba,yayi ne saboda shi ne mafi sani ga abinda ya dace ga bawansa
raliya har da hawayen farinciki
''damuwarki tazo qarshe diyana,Allah ya yanke miki,maqiya kuma sai su kashe kansu don baqinciki''abinda ta dinga fadi kenan fuskarta qunshe da murmushi
hindatu kam buri ya cika,don tace ko iya haka Allah ya barsu sun gode masa,Allah ya nuna isa da buwayarshi,itama tata visa din umarar na nan jabir ya tanadar mata bayan sun angwance da wata daya
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
qarfe biyu na azahar jirgin ethopian airline zai debe su zuwa ethopia inda anan zasu fara yada zango kafin su isa qasar sin,cikin masu rakiyar tasu harda jabir da hindatunshi,abdulrahim sai zubaida,raliya da yaronta fadil,
ranan ne abdulrahim suka fara haduwa da jabir,tuni ya dade da sanin waye jabir din da kuma matsayin da yake kai a yanzu a gun maryam din,don haka gaisuwar mutunci sukayi tamkar sun jima da sanin juna,kusan dukkansu sama sama suka gaisa da abdallah yaja gefe yana faman cin magani tamkar wanda aka yiwa dolen tafiyar,ita kuwa zubaidan bata damu da ta qyaleshi ba ganin yadda yake faman fuskewa ba tana liqe da shi tana zuba rawar kai yayin da shi kuma yayi mata dif ko kanzil yaqi tanka mata da ita cikin hirarta
cike da bege da qaunar juna suka yi sallama lokacin da aka soma neman matafiyan
maryam ce qarshe saboda tsayawan da sukayi da abdulrahim
''abun mamaki banga irin sallmar nan da masoua kanyi ba yayin rabuwa da juna abdulrahim meke faruwa?''
murmushi ya saki yace
''me kika gani maryam?,kina tuhumata ne kan rashin damuwa da tafiyar da zakigi ki barni?''
''dole in tuhumeka mana abdulrahim,ba sau daya ba basau biyu nasha kamaka da laifin qin sakin jikinka idan muna tare matuqar abdallah na agun,wai shin tsoronshi kake ne ko meye?,aure fa zamuyi nan da sati uku kowa yasan da zamanka,ko wata barazana yake maka aboue wadda mu bamu san da ita ba''
sai taga ya tuntsire da dariyar har yana dan duqawa
''babu tsoro balle barazana tsakanina da shi,ke kika dai fuskanci hakan,hasalima abinda kike zaton ba haka bane,Allah shine mafi sani ga abinda yake cikin zukatan bayinshi,Allah ya kaimun ke lpy ya dawo min da me lpy,ki kula min da kanki matuqa,ki yiwa kanki addu'a mai yawa maryam,kada ki kashe wayarki da wuri zan kiraki kafin ku tashi''sallamar da sukayi kenan
koda ta shiga gurin tayi tsammanin ya dade da wucewa tunda sun rigata shigowa da wajen minti goma sha biyar,sai gashi tana gaba gun screening shi kuma yana tsaye a bayanta,gaba daya sai ta takura,tana ji a jikinta tamkar yana qare mata kallo ne kawai,gashi doguwar riga ta saka sai rolling da tayi wanda iyakacinsa kafada,hill shoes ta saka wanda sanadiyyar hakan yasa ta kusa kama abdallan a tsawon
ko cikin jirgi ma number din sit din nasu daga shi sai ita,mami na a sit din bayansu,tamkar ta zura a guje ta bar sit din haka ta dinga ji,tunda take basu taba zaman kusanci na tsawon lokacin da zasuyi yanzu ba,ta njtsu tsaf tamkar ace ket!ta zura aguje
wayarta tayi tsuwwa ta duba saiga kiran abdur rahim,tamkar ance mata ta kalli gefanshi sai ta tsinci idanunshi a kanta,wani irin kallo yake mata da ta kasa fassara ma'anarsa,shi ba harara ba ba kuma normal kallo ba,ya kafeta da mayun idanunshi masu cike da kwarjini,sai ta tainci kanta da kasa dagawa har wayar ta tsinke,gani tayi ya ciro tashi wayar ya fara danne danne hakan ne yasa tayi saurin jan tata wayar ta soma dubutawa abdulrahim din saqon karta kwana kan bazata iya amsa waya ba a yanzun cikin yi masa sallama da bankwana,saida kamfanin layin sadarwa suka tabbatar mata da yake sanna ta sauke idanunta daga kan wayar,ta sauke siririyar ajiyar zuciya daidai kokacin da taji shi kuma anasan bangaren yaja tsaki qasa qasa ya furta
''fool''
dayar wayarshi data fara ringin taga ya janyo ya zura earpiece
''hello baby......muna jirgi yanzu zamu tashi.....ok...ok bye take care,i will missed you too''ya kashe wayar gaba daya ya ajjiyeta guri daya
''janye cat eyes dinkin nan daga kaina,yanzun zansa a canza miki gurin zama indai kika ci gaba kallona,bansin kallo kin gane?''
ji tayi kanar ta hukunta idon nata da har yayi kuskuren kallonshi
''me zan kalla wanda babu shi jikin abdul dina?''ta fada cikin dakiya kamar ma bada shi take ba,kanta na kallon wani sashin
''there ar many,ko skin dina kawai batayi kama data baqin mijinki ba mai zubin ta 'yan garuwa,after all ma kinsan da hakan kike qarewa mijin wata kallo,kinsan kina so tun farko bakiyi magana a taimakeki ko a qwarqwara kixo,yanzun kam its too late qwalelanki''
maganan ta mata baqi da yawa,tayi qoqarin control din bacin ranta don ta samu maida masa amsa yadda ya kamata
''shi dan garuwan ai Allah ne ya halicceshi......''
''eh mana,da ke kika halicceshi''ya katsi numfashinta ba tare data idar ba
da sauri ta dora don kada yaci da rabonta ba tare data samu ta rama ba
''ba kyau ko kudi nakeso ba mutunci nake bida da daraja,kai din kuma ai inama kallon mace ne 'yar uwata kaga babu yadda za'ayi ince inason jinsina,abdul dina yafimin kowanne namiji cikin jinsin maza,ko a mai min shara bazan iya daukarka ba da dai mai wankin toile......''
''qarya kike wlh ya fada cikin fushi da dan daga sautinshi,ita kanta ta dan tsorata don qasa qasa suke maganar lokaci daya ya daga muryarshi,idanunshi data kalla kawai suka sake sata a zulumi,sai a lokacin ta tuna waye fa,abdallah ne,ta runtse ido tana jin zafin matsar da ya yiwa yatsunta kamar zai karya su ya kuma qi saki
''meye ne abdallah''mami ta fada tana dan leqo da kanta
''babu komai''yace
''ko baka jin dadi ne?''
mami ta tambayeshi cikin yar damuwa jin sautin muryarshi ya canza lokaci guda
''am fyn''ya fada a taqaice
''ok,to ku kashe wayoyinku''tace mishi bayan ta koma ta zauna daidai ksn sit dinta
sai da ya fara hucewa da kanshi sannan ya sakar mata hannu,zuwa lokacin tuni ta fara share qwalla don azaba,jin hannun take kamar ba'a jikinta ba sanadiyyar taruwar jinin da taji ya mata,tuni har jirgin ya daidata a sama,da qyar ta janye hannun tana yarfar da shi tare da fatan jin ya sake daga daurewa da zugin da yaje mata,ko da aka tamvayesu abinda zasu ci cikin jirgin kasa ma mafa na tayi,tanaji yasa aka kawo baqin coffe aka ajjiye musu,itakam ko kallo ma bai isheta ba
a hankali suke sauka daga jirgin daya bayan daya,gaba daya qafafunta sun mata tsami ga hannunta na damunta,itace a gaba abdallah a bayanta mami a bayanshi,rashin qwarin jiki ya sanya qafarta hardewa ta tafi luu zara gangara daga matattakalar
a tsorace mami tace
''subhanallahi,abdallah tarota''
tuni ya tallafota ta dawo jikinsa
''kin zame mana kaya wallahi,dama so kike a rungumeki din an miki hankalinki ya kwanta,amma net tine kika qara sai nayi maganinki''ya fadi yana tureta daga jikinsa
''sannu'' mami ke ta mata har suka sauka,duk da yanayin rashin dadin jikinta baihanata ganin qawatuwar garin ba
gida ne mai hawa ashirin cikin unguwar,gini ne qawatacce mai kyawu matuqa da gaske,cikin hawa na takwas nasu gidan yake,gida ne mallakinsu abdallan da suka siya da kudinsu,da fari falone madaidaici sai corridor daga damanka wanda idan ka shiga zaka tadda kitchen wani corridor dinne yake kallan kitchen din shi kuma dakunan bacci ne guda uku kowanne dactoilet cikinsa,sai valcony 'yar qarana mai kyau daga fuskar kowanne hawa na gidan wanda ta nan kana iya gano ainihin cikin unguwar da layinku da kuke an qawatashi da kyawawan kujeru guda hudu da yan shuke shuke
daki daidai kowa ya dauka,tunda ta shiga dakin tayi wanka tayi akwala tayi sallah ta nade a gado sai bacci,tun la'asar dinsu sai da aka kusa idar da sallar magariba sannan mami ta tadata tayi sallah,tuni sunyi order din abinci an kawo musu har gida don haka shi kowa yaci,ba damar girki an dai siyo dan abinda zasu buqata kafin su gama kwanakinsu kamar ruwan roba qwai suger da sauran abinda zasu iya buqata,tana shirin basu guri don taji sun fara lissafe lissafen siyayyarsu mami ta tsaidata.
''maryam gaya min dame dame kike so,don gobe insha Allahu zamu fita bana son mu wuce kwana hudu,muje muyi kwana goma ko sha biyu a makka mu wuce gida lokaci na qurewa''
a kunyace tace
''bani da zabi mami,duk abinda kika zabarmin yayi''
bata ce mata komai ba ta miqa mata takarda da biro tace taje tayi mata list din duka abinda takeso nan da goma ko sha daya tazo ta kawo mata,hannu biyu tasa ta amsa ta koma daki
sai ta rasa ma me zata rubuta,bata da layin qasar balle ta kiraliya ko hindatu suyi shawara,wani tunani tayi ta koma falon,nan ta samesu yadda ta barsu,saidai wannna karo sunyi kace kace cikin takardu,rubutu kawai kowannansu ya duqufa yana yi
''hmmm,gaskiya ne,ai dole ayi bikin da babu kamarsa,da daya tilo''maryam tace cikin zuciyarta
''ya akayi maryama,har kin gama?''mami ta tambayeta bayan ta dago kanta ta maida kan rubutun da takeyi
''ummm...mami cewa nayi don Allah ko zaki aramin wayarki in dan kira gida?''
''ayya nima kuwa bani da layin qasar nan duk sanda muka zo sabo nake siya wancan faduwa yake,sai gobe idan Allah ya kaimu zan siyi wani''
har ta juya zata koma dakin mamin ta sake kiranta
''maryama zo....abdallah naga kai har ka hada naka layin ara mata tayi wayan''
yayi wani kicin kicin da rai ya saci idon mamin ya harareta kana ya ciro wayar daga aljihun trouser dinashi ya miqo mata
ta miqo hannu zata karba
''idan kinsan wannna baqin basamuden zaki kira da wayata ma gwara kiyi tafiyarki ki barmun abata,don wlh kika sake kika cinyemin credit sai na zara asalary dinki,don shi na fuskanci baya da arziqin da zai iya biya na''ya fada qasa qasa yana kallon paper din hannunshi da yayi rubutu,sai ka rantse ba da ita yake ba,murguda mishi baki tayi bayan itama ta harareshi kana ta karba duk da cewa bai ganinta,shi baisan yadda ta tsaneshi bane,idan banda lalra babu abinda zai hadata da wayarshi ma.
Ta loda numbers din raliyan ta kirata,sosai taji dadin shawarar data samu na abinda ya dace ta siya dim,ta kira hindatu ta zabi abinda itama takeso sai ta rage nata ta hada da na hindatun,kasa jurewa tayi don haka ta saka numbers din abdulrahim ta kirashi,sun taba hira sanna ta kashe,tana shirin ajjiyewa wani kiran ya shigo
*my suger* ta gani a rubuce,ta zubawa numbers din ido tana kallo,sai ta tabe baki sanna tayi rejecting.
ci gaba akayi da kira ita kam bazqta taahi ba sai ta gama rubuta duka abinda zata rubuta din ta fita gaba daya,kiran yaci gaba da shigowa ba qaqqautawa,tsaki ta ja ta janyo wayar ta daga kana ta kara akunnenta
''kada a cika mana kunne mai wayar bayi kusa''dum akayi kana taji ance
''ok''can qasa qasa
wayarta mata kyau ta dan juyata a hannunta,garin cire lock ta taba gurin pictures,daya bayan daya ta dinga bin folders din tana kalla,abinda ya daure mata kai ganin hounan abdallah da yammata kala kala,tana kalla tana tabe baki,wannnan guy din dan garari ne,waishin ma a ina yake haduwa da yammata haka zuqa zuqa yadda yake nuna he was always busy,ta shafe aqalla awa guda har taso shagala,duka hotunan babu na yarwa ya iya wanka kam babu ja a wannna tana iya bashi maki hundred parcent cif
larm din da agogon dakin yayi na qarfe goman dare ya tunasar da ita,garin sauro ta manta bata sauka daga folder din pics din ba ta kashi takardar ta fita falon,shi kadaine yanzun sai gun da mamin ta zauna,da alama yanzu ta tashi kuma ba dadewa zata yi ba,jin fitowarta bai sanyaahi daga kanshi ba,wayar ta miqa masa kana cikin cool voice dinta tace
''na gode''ya amshi wayar baiko dubeta ba,sai da ya bude screen din yaga inda ta shiga sanna yace
''awa ukun da kika kwashe wayar na gurinki hoton mitum daya dama kika tsaya kalla?''ya tambayeta idonsa cikin nata
ta dan zaro ido tana duban wayar,sai lokacin takula hotonshi ne a kai,yayi kyau cikin shigar suit yana murmushi,da alama ba'a qasar aka dauki hoton ba,bata kai ga cewa komai ba mami ta shigo falon
''kin gama maryamu''
''eh mami''ta fada tana miqa mata takardar,ta karba tana dubawa kuma tana qoqarin zama kan kujerar
''an gaisheki maryam,duk tsawon awoyin man iya ka kadai wadan nan abubuwan kika rubuta?,sunyi kadan''tace tana sake qarewa takardar kallo tana girgiza kai''
kararki tayi yawa dama nasan ba iyawa zakiyi ba,jeki kawai,zanyi amfani da wannan din da kuma wadanda na rubuta''
tana murmushi ta juya ya shige dakin ta barsu nan suna ci gaba da lissafe lissafensu
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
ta riga su tashi kamar yadda ta rigasu kwanciya su sai yanzu suke nasu baccin gajiyar,kafin su farka harta kammala breakfast taci nata,sai tayi zaune a parlour tana kallo abinta cikin riga da wando na pakistan orange da baqi,ya mata kyau kuwa sosai
takun da taji shi ya ja hankallinta abdallah ne ke fitowa sanye da riga armless da wando three quater,fuskar an ahade kirtif ya qarasa gaban freezer ha ciro fresh milk da ta hada sanyi ya balle robar ya soma sha,baifi rabi ba ya ajiye saman freezer din ya nufi kitchen sai gashi da plate da cup,mamaki tayi yau da kanshi ya zuba baiko nemi ta zuba masa ba lallai da alamu tunwa ce ta koroshi ma,zaya zo yana wani ciccin magani kamar wanda wani ya zageshi
can gefe guda ya samu ya zauna kan ya fara break din,duk sai taji kamar ya cika falon,zaman ya daina mata dadi,neman dalilin da zaisa ta tabar falon kawai takeyi,don bata buqatar ko qanqani zama inuwa daya ya dinga hadata da shi ko naminti dayane idan ba lalura ba
''ke''taji yace sai tayi banza da shi kamar bata jishi ba,ta fuskanci wani jan bala'i gake nema da ita tunda suka taho,ita kuwa kodan daraja da kunyar mami bazata bari su raba abun fada ba
''bakiji kashein da na miki jiya ba kenan sai da kika kira wani da phone dina ko,to ki gayawa rubabben saurayinkin kada ya kuma kiran numberta don ba sa'anshi bane ni''ya miqe yana dauke cup din tea tare da bari plate din a gun,bai kai ga shiga corridor din ba sukayi kacibus da mami tana fitowa da hijabi jikinta qafarta sanye da silifas
''mami ina zaki?''
''zan sauka ne floor na qasa mu gaisa da maman farida,jiya kaga ban samu na ahiga ba saboda gajiya''
''pls mami ki taimakeni kada ki cewa zeenah tare muke,wallahi kika bari ta sani tofa na banu kafin mubar qasar nan nacinta sai yasa na rame,ango kuma da rama ami ai babu kanta kada ta koro miki ni tace na mata rama da yawa''
dariya ma ya bata gani irin marairaicewar da yayi
''ka maida ni kakarka Allah abdallah,kakannin naka ma ka shafa musu lpy a kaina abun yake qarewa,ni dai Allah ya kusa rabani da alaqaqai gwara kayi auren ko kunnuwa da idanuna zasu huta da ganin yammata,ka shirya kafin na dawo mu fita da wuri so nake a yau a gama siyayyar baki daya''
tayi gaba suka gaisa da maryam ta fita,tayi zaton ya shige dakinsa tana zuwa sukayi kacibus bakib qofa,tana mura handle din dakin da qoqarin shigewa ciki taji yace
''kika sake mami ta miki tayin fita kika ce zaki bimu wata siyayya sai na qarasa targaden da na miki jiya''wuf ta shig dakin ta saka maqulli tadan daga murya
''to baaba na'' sanna taja tsaki,gado ta fada cikin jin haushinsa,dama ita bata sha'awar zuwan ma sam,dadai ba da si din zasu je ba shine,amma indai da shine zamanta a gida ya fiye mata dadi,qofar ya tsaya yana kallo,dan qaramin murmushi irin na gefan baki ya subuce masa ya cije lebansa na qasa kadan kana ya tura qofar nashi dakin ya shige ya cire kayan jikinshi ya fada wanka
*Mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: *ABADAN*36
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*_home of expert and perfect writers_*
*_annabi muhammad s a w ya tambayi sahabbansa_*
*_''shin ko kunsan waye matsiyaci?''_*
*_sai sahabbai suka ce''matsiyaci shine wanda bashi sa dirhami ko dirane''ma'ana bashi da cin yau bare na gobe_*
*_sai annabi yace musu''matsiyaci shine wanda zaizo ranar qiyama,yayi azumi yayi sallah yayi sadaka yayi zakka yayi hajji saidai kuma ya cuci wancan ya zalunci wancan ya zagi wancan yaci dukiyar wancan,sai Allah ya dinga dibanadan wadancan ayyuka na alkhairin da yayi ya dinga rabawa yana biyan wadanda ya zaluntar har sai ya tashi bashi da komai cikin aikin ladansa,ga ragowar wadanda ya zalunta ba'a gama biyansu ba,sai Allah ya dinga diban zunubinsu yana bashi da haka da haka har sai ya tashi bashi da komai face kayan zunubi sai Allah ya jefa shi a wuta''_*
*ya ubangiji kayi mana tsari don isarka*
Har mami ta dawo daga gidan maman farida ta shirya bai gama nashi shirin ba,sai da ta leqa ta masa magana,ta leqa dakin maryam ta taddatakwance
''ya kike a kwance mu da zamu fita?''
sai ta miqe zaune
''bana jin dadi sosai mami''
''ashsha,Allah ya sawwaqe,ki kwanta ki huta qila gajiyar tafiyar ce bata sake ki ba,Allah ya qara sauqi ma fita gobe ba damuwa,ungo wannan ajjiye min''ta miqa mata baqar leda,kayan bacci ne masu azabar kyau guda hudu
''maman farida ce ta bani su,nikam ina ni ina saka wadan nan qannnan tsirarar ai sai ku''
kunya ce ta kama maryam ta karbi kayan fana sunne kai,sanann ta tashi tayiwa mamin rakiya zuwa falo,sgi din ma ya fito sanye da qananun kaya,t shirt ce mai gajeran hannu baqa wanda a gaban rigar akayi rubutu gwara gwara kamara haka *we all have story to tell*,sai baqin trouser da ya saka,sun masa kyau aoaai kasancewarsa fari sai suka haskashi,qofan ta maida ta rufe ami tace sai sun dawo
kusan wuni sukayi ranar a waje har maryam ta qosa da zaman kadaitakar,duk da cewa ko a gida ma idan duka suka fice kusan haka ne amma acan wani okaci takan fice gidan baaba uwani susha hirarsu,da zaman shirun ya isheta sai ta fito valcony din gaban floor dinsu tayi zamanta tana qarewa unguwar tasu kallo
basu suka dawo gida ba sai da suka kammala siyayyar lefe kaf baki daya,hatta da akwatunan basu bari ba,daga can kuwa gurin da zasu dora kayansu a jirgi suka zarce basu ko dawo gidan ba,sun zabi zuwan kayan ta iska wato ta jirgin sama don shine mafi sauri,tunda kafin su koma za'a kai kayan suna sa ran kuma idan ta jirgin saman ne bazaya wuce kwana hudu zuwa biyar ba yaje sabanin ta jirgin ruwa da,zaya dauki watanni
sai da mami ta tabbatar komai ya kammala sannan ta karbi wayar abdallah ta kira qanwarta hajiya ruqayya ta mata bayanin kaya sun taho,tayi qoqari don Allah da sunzo a shirya komai yadda ya kamata aje a kai lokaci yana qurewa
a mugun gajiye suka dawo don haka suna dawowa wanka sallah da cin abinci kawai sukayi,cikin qanqanin lokaci gidan ya sake zamowa shiru saboda yau babu zaman hirar daki kowa ya shiga ya kwanta
Washegari dukkansu su ukun suka fita kai tsaye kamfanin sarrafa kayan gado suka shiga,katafaren kamfani ne da suka qware wajen qera da sarrafa kayan daki da suka hada da gadaje sif madubi zuwaafiyayyun kujeru iri iri,inda suke ajjiyesun bayan sun gama sarafa su aka shiga da su,mami ta bawa maruam dama ta zabi irin wanda takeao,duk sai ta duburbuce ta kasa zabar kowanne daga ciki
sun kusa shafe awa guda saboda girman gun ba tare sa ta iya zabar koda kala daya ba daga ciki
abdallah ne ya ja tsaki
''yarinyar nan fa wahal da mu kawai take yi mqmi,kawai ki fidda mata wanda kika ga ke ya miki''
''meye naka a ciki dakina ko naka ko kuma dakinta ita zata zabi abinta''
''Allah ya baku haquri''ya fadi yana kewayesu ya barsu a gun ya nufi inda ma'aikatan ke zaune
ma'aikata biyu da leburorin gurin guda biyar suka qaraso inda suke tsaye ita da mamin,daya daa cikin su yace da mami cikin harshen nasara
''madam,ku zaku yi signing a nan za'a fitar da kayan,motocin kamfaninmu zasu kaimuku har inda kuke buqata suna wajen kamfanin suna jira''ya fada yana miqa mata wata yar matsakaiciyar takarda,ta amsa ta duba kana ta kalleshi cikin arahen nasaran itama ta maida masa
''ai bamu kai ga zabar wadanda mukeso din ba ai''
''yallabai ya riga ya zaba har ma ya biya kudaden''yayi maganar yana nuna wasu tsadaddu kuma tsararrun kayan gado dake gefan hannun damansu,kala biyu ne kujeru sif gado da madubi curtains,dressing chair da bedside sai abun maqale jakankuna dukkan kalolinsu light and dark purple ne sai wasu set din kamar haka amma su blue black ne da light blue
ba qaramin burge mami kalolin sukayi ba har ta tsaya kallinsu saboda kyawun da sukayi mata,abdallah ya iya zabe kamar mace,ta daga kai sai ta hangoshi can sama wata kujera mai siffar kwano mai azabar tsawo a zaune hannunshi riqe da cup din glass yana shan lemo,kashe mata ido yayi ya langwabar da kai alamun bada haquri tare da nuna mata agogo lokaci na tafiya kenan kana ya mata alama da hannu na kayan sunyi?,dariya ma ya bata sai ta daga masa girarta alamar eh,hannunshi ya sake dagawa ya mata alamar i love u,murmushi ta kuma yi ta girgiza kai kana ta samu gefe ta zauna tana fara signing din paper din zuciyarta cike da tunanin mahaifin abdallah,wani lokaci idan hayi wani abun sai taga ya koma mata alh abdulkareem sak,barewa batayi gusu danta ya rarrafa ba ta fada cikin zuciyarta
duka cikin kamfanin suka nufi bangaren kayan kitchen anan kam dama kawai ta basu nasu hada mata duk wani abu da yake,da amfani cikin kitchen,cikin lokaci qanqani sai gasu da,kaya bila adadin sukayi total ta biya,yawan kudin da maryam taga mamin ta kashe mata shi ya sake raunata mata zuciya sanyata kuka,kuka sosai ta saka har ta kasa magana ma,hatta da abdallahn dan garari tsayawa yayi yana kallonta,karo na farko da ta bashi tausayi,jawota mamin tayi jikinta sai ta ora kanta a kafadarta,hawaye naci gaba da zuba,itama mamin kasa magna tayi sai bayan maryam din da take dan bubbugawa a hankali cikin sigar lallashi,har cikin zuciyarta tanq jin ciwon rabuwa da maryam din,idan banda aure batq jin akwai abinda zata lamunce ya tsinke zamansu mai dadi da suka fara
washe gari ma baccinsu suka sha sai yamma sanan mamin tace su shirya su fita maryam ta danga gari,kada tazo ta kuma koma bata san ya garin yake ba
babu musu ta shirya cikin doguwar riga dark blue da adon golden din duwatsu saqar india ce,ta haskata qwarai,saidai kasala da rashin dadin zuciya da take ji ya rage walwalarta qwarai,wanna fargabar ta aure sai yqnzu taji ta fara shigarta daga lokacin da tayi tozali da kayan dakin aurenta,Allah ya sani ba zata yiwa Allah butulci ba amma tilas amatsayinta na budurwa taji fargabar aure kamar yadda kusan kowacce soya mace take ji a auren farinta a rayuwa
da qafa suka dinga tattakin suna taba hira kadan kadan cikin sassanyar la'asar din,yanayin garin ami kyau ne,babu ruwan wani da harkar wani,kusan hirar dake gudana jefi jefi tsakanin mami ne da abdallah,bata ankara ba sai da taji shirun na maryam yayi yawa,a hankali ta juyo ta dubi maryama dake hannun hagunta
''maryam''
da sauri ta juyo tamkar mutumin dake cikin tunani aka katse masa,nazarinta tayi na yan sakanni kafin tace
''lafiya kike kuwa,daga jiya zuwa yau naga duka kin canza,ko bakijin dadi ne?''kai kawai ta iya girgizawa tayi qas da kan nata tana qoqarin mayar da qwallar data cika mata idanu,hannunta mamin ta kama ta jata kan kujerar dake girke daura da su yayin da abdallah yayi tsaye hannayenshi harde a qirjinsa yana kallonsu,bai iya jin me suke fada amma yana iya ganin me ke gudana,motsawar bakin mami da gyada kan maryam,a hankali ta dinga share hawayen idanunta qarshe ta buge da murmushi kana suka taso suka iske shi
mami ta dubeshi ya wani hade rai yayi kitchen kitchen,ta dan ranqwashi qeyarsa
''kai kuma da wa mai aljanun sauyin yanayi''dariya taso qwacewa maryam har sautinta ya dan fita,tayi gaggawar gumtse bakinta ganin yadda ya zuba mata harara cikin shan mur
''nifa mami gaskiya ina da kishi,don me za'a tafi ni a barni ni kadai a tsaye kamar maye bayan da can ba haka kike min ba,kawai don an samu wasu''
''maganarmu ce ra mata bai kuma cancan ci kaji ba ehe,ciwon 'ya mace na 'ya mace ne,sannan wasun ma da ka kafawa qahon zuqa suka tsole maka idanu sun kusa tafiya su baka sararin gurin kaga qarewarta sai ka koma shan nono kace ma ko yaye ka banyi ba''sosai mami ta bashi dariya har sai da ya dara yana fadin
''ni na isa,amma dai nasan tattalin da ake min irin na da zai dawo,kinga na zama dab lelen murum biyu,ga na my dear ga naki,thank god''
Da daddare suka hada dukkan wasu kayayyakinsu washegari jirgi ya debesu sai qasa mai tsarki,washegarin ranar da suka je suka sauke faralin ibadarsu ta umara,hakan bai sanyasu shiga wasu sabgogin ba sai da suka kwashe kwana biyar basu rabo da masallaci wanka ko cin abinci ke fiddasu,har gwara mami wani lokacin ta dan koma ta runtsa,maryam kuwa bata bawa kanta wannan hutun ba,tun mami na mata mita kan ta huta harta gaji ta barta,cikin kwana biyar din nan sai da tayi saukar alqur'ani biyu,dukkan alkhairi babu wanda bata roqawa mami mamanta raliya hindatu da ita kanta ba
kwana uku sukayi a madina ziyara,daga nan suka hada ya nasu ya nasu,mami tace itafa sai ta sauka a sudan tukun,cikin alamun tuburewa yace
''me zamuyi kuma a sudan mami,dear fa ta matsanta tana da buqatar gani na,i have alort to do mami a gida,inaga tafiya zanyi nikam sai kin taho''
''wa salaam wa kitabi,nima na huta da qorafi kama gabanka Allah ya miyaye hanya sai mun taho''anan suka raba jaha da shi,maryam batasan me zasuyi a sudan ba sai da suka je,unguwar tamkar tana cikin qasarta haka ta gani,sai dai 'yan bambance banbance da ba'a rasa ba na suturu abinci da al'adu.
kallo daya zaka yiwa matar ka tabbatar da 'yar sudance gabanta da bayanta,saidai mamakin da maryam tayi yadda hausa radam ta kama bakinta yanayin karyewar hatshen bw kawai zai nuba maka ba yarenta bane ara tayi ta yafa,ba abun mamaki bane jin yaren gausa bisa harsukan wasu al'umma ko qabilun da ba ahalin hausa ba,saboda yaren hausa yare ne sha kundum da ya fantsama lungu da saqo na fadin duniya,kusan a yanzu shine yare na biyu ko na uku da akafi amfani da shi,babu inda zaka tsoma qafarka a duniya ka rasa wanda ya iya ko yakejin yaren
gida ne babba mai bangare biyu bangare daya na matar ne daya bangaren kuwa harkar sana'arta kawai take gudanarwa,gyaran jiki gyaran gashi lalle ne kayan gyaran jikin na mata turaruka na ruwa dana ice da humra na tsuguno harda na wanka,kai hatta da kitso idan kana da buqata akwai mai yi maka,yadda maryam taji suna hira da matar tana tambayar mamin bayan saduwa ya fahimtar da ita lallai sun san juna dama can da mami,tunda har taji tana tambayar matar wata najwa tace taje daarfur sai gobe zata dawo,hajiya laila ita kewa mami irin wadan nan gyararrki zamanin alh abdulkareem mai nasara nada rai,gayu kam da gyaran kai mami ta yishi lokacin da mijin nata ke raye shi yasa ta zama ta gaban goshinsa,duk da a yanzun ma bata saki gayunta ba saidai ta daina wasu abubuwan tunda babu mijin
cikin kwana uku matar ta fara tsuma maryam,gyara take mata bana wasa ba tunda ta san haj bintu akwai sakin hannu idan harka ta hadaku,wani irin daddadan qamshi ta zaunar a jikinta wanda ko zama tayi a gu sai qamshin ya nasheka,farar fatarta ta canza yanayi farin nata ya saje armashi kyau gami da daukan hankali,sati guda ana mata gyararrkun taki wanne b'angare kafin suyo gida nijeria bayan haj laila ta hada muta wasu hade haden da zata ci gaba da amfani da su koda bayan bikin ne
bayan sun koma boyonta mami ta dinga yi,tuni ta daina komai a cewarta bataso nan da kwanakin da suka rage biki wani abu na gyaran da akayi mata ya samu naqasu,baaba uwani ita ta goyi bayan mami tayi uwa tayi makarbiya take komai
sunyi waya da mama da hindatu,mama cewa tayi sai tazo godiya don sam bai canci ta yiwa mami godiya iya ta waya kadai ba,amma da maryam ta sanar da mamin sai tace sam wallahi kada tazo,idan kuwa tazo din to ta nuna ba ita ta haifi,maryam ba,karamci da mutuncin mamin sunyi yawa har suka sa mama ta rasa ma me zata ce ko ta saka mata da shi?,hindatu amarya kam babu zama,ita da qawayenta ke gudanar da komai,don hatta da rabon kati su suka dinga yi,saboda mami ta riqe maryam tace babu yawon rabon iv da zata ta bata jikinta,ganin komai take tamkar a mafarki,wai tau ita maryam ce ake kira da sunan *amarya*,lallai babu wani abu da yake tabbatace sai mulkin ubangiji
bata fidda ran ganin irin wanan lokacin ba saidai koda wasa bata taba kawoshi nan kusa ba haka,dukka kayan da zata saka raliya ta fidda takai dinki,duk wata sabga da ya zamto ita zatayi raliya ta tsaya kan komai ita keyi kan jiki kan qarfi kamar a itace maryam din,kyakkyawan amincin da aka gina shi bisa turbar gaskiya da amana kenan,yakan iya kai ku zama qasan inuwar al'arshin ubangiji ranar da babu wata inuwa sai taahi
Biki ya rage saura kwana uku da daddare tana gurin baba uwani ta kai mata wasu kaya da take son bata ita da yan jikokinta kiran hindatu ya shigo wayarta
''kinyi tsada adda maryam,mami ta tsaya miki''inji hindatu cikin salon tsokana
''kema mama ta tsaya miki ai ya akayi ya gidan''
ajiyar zuciya tayi
''lpy lau,gida alhmdlh don har wasu daga 'yan gaya sun fara sauka,saidai ta wani bangaren ba lafiya lu ake ba''sai da gaban maryam din ua tsinke ya fadi,cikin sakonni zuciyarta ta fara raya mata faruwar abubuwa marasa dadi masu yawan gaske kuma duka akanta,muryarta na rawa t tambayeta mai ya faru
dariya hindatun ta qyalqyale da ita
''kwantar da hankalinki adda mana,na gaya miki mu lpy muke alhmdlh,bangaren da babu lafiyar su inna huwaila ne da baaba hadiza,kinsan watan baqincikinsu ya kama,yanzu haka jamila na daki ita da sauran yan uwanta anata mata ruqiyyar banza da wofi ta tada aljanun qarya,wai wlh indai na auri jabir sai ta kashe kanta,ni kuwa nace shashasha ki kashe kan naki mana kanki da uwarki kika yiwa asara,ita kuwa inna huwaila sai zirga zirga take ta fita aje ta dawo ta kasa zaune ta kasa tsaye,zuwa dare saiga aminiyarta uwani sai ji mukayi tsakiyar tsakar gida tana cewa,ke kika kawo kanki kikace na kaiki gun bokan nan bani na jawoki ba,don aiki bai ci ba kuma zak nemi tijara ni gaban kishiya?,to ai ramuwar gayya tafi ta gayya zafi shi yasa na biyoki ayita mai kankat kema kowa yaji,mugun qullin da kika so qullawa,ta fayyace duk abinda suka qulla din sannan ta dora da fadin,bola kuma na bogi ne kudi kuma muni babu yadda kika iya,aminad da kuke baqinciki da ita daga ke har hadizan ai ta fiku,yanzu gashi data miqawa Allah kukanta ta jadiye baqicikinta na shekara da shekaru Allah ya yaye mata damuwarta ba tare da tayi hasarar sisin kwabonta ba,ku kuwa haihuwar asara babu kudi babu biyan buqata ga asarar imani,sallolin kwana arba'in a ajejere kun rasa ta kusan kwana dari bakwai,amina Allah ya sanya alkhairi ya tsone idon maqiya,kuma wallahi ni da ku dukanku ke da hadizar shege ka fasa,naci uwar mace a iya tijara da ramuwar gayya,duk kuma wadda take jin ta haifu da jini uwarta ta haifeta ta fito ta tanka
wai in gaya miki adda saiga inna huwaila ta fito da borin kunyarta waisai sun daky wallahi bugu daya uwale rayi mata sai gata tayi plate a qasa''hindatu ta fada tana sheqa dariya
''wai kuma ta sumewa mutane jadiza tayo kanta wai huwaila kinci amanata ta hau dukanta,lubabat
u kuwa itama tayo kan,hadizar ke in taqaice miki labari kowa sai ya ahigarwa uwarsa gida ya zama na wrestling,ina ta laluben wayata in miki vedieo don,kada ayi babu ke saiga babamu nan ya shigo shi ya raba cakwakiyar,kowacce da dogon bakinta ta taho zungi zungi zata yi masa bayani don ya bata gaskiya yadda suka saba yace babu wadda zai saurara,wanna ya ishesu ishara,mama ce......''
''haba aku mai vakin magana,sai kace na kunna freedom?''inji maryam tana murmushi bayan ta katse hindatu
''kefa adda ba'a miki abun arziqi''
''to ai wanna ba baun arziqi bane''
''wallahi nikam abun arziqi ne tunda na gano tashin hankalinsu ranar kawo lefenki,da farko da suka ga anfara shigowa da qananun akwatuna har sun fara yada habaici,da suka ga dai shigowara ke sai suka fara lissafi suna tabe baki,qarshe da suka lissafi akwati ashirin da hudu cif manya da qananu sai aka nemesu aka rasa,inna hadiza na quryar daki suna safa da marwa huwaila kuwa anyi tsamo tsamo an rasa na kamawa,ana cikin haka saiga nawa lefen akwati sha uku,qarshe saiga inna hadiza na dora hannu aka tana xunduma ihu huwaila a taya ta da sharbe hawaye da fyace majina,a gaban idon mutane fa abin mamaki da dariya,ko kunya babu''ta sake qyalqyalewa da daria don tuna abun da tayi
''Allah ya rufa asiri,yanzu ya abubuwa suke tafiya?''
''komai na tafiya daidai,amma wlh adda kizo ki kalli lefanki''
''kai hindatu,me kike ci na baka na zuba,abinda za a ajjiye maka su a dakinka wataran har sai ka gaji da su''
''to ai shikenan,dazu yaya abdur rahim yazo ya kawo kudin dinkunanki,dazu naje gidan adda raliyan na kai mata,har ta fara karbo wasu ma ta bayar an goge miki,gaskiya adda raliya tayi wallahi,akwai zumunci tayi qoqari''
''gaskiya ne Allah ya bar zumunci ya saka mata alkhairi''
''ameen''
nan take aya mata kayan gadonsu da aka siya duka an hada mata sun zama biyu kenan har kayan kitchen dinsu,madyam din tace yayi babu laiciya zama dakin baqi kenan da naki dakin tunda kince shima jabir din ya zuba naahi furniture din,jibi insha Allah nima zan taho gidan gaba daya ai,ki gaida mama''
''Allah ya kaimu,zata ji insha Allah''
daga haka dukkaninsu suka katse wayar