HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Arewa hausa novels
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)
WHATSAPP NO:
+2347039625239
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD✍🏻*
Da sunan Allah mai Rahama mai jin kai.
Yanda zan fara rubutun nan lafiya, ina rokon Allah dayasa in gamashi lafiya, sannan abinda ke ciki na kuskuren Allah ya yafe mana, wanda muka fad'a daidai kuma Allah ubangiji yasa masu karatu su amfana dashi(Ameen).
Ina godiya ga masoyana akan kullawar da kuke nunamin.
Hope zaku biyoni danjin wannan labarin............luv u all😘
Episode 1⃣
Wani irin ihu ta sake mai tsananin kara, duk mutanen dake cikin gidan sai da hankalinsu ya tashi, mazan dake zaune a dinning suna breakfast suka kalli juna sai kuma suka mik'e da gudu sukai sama, masu aikin gidan suma duk suka hau gudu sai rige rigen hawa beni akeyi, mutum d'ayace bata ko d'aga kafar taba bare insa ran zatasa gudu kamar kowa, tsaki ma naga taja ta wuce d'akinta.
Sukam duk sun isa kofar d'akin da ake ihun suka shiga knocking jin kofar a kulle, babban cikinsu wanda ina tunanin ma mahaifinsune ya matso jikin kofar yace "my swthrt open the door please. "
Daga cikin d'akin cikin wata murya mai sanyi akace " Dad kaga fuskata kuwa? Banasan ganin kowa."
Kallan juna sukai shida mazan dake gun guda 2 sukai murmushi, wanda takira da dad d'in ya kalli wasu turawa dake sanye dakayan aiki kana ganinsu kasan masu aikine garin irin kayansu, ya musu alama da kai yace "Spare key."
Cikin sauri sukace "ok Sir."
Suka juya.
Basu dad'e ba sai gasu sun dawo, dasauri suka mik'a makullin.
D'an saurayin cikinsu ne wanda da alama shine karami ya amsa tare da bud'ewa, suka d'uru cikin d'akin dukansu, azaune suka ganta a kasa ta rufe fuskarta ta hannunta biyu.
Dad yai murmushi ya karasa kusa da ita yace " My Swthrt meke ya faruwa? Bazaki bud'e ido ki kalli fuskar Dad d'in naki ba?."
Cikin shagwab'a ta sauke hannun tare da bare baki tasa kuka tace " Dad kalli fuskar Princess d'inkafa?"
Dariya suka kunshe dukansu, d'ayan namijin yace " Wai! Wai! Wai! Seemah kin ganki kuwa? gaskiya na tausaya miki." Yafad'a tare da kunshe dariyarsa.
Seemah ta kalleshi tace " Yaya Janaid da gaske?" Takalli dad takara sa kuka tace " Dad dama na fad'a maka shi yasa banso kuka ganni ba."
Dariya karamin yai yace " Ohhhh ni yazanyi? Kanwata takasa girma," ya fad'a tare ta tab'a kasan id'anta ya lakutu bakin abu, yace " wannan ba Mascara bane Seemah? "
Sai alokacin ta kalleshi tace " do u think so?"
Ya d'aga mata kai alamar eh,ta kalli masu aikin tare da mik'ewa taje kusa dasu, ta tsaya a kusa da d'aya tace "Anna mascarar dana sa jiyace tamin haka?"
Anna tace "Sorry Madam it's my fault."
Seemah takarasa jikin madubi ta kalli kanta kamar wata aljana da sauri ta rufe fuska takalli karamin saurayin tace " Ya Ammar to ya akai hakan ta faru dani? Jini fa? Zai fita ma kuwa?"
Dariya sukai su dukansu, dad ya kamota ya zaunar a bakin gado, yace "Anna zo ki gyara mata fuska. "
Dasauri tace "ok sir"
Ammar yace "amma meyasa kika kwana da kwalliya?bana hana ba?"
Ta turo baki tace "laifin Anna ne kullum in nai bacci ita take zuwa ta gogemin, amma shine jiya bata gogemin ba."
Junaid yai dariya yace "da alama da asuba dakikai alwala duk ya zazzago miki, ke kuma shugabar bacci baki kulaba ki ka kwanta bacci."
Tace" I think so yaya."
Dariya sukai dukansu.
Dad ya mik'e ya kalleta yace " Swthrt zamuyi late bari mu fita."
Tai murmushi tace "nima inada lectures yanzu zan shirya."
Shafa mata kai yai yace "yauwa baby na."
Suna fita Anna tashigo ta goge mata fuska sannan Seemah ta shiga wanka.
Su dad na sauka kasa suka taradda matar d'azu ta fito daga d'akinta, ran dad ya b'aci ya kalleta cikin b'acin rai kafin yai magana su Ammar suka ja jakarsu sukai waje gun mota, ya kalleta, itama tsoron mai zaice take.
Ta d'aure tace "bakuyi breakfast d'in ba? na shiga toilet ne sai yanzu na fito."
Dad ya maka mata hararra yace " Yanzu in wani abu serious ne yasamu Seemah sai ki wuce toilet?" Ta d'aure tace " it's a relief ai tunda ba serious bane."
Yace " oh da kikai kamar baki sani ba? Kin kyauta." Ya fad'a tare da yin kwafa ya wuce waje.
Tabishi da kallo tace yau koma me za'amin na tab'o 'yar gwal? Sun bar yarinya duk tagama sangarcewa, datayi magana sai yacemata kar ta manta aurantama dayai saboda Seemah ne, tsaki tai ta wuce kitchen.
Seemah na fitowa daga wanka ta kure disco tana rawa tanasa kaya, Anna na tayata shiryawa, riga da wando tasa sanna ta zura suwaita doguwa a sama tasa karamin nayafi ta yane kanta, ta fito tare da d'aukan karamar jakarta.
A hankali ta sauko kasa ta kalli dinning kamar yanda masu aiki aka umarcesu, sun jera mata nata kayan abincin, ta karasa dinning ta bubud'e kwannukan, ta kalli matar dake zaune itama tana nata breakfast d'in tace " Small Mom banajin zan iya cin abinci, in dad ya kira ya tambaya please kicemai na ci."bata jira amsar taba tai waje, tana gyad'a kai.
Haushi yakamata tace "Small mom? Da haka ki kirani da sunana mana Sadiya"
Seemah na fita ta taradda driver ya gama goge mota yana tsaye yana jiranta, ta kalleshi tace " da wace mota zamu? "
Dasauri ya nuna mata wanda yake tsaye, tsaki tai tace "ni bana santa kujerar cikinta basu da laushi sosai, muje a waccen." Tafad'a tare da nuna wata.
Da sauri yace to madam.
Kallan garin tai tace " it's snowing."
Takarasa ta shiga mota suka fita daga gidan.
Garin England yau sun tashi ana ruwan kankara sai dai sukam mazauna garin sun saba da wannan rayuwa, hada_hadar su kawai sukeyi, nikam banda rawar sanyi ba abinda nakeyi, nace kaii! Ina zan iya rayuwa a nan? Seemah na kallah dako ajikinta, nace uhmm keda aka haifeki anan dama.......wayarta ce takatseni datai kara, da sauri Seemah tad'aga ganin sunan dake jiki Big Bros.
Cikin shagwab'a tace " Yaya Habib."
Yace " Princess dafatan kin tashi lafiya?" Tace "lafiya lau Bros bayan kak'i zuwa?"
Ya kalli matarsa dake kusa dashi yace "Ai zuwa zai ban wahala yanzu d'an company d'in dad na bukatata sosai."
Seemah Tace " dama za'a barni inzo im ganka, If you think it yaya ban tab'a zuwan garin iyayena ba, gashi kai yanzu ka koma can, sannan su Ya Junaid da Ammar suna zuwa duk bayan 5 month haka ma Dad amma ni bandani."
Habib yai murmushi yace "gaskiya kam, kunyi hutun skul?"
Cikin zumud'i tace "yau zamu gama exams, kasan kuma inmun gama shikenan an gama zuwa sai an dawo."
Yace "Good, zan ma Dad magana yabarki kizo ko 1 month ne kimana."
Dakarfi tace " *YESSSS* Kai Bros shiyasa nake sanka sosai."
Nan sukai sallama akan sai ya tambayi dad.
*************************
Seemah cikin farin ciki ta isa makaranta, ra k'osa taga ya Nigeria take, suna isa ta sauka daga motar tare da shiga cikin skul d'in, tana taka kafa zata ciga class d'insu taji ansa ihu ana fesa mata spray, mamaki ya kamata ta kallesu zatai magana taga abokinta Alex yazo kusa da ita yayi knell down tare da miko mata flower, yace " Seemah will you date me?"
Ihu yan class d'in suka sa suna tafi suna cewa " ACCEPT IT!!!!!!"
Kallan Alex tai cikin mamaki tace " Alex what's going on? "
Ya kara m'iko mata flower yace " Seemah please accept my love."
Kallansa ta sake yi ta d'an tab'e baki tace " Alex will you stop all this drama?"
Alex ya mik'e tare da cewa " Seemah!!!"
Hararsa tai sannan tace " do I look easy to u? Meyasa kowa yake neman raina min hankali? Rannan Abokin ka yazo min da zancen yana sona, yau kuma kai? Am I a toy to u? "
Alex zai yi magana ta amshi flower hannunsa ta kalli wata mate d'insu datake sanshi, kowa na skul d'in ya sani har shi Alex d'in ta ajiye mata flower a gabanta sannan ta kalleshi ta wuce ta zauna, Alex ya bita da kallo, abokanansa sukace kaima kasani ai yarinyar nan datakejin kanta kamar 'yar gidan sarauniyar England itace zata so ka? Get a hold of yourself buddy!!!.......
Tana zama waya ta d'aga tama Ammar text, tana ajiye wayar ya kira, yace " Princess ya akai? Ki kace wani ya miki proposing?"
Tace " eh mana yaya wai kuma ka san wa? Alex fa?"
Dariya yasa yace " yanzu ya akai?" Tace " ya akai kuwa? I reject him kaima kasani yaya Alex is not my type."
Dariya Ammar yai tace " nifa yaya wanda zan aura dole ne sai ya cika abubuwa guda 5, na farko kyau, na biyu ya d'inga bani respect, na uku bai isa yamin abinda zai b'atamin raiba, na hud'u ya zama mai kud'i d'an ni ban taso a babu ba, na biyar in har nace kaza to lalai sai an min."
Ammar yasa dariya sosai yace " anya kuwa zaki samu duka?" Tace "umm wait an see yaya I will definitely find him."
Ammar yace kai amma na kosa inganshi.
Dariya itama tai tace "yaya plz kasa baki a barni naje Nigeria. "
Yace "ok ba matsala, ai kin kai 20yrs ya kamata dad ya barki."
Tace tnx Yaya
Ammar yace "ki share kiyi exams d'inki a nutse."
Murmushi tai tace "ok tnx Oppa".
♡♡♡♡♡♡♡♡♡
Zaune yake a gaban mahaifiyarsa ga kanwarsa dake kwance bata da lafiya, tun tana 'yar shekara 10 ciwo ya kamata, take a kwance har yau Allah bai bata damar mik'ewa ba, komai yi mata ake.
Goge mata bakinta yai da miyau yake zuba, ya kalli umma yace " umma ina tunanin tau zan koma."
Tace " Jalal in ka tafi wannan karan ka d'inga bari sai sati bibiyu, daga Abuja zuwa binin_gwari da nisa."
Murmushi yai yace" zan duba, amma Abba fa? Naga har zan tafi bai dawoba."
Tace "yaje kai Zainab kauye ne gun iyayenta, ta damu tanasan zuwa," tai shiru can tace jalal nikam har yanzu baka duba maganar dana cema ba? Na auren Zainab? Kaga 'yar uwace gata ba ruwanta."
Jalal ya mik'e tare da cewa " Umma bari na wuce, zan kiraki a waya."
Takalleshi tare da cewa "to Allah ya kiyaye hanya."
*Jalaludeen* kenan talakawa ne sosai sai dai mutum ne shi da bayasan a rainashi dan bashi da hali, kuma baya tab'a kaskantar da kanshi akan wani mai hali, baya d'aukar raini, ba kuma ya so a rainashi.
**************************
Seemah na gama exams da sauri ta shige mota dan batasan su had'u da Alex tana shiga, ta kira yaya Habib, yai murmurshi yace " lalai na yadda kanwar nan tawa ta kosa tazo ta ganni"
Seemah tace " yaya ya kukai da dad?" Yace "ya ce ba matsala indai zan kula dake."
Ihu tasa tace" wow yaya amma nifa tunda na gama exam so nake a satin nan, in fact gobe ko jibi na k'osa inganka."
Habib yace " bakomai zan duba flight na kusa nima na k'osa inga my kanwa."
By[truncated by WhatsApp]
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JALALUDEEN*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
No 2⃣
Seemah tana isa gida a falo ta tarad da Matar babanta tana kwance ta mik'e akan kujera, ta saka apple a gaba tana ci, haushi ya kama Seemah itakam yanda matar takeyi yana bata haushi sam bata santa, ita tanaso taga mutum ya damu da ita bakamar wannan ba.
Shiga tai tare da tsaya a inda take kwance, ta kalleta tace "Small mom bakiga na dawo bane?"
Tad'aure ta d'an kalleta kasa kasa tace " to in kindawo Seemah so kikeyi in mik'e in shiga tsalle? Ga 'yar shugaban kasar England ta iso?"
Kallaman sun ma Seemah ciwo ta kalleta tace " a gurin iyayena na fi wata sarauniyar England matsayi, amma ina tunanin dole yau injira Dad yazo d'an ya tabbatar miki da hakan."
Tana kainan ta juya tai d'aki ta fad'a gado, d'an shagwab'a irin na Seemah ta hau kuka baji ba gani, sai data daidaici lokacin dawowar dad ta sake ware murya tana kuka.
Itakam mata hankalinta ya tashi, gashi batajin zata iya ba Seemah hakuri.
Dad tare suka dawo su 3 kamar yanda suka fita, haka suke dawowa kullum.
Dad na shiga ya kalli falon ya saba yana shigowa Seemah zata rugo da gudu ta rungumeshi, ganin ba ta nan yasa ya kalli matarshi yace " Sauda ina Seema?" Cikin rawar murya ta nuna sama, dasauri dad yai hanyar suma su junaid suka bishi.
Seemah kam jin motsinsu yasa takara sa kuka da sauri suka bud'e kofar, dad ya karasa tare da cewa " Baby menene? Waya tab'amin ke?"
Seemah Cikin kuka tarik'e hannun dad tace " Dad tambayar ka zanyi, tsakanin ni da sarauniyar England wayafi matsayi a gunka?"
Da sauri Dad yace " wace irin tambaya ce wannan Seemah? Wake wani zancen sarauniya bayan ni kece sarauniya ta?"
Ta kalli junaid tace kaifa yaya?
Ya kalleta yace " Haba princess yama za'ayi ki mana wannan tambayar? Ai ko d'an sarauniyar ne ya nemi yana sanki saboda matsayinki bana jin zamu iya amincemai har sai ya yadda da dokokin mu bare kuma ace matsayi."
Dariya tai tace " yaya Ammar fa?"
Dariya yai ya matso tare da rik'e kunnenta kad'an yace " waye ya miki wannan banzar tambayar ke kuma har kika rik'e a ranki?"
Tad'anyi kara tare da kallan Dad tace " Small mom ce."
A zabure Dad ya mik'e ranshi ya gama b'aci ya juya yai waje da alama gun matar tashi zai je.
Ammar ya kalleta yace "da baki fad'aba Seemah, Dad bazai mata dasauki ba dama ta b'ata mai rai da safe."
Seema ta murgud'a baki tace " wayace karta d'inga kula dani? Ni fa yaya banasan mutumin da bai damu dani ba, nafisan kowa na duniyarnan ya soni kar kowa yad'inga nunamin halin ko in kula."
Dariya Junaid yai yace " lalai Seema ai kuma hakan bazai yiwo ba, tunda mu muna sanki ba shikenan ba? Karki damu dan wani bai damu dake ba."
Kallanshi tai tadai jishi amma bata aminta ba, itafa tafisan kowa ya sota yakawai......
Nikam nace tab da matsala........
***********************
Dad kam yana fita ya tarad da Sauda a tsaye a kasan beni, ya kalleta yace " waya baki izinin kid'inga had'amin 'yata da wasu can mutane? Harki samin ita kuka?"
Tai shiru can tace" Alhaji bafa haka bane kasan me?...."
Katseta yai cikin zafin rai yace " bansan komai ba, kuma banasan insan komai, abu d'aya nakeso in sani, a wani dalilin kike samin 'yata kuka? Ko d'an ke bakisan darajar d'a ba? "
Cike da mamaki ta kalleshi tace "Alhaji yazaka fad'amin wannan kalmar? Abinfa bai kai nan ba."
Yace " what? Bai kai nan ba? In bai kaiba meyasa 'yata na sameta tana kuka? Karki manta zan iya jure komai amma banda hawaye daga idan 'yata, banga d'an Adam d'in dazai wahalarmin da 'ya ba nikuma in kasa d'aukar mataki ba, na aurekine d'an ki kularmin da 'ya kuma akan haka kuka amince daga ke har iyayenki, kukace ku kuma so kuke in barki kiyi karatu a nan kasar na aminta, sannan ni na cika nawa kin gama masters d'inki sai nine bazaki cika min ba?"
Sauda ta had'iyi wani abu, ta d'aure tace " kayi hakuri, ba da wani abun na fad'aba amma tunda abin ya kai haka amin hakuri."
Dad baice komai ba ya juya ya hau sama, ta bishi da kallo ranta yakai matuka gun b'aci, tasan sarai me yake nufi da ya hau sama wato ta biyoshi ta bada hakuri.
Itakam ta rasa wani irin so sukema Seemah, itakam da Seemah gwara a mata kishiyoyi guda 3 su zama su hud'u, in kishiyoyine bata tunanin zasu samu wannan damar, haka ta d'aure tahau sama.
Seemah na zaune suna hira da shewa sai labarin abin dariya suke bata, itakuma tanayi, can ta d'aure tace "Dad please ka barni inje Nigeria. "
Dad yace " Seemah mu jira sai wani hutun, ban shirya missing d'inki wannan hutun ba."
Turo baki tai cikin shagwab'a tace " Dad please ka barni, bafa dad'ewa zanyi ba, sannan ga waya." Tafad'a tana d'aga wayarta.
Ammar tad'an kalla da alama magana tamai ta ido, shima yace " eh Dad ka barta please ko d'an taje ta gaida su Inna."
Dad zaiyi magana sallamar Sauda ya katseshi, suka amsa ta karaso ta tsaya a kusa da Seemah, ta saki murmushi tace " Haba Princess daga wasa ashe kinji haushi? Na d'auka tsakanin d'a da mahaifi akwai lokacin wasa?."
Seemah ta kalleta zatai fitsara Ammar yai saurin toshe mata baki yace " Aunty ba komai ya wuce."
Takalleshi tace " Seemah ina kike san zuwa nazo shigowa naji ana zancen." Tai maganar tana murmushi.
Seemah tai shiru can tace" gun Yaya Habib nakesan zuwa amma naga Dad kamar bayaso."
Yanda tai maganar ne yasa tabasu dariya, junaid yace " da alama yau zamu ganku a rana Dad."
Hawayene ya zubo mata tace "dad kaji ko? Gashi ka bari su yaya Junaid zasu mana dariya."
Da sauri ya jawota ya rungume yace " barshi da gulmarshi, so yake yaga munyi fad'a tunda bai tab'a gani ba, zuwa gun Habib kuwa na amince."
Ihu tasa ta kara rungume dad tace " Dad shiyasa nake bala'in sanka."
Dariya suka mata Dad yace " Amma in zaki inaji sai na had'aki da securities da zasu d'inga kula dake, haka kawai Habib na can gun aiki ke kuma kina guri ke kad'ai bazan bar hakan ta kasance ba."
Ta kalli Ammar tad'an lagwab'ar dakai kamar zatai kuka Ammar yace " Dad amma ina ganin kabari kawai in yaso in taje can sai a sanar da Habib ya samarmata bodyguards dazasuna kula da ita. "
Dad ya kalle Ammar yace "kana ganin hakan ya fi?" Dasauri Seemah tace eh mana Dad.
Nace uhmm..................
****************************
Yau Seemah tun Safe akai wanka dan flight d'in sukai booking, Sauda tafi kowa murnar wannan tafiya d'an ko Seemah dazatai tafiyar ta fita murna.
Seemah ta shirya cikin riga da wando d'an ita banaji akayanta akwai atamfa ko ince bata tab'a gwada sawa bama, bayan tasa riga da wandon sai kuma ta d'auko rigar sanyi tasa, d'an garin sai da rigar sanyi, ta yi kyau Anna ta kalleta tace " Madam I will miss you."
Harararta Seemah tai tace " bayan yanzu kin rage damuwa dani?"
Anna ta karaso ta rungumeta a hankali kwalla ya zubo mata, Seemah ta juyo tace " wasa nake Anna na sani kin damu dani sosai, tun ina karama, nima I will miss u."
Tare suka fito Anna na rik'e da jakarta, a falo sukaga Sauda sai murmushi take, suna saukowa ta kalli Seemah cikin tsananin farin cikin da kana gani zaka gane tace " Seemah yanzu tafiya zakiyi? Sai kuma yaushe?"
Seemah ta kalleta ta had'e rai tace " Small mom nasani kinfi kowa murnar tafiya tai, sai dai ba dad'ewa zanyi ba."tana kainan tai waje gun dasu Dad ke jiranta a mota.
Kowa yana zaune a cikin motarsa da driver d'insa, ta kallesu tare da sa dariya tace " Dad ahaka za'ayi rakiyar? Kowa na motarsa? Nima in shiga tawa?"
Junaid yace " to a ya za'ayi?"
Ta bud'e motar junaid tace yaya fito, junaid ya fito, ta bud'e motar Ammar tace bros kaima fito, shima ya fito, sukace me za'ayi? Motar Abba ta bud'e ta gaba tace Ya junad shiga nan, ya kalleta yace tohh.
Nan ya shiga ta kalli driver d'in Dad tace fito shima ya fito ta kalli Ammar tace bros jamu.........tafad'a tare da shiga kusa da Dad.
Dariya sukai nan suka shiga tare da fara tafiya, Dad yace " kai Seema zamuyi missing d'inki, baki tab'ayin tafiya ba tunda aka haifeki."
Tai raurau da ido tace " yauwa, dole ne kowa a rana ya kirani sau 5 in ba so yake muyi fad'a ba."
Haka suka cigaba da tafiya ana raha, Dad yace" na fad'ama Habib ya kularmin dake sosai duk abinda kikeso a tabbatar an miki shi."
Dariya tai tace " inada Dad irinka me zai dameni?" Sun isa takira Habib tafad'amai zasu taho.
Sai da aka gama musu checking suka shiga jirgi sannan suka juya zuciyarsu duk ba dad'i.
**************************
Habib na isa company d'insu ya fara shiga meeting, sun dad'e kafin su gama suka fito sukai sallar azahar, ya duba agoggo akala saura hour d'aya su seemah su iso, yana komawa yataradda wani aikin ya kara tasowa dolene su shiga wani meeting d'in gashi baisan sanda zai fito ba, Secretary d'insa ya kalla yace " Kanwata tana hanya gashi zamu shiga meeting kasa wani ya je airport nan da minti 30 ya jirata ta iso ya tahomin da ita nan, sunanta Seemah, ka tabbatar wanda ka tura mutum ne mai hankali yakuma je ya jirata yanda tana isow zai kawomin ita."
Secretary d'in ya amsa da to, nan ya shiga tunanin wazai tura, abokinshi ya tuno, dasauri ya danna number, daga can aka d'aga yace " ya akai Sagir?"
Sagir yace " Jalal please kataimakamin meeting zamu shiga da Chairman to kuma kafin mu fito kanwarsa ta iso shine ya keso a taimaka d'aukota, nikuma banyi tunanin kowa a company d'in nan ba sai kai."
Jalal yai tsaki yace " ta hawo taxi mana? Dole sai an d'aukota? Ni ma aiki nakeyi."
Sagir yai dariya yace " Taxi jalal? Kanwar Chairman d'in company d'inmu fa nace? Kuma bana tunanin ma ta tab'a zuwa kasar'"
Jalal ya nisa yace" to kanwar Chairman tafi karfin taxi?"
"Nidai plz kataimakamin abokina d'an Allah, sunnanta Seemah, bari na shiga meeting zan ba da makullin motar chairman d'in akawo maka, nan da 30mins zasu iso."Sagir nakainan ya kashe wayar.
Tsaki Jalal yai sannan ya kalli takardun da aka bashi yai sorting, shifa baisan rainin hankali, shi driver ne? Dandai Sagir ne amma da ina..............
By *Ayusher Mohd*
© *NWA*
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JALALUDEEN*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
NO 3⃣
A hankali Jalal ya mik'e ganin minti 30 d'in tayi, tsaki ya sakeyi yace amma Sagir ya ci mutuncina.
Kallan 'yan uwansa nagun aiki yai yad'an sosq k'eya yace " zan d'an fita gun wani friend d'ina."
Sukace sai ya dawo, waje yai yana cewa haka kawai da mutuncina an sani karya, makulli ya amsa tare da tambayar security d'in ina motar take? Nan ya nuna mai, ya kalli motar tayi kyau sosai, bud'ewa yai ya shiga tare da jaa....
Ya isa airport sa alokacin yashiga tunanin wai ma yazaiyi yasan itace? Zuwa zaiyi yai ta tambayar mutane Seema ko me? Shiru yai can yace " Seemah? Amma sunan kamar ba na kasar nan ba, yai kama dana india, to amma Sagir yace wai kanwa" yai shiru a ranshi yace da alama Sagir d'in bai fahimta bane.
Ya dad'e a zaune baiga jirgi ya sauka ba, haushi ya isheshi ya kalli agoggo kusan mintinsa 30 kenan da zauwa, haushi ya isheshi ya mik'e zaiyi hanyar waje, karar jirgin dake alamar sauka ne yasa ya koma ya zauna.
Kallan mutane ya shigayi wad'anda sukazo d'aukar 'yan uwansu, to shi wai ya zaiyi ya ganeta? Ganin mutane sun fara tahowa yasa wata idea tazo mai, juyawa yai yaga wasu rik'e da manyan abu d'auke da sunayen wad'anda sukazo tarba, a ranshi yace nima bari nai haka.
Jakarsa ya bud'e ya d'auko littafin rubutunsa, ya gutsuro takarda karama, tare da rubuta Seemah da biro a jiki.
A zahiri in ba kazo kusa ba bazaka tab'a ganin me aka rubuta ba.
Nikam dariya ne ya rufeni ganin wata 'yar takarda d'auke da sunan Seemah gashi sai kunyar rike takardar yake da kyar ya d'aure ganin zai b'atama kansa lokaci yasa ya d'an rike da hannun hagu.
'Yan jirgi sun fara fitowa, Seemah kam duk ta gaji a jirgi ta fito sanye da glass ta cire rigar sanyin datasa ta jacket ta rik'e a hannunta, ga takalmin da tasa mai masifar tsinine, rigar jikinta takai gwiwarta sai wando pencil dake jikinta, tasha jambaki pink, gaskiya tayi kyau sai dai tunda ba al'adarmu bace hakan yasa kowa take kallanta, itakam ko ajikinta.
Raba ido kawai take taga an rubuta Seemah a katon symbol wanda zai d'au hankalin mutane, sai dai duk wanda ta leka sai taga ba sunanta, mamaki ya kamata nan tace ko dai yaya yana kunyar rubutawa ne? Nan ta shiga duba mutane ko zata ganshi, mamaki ne ya kamata ganin har ta iso gun da mutane ke tsaye suna jira bataga yayanta ba.
Jalal kam ya baza ido sai neman ba india yakeyi, sai dai turawa kad'an da suka fito.
Seemah da sauri ta kunna wayarta, sakon yaya ne ya shigo na zai shiga meeting amma ya turo a d'auketa, haushi ya kamata tace " akwai meeting d'in daya fini mahimmanci ne?...."
Maganarta ce ta katse ganin wata 'yar karamar takarda wani saurayi sanye da coat yana rik'e dashi, dariya ne yazo mata tace " lalai wasu basuda mutunci, yanzu wannan 'yar iskar takardar da ita za'a tarbi mutum? Da alama dai mutumin nan ko bashi da mutunci ko kuma mammako ne ya mai yawa.
Hartazo kusa dashi tana d'an duba mutane, to ta ina zata gane d'an aiken? Ga wayar yaya a kashe, idanta ne yakai kan rubutun dake jikin 'yar takardar, in batai kuskure ba *SEEMAH* taga an rubuta, wani kululun bakin cikine ya ziyarceta, badai ita Seeman ba d'an itakam tasan tafi karfin wannan takardar.
Karasawa tai kusa dashi, daidai nan shikuma wani Sagir ya kirashi, Jalal ya d'aga cikin kunnar rai yace " Sagir me kad'aukeni? Tun d'azu ka aikoni d'auko wata banza itakuma tana neman b'atamin lokaci, ce maka akai banda aikin, yi ko me?"
Sagir yace " Sorry Jalal yanzun ma ba gama meeting d'in mukai ba, Chairman ne ya kalleni, hakan yasa na gane so yake yaji maganar kanwarsa, dagani yanaji da ita."
Cikim zafinrai Jalal yace" me yadameni da wani ji da ita dayake? In hakane ya bar meeting d'in yad'aukota mana, ni mubar wannan maganar, india ce kome? Naji kace Seemah?"
Seemah dake tsaye tana jinsa bakin ciki yazo mata wuya, ita ake ciwa mutunci?
Haushi ya kamata ta juya ta kara juyawa nan taga wani rike da d'an karamin cup da alama ko lemo ko ruwa ko tea yake sha, ajiye trolly d'inta tai ta karasa gun mutumin, addu'ar ta d'aya Allah yasa tea ne mai zafi.
Tana isa gunsa tace sannu bawan Allah, ya kalleta ganin shigarta yasa yad'an had'iyi yawo, yace " mekikeso madan?"
Murmushi tai tace " please abinda kake sha nake so, "
Da sauri ya mik'a mata cup d'in ta kalli ciki, tea ne mai madara yaji milo sai dai abin haushi ba zafi sai dumi dai kawai, godiya tai ta juya tai gaba shikuma ya bita da kallo.
Seemah na isa kusa da mutumin, sai ta juya kai kamar bashi take kallo ba, shi kuma ya zak'e sai fad'a yake a waya sam bai kula da itaba, Seemah na matsowa ta saita takalminta ta takamai kafa da karfi, zai juyo ta kwaramai ruwan tea a cikin kayansa wajen farin coat d'in na ciki cikin tsananin mamaki Jalal ya d'ago d'an ganin wace 'yar duniyar ce wannan? Yana d'agowa Seema ta kwad'amai jacket d'inta, da karfi ya zare jacket d'in takard'ar hannunsa ta fad'i.
Cikin wani irin takaici yace " wani irin hauka ne wannan?"
Kallansa tai shima ya kalleta, tab'e baki tai tace " Sorry ban kula ba."
Tafad'a tare da juyawa, da karfi Jalal ya d'amko hannunta ta tsaya tare da d'an kara d'an taji zafin damkar, ta juyo tace " Malam wani irin rainin hankali ne wannan? Sakeni ko?"
Jalal yai wani mugun Murmushi yace " me da me kika ce? Bakiga ke abinda kika min ba?" Ya fad'a yana kallan kayan jikinsa ga kafarsa dake zafi.
Tace "sake ni ko? Kai meye dalilinka na tsaya a hanya? Ko nan gidanku ne dazaka tsaya kana gulmar mutane a waya. "
Jalal yazabura yace " Gulma? Ke tsaya in ma gulmar ce meye naki a ciki? Ohh shine kikamin haka da sanin ki kenan ko me?"
Seemah ta kalleshi tace sakeni ko? Jalal ya zare hannunshi tare da cewa " tambayar ki nake? Meke damunki? Kuma a wani dalilin zaki min haka? Banasan rainin hankali kuma akanki bazan jura ba, kawai kiyi godiya d'aya ke macece dabadan haka ba I don't know what will happen. "
Seemah ta makamai harara tace " ka kuma d'auko jakar ka taho mu tafi."
Jalal kam ranshi ya kai matuka gun b'aci yace " what?"
Seema tace "kanaso in kara fad'ane? Ko ba Seemah kazo d'aukaba?"
Jalal yai wani murmushi yanzu ya gane wai itace yace " ko ita nazo d'auka bata isa tasani ind'aukar mata jaka ba, d'an banaji nid'in mai aikinta ne." Yafad'a tare dayin gaba yace " kibiyoni zan jiraki a mota."
Seemah ta bishi da kallo tare da d'anyin kara tace " wannan wani irin mutum ne? Wayyo bakin ciki zai kasheni."
Yazatai? Haka taja jakarta, yana tsaye jikin mota takarasa fuskarnan a had'e duk da da glass a idanta.
Jalal ya shiga mota, itama ta karasa ta shiga baya ta zauna, lalai ba shakka sai ta gyarama mutumin nan zama, shi harya isa? Shid'in wa?
Tafiya suka fara bamaima kowa magana, shi haushinshi ma maidashi driver datai, Seemah kam waka tasa a wayarta ta kuma kuri volume, Jalal ya juyo tare da ciro earphone ya cilla mata yace " malama yi amfani da wannan banaso a cika min kunne."
Cillamai a binsa tai tace " sai kuma naga kamar ba a kanka nake ba, sannan ta kalli motar ganin abin bit da ta ba yaya habib a jikin madubin gabar motar yasa tace "sai kuma naga motar yayanace bana tunanin kanada iko da ita."
Jalal yai tsaki tare da juyawa, yanaji bai tab'a ganin mace 'yar rainin hankali irin wannan ba.
Seemah ta kauda kai a ranta tace wannan wani irjn mutum ne? Da alama kuma ba wani kud'i gareshi ba ganin coat d'in jikinsa bamai tsada bace.
Yana talaka shine zai raina mata hankali? Tafi karfin a wulakanta, ita datakesan taga kowa na mutuntata yana santa shine yau zata had'u da wannan wanda ko kwayar mutinci bataji yanada shi.
By *Ayusher Mohd*
© *NWA*
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
4⃣
Har suka isa Company d'in ba wanda yama wani magana a cikinsu, haushi duk ya cika Jalal aikuwa da yazo taka burki da karfi ya taka har sai dayasa Seema ta bugi kujarar gaba, cikin b'acin rai ta d'ago tare da dafa gun kamar tai kuka dan taji zafi.
Jalal ya juyo yace " Sorry bankula bane."
Ta tuna itama haka tace data mai tsiya a airport wato ramawa yai ko me? Juyawa tai ta kalli Company d'in, babban ne sosai duk an bishi da glass lekawa tai taga kamar mutane sun taro daga bakin kofar, ido ta kura nan ta hango yayanta, wani murmushin dad'i ta saki tanaso taga ana ji da ita, wannan tarbar da aka mata yasa taji zafin goshin ya tafi, kallan Jalal tai dake miko mata key, yace " gashi kyaba yayanki."
Ta kalleshi tace " bud'emin kofa."
Jalal ya kalleta cikin rashin fahimta yace " what did you just say? "
Ta murgud'a baki tace " bakaga an taro ana jirana ba? Ko so kake ka b'atama yaya na rai?"
Jalal yad'an yi wani dariya dakanaji kasan ta bakin ciki ce, yace " Servant d'inki ne ni?"
Zatai magana taga an bud'e mata kofa, cikin mamaki ta kalli waje, wani saurayi ne yace " Welcome Madam"
A hankali ta zuro takalminta mai mugun tsini sannan ta fito, sai dataje tsakiya yanda jalal zai jita haka kuma mutanen dake jiranta zasu jita, ta juyo cikin wani rainin hankali takalli jalal dake tsaye jikin mota, tace " Mr Pride d'an Allah jakata na manta nan kawomin."
Jalal ya kalleta tare da nuna kansa da hannu yace " Me?"
Ta d'aga kai tace" Sorry."
Wanda ya bud'e mata kofa yace " bari na anso miki madam.
Seemah tace " barshi shi nakeso ya kawomin."
Tana kainan ta cigaba da tafiya.
Jalal ya furzar da wata iska cikin takaici ya bud'e boot ya d'auko trolly d'in.
Seemah ta karasa gunsu yaya tana tafe tana murmushi, Habib na gani ta kusa zuwa ya karasa tare da rike hannuwanta duka biyu, tab'e baki tai tace "yaya haka ake oyoyon?"
Yace " Sorry Seemah ta bakiga da mutane bane? Kuma kinsan a kasa na suke kar su rainani."
Tace " nagane, oh ni yaya ashe zanganka?"
Dariya yai yace "mu wuce office d'ina muyi murnar ganin juna, ko?" Cikin zumud'i ta d'aga kai, nan suka fara tafiya, nan ta waiga ko zataga d'an rainin hankalin nan, sai dai ga mamakinta duk inda ta duba bayannan mamaki ya kamata, ina yaje? Jakarta ta hango a hanyar shiga, wato har ya ajiye ya tafi? Lebenta tad'an ciza tare dayin kwafa a hankali.
Sun isa mutane na ta gaisheta tana amsawa, farinciki ya cikata tanasan kulawa, har suka isa office d'in kowa ya gansu sai ya gaidasu, suna isa suka rungume juna, ta rik'e hannun Habib tace " Yaya I really miss you. "
Yace "nima kanwata, ni kad'ai nasan dad'in danakeji na ganinki."
Dariya tai tace " yaya sai yau nazo mahaifata, bakaji dad'in da nakeji ba dan ma d'an......." sai kuma tai shiro.
Habib yai dariya yace" badai daga isowar kanwata har an samu rikaken dazai b'ata mata rai ba? "
Ta turo baki tace " sosai ma kuwa yaya, kuma nad'au alwashin sai ya tsugunna ya nemi yafiyar abubuwan dayamin."
Dariya sosai Habib yai yace " namanta ashefa Seemah aka tab'o wacce bata hakuri in aka mata abu."
Tai dariya itama tace " yaya dad'i nakeji sosai."
Sun dad'e suna hira, har waya sukai dasu dad yakara tunamai ya kular masa da Seemah, suna gama waya Habib yace " kai dad ma sai a hankali, tun kafin kizo yake tunamin in kula dake."
Dariya tai tace " ai nasani dad duk yafi sona akanku, bayasan abu ya tab'ani."
Habib yace "muma duk muna sanki sosai, yanzu dai dolene in samarmiki wanda zai dunga kula dake a duk harkokin da zakiyi a nan kasar, amma kamar mutane nawa kikeso?"
Shiru tai can wani abu ya fad'o mata wani mik'ewa tai tare dayin tsalle, tace " kaii!!!!! Amma naji dad'i."
Kallanta Habib yai tare da tambayarta mene? Ta tsugunna agabanshi tace " yaya wani abu nakesan kataimakamin dashi."
Yace menene wannan? Seemah ta saki murmushi tace " akwai wanda nakesan yazama driver na kuma bodyguard d'ina."
Habib ya kalleta da mamaki yace " au yanzu daga shigowar ki gari har kinsan wani da kikeson ya kula dake?"
Tace " sosai kuwa yaya, kuma shid'in nan nakeso yad'inga min aiki."
Habib yace "ba matsala in dai har ba ma'aikaci bane."
Cikin shagwab'a tace " nidai ko ma'aikacin ne shi nakeso Yaya, in yaso sai a tsayar dashi in na koma sai ya koma aikinsan tunda ba dad'ewa zanyi ba."
Habib yace " dole a miki duk abinda kikeso Princess. "
Wani murmushi tasaki, harta hango tana sashi aiki yana mata....hahhh lalai zataci dariya.
***************************
Jalal kam yana kai jakarnan ya wuce department d'insu yanashiga, ya zauna a kujerarsa cikin b'acin rai, shugabansu nagun aiki ya shigo tare da cewa " Jalal bakai nagani yanzu ba? Rik'e da jakar kanwar Chairman? "
Wani takaici ya kamashi ya kasa magana, shugaban yasake cewa " kai amma kaji dad'i gwara daka kama kafarta, d'an ancemana Chairman d'in Company d'inan nasan kanwar nan tasa, kasani ko tamaka hanya ka zama mai office d'in kanka ba irin wannan ba na kusan mutane biyar?"
Jalal ya mik'e cikin tsananin bakin ciki da sauri yai waje tare da bugo kofar office d'in da karfi.
kama kafa? Kamar shi? Da iliminsa da komai? Ajiyar zuciya yai tare da kiran Abbansa, bayan sun gaisa ya tambayi jikin kanwar sa, Abba yace " jiki nanan yanda yake."
Sun d'anyi hira kafin suyi Sallama.
By *Ayusher Mohd*
© *NWA*
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
*NO*5⃣
_*This page is dedicated to you Beely Badaru*_😍😍
Sun fito rike da hannun juna, kana ganinsu kasan suna cikin tsananin farin ciki, suna tafe ana gaidasu, sai gulma da mutane sukeyi ganin abun banbarakwai,nan suka shiga motar Habib, suna baya driver na jansu.
Seemah takalleshi tace "yaya amma d'azu ba wannan bane yazo d'aukana?"taimaganar tana nuna drivern da ido, Habib ya kalli mai tukin sannan yace mata" yaje gida ne d'azu 'yarsa ce bataji dad'i ba."
Ta d'aga kai tare da tuno birkin da ya ja ta k'umu, kallan Habib tai tace " amma yaya wannan waye?"
Habib yace " bansani ba gaskiya."da sauri tace " yaya ban gane ba?"
Habib yace " Sagir nasa ya tura wani ya d'aukoki."turo baki tai cikin shagwab'a tace " au yaya kanwar taka zata dawo bama kasan waya tafi d'aukota ba?"
Ta juya kai tare da hard'e hannayenta, dariya yai yace " kanwata ayi hakuri ko sai na kira Dad ya bada hakuri a madadi na."
Har suka isa gida Habib na lallab'ata suna shiga daga gate tashiga kallen gidan, gida ne karami daidai saidai tsarin gidan yayi kyau sosai, suna parking wata had'ad'iyar mace ta fito da wata kuma sa'ar Seemah, suna tsaye daga jikin kofa suna murmushi, Seemah ta kallesu ta tabbatar matar yaya Habib ce dan taganta a hotuna, sai dai wace take sa'arta ce bata san ko wace ba.
A hankali suka karasa gun da sauri matar yayan ta karaso tare da rungume Seemah cikin tsananin farinciki tace " Kanwata sannu da zuwa, naji dad'in ganinki sosai."
Seemah ta saki murmushin dad'in taji dad'in yanda aka nuna mata so, yaran suka taho da gudu su biyu mace da namiji, Seemah ta rungumesu tace " Ra'is da Ra'isa sai yau naganku."
Sun dad'e kafin matar habib tace muje ciki kanwata.
Sun shiga ciki, nan sa'ar seemah taja jakar seemah tai ciki da ita, kallan matar yayanta tai tace " Aunty Farida amma kanwarki ce ko? Naga kama."
Daga mata kai tai tace " D'aukota nai d'an kiji dad'in hutun anan kinsan in akwai sa'arka kafi jin dad'i" dariya Seemah tai tace " naji dad'i Aunty amma ya sunanta?"
Jisukai ance " Aisha Mohd Rabi'u" da sauri Seemah ta juya tare da dariya tace " Aisha irin wannan fad'ar suna har ka ka?" Nan sukasa dariya dukansu.
Tayi sallah sannan aka jera abinci kala kala a dinning, Sun zauna Seemah tai murmushi tace " Auntyna duk wannan na welcome ne?" Habib yace " I Farida na sanki sosai seemah tanaso kizo, yanzu tunda kika samu zuwa kuwa ai ba dama...........
Sun gama cin Abinci suka shiga d'aki suna hira, duk da ba sabawa sukai ba amma Aisha na kok'arin janta da hira, itadai ba wani sakewa take ko jin dad'in hirar takeyi ba, tunanin cin fuskar da aka mata yau takeyi, aiya sanin rayuwarta sai dai ita tacima mutum mutunci badai ita a mata ba, tai shiru tana hango sanda ya kumeta a kujera, wai sorry?
Jitai Aisha ta tab'ata tace kinajina? Seemah tace " naga magrib ta kusa bari na shiga wanka, amma nikam garin nan sam ba sanyi."
Aisha ta kalleta da mamaki tace "sanyi kuwa, ke bakyaji?"
Seemah bata amsa mata ba ta shiga toilet, Aisha ta bita da kallo tace " sai a tambayi mutum kuma inya bada amsa sai ta shareshi" tsaki tai tace nifa bansan rainin hankali.
Seemah na fitowa bayan tayi sallah batare datama Aisha magana ba kawai ta fita daga d'akin.
Su Ra'is ta jiyo kamar suna wasa, hartaje zata shiga taji Yaya yace " kanwata?" Da sauri ta juyo tare da murmushi tace " yaya? Ashe kana nan?"
Alama yamata data karaso, dasauri taje inda yake, tare da cewa" yaya nima ina san irin kayansu Aunty Farida."
Cikin mamaki yace " Atamfa?" Tad'aga kai yace " ba matsala in yaso gobe sai kuje ke da ko Aisha ne."
Hannunshi ta rik'e cikin shagwab'a tace " ni da kai nakeso yaya." Tafad'a tare da turo baki.
Ya saki ajiyar zuciya yace " shikenan in yaso gobe ina tasowa daga gun aiki sai muje." Tace eh yayana.
Sun dad'e suna hira kafin Farida ta iso itama ta shiga aka cigaba dayi da ita.
Seemah ta mik'e zata tafi tace " yaya yaushe kuma zani gurun iyayen su mumy na da dad?"
Habib yai shiru, can yace " zan tambayi Dad."
Seemah ta kalleshi tace Ok
**************************
Seemah ta kwanta da niyyar bacci sai dai ta rasa dalilin dayasa ta kasa, tai tunanin hala canjin guri ne d'an tunda aka haifeta a can take.
Wayar Ammar ce ta shigo, da sauri ta d'aga yace " kin kasa bacci ko?" Tace " yaya shiyasa nake sanka dayawa, kasan ni sosai."
Cikin wani yanayi na tausayi yace " to yanzu ya za'ayi?" Tace "oho kasan yanda zakai kawai inyi bacci nidai."
Dariya yai sosai sannan yace bari na baki story, nan ya shiga bata labari hartai bacci jin shiru yasa ya kashe wayar tare da sakin wani murmushi shima ya kwanta.
*********************
Da safe Seemah sai 11 ta tashi, tana tashi tai wanka sannan tasa kaya ta sauko, su Ra'isa har sun tafi makaranta, sannan Aisha bata d'akin, a falo ta gansu suna hira, ta karasa tare da gaida Farida, cikin sakin fuska ta nuna mata dinning sannan tad'an harari Aisha, nan Aisha ta juyo tare da k'akaro murmushi tace " Seemah kin tashi? Aunty ta hanani cin abinci wai sai kin taso."
Cikin ko in kula Seemah tace " Aunty da kin barta ai ni nafisan cin abinci ni kad'ai indai har bada family's d'ina bane." Ba Aisha ba har farida taji haushin wannan maganar sai dai bata nuna ba.
Seemah kam ko a jikinta ta wuce dinning taci abinci,tana gamawa ta taso ta dawo falon tace " yaya na office ?" Farida tace eh, Aisha ta kalleta ta sannan tace " nima yanzu zan fita skul ina da lectures by 1 zanje da wuri d'an akwai abinda zanyin."
Seemah tad'an kauda kai ko meta tuna sai kuma ta juyo tace " nikam Aisha kin iya driving? " Aisha takalli farida tace " inadai koya." Seemah tace" mu fita tare inyaso sai ki ajiyeni a office da motar sai ki hau Taxi." Aisha ranta yakara b'aci amma ganin yanda farida tai yasa ta d'aure tace " towa zai dawo dake? " inada driver acan ai abinda Seemah tace kenen, Farida tace " gun Habib zaki? Memakwan ki zauna muyi hira?"
"Am sorry Aunty akwai abinda nakesan yine a can."
Nan ta mik'e.
Aisha ta bita da harara tace kamar in kifa mata mari nakeji wlh.
Farida tace " banasan haka Aisha ki rufan asiri wannan yarinya akanta Habib zai iya sakina."tana kai nan ta mik'e tare da mik'a mata key tace kuma kuyi a hankali kinga baki da licence.
*************************
Sun fito sun shiga mota,Seemah ta shiga baya, Aisha bakin ciki ya kamata sai dai ya zatai? sai da sukai d'an nisa Seemah tace " namanta phone d'ina a gida." Aisha tace mukoma ne?
Seemah tad'an kauda kai tace " mutafi kawai."
Sun kusa isa office zasu shiga kwana sam Aisha bata kula da wanda ke kokarin shigowa ba, da karfi ta taka burki, Seemah tad'an gwaru da kujera, cikin b'acin rai tace " Aisha meye hakan? " Cike da tsoro Aisha tace " Seema wani na kusa kad'ewa.........bata karasa maganar ba taji anyi knocking d'in glass d'in motar inda zake, cikin tsoro ta zuge, wanda aka kusa kad'ewa cikin had'e rai yace " muga licence d' inki?" Miyau ta had'iya tace " hmmm namanta da shi gida,"
Seemah dake jinsu sai dai tana tunanin wannan muryar, Aisha kam kallansa kawai takeyi, kwarjinshi ya hanata magana sosai, kirjinsa takalla, mai fad'in gaske da gani yana motsa jiki ganin yanda jikinsa yake da fad'i, jitai an katseta ance " in baki iya mota ba meye naki na ja? Ku mutane sai ku d'inga abu ba tunani." Da sauri Aisha tace yahakuri, cikin b'acin rai Seemah ta bud'e bayan motar tafito, idanunta in bai mata k'aryaba mutumin jiya ne, kuma ga mamakinta coat d'in nan ta jiya ce kawai dai an wanketa ne, Jalal ta kalleta sarai ya ganeta amma bai nuna mata ba ya kalli Aisha yace " you hav to be careful." Ya juya zai wuce.
Da karfi Seemah cikin takaicin yanda ya shareta tace " Kai driver?" Jalal ya juyo cikin b'acin rai sannan ya karaso inda take ya junata da ' yatsa yace " kisan me zaki d'inga fad'a niba drivernki bane kuma bana tunanin zan zama d'aya."
Seemah tai wani murmushi tace " ko zanyi doubling d'in albashinka?" Tafad'a cikin salon rainin hankali, Jalal haushi ya kamashi batare da ya amsa mata ba ya juya zai wuce, da sauri Seemah ta riko hannunsa tace " Who gave you permission to live? According to whom? "
Jalal ya kalleta tare da zare hannunshi yace " According to me." Yana kainan ya juya, da sauri Seemah ta sha gabanshi tace " malam magana fa nake, a ka'idata in ina magana dole ne a tsaya in gama kuma dole ne a ji, d'an haka ka wuce muje ka karasa dani Company d'in yayana." Jalal zaiyi magana yaga text ya shigo mai, shiru yai idanunsa suka kad'a sukai jaa, meya sami kanwar sa? Gashi daga office yake ko kud'i bai fito da shi ba, jiyai Seemah na cewa " Driver dakai nake magana wato kaji zancen doubling d'in kud'i shine ka kasa kagana ko?" Ta kalli Aisha dake tsaye tace bani key ki wuce skul d'in.
Aisha ta mik'a mata ita kuma ta mik'ama Jalal dake tsaye duk tunaninsa ya kule, kallan key d'in yai yace " meye hakan?" Tace " ka wuce muje ko?"
Jalal ya kalleta da alama sai ya gyara yarinyarnan, key d'in ya amsa yace " muje ko?" Murmushi tai tace " aikin kawai a ido kamar kud'i bazai rinjayeshi ba, dama ai hakane d'an adam inyaji kud'i?" Ta saki tsaki, Jalal na jinta yai kwafa tare da shiga mota, itama ta shiga baya.
Jalal ya fizge mota ya juya yai hanyar fita daga gari, Seemah ta kalleshi cikin mamaki tace " ina kuma zamu? Duk da ni ba ' yar garin bace amma nasani kwarai nisan company d'in bai kai haka ba."
Jalal ko kulata baiyi ba kawai gudu yakeyi tunaninshi d'aya meyasamu kanwarsa da har zainab ta turomai sako???????
Seemah kam ganin sun bar gari kuma gudu yakeyi yasa tsoro ya fara kamata, ta fara masifa, malam meye hakan? Me kake nufi dani? Ina kake k'okarin kaine?
Jalal bai kulata ba tafiyarsa kawai yake, Seemah ta shiga ihu, ta d'auka ko fyad'e zai mata ko wani abun, tunda ita batasan ana satar mutane ba, duk masifa da ihun datake Jalal bai kulata ba, gashi bata d'auko sayarta ba, a hankali ta shiga bashi hakuri ganin tsoro ya kamata da gaske Jalal yace " Sorry akwai inda zani ne,ba wani abun zan miki ba."
Cikin hawaye tace ina zanyarda dakai? Bansan gari ba kazo ka fita dani kawai kana gudu dani a titi, kayi hakuri in har haushi kaji nacema driver.
JALAL bai sake magana ba, itama tun tanayi har ta gaji ta takure a gefe har suka isa binin/gwari, Jalal ya karasa gidansu yai parking tare da rufeta a mota, ya wuce ciki, kuka take sosai itakam tasan yau karshen rayuwarta yazo.
BY *ÀYUSHER MÒHD*
🏌♀
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
No6⃣
Seemah duk tagama rud'ewa kafin a isa birnin/gwari har ta gaji da kuka tayi shiru, sai ajiyar zuciya take, jalal kam na isa lungun gidansu yai parking d'an mota bata shiga gun, ya juyo ya kalli Seemah kwarai tabashi tausayi, shikanshi baisan meyasa yamata haka ba, daurewa yai yace " Kid'an jirani kad'an."
Kafin tai magana ya fita tare da kulle motar tsoro yakara kamata mr zai jeyi? Jijiga kofar tashiga yi sai dai yariga ya kulleta.
Jalal kam da sauri ya karasa gida, Umma na zaune a barandar tayi shiru tare da zuba tagumi, Sallamar dataji ne yasa ta mik'e, Jalal ya shiga da sauru tare da rik'e hannunta yace " Umma ya jikin Zaheedan? Umma ta kalleshi tace " Jalal menene hakan? Ya akai ka tahu yay bayan kasan yau kanada aiki?wama yafad'ama bata da lafiya?"
Jalal bai maganaba kawai yazare hannunsa daga gun Umma yai hanyar d'akin kanwarsa, a kwance yaganta yanda dai take, ajiyar zuciya yai sannan ya rike hannunta idansa taf kwalla, bacci takeyi hakan yasa bayan yagama mata add'ua ya fito daga d'akin, Umma ya kalla yace " meya sameta umma? "
Umma ta kalleshi cike da tausayi tace " Jalal bafa wani abu bane, kawai d'azu ne ta shiga yin jijjiga, sai kuma kumfa data d'inga fitowa daga bakinta, amma ana kiran likita ya dubata, yace bakomai yana mata allura kuwa tadaina."
Ajiyar zuciya yai ya kallin hanyar toilet jin motsi, Zainab ce d'aure da zane sai hijab datasa da alama daga wanka take, kallanta yai, itama da sauri ta gaidashi, ya amsa sannan ya juyo ya kalli umma yace " zan wuce inada abinyi, sannan kicema Abba zan turo kud'in."
Umma ta kalleshi tace " to Jalal Allah ya tsare." Juyawa yai da sauri Zainab tace " yaya?" Juyowa yai batare da ya sake rai ba, tad'an matso, ganin haka yasa umma tai ciki.
Kanta a kasa cikin nutsuwa da hankali tace " Kayi hakuri yaya laifinane." Yace namefa?
Tad'ago a hankali tace " natasoka na fad'amaka Zaheeda batada lafiya."
Fuska yad'an saki kad'an yace " nagode sosai kuma inaso in wani abun ya faru ki d'inga fad'amin kamar yanda kikai yau."
Kai tad'aga tare da cewa " Allah ya tsare.
Juyawa yai yai waje da sauri ya koma mota, ga mamakinsa mutane ya gani a gun, cikin sauri ya karasa gun tare da tambayarsu lafiya? Kallamsa sukai suka kalli maccen dake cikin mota tanata bubuga glass, hakuri ya basu yace " batada lafiya ne asibiti zan kaita.
Jin haka yasa suka wuce tare da musu sallama.
Jalal ya shiga mota tare da kallanta, duk ta gama rikicewa, wani tausayinta ne ya kamashi, me ya kaishi yin haka, kasa magana yai kawai ya juya mota suka fara tafiya sunyi nisa sosai kafin Seema ta d'aure tace" har yanzu bamu iso inda kake shirin lalatamin rayuwar ba?" Kallanta yai ta glass ya d'auka tagama tsorata lalai yarinyarnan wato fitsara dai bazata daina ba, bai amsa mata ba hakan yasa ta shigaba, " kada kai tunanin zan tsorata akan wani banzan sharri dakake shirin yimin, sai dai ka makaro dan ni bana shakkar komai, sqi tausayinka danake, d'an in ka bari yayana ko mahaifina ya kamaka?" Tai ajiya zuciya tace "I don't think you will go away easily. "Tafad'a tare da yin kwafa.
Murmushi yai a ranshi yace " she is bold, wato ko tana tsoro bataso ta nuna?."
Seemah kam zuciyart fal take da tsoro, sai dai batason raini.
Sunyi nisa sosai d'an baifi saura 1hr su isa Abuja ba, mota tafara nuna musu danger, Jalal ya kalleta yarasa mai zaice ga ba kud'i a gunshi, ya d'aure yace " ba mai a motar, zaki iya ban aron kud'i?"
Kallanshi tai sannan tasa wata dariya, tace " What did you just said? " ran Jalal ya b'aci yace " ban fito da kud'i ba ga magrib ta kawo kai ko so kike muyi dare a hanya?"
Tsaki taja tace " wannan matsalarka ce kuma, ba dare ba mu kwana ma mana ni ina ruwana."
Haushi ya kamashi, ga motar tama fara kokarin mutuwa, gashi gun daji ne, parking yai a gefe sannan ya juyo ya kalleta sannan ya nunata da yatsa yace " don't you dare do that to me again, d'an ba abinda na tsana irin a min tsaki, bare ke mace macema yarinya."
Dariya tasake yi kad'an tace " in kuma na sake fa? Me zakamin?" Tafad'a tare da matse kafofinta dake d'an rawa.
Ya harareta yace" ko zaki gwada?" Ta murgud'a mai baki tace " oho kuma yau ina tausaya ma dan watan barin aikinka ya kama."
Jalal ya juya yana kallan titi ya zasuyi? Ganin zaman bazai mai amfani ba yasa ya fita tare da fara tsaida motocin da suke wucewa, sai dai abin haushi duk ba wanda ya tsaya kowa wucewa kawai yakeyi.
Seema dake zaune a mota ta makamai harara tace" kalleshi kamar na kwarai, kirjinsa takalla, da sauri tai tsaki tace "irin wad'an nan mutanen nafi tsana a rayuwa ta masu nuna su na Allah ne bayan kuma ba haka bane a ransu."
Jalal ganin abun yaki ci yaki cinyewa gashi magrib har tayi yasa ya dawo mota yai shiru, wayarsa ya d'aga wa zai kira to? Shi duk abokanansa ba wani abota bace ta kud da kud kowa in ya ganshi da yarinyarnan zarginsa zaiyi.
¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤
Habib kam da rana ya k'ira Farida d'an jin lafiyarta, itakam cike da mamaki tace " Seemah ai tun wajen 12 ta taho gunka office." cikin tsananin mamaki yace " Farida mai kike nufi da wannan zancen? Wani irin Seemah tazo? Bayan ni ban ganta ba? Kuma wama zai kawota? D'an nasan bata iya driving ba."
Tsoro yakama Farida tace '"tare suka fita da Aisha bari na kirata inji."
Da sauri Habib ya kashw wayar ya kara k'iran wayar Seemah datun dazu bata dauka ba.
Farida tak'ira Aisha itakam nan ta sanar da duk abinda ya faru.
Farida cikin tsoro ta kashe kafin takira Habib yasake k'iranta, yace " ya sukai?" Cikin tsoro ta shiga fad'amai abinda akai.
Yana gama ji ya kashe wayar tare da jawo coat d'inshi take lankaye, yasa ya fita da sauri, nemanta ya shigayi sai dai abin tambayar? Wanene wanda auka tafi taren? Itadai Aisha batasani ba bare kuma su Habib.
Nan aka sanar da Security's na Company d'in aka shiga nemanta, har police station aka sanar mawa, ganin abun yaki cinyewa yasa aka baza cigiya gidan radio da Tv.
Hmmmmmmm
●●●●●●●○●●●●●○●●●●●○
Jalal kam kansa ya dafe, can ya juyo ya kalli Seemah dake rik'e da ciki da alama yunwa takeji, shikanshi yunwa yakeji, fita yai daga motar ya rufeta yai d'an dajin, bishiyar mango yagani rigarsa ya cire ta sama ya hau kad'owa, ba laifi ya samo guda 5 sakosu yai a rigarsa ya koma mota, yana zuwa ya mika mata, ta kalleshi tare da hararsa tace " ce maka akai yunwa nake ji?" Kalanta yai yace " im ba yunwa kikeji ba ki barsu."
Yana gama fad'ar hakan ya bud'e mota ya fita, Seemah ta harareshi tare da jawo mango d'in nan ta shiga sha.
Shikam wayarsa ya d'auka ya k'ira Sagir, Sagir na d'agawa yace " Mutumin ina ka shiga?" Jalal yace " ba wannan ba da matsala fa, yarinyar nan fa na tare da ni."
Cikin rashin fahimta Sagir yace wacce? Jalal yace wace nad'auko jiya.
Cikin tsananin mamaki Sagir yace " What? Jalal meke faruwa? Dama kaine wanda kuka fita tare? Kasan yanda ake nemanta kuwa? Jalal in akasan kaine da......."
Katseshi Jalal yai yace " man mota ya kare inaso ka sanar azo a d'auketa ko kai kazo ka d'auketa, nan ya mai kwatance ya kashe wayar.
Sagir yabi wayar da kallo, bai tsaya wani tunani ba ya zari key. ......
Seemah kam sai datasha guda 4 tad'aga na karshen zata sha sai kuma ta kalli Jalal dake tsaye a waje gashi da alama sanyi yakeji yanda taga yana takurewa,zuge glass d'in motar tai tace " ungo na k'oshi? " kallanta yai sannan ya juya kai gefe kamar bai jita ba, tai tsaki tace " mutum sai rainin hankali,"
Komawa tai ta zauna tace oho cikin wa? Can kuma tace ba dai poison yasamin ba? Da sauri ta kalleshi sai kuma tace " ah ai kayan fruit ne" can kuma tace in yai injecting d'in mango d'in fa da poison? Sai kuma tace "kaiii yaushe har ya fita dashi, Can kuma tace wayyo in kuma ya shirya fa? Da sauri ta bud'e motar taje kusa da shi ta mik'amai mango d'in, ya kalleta tare da juya kai, kallansa tai tace " wato magani kasa min na guba ko?" Kallanta yai kamar ya? Ta kara mik'amai tace " sha in gani." Kansa ya kara juyawa sannan ya mik'a mata rigar coat d'insa takalleshi tare da kallan rigar, sai dayai d'an nisa kad'an yace " nafi karfin nasama mutum guba, sannan kisa rigar d' an na tsane inga mace da irin kayan nan tana tallar kanta."
Ha! ha! ha! What? Talla? Leb'enta ta tad'an ciza sannan ta kalli coat d'in.
Mota suka koma ba wanda yai magana can Seemah tace " wai anan kake tunanin zan kwana?" Jalal baiyi magana ba" tace namanta da jakata ne nima ban fito da kud'i ba, bai kulata ba, ganin haka yasa ta mik'amai coat d'insa tace "nima nafi karfin sa wannan rigar."
Baiyi magana ba ya fita ganin kamar mota na nufosu.
By *Ayusher Mohd*
© *NWA*
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *Ayusher Mohd*
No 7⃣
Seemah dake zaune a mota ta bishi da harara. Jalal kam yana ganin motar har tazo kusa dasu ta tsaya, Sagir da sauri ya bud'e motar yazo gun Jalal yace " Jalal tana ina?" Kallansa yai sannan ya kalli motar hakan ya sa Sagir yagane tana motar kenan, da sauri yakarasa motar ya bud'e baya tare da kallanta, ba tantama itace da sauri ya gaida ita, ita kanta kallansa take da mamaki ta amsa tare da tambayar " kai ma accomplice ne?"
Da sauri Sagir yace " a'a Ranki ya dad'e, yanzu ya k'irani na taho, amma ya akai haka?"
Kallansa tai sannan tace " kai waye da zakamin wannan tambayar?" Sagir yace " baki gane ni ba? Secretary d'in yallab'ai ne."
Kallansa tai tare da kauda kai gefe tace " maidani gida."
Da sauri Sagir yace " to ranki ya dad'e yanzu ma kuwa."
Fitowa tai nan taga Jalal a tsaye, ta harareshi tare da kauda kai gefe, Sagir ya kalli Jalal yace mutafi.
Jalal ya kalleshi yace ina? Sagir yace gida mana.
Kallan Seemah yai yace " so kake laifina ya shafeka? Na tab'a 'yar gwal kana tunanin zan bari laifina ya sha feka?"
Sagir yace to yaza'ayi Jalal?
A ranta ta na nata sunan *JALAL* *JALAL* *JALAL*
Jala yace " manka za muyi sharing a motar in yaso sai in maidata da kaina."
Sagir yai shiru amma shikam yasan tabbas da matsala, in har Habib yagansu bayaji Jalal zai tsira da aikinsa.
Seemah ta kalleshi tace " nidai ka barni na tafi, banasan tafiya da kai sai dai in kuma wani abun kake shirin yi min."
Jala ya watsa mata wani kallo yace " ni na ba kaina makulin motarki? Ko kuwa kidnapping d'inki nai? A iya sanina ke da kanki kika shiga mota kika kuma bani makulli, so I don't think kinada hujjar da zaki yanke hukunci akan wannan maganar."
Seemah wani kululun bak'inciki ya kamata ta bugamai wani kallo, wani k'arin bak'incikin kuma ko kallanta baiyi ba magana ma yake da Sagir, jitai kamar tasa ihu d'an bakin ciki.
Shikam sun sa tiyo sun d'an zuk'i man motar Sagir suna gamawa Jalal ya kalli Seemah yace wuce muje ko? Takalleshi tace "in naki shiga fa?" Jalal ya kalleta yace "ko zaki gwada ne kiga abinda zai biyo baya?"
Sagir ya kalli Jalal yace "Jalal ka d'inga hakuri d'an Allah."
Sannan ya kalli Seemah yace " kiyi hakuri ranki ya dad'e haka yake hakuri muke dashi muma."
Jalal ya kalleshi yace " Sagir banaso karkasa yarinya karama ta rainani." Yanakainan ya juya sai dayaje wajen motar yace kizo mu tafi dare na yi.
Sagir ya kalleta yace " kiyi hakuri Madam haka yake, a hak bazaki gane ba amma Jalal mutum ne nagari sosai." Kallansa tai ta tab'a baki wayaga na gari, ju yawatai itama takarasa motar, ta bud'e ta shiga baya.
Jalal ya tada mota ya hau kan titi, sunyi nisa sosai ba wanda yace komai, can Seemah ta d'aure tace " dama d'an kawai ka ci mutuncina ka jani a motar? Ko d'an na cemaka driver?" Jalal yai shiru can yace " tambaya kike?"
Haushi ya kamata tace " ba tambaya nake ba, ina dai tausaya maka ne na shirin dakai ya ruguje."
" Bana tunanin yarinya dake harkin kai matsayin dazaki rugujemin shirina." Ya fad'a yana kallan titi.
Tad'an matso da kanta jikin kujera sannan tace "ina tausaya maka abin da zai faru dakai." Jalal yad' an waigo kad'an yace " bana tunanin kinkai shekaru 20 in case in ma kinkai bana tunanin kin wuce, kinga kuwa baki kai lokacin tausaya ma wani ba sai dai ke atausaya miki."
Turo baki tai kamar tai kuka cikin shagwab'a tace " Wlh kacigaba da abinda kakemin, karkuma kai tunanin tsoro nake ji."
Baisan sanda yad'anyi murmushi ba yace " da alama ke mammah girl ce."
Tanajin haka tai shiru, idanunta suka cika da kwalla, Jalal jin shiru yasa ya cigaba da tuk'insa, anfi minti 5 da maganar jiyai tace " Banda mahaifiya ai, ban ma santa ba zance." Itakanta batasan meyasata fad'amai ba d'an a zahiri ko 'yan skul d'insu basu sani ba.
Shiru yai jikinsa yai sanyi, tausayinta yakamashi da kuma maganar dayai, ya rasa mai zaici, shikanshi mamakin kanshi yai dayaji yace " Bakomai ita dama rayuwa haka take, mutum baya samin komai, Allah yajikanta."
Kallansa tai idanunta taf da kwalla, sun shiga garin Abuja ya kalleta ta madubi yace " kinsan gidan?" tace " bazan gane ba gaskiya ban tab'a zuwa kasar nan ba sai jiya."
Juya kai yai yace " bana tunanin na tambayeki ko kin tab'a zuwa."
Tace " What? Kai wai wani irin mutum ne da ba'a iya maganar mutunci dashi?."
Jalal bai amsa mata ba ya d'aga waya ya kira Sagir nan yamai kwatance, sun kusa isa gidan Jalal ya kalleta ta madubi a ranshi yace da alama bata tab'a shan wahala irin ta yau ba, dan yaga harta fuskarta ta canza.
Ajiyar zuciya yai, shi kanshi yasan yayi laifi, Seemah ce ta katseshi da cewa dafatan ka fahimci kwatancen na gaji da wannan zirga_zirgan.
Jalal ya kalleta yace " to ko ke zaki zo ki jamu?" Tace ni driver ce? In fact ni ko mota ban tab'a tunanin koya ba."
Jalal yace " karki kuskura kisa a ranki wai d'an na ja ki a mota kina baya yana nufin nid'in driver d'inkine, sai dai hakan na nufin banasan zama guri d'aya......."
Katseshi tai tare da murgud'a baki tace " whatever banasan jin komai nidai ka kaini gida."
Jalal yad'anyi murmushi daga gefe sannan yai kwana, suna zuwa kofar gidan yai parking tare da juyowa ya mik'a mata key, ta amsa tare da kallan gidan, jitai yace " badai bakisan inda kika kwana ba?" Hararsa tai tare da d'an murgud'a baki kad'an tace " ce maka akai ban gane ba?"
Kofa ya bud'e batare da ya amsa mata ba ya juya ya fara tafiya, da sauri ta fito tare da cewa *JAL* cike da mamaki ya juyo jal? Meke nan? Daga inda yake yace " Jal? Da wa kike?"
Cikin wata murya tace " bazan iya fad'an sunan duka ba yamin yawa."
Murmushi yai kad'an yace " waya fad'a miki sunana? Kuma ni sunana in baza'a fad'a duka ba banaji zan iya amsawa."
Tad'an tab'e baki tace " ka ce baka da kud'i dame zaka karasa gida to?"
Yace " Don't tell me u are worried about me? "
Tace " wa? Ni? Allah ya sauwake."
Juyawa yai yacigaba da tafiya kawai yasamu kansa da murmushi.
Itama murmushin tai sannan tai knocking. ........
♧♧♧♧♧♧♧♧♧
Habib kam yakasa zaune ya kasa tsaye ko ruwa ya kasa sha masifa kuwa farida harta gaji itada Aisha, kowa yai jugum banda waya ba abinda yakeyi.
Mai gadi na bud'ewa cikin mamaki ya kalleta yace " kamar Hajiya ko?"
Seemah tace nice, nan ya bud'e mata yana cewa ina kika shiga Hajiya sai cigiyarki ake.
Bata amsa mai ba tai cikin gida, tana shiga ta murd'a kofar a hankali, tare da turawa, dukansu sun kurama kofar ido suna san suga wanene, ga mamakinsu Seemah ce ta shigo, da gudu Habib ya karasa cikin tsananin mamaki, yana zuwa ya rungumeta, ya shiga tambayarta Seemah ina kika shiga? Kinsan yanayin da kika sani? D'agowa yai ya kalleta yaganta tana lumshe ido, yace Seema are u alright?
Kafin ya kara cewa wani abun yaga tayi baya luuu ta fad'i.
Farida ta taho da gudu nan suka shiga jijigata, Habib yace a k'ira likita.
Sun kaita d'akin sun kwantar, Aisha taji wayar Seemah na kara, karasawa tai ta d'au wayar gani tai ansa *Special Bros* d'agawa tai jitai ance "Seemah na wato kinzo gun yaya kin manta dani ko?"
Aisha a hankali tace ba ita bace, Ammar da mamaki yace " waye? Ina Seeman?"
Aisha tace "hmm ta shiga toilet zan fad'a mata inta fito."
Yace alright yana kai nan ya kashe wayar.
Aisha tabi wayar da kallo ba shakka anaji da yarinyarnan kod'an yanda taga yaya Habib yayi.
By *AYUSHER MOHD*
© *NWA*
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
NO 9⃣
Waya ta d'aga ta k'ira Ammar yana d'agawa cikin shagwab'a tace "yaya!!!!"
Cikin rud'ewa ya tambayeta " Seemah menene? Waya tab'amin ke?"
Takara shagwab'ewa tace " yaya an wulakantani yau."
" waya isa ya wulakanta min ke kanwata? Banaji an haifeshi, kinaso yayanki yazo yad'au hukunci?"
Ammar yai maganar cikin b'acin rai.
Seemah tasa dariya tace " Kai yaya ni kainan inajin dad'in kasancewa kanwarka, amma a yau inaji amai uzuri amma in har ya sake zan fad'ama kad'au min mataki."
Shima dariyar yai yace " kin hucce?" D'aga kai tai kamar yana ganinta tace " sosai ma." Hira sukai tayi sai dayaga ta ware sosai sannan sukai sallama.
Murmushi tabi wayar dashi sannan ta koma ta zauna a kan kujera.
Seemah kwafa tai sannan ta leko ta k'ira Sagir, tace zo kasamin number office d'insu abokinka, ta fad'a tana nuna landline na office d'in, Sagir ya karaso ya nuna mata tace tnx, yana fita ta kira number.
Manager d'insu ya d'aga tare da tambaya, Seemah tace " daga office d'in chairman ne, inaso a turomin Jalal yanzun nan." Tana kainan ta kashe.
Cike da mamaki manager d'in yabi wayar da kallo, Jalal?
Jalal kam ya dad'e agun kafin ya d'aure ya sauko, sai dai yana zuwa office d'insu Manager d'in yace " kaikuma ina ka shiga?" Jalal yace na d'an fita ne,
"Kayi sauri ana nemanka a office d'in Chairman." Manager d'in yai maganar yana kallansa.
Gaban Jalal ne ya fad'i sai dai bai bari Manager d'in ya gane ba kawai ya juya ya fita, yana zuwa ya bude kofar tare da kallan Sagir, yace " Ana k'irana ko?" Sagir yace bari in sanar sai ka shiga.
Nan ya mik'e daga mazauninshi yai knocking office d'in, Seemah ta bada izini ya shiga ya sanar mata yazo, tace ya shigo, nan ya juya ya fita.
Kallan Jalal yai yace " ka shiga."
A hankali Jalal ya karasa yai knocking ta bashi izini ya shiga da sallama, Seemah na tsaye jikin window tana kallan waje kallanta yai da mamaki yace " ke kika kirani?" Juyowa tai tare da yin murmushi tace " ayya shikenan ma je ka." Jalal da mamaki ya kalleta bangane ba.
Kallansa tai tace " nace ka tafi na fasa." Cikin b'acin rai ya fito tare da bugo kofar da karfi, ko Sagir bai kallaba ya juya ya fita, yana koma wa office d'insu ya sake had'uwa da Manager a kofar office d'in yace " Jalal kayi sauri Madam tace ka koma."
Jalal ya kalleshi yace " daga gunta fa nake tace in komo." Yace " kayi hakuri ka koma tace lalai kaje yanzu."
Jalal cikin mugun takaici ya koma, yana zuwa ko Sagir bai jira ya neman mai izini ba ya bud'e kofar ya shiga, tana tsaye jikin fridge d'in office d'in tana shan ruwa, ta juyo tace ka koma na fasa, Jalal ya kalleta wani takaici ya kamashi karasawa kusa da ita tare da fizge jarkar ya ajiye sannan cikin b'acin rai ya kalleta yace " am I a joke?"
Kallansa tai tace " bakaga ruwa nake sha ba?"
Jalal ya nunata da yatsa ya kara matsowa kusa da ita yace " bazan d'auki wannan rainin hankalin ba d'an haka don't you dare repeat that to me." Yana gamawa ya juya zai fita.
Hannunshi ta kamo tace " ka manta ni kanwar mai Company d'in ce?"
Yace " if u need respect then act right." Sannan ya juyo yace " Sakeni in tafi ko?"
Tace " waya baka damar tafiya?" Tafad'a tana hararsa.
Ya juya tare da fizge hannunsa sannan yace " ni naba kaina."
Yana kainan ya fita da sauri, kallansa tai da mamaki sai ta sami kanta da sakin wani sansanyar murmushi, sai kuma can tace "Not Bad."
Nikam Ayusher nace mefa?
Jalal ya fito cikin takaici ya karasa office d'insu sai da abinda yakara d'aure mai kai Manager ya kara gani a tsaye a kofar, yace lafiya? Manager yace " ance in kaika da kaina, d'an haka wuce muje." Jalal ya kalleshi yace ina?
Hannunsa manager d'in ya kama suka fara tafiya, Jalal ya kwace hannunsa yace itace dai? A hankali Manager ya d'aga kansa alamar eh, Jalal yace zanje da kaina, nan ya fara tafiya yagama shirya yawan rashin mutuncin dazai kwara mata.
Da karfi ya bud'e kofar ko sallama baiyi ba, sai dai me? Habib ya gani zaune a kujerar sa Seemah na tsaye tana waya jikinsa ne yai sanyi a hankali yace "am sorry."
Habib ya kalli Seemah dake ta shagwab'a a waya, Jalal kam takaicin yanda take shagwab'a yakeyi amma da alama ko saurayinta ne, sai dai jin tace " Dad sai anjima." Yasa ya d'ago, Dad?
Maganar Habib ce ta katseshi dayace " Seemah wannan ne?"
Seemah ta kalli Jalal tace eh yaya please.
Habib ya kalleshi yace " d'an Allah so nake ka taimakamin, kanwata ce kesan zuwa yin shopping to nikuma inada aikin yi shine tace tanaso kad'an kaita."
Jalal da mamaki ya kalli Seemah ya mata kallan jiya baki daddara ba ko? Baki ta murgud'amai tace " ni yaya dama shi ka bani a matsayin driver na." Wani kallo da Jalal ya watsa mata ba ita ba har Habib sai dayasha jinin jikinsa, ganin yanda ya kafeta da ido yasa ta had'iyi wani yawo tace" Wasa nakeyi maida wukar."
Habib ya d'an kakaro dariya yace " karka damu akwaita da tsokana, she is just joking."
Sai a lokacin Jalal yad'auke idanunsa, sannan yace " yau ne kad'ai zan kaita ko?"
Habib ya d'aga kai yace yau ne kad'ai, in ka kaita ka karasa da ita gida, Jalal yace to sannan ya kalleta yace " muje ko Madam?"
Seemah ta anshi key sannan ta fito.
Sunje shiga mota Seemah harta bud'e baya Jalal ya sa hannu ya fizgota ya sata a gaba sannan ya rufe shima ya shiga, kallansa tai tace " meye hakan kuma?"
Jalal yace tambaya kike? Batace komak ba kawai ta juya kanta tana kallan window, Jalal ya tada mota sun d'an fara tafiya tace " wato bazaka bani hakuri ba ko?"
Jalal ya kalleta yace " laifin menai dazan baki hakuri? Bakya tunanin ke zaki bani?"
Juyowa tai tace " kamanta me kamin ne?"
Jalal ya saki murmushi yace " au duk wannan abun da kikemin so kike in baki hakuri?"
Ta d'an turo baki tace " eh mana, kuma inaso kabani yanzu."
Jalal yace " lalai kin da aiki a gabanki."
Tace sai in taka burk'i yanzu, ko in bud'e kofar motar, uhmmm ko insa ihu in ma sharri.
Ga mamakinta dariya taga Jalal yasa abinda bata tab'a gani ba, dariya sosai yai, sannan ya kalleta yace ko zaki gwada?
Ganin yanda take kallansa yace " kallan fa?"
Ta kifta ido tace " dama kana dariya?" Da sauri ya had'e rai yace " baki gani daidai bane, ba dariya nai ba."
Seemah tai murmushi tace "yau naga side d'inka kala kala, d'azu ka makamin kallo kamar zaka dakeni yanzu kuma dariya?"
Jalal ya had'e rai ya cigaba da tuk'insa, Seemah ma shiru tai sai dai murmushi bai bar fuskarta ba......
© *NWA*
🏌♀
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
No. 1⃣2⃣
Habib kam sam jiyai gidan ya isheshi hakan yasa yace zasu wuce, sun musu sallama sannan suka fito, harsun zauna a mota yaga yanda idan Seemah ya kad'a yai jaa kawai ya bud'e motar ya koma ciki, suna zaune sunyi tagume sallamar Habib ne ya katsesu, da sauri suka mik'e suka fito.
Habib yace " har na shiga mota naga kamar ya kamata inji menene dalilinku na k'in sakema Seemah?ko d'an bata tab'a zuwa ba sai yau?"
Kawo yai saurin cewa shine dalili yaza'ayi ace sai yau zata tab'a zuwa gaidamu?
Kallansa Habib yai bayajin zuciyarsa ta gamsu da maganar saidai tunda sunce hakan yace " ayya amma kawo kasan ba laifinta bane Dad ne yake hanata zuwa."
Hajiya tace to jeka ku tafi ko ka manta kanada aiki ne?
Nan Habib ya juyo ya shiga mota, dad'insa d'aya yana shiga yaganta tana waya da Ammar sai dariya take, hakan yasashi dariya, sun fara tafiya shima yanata janta da hira, bayan sun shiga Abuja ne ta kalleshi tace "yaya muje Company sai anjima sai in koma gida."
Yace "shikenan dama yau driver d'inki zaizo sai yazo ya d'aukeki"
Murmushi tasaki a ranta tace Jal we will meet again.
Suna isa Company d'in Sagir yazo ya sanar ma habib akwai meeting dazasuyi yanzu, nan ya kalli Seemah yace kije office d'ina tace to nan ya juya a hankali tace Sagir? Juyowa yai yazo kusa da ita, tace " ina Abokink?"
Cike da mamaki ya kalleta? Yace wa kenan?
kallansa tai batare datace komai ba hakan yasa yace Jalal? Ta had'e rai tace " yana ina? D'an yau sai na zabgamai rashin mutunci.
Kai ya jinjina yace hmm yana office a k'irashi ne?, tad'an juya kai tace inane office d'in ku ba meeting zaku shiga ba? Nuna min kawai.
Yace a third floor yake kina shiga daga hagu zakiga Department d'insu, tace ok ta juya tai gaba, Sagir yace " Yau kuma wani fad'an za'ayi?"
Elevator ta hau ganin ba kowa yasa tad'an fito da madubi daga jakarta tad'an duba fuskarta murmushi tai sannan tad'an sa janbaki kad'an tace " yau sai ka kasa ganeni."
Tana isa tai inda akace tare da murd'a kofar tai sallama, office ne babba sai dai kowa da desk d'inshi sai gurin da aka kewaye ma manager, sunajin sallamar suka juyo gaba d'aya suka zuba mata ido, kallansu ta shiga yi sai dai bataga Jalal ba, karasawa tai ciki tace " Jalal nake nema?" Wani ya matso kusa da ita yace ga desk d'inshi nan ya fita inaji ko kasa yaje submitting d'in proposal.
Desk d'in ta kalla sannan tace bari na jirashi, karasawa tai ta zauna a inda yake zama tare da bud'e takardun dake gun, kowa sai kallanta yakeyi, manager d'inne ya fito ganin Seemah yasa ya karasa da sauri yace " Ranki ya dad'e me kikeso? Ai da baki zo ba kin turo kawai."
Had'e rai tai tace " inasan ganin Jalal ne d'an yau banajin zan iya kyaleshi."
Yawo ya had'iya aransa yace Jalal me kayi?
A fili yace " ayi hakuri Madam......."
Katseshi tai tace " asa a k'irashi yanzun nan."
Nan ya fita da sauri yai waje, Seemah ta kalli ragowar tace " kucigaba da aikinku." Wata mace ce tad'an matso kusa da ita tace " laifin me ya mik'i? Naji dad'i da kikace zaki hukuntashi dama haushi yake bani, farkon zuwa na ina bala'in san mutumin nan har abinci nake zama a gida in had'omai sai dai duk wannan wahalar danake bazai ci abincin ba kuma baya kulani, rannan ma ba ka ra yacemin bayasona."
Seemah ta saki dariya tace " ke meya kaiki san wanda baya sanki? Ai kece mak kuskuren ba wani ba."
Haushi ya kama matar ta juya ta zauna a ranta tace " Allah yasa kema kiyayyace ba so kike masa ba."
☆☆☆☆☆☆☆☆☆
Jalal ne ya shigo da sauri yana neman me nansa, kallan kowa ya shiga yi yaga suna nunamai desk d'insa karasawa yai desk d'in d'an baya gano kowaye tunda ta juya kujerar baya tana game, jin sallamar Jalal yasa ta kashe game d'in tana jiran k'arasowarsa.
Jala mamaki yake wani rik'eken ne wannan? yana zuwa gun yace " excuse me"
Seemah ta juyo da kujerar ta cik'e da mamaki ya kalleta yace " You?" Gira yad'agamai sannan ta mik'e tare da had'e rai tace " Follow me."
Tana kainan tai waje, hartaje kofa taga bashi da niyyar tahowa haushi ya kamata ta juyo tazo inda yake cikin magana mai rad'a tace " so kake in jaka da kaina?"
Yace muje.
Sun fito ta kalleshi tace " kar mutane suganmu ka sameni a gun jiya rooftop, tana kainan ta wuce.
Iska ya furzar yace " Ahh wannan tagama rainani, me? In sameki a ina?" Sai a lokacin ma yabi bayanta da kallo, atamfa? Shi da sam bai kula bama, daga kanta yafara kallanta har kan takalmin datasa mai tsini sosai, tayi kyau sosai, wani b'angare na zuciyarsa ya fad'a da sauri ya girgiza kai sannan ya wuce shima.
Ta rigashi isa hakan yasa ta karasan can bango tana kallan kasan titi yanda motoci suke wucewa, Jalal ne ya bud'e kofar tare da kallan inda take tsaye murmushi yai sannan ya karasa gun, gefenta kad'an yaje ya tsaya, batare da ta kalleshi ba tace " a haka mutum sai yaga kamar kowa na duniya yana cikin kwanciyar hankali."
Kallanta yai sannan ya kalli kasa yace " a binda mutum yake gani daga nesa dama haka yake ai sai kiga kamar kowa yana walwala, amma me ya kawo ki office d'inmu?"
Juyowa tai ta kalleshi sannan tace " ya kagan ni?"
Kallanta yai kad'an sannan yad'auke kai yace " bangane yaran ba?"
Leb'enta tad'an ciza sannan tace " kalleni da kyau ka gani baka ga komai ba?"
" Banga komai ba, akwai abinda yakamata in gani ne?" Ya fad'a yana kallanta.
Haushi ya kamata ta juya cikin fishi zata wuce tsinin takalminta ne ya shige d'an rami tai wala wala zata fad'i da sauri yasa hannu ya tarbota kallan juna suka fara, Seemah kam zuciyarya sai duka take, kallanta yai sannan yace " da saninki ko? So kike in tare ki."
Harararshi tai tace " nina saka?" Baya yai da ita kamar zai saketa, kara tad'an saki yace " au ashe kina tsoro."
Cikin shagwab'a tace " da yarda ni zakai?"
Kai ya rangwab'ar yace " sai in yadda ke indai baki fad'amin me zan gani ba."
Hannu tasa ta rufe idanta a hankali tace bakaga kayan danasa ba?
D'agota yai ta tsaya daidai sannan ya juya ya kalli titi yace " au sai yanzu na kula ai."
Haushi ya kamata tace " hakama zakace?"
" a ina kika ari kaya? D'an a yadda kika nuna baki da wani kayan hausawa sannan jiya kika siyo naki nasan a k'ala baza........"
Zuciya ta kawo mata wuya jakarta ta d'aga ta kwad'a mai a kafa, tace " kace ka gani ko yamin kyau shine bazaka iya ba? Gwara ka cimin mutunci?"
Juyowa yai yace zan iya tafiya?
Haushi yakara kamata tace kabar kasar ma,
Juyowa yai zai tafi sai dayaje kusada kofar fita ya juyo yace " kayan kasarmu sunfi miki kyau."
Yana kainan ya fita, kallan kofar tai sannan tai murmushi tace " kafad'i hakan tun d'azu shine bazaka iya ba?" Baki ta murgud'a sannan ta juya ta cigaba da kallan titi tana kallo tana murmushi. .....
© *NWA*
🏌♀
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
NO8⃣
Likita yazo ya dubata, wahalace kawai da yunwa suka had'un mata nan ya bata magani ya tafi, Habib ya kalli wayarsa dake ka ra yai shiru ya rasa mai zaice d'an tun rana Dad ke k'iransa akan yaji Seemah shiru, yanason lale abashi 'yarsa suyi magana.
Kallanta yai sannan ya kalli wayar, jiyai ance " Dad ne ko?" Habib ya kalli Seemah yace " eh" hannu ta mik'amai ya bata wayar daga kwance ta d'aga wayar tare da cewa " Dad d'ina."
Dad yace " Princess ina kika shiga? Bayan tun rama nake nemanki, sannan ya naji muryarki haka?"
Da sauri tace " Dad bacci fa nakeyi yaya ya tasheni."
" Ayya kiyi hak'uri ban sani ba, tunda naji muryarki yanzu mayi waya da safe."
Dad ya fad'a cike da namaki ganin seemah ba baccin wuri takeyi ba.
Seemah tace "to Dad nyt, love u." Tana kai nan ta kashe wayar tare da sakin ajiyar zuciya.
Habib ya kalleta yace " Bari a kawo miki abinci." Kafin ya mik'e Farida ta shigo d'auke ta tire ta ajiye kusa da Seemah tace " Seemah tashi kid'an ci wani abun."
Habib ya taimaka mata ta zauna, Farida ta zuba mata nan tafara ci, tad'anci dayawa kafin tace ta koshi, Farida ta zuba mata juice ta sha sannan tajingina.
Habib ya kalleta yace " Seemah meta faru wai?ance da wani kuka tafi, waye shi?"
Tai ajiyar zuciya tace
" Yaya irin wannan tambaya?"
Habib ya had'e rai sosai yace " ki fad'amin wanene in ba haka ba indai nai bincike da kaina, banajin zan barshi haka."
Shiru tai can tace " nima ban sanshi ba yaya, kawai dai da Aisha takusan kad'ashi ne na fita bashi hakuri sai yake cemin kamar jiya ya ganni a Company d'in dayake aiki, nikuma ganin a Company d'inka yake aiki yasa nace ya karasa dani shine yai wani gurin dani."
Habin ya mik'e cikin b'acin rai yace " ki kwanta ki huta gobe karfe 10 zansa a d'aukoki ki duba kaf ma'aikatan Company d'in ki nuna min shi."
Gaban Seemah ya fad'i a hankali tace to yaya.
Nan ya juya ya fita ta bishi da kallo, itakam menene nata na kare Jal? Meyasa batasan asan shine?
Mik'ewa tai ta shiga toilet tai alwalata dawo ta tada Sallah, bayan ta idar ne ta mik'e ta hau gado, Aisha ce ta kalleta tace Sannu Seemah, sannan d'azu Special Bros ya k'iraki, da sauri ta d'au waya ganin missed call 40 ta duba duk yayinta 3 sun nemeta da kuma dad sai dai na yaya habib yafi yawa tunda shi kad'ai yasan meke faruwa, layin Ammar ta d'anna, ringing 2 yad'aga ta saki murmushi tare da cewa" Oppa ya? Da alama yau kayi missing d'in kanwarka dayawa."
Murmushi yai yace " Seemah kinsan dai bana jure rashinki ko? Sanda na tafi South Korea wani Conference sau nawa muke waya dake?"
Dariya tai tace " Kai yaya wayar fa damukeyi yawanci ni nafi nemanka."
"Seemah ni dai banasan haka daga yau na k'ayade mana waya sau 8 a rana, ni zan k'ira sau biyar ke ki k'ira sau 3 duk wanda yai missing k'ira ko d'auka zai biya kud'i."
Dariya sosai tayi tace " shikenan yaya deal?" Yace deal.
Sun dad'e suna waya Aisha dake kwance tanata mamaki wannan dabad'an yayanta bane lalai sai ta ce su masoyane.
《《《《《《《《《《《《
Seemah ta kwanta bacci tad'ade kafin tai baccin sam ta rasa meke damunta, sai dai 1 thing is cleared sai tai ta hango Jalal sanda yana tsaye a waje ita kuma tana mota, bargo taja ta rufe kanta gaba d'aya sai dai duk da haka ta sake ganinshi yaye bargon tai sannan ta d'an sa ihu kad'an tace " Frustration! !!!!! Yau kuma meke damuna? Can tace nama gane, tsabar tsanar dana mai ne."
Tadad'e bata bacci ba sai can ya sace ta.
♢♢♢♢♢♢♢♢♢
9 ta tashi tai wanka tasa kayanta, yau doguwa ce rigar sai dai ta kanti ce mai bin jiki ta d'auko har zata fito sai kuma ta koma ta cire ta kara duba akwatinta, riga da wando ta d'auko na pakistan da yaya junaid ya siyo mata dayaje india tasa tare da yafa mayafin, tayi kyau sosai.
Ta sauko kasa ta taradda Aunty Farida kad'ai nan tai breakfast ko tambayar Aisha batai ba, kafin ta gama har driver yazo, Nan sukai sallama da Farida ta fita.
Suna isa company d'in ta sauko a hankali, Habib tagani a tsaye mamaki ya kamata a hankali ta karasa, sai dai abinda yabata mamaki tun daga cikin bakin kofar company d'in mutane suka jeru, ajiyar zuciya gai takarasa gun habib, yace " muje ki duba ga kananan ma'aikata anan manyan kuma na inda muke meeting." kallan yaya tai a hankali tace to.
Sun fara dubawa tana tafe yana binta a baya, sai kallan mutane takeyi, kowa tagani tace bashi bane, sai da suka zo kusan karshe, idanunsu ya had'u da Jalal, kallan juna sukai ta kuramai ido mamakinta babu alamar tsoro a idanunsa, jitai Habib yace " Shine?" Da sauri ta girgiza kai alamar a'a, mamakine ya kama Jalal da sagir, me take nufi? Jitai Jalal yace ki kara dubawa dai.
Yawo ta had'iya sannan ta kalleshi ta wuce na gaba dashi, har taje karshe tace ba kowa, nan sukai hanyar inda manya suke, ba shakka sunji haushin wannan rainin hankalin, wai an tarasu saboda wata 'yar yarinya, Seemah ta duba nan ma tace ba kowa, Habib yai shiru can ya kalli Sagir yace kaita office ni zamuyi meeting.
Suna fitowa suka had'u da Jalal, ya matso kusa dasu kad'an yace " Follow me. "
Tad'an harareshi tace dalili? Yace " karki b'atan rai ki biyoni ko?"
Nan ta kalli sagir tace ina zuwa.
Elevator ya bud'e ya shiga itama ta shiga, sun yi shiru har suka isa last foor suna zuwa ya karasa sama itama ta bishi, saman ba komai a gun sai flowers da kujeru, suna shiga gun Jalal ya kalleta da karfi yace " What are you doing? "
Seemah ta kalleshi da mamaki tace " haka zaka cemin?"
Jalal ya matso daf da ita tad'anyi baya ya bita sai da sukaje jikin bango yasa hannu d'aya a jikin bangon, tsoro ya fara kamata, Jalal cikin b'acin rai yace " Do you find me pitiful? Don't tell me kinaso in miki godiya akan abinda kike tunanin kinmin."
Cike da mamaki da takaici tasa hannu ta ture hannunshi zuciya tazo mata wuya, ta d'unkule hannunta ta kaima duka a kirji cikin takaici da hawaye tace " haka kake? Me yasa bazaka duba alkairin mutum ba? Sai ka d'inga kok'arin juya alkairi zuwa sharri."
Ta had'iye wani abun sannan ta cigaba, "you don't want me to pity you? Ko kuwa kana tunanin kafi karfin hakan?" Tai shiru tarasa me zatace juyawa tai kawai tai ta wuce.
Jalal ya bita da kallo yarasa me yasa yakejin zuciyarshi ba dad'i, zama yai a gun tare da dafe kai.....
Seemah kam da gudu ta karasa elevator tana shiga ta tsugunna a ciki tasa kuka mai ban tausayi, can wata zuciyar tace me kikema kuka? Mik'ewa tai da sauri ganin har sun zo, office d'in Habib ta wuce, Sagir ganin fuskarta yasan Jalal ya b'ata mata rai.
Seemah na shiga ta rufe kofar tare da jingina da kofar idanta na zubar da hawaye............
Na *Ayusher Mohd*
© *NWA*
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
🐾 *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*🐾
🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Na *AYUSHER MOHD*
No. 1⃣0⃣
Can Jalal yace " me zaki siya wai? Dakika sani na taso?" Kallansa tai sannan tace " so nake nima na fara shiga irin ta kasata, d'an naga alama wasu kallan 'yar iska sukemin, wasu ma harda cewa......."
Kallanta dayai yasa ta kasa karasa maganar, baisan sanda ya saki wani murmushi ba, jitai zuciyarta ta buga, da sauri ta d'auke kanta tace " ehem, Jal me kakema dariya?"
Kallanta yakarayi da murmushi a fuskarsa yace " da alama kin k'ulaceni."
Baki ta turo ta d'an harareshi tace " ina tausaya yama matarka, zatai fama."
Jalal ya had'e rai yace " waya baki pass d'in hirar matata? Bayan b'an yarje miki ba?" Kallanshi tai cikin b'acin rai ta kafeshi da ido, wayarsa datake kara ya d'aga ganin ansa Zainab yasa ya d'aga da sauri.
Seemah da itama taga sunan jiki yasa ta juya kai jikin window da sauri ta had'iyi wani yawu tarasa dalilin ta najin ba dadi.
Jalal ya d'aga wayar tare da amsa sallamar da akamai, ya cigaba" Zainab ya akai? Jikin Zaheedan ne?"
Cikin sanyin muryarta ta amsa "a'a yaya k'ira nai inji jiya ya ka isa Abuja?" Yace " Lfy lau Alhamdulila, Abba fa?" Tace " ya fita d'azu." Jalal yace " keda ba kud'i kike dashi ba me makon kimin flashing?amma bari na kashe zan turo miki kati yanzu." Godiya tai sosai nan sukai sallama.
Seemah kam tanajinsu, da sauri ta juyo tace " kanada aure ne?" Jalal ya kalleta yace " meya dameki in inadashi ko bani dashi?" Itama ta had'e rai tace " me kuwa ya dameni, tausayin ta kawai nakeyi, kuma in kasan bata da kud'i a waya meyasa tun farko ka d'auka? Sai ka kashe sai ka k'irata kai kuma."
Jalal ya karasa gefen titi yai parking, yace " ina zan kaiki? Kim barni sai tafiya nake, kinzo kina shiga abinda bana tunanin ya shafeki."
Kallansa tai ta tab'e baki sannan tace " nasan garin ne? Ka kaini inda zan sai kayan kasar mu."
Girgiza kai Jalal yai yace " to ai banaji matata ce zatai fama dani, da alama kece za'ai fama dake." Cikin shagwab'a da b'acin rai tace " *YOU?*" Jalal yace " What? " juyawa tai kamar tai kuka, kara girgiza kai yai yace tab lalai.......
Wuse Zone ya wuce, ya shiga Bengari Street, a Sahad Store yai parkin, ta d'aga kai ta kalli store d'in, yace " sai kin fito, kuma karki kuskura ki shanyani a waje."
Kallansa tai ciki da mamaki tace "au ni kad'ai zan shiga?" Jalal yace " da ni ne mai siyan kayan? " leb'enta ta ciza idanta ya ciko tace " wai kai wani irin mutum ne? Yama za'ayi ka cusa mace cikin shagon da bata tab'a zuwa ba kuma ita kad'ai?"
Kallanta yai yace " a tunanina kawo ki kikace inyi bawai in rakaki siyayya ba?" A zuciye ta fito daga motar tare da rufo kofar da karfi, ta fara tafiya, murmushi yai sannan shima ya fito tare da rufe motar, a baya ya bita.
Seemah kam ran nan nata a had'e take tafiya tana shiga taja shopping cart tafara tafiya, jitai ance bana zakiyi ba, dasauri ta juya jin muryar Jalal cikin shagwab'a tace " Jal da saninka kenan?" Bai kulataba yafa tafiya, binshi tai tana tafe tana smiling, sunje wajen atamfofi dasu shadda da lesuka nan ta fara zab'a kallan Jalal tai dake tsaye yana danna waya, karasawa tai gunsa tace " Jal tayani zab'a." kallanta yai sannan ya cigaba da kallan wayarsa yace " ina duba time ne, minti 30 na baki ki gama zab'a minti 10 ki biya kud'i minti 5 mu koma mota minti 15 ta maidamu, so nake in koma office a cikin 1hr."
Kallan mamaki Seemah tamai a ranta tace harda wani lissafi? Hmm aikuwa zakaga 1hr.
Juyawa tai batare da ta kara magana ba, a hankali take duba kayan ta gama da kaya sannan ta kalleshi tace " inasan turaruka da kayan makeup,"
Agoggon hannunsa yaduba yace " kinfa cinye time d'inki anan." Tace "to ko in k'ira yaya ya nemarmin izinin wasu lokutan?"
Juyawa yai yace biyoni...
Nan ta fara binshi tana murmushin mugunta, juyawa tai taga yawanci maza ne ke jan cart d'in hakan yasa kawai tad'ansa kara kad'an tare da tsugunnawa, da sauri Jalal ya juyo yace lafiya? Kallansa tai tare da kallan kafarta data rik'e, ya kalleta yace bigewa kikai? Kai tad'aga tace " eh, sam bankula ba ina kallan wani abun na bige."
Jalal ya matso tare da cewa " ke da kika taso a England har akwai abinda zai sa ki kallansa har ki bige baki kula ba?"
Kasa tai da idanta, yace to tashi muje kima b'ata min tym, mik'ewa tai irin da kyar d'in nan yace muje to, har ya fara tafiya tace Jal? Cikin b'acin rai ya juyo da masifa yace " sunana wai kenan?" Kallansa tai ta kalli cart d'in tace " bazan iya ja ba."
Oh God!!!!! Jalal ya fad'a sannan ya karaso tare da ansa ya fara turawa, jitai dariya na neman ka mata haka ta d'aure tana d'an d'ingisa kafa, ta gama siyayyarta sai dai Jalal ya kullu sosai ganin a siyayya sai data kai 1hr, sunje gurin biyan kud'i ta mik'a Atm, Jalal kam kallan uban kayan data siya yake sai dai in ya tina yayanta waye sai yaga ba komai bane.
Sun fito Jalal rik'e da ledoji sukasa a booth, Jalal ya kalleta yace shiga muje, ga mamakinsa gani yai bata d'ingishi, kallanta yai harta shige mota inda ta zauna d'azu, a ranshi yace ni kikai fooling? Kwafa yai sannan ya shiga shima.
Baice mata komai ba sai dai fara tuk'i dayai, basuyi tafiya mai nisa ba yaga wani asibiti, gangarawa wa yai tare da yin parking a asibitin, Seemah da mamaki ta kalli asibitin tace" baka jin dad'i ne?" Murmushin mugunta yai yace muje, kallansa tai tace harda ni? Nifa banasan ko shiga asibiti.
Jalal yace " ni ce miki akai inasan shiga store?" Jin haka yasa ta bud'e motar a hankali ta fito.
Suna shiga akace sai sun sai kati, Jalal yace muna d'an sauri ne ba likita zamu gani ba allura kawai za'a mata ta tetanus, nan aka nuna masa inda nurses suke, ya kalleta tare da mata alama da hannu, suna shiga ya kalli nurses d'in yace " bata d'an ji dad'i bane, ba big'e da karfe ne shine nake tunanin ko da abinda za'a mata ko allura ne."
Seemah da sauri cikin tsoro ta kalleshi, ba abinda ta tsana irin allura, cikin in ina tace " ahh ah ba big'e wa nai ba takalminane yad'en bugeni kad'an."nurse d'in tace " matso mu duba" ai tanajin haka ta fara baya baya, Idanunta suka kad'a Jalal ta kalla tace " Jal mu tafi please." Ganin yanda idanta ya kad'a yasa ya kallesu yace " kuyi hakuri inajin ni na d'aukaka abin maybe ba serious bane.
Tanaganin haka Seemah tai waje da sauri, Jalal ya karaso ya bud'e mota tana shiga ta d'au waya ta k'ira Ammar, yad'aga tare da cewa " Seemah na ya kke? Yau naji dad'i ana kirana."
Kallan Jalal tai sannan ta sa hannu tasa wayar a hand's free tace " Yaya Ammar saura kad'an yau a min allura."
Daga can b'an garen cikin tashin hankali Ammar yace " Seemah waya isa yasa a miki allura bayan bakyaso? Me ma yasameki? Ya Habib ne?"
Kallan Jalal tai tace " bashi bane wani d'an gadara ne."
Ammar yace " Seemah anya ana kula dake yanda ya kamata kuwa? Anya bazanzo dakaina ba? Ko kuma ke ki dawo ba?"
Jalal ta kalla da ya kafe ta da wani mugun kallomaka, ta murgud'a mai baku tacigaba" karka damu yayana I will take care of myself. " tana kai nan ta kashe ta kalli Jalal tace "what? Ka kaini asibiti a min allura? Shiyasa na nuna maka matsayina, banaji yayuna in sukaji me kamin zasu kyaleka tun balle wanda mukai waya dashi yanzu.
Jalal ya kalleta yace " da alama baki daddara ba kenan, har ni zakima pretending? Kisani aiki?"
Dariya ne ya kamata auuuu yanzu tasan dalili, darita tasa sosai, Jalal ya saki baki yana kallanta, tad'an tsagaita tace "ohhhh dama haka ne?"
yace " Do u just laugh at me? "
Dariya tasakeyi tace " au sorry, amma yazanyi dariya kake bani."
Jalal ya furzar da wani iska yace " mene? Dariya nake baki? Nid'in?"
Had'iye dariya tai tace " ni ai ban gane saboda haka ka kaini asibiti ba ai, amma lalai u r really funny."
Jalal jiyai kamar yasa ihu, kamar shi acemai funny? Bai kulata ba da karfi ya fizgi motar suka hau titi, Seemah a ranta tace " zakasan ni ka kai asibiti, ka gano weakness d'ina d'aya nima na gano d'aya, bakasan ama dariya nikuma banasan allura."
0 comments:
Post a Comment