Turab na zaune a cikin mota yai shiru yana tunani, me ya samu Khadija?
A can kuwa Hisham na shiga da ita cikin gida ya rike hannayenta duka biyu yace "Khadija, menene? Me kikaji?"
Kallansa tai tsananin tsoronsa taji ya shigeta, kai ta girgiza batace komai ba, kara jijiga ta yai yace " wanene ni?"
A hankali tace " Abba ne."
Yace " me kike kokarin sanar ma Abu Turab?"
Kai ta girgiza da sauri tace "bakomai."
Idanu ya kankance yana san gano abunda take b'oyewa, mahaifiyarta ce tazo gun tace " Khadija? Lafiya inata kiranki shiru?"
Kwace hannunta tai ta tafi gun Uwarta da gudu.
Hisham cikin zargi ya ke kallanta, Ummanta ta riketa tace "lafiya Khadija?"
Tattaro nutsuwarta tai sannan ta samun kanta da cewa " Bakomai Umma faduwa nai a waje."
Umma ta kama hannunta cikin kulawa sukai ciki.
Hisham ya bisu da kallon zargi sai dai bashida tabbas akan abinda yake zargi, sannan yasan Khadija da ace taji maganar da sukai da matarsa dazu da ciki zata shigo taji me suke nufi bawai waje zatai ba.
*****
Sun isa gida, Turab ya fito sannan ya nufi hanyar b'angarensa.
Abdulmajid ya hango yana tahowa shima da alama shima fita zaiyi, tsaya wai cak yana kallansa sannan yana maimaita kalamun Jakadiya, da kuma Khadija, da alama duk maganarsu a karkashinta dai maganace wacce ta shafi Abdulmajid, to amma me suke nufi? Sam hankalinsa bai kawo ba d'an sarki bane dan shi a ganinsa duk mugunta da makircin magajiya bazata taba tunanin yin wani abu mai kama da haka ba.
Abdulmajid ne ya iso inda yake kallan banza yamai yai gaba abinsa.
Turab ya bishi da kallo sannan yai gaba.
Har ya je zai shiga b'angarensa sai ya juya ya nufi bangaren Hajiya.
Yaje shiga yai kicibis damai kula da ita, sam bata san ya taho ba haka shima.
Bigetan dayai ne kufin dake hannunta ya fad'i kasa.
Turab ya kalleta yace " sannu....."
Ganin yanda ta shiga saurin dauke kofin da tayar sam tama manta da bigeta akai, tana d'aukewa tai hanhar fita, kasa ya tsuguna ya d'au yar karamar ledar data fad'o daga jikinta yana kokarin mata magana akan ta yarda abu sai gani yai ba kowa agun.
Mamaki ya kamashi ina tai? Kallan maganin yai sannan ya shinshina maganin, a aljihunsa ya saka sannan ya shiga ciki.
Sam jikinta ba sauki sai ma karuwa da yakeyi, kusa da ita yaje sannan ya riko hannunta yace " Hajiya nine Abu Turab."
A hankali ta bud'e idanunta ta kalleshi cikin karfin hali ta sakarmai murmushi.
Cikin kulawa da tausayawa yace" Hajiya kinganni shiru ko? Tafiya nai sannan abubuwa sunyi yawa dana dawo, ya jikin?"
Idanu ta lumshe sannan ta bud'e, kallan d'aki yai sannan yace " kin gaji da kwanciya ko?."
Tunani tai yanzu ne lokacin daya kamata ta yunkura ta fadama Turab abinda ta sani.
Bakinta ta shiga motsawa tana kokarin yin magana, kallanta yai yace " akwai abinda kikesan fad'amin?"
Kai ta d'aga da sauri alamar eh.
Matsowa yai da kansa kusa da bakinta yace "menene Hajiya?abu kikeso?"
Daurewa take sosai da kyar ta iya cewa "Maga...."
Yace "magani?"
Kai ta girgiza alamar a'a yace "Magajiya?"
Kai ta d'aga da sauri alamar eh.
Cikin mamaki ya kalleta yace " wani abun ta miki?"
Da kyar ta kara daurewa tace "Abb duu........"
Yace " Abdulmajid?"
Kai ta jijiga alamar a'a yai shiru yana tunani can a ransa yace Abdussamad?
Kallanta yai yace " Abba?"
Kai ta girgiza da sauri yace " me ya faru?"
Kokarin magana take sai dai ina ta kasa, ganin yanda take shan wahala yasa yace " Hajiya daina magana."
Yawo ne yashiga zubowa mai kumfa, cikin tausayawa ya mike da sauri yana neman mai kula da ita.
Yarinyar nan ya gani a waje tana ta dube dube cikin b'acin rai yace "bakiji ina kiranki ba?"
Tahowa tai gunsa, yace " Hajiya jikinta ya motsa nemo mai magani."
Ya fada tare da komawa ciki ya d'agata yana goge mata, sai far fari take da idanunta, mai bada magani tana zuwa ta shiga mata jike jike tana bata, sai dayaga ta samu bacci sannan ya mike cikin tausaya mata.
Dakinsa ya shiga ya kwanta akan gado kansa na kallan sama ya d'aura hannunsa akan goshinsa, me Hajiya takesan fada mai? Ya tabbatar yanzu kuma abu ne tsakanin Magajiya da Mahaifinsa.
Hannu yasa a aljihunsa ya d'auko wannan maganin, mikewa yai ya fito waje.
Garzali ya taso da sauri yazo gunsa, Turab ya kalleshi yace " ka kiramib jakadiya kace ta sameni a gun shakatawar Takawa."
Garzali ya amsa da to, juyawa yai ya fita.
A kan kujera ya zauna, bai dade ba sai ga Jakadiya.
Tana zuwa ta zube a gabansa ta shiga gaidashi, Turab ya amsa sannan ya kalleta yace " tambaya zan miki, banasan gulma ba kuma nasan had'i sannan kada ki kuskura kimin karya abinda na tambayeki shi kadai zaki amsa min bana bukatar wasu kalamai na daban."
Kanta na kasa tace " To ranka ya dade" a gaskiya tana ganin girma da kimar yaron tunda yake bata taba ji ance ya nemi jin magana daga bakin wani ba a masarautar, sannan ga kwarjini da izza ta sarauta da yake da ita.
Turab ne ya katseta da cewa " Menene tsakanin Magajiya da Abdulmajid da kuma Hisham? Wani sirri ne a tsakaninsu?"
Gabanta ne ya fadi ta kalleshi tace " Ranka ya dade."
Kallanta yai yace " jiranki nake."
Yawo ta hadiya sannan tace " Amsar d'an kaninta da juyawa a matsayin nata."
Idanu Turab ya zaro cikin tsananin tashin hankali, mikewa yai tsaye gabansa na wani irin fad'uwa gabansa yai, idanunsa ne suka kada sosai kallanta yai cikin kokonto yace " meye naki na sanar dani wannan babban sirrin? Sannan ta yaya ke kika san haka?"
Jakadiya ta kalleshi cikin tsoro tace " Tuba nake ranka ya dade amma wannan magana haka take sannan sanar dakai danai bawai da wata manufa na fadama ba......"
" Badai kina tunanin kin sanar dani hakan bane dan kar asiri ya tuno kiyi tunanin zan taimaka miki? Sannan meye dalilinki na b'oye wannan siriin bayan ked'in jakadiyar sarki ce?"
Tsoro ne ya kama Jakadiya jikinta ne ya hau rawa ta kalleshi tace " Ranka ya dade........."
Kallanta yai cikin takaici yace " ba dai dake aka shirya b......"
Tsugunawa tai cikin tsoro tace "wlh ba dani bane Ranka ya dade, wlh ba dani bane."
Komawa yai ya zauna sannan yace " jeki zan nemiki in nayi tunani."
Fita tai cikin tsananin fargaba.
Jiyai hannunsa na rawa, da sauri ya had'e hannayensa guri daya sannan ya bud'e idanunsa da sukai jawur.
Mikewa yai cikin takaici yai bangaren Magajiya.
Tana zaune a kilisarta aka sanar mata da zuwansa.
Murmushin jin dadi tai tace ace ya shigo dan ta tabbata yau dolene ya nemi ya fiyarta.
Turab ne ya shigo, tsayawa yai yana kallanta cikin tsananin mamaki.
D'agowa tai ta kalleshi tace " meye hakan? "
Murmushi yai sannan ya matso ya zauna tare da gaisheta.
Amsawa tai cikin isa sannan tace " kun yanke shawarar?"
Turab yace " sosai ma Umma shiyasa nazo miki da umarni."
Kallansa tai shekeke tace " Umarni? Kai zaka ban?"
Kai ya d'aga mata tare da yin murmushin gefe yace " inaso a satin nan ki fara shirya lefe na daga nan zuwa sati biyu ki gama hada komau dan zuwa kaiwa Masarautar kano, sannan in zaki saka lokacin biki banasan kijashi da nisa."
Kallan mamaki ta mai batasan sanda tasa wata dariya ba tace " me da me?"
Yace "kamar yanda kikaji na baki umarni hakan nakeso ki aiwatar min, sannan sirrin ki da nake rike dashi a hannuna zan aunashi a ma'auni, da namu sirrin da kike rike dashi zan duba inga da ni dake wanene nashi sirrin yafi nauyi, inhar naki yafi nauyi dole ne kiyi tabin umarnin d'anki Abu Turab har sai sirrinki ya kai daidai d'aya da namu inyaso sai kowa ya tona nashi sirrin a lokacin ne zamuga wanda zai ci galaba."
Gabanta ne ya shiga fad'uwa dan yanda idanunsa suke nunawa tasan tabbas akwai wani babban sirrinta daya sani, menene? Wanene daga ciki?"
Daurewa tai tace " kana tunanin zan yarda da wannan shirman naka?"
Kallanta yai cikin tsana yace " to ko in sanar ma Abdulmajid?"
Gabanta ne yai wani wawan faduwa cikin rawar murya tace " Abu Turab."
Murmushi ya sakar mata sannan ya mike ya kalleta yace " kiyi gaggawar sa d'anki ya janye auren Mairo, ahh ba......" sai kuma yasa yatsa a baki alamar yin shiru yace " sry" ya fada tare da nuna alamar zip a bakinsa.
Juyawa yai yai waje.
Yana fita ta shiga kakkarwa, mikewa tai da sauri cikin tsoro me ya jiyo? Me ke faruwa?
Turab na fita ya kalli bangarenta cikin takaici sannan yace " kin cuci Abba yanda kika ci amanar sa da cutar da mutane sai na nuna miki abinda kika aikata babbam kuskurene, babu babban yaki sai wanda kika yarda dashi yaci amanarki, kijira juya miki baya da zansa Hisham yai, sai kinyi dana sanin abinda kika aikata."
Darajar mahaifinsa kawai taci amma da....Yai kwafa ya tuna yanda aka bashi labari dadin da mahaifinsa yaji a lokacin da aka haifi Abdulmajid.
Kallan bangarenta ya karayi cikin tsananin takaici sannan yai gaba.
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*57*
Turab na fita Magajiya ta d'auki kofin da ke gabanta ta jefi madubin dake manne a kilisar.
Mikewa tai cikin tsananin tsoro da fargaba tai cikin d'akinta.
Me ya sani? Me ya sani? Me ya sani?
Wannan kalmar ita kawai take mata yawo a kwakwalwarta gaba daya ta rasa inda zatasa kansa, fitowa tai ta bada umarnin a kira mata Jakadiya cikin gaggawa.
Jakadiya na zaune tasa kwanan abinci agaba sam ta kasa ci akazo aka sanar da ita kiran Magajiya.
Zufa ce ta shiga karyo mata, mikewa tai ta fito.
Haka ta karasa tana ta tsoron abinda zai faru.
Magajiya na zaune a kan gadonta yayi shiru tare da kurama kasa ido.
Ko sallamar Jakadiya bata amsa ba, har Jakadiyar ta zauna tare da gaisheta.
Magajiya bata amsa ba sai dai ta kalleta cikin wani yanayi na zargi, sai kuma ta murmusa tace " Jakadiya ba tin yau ba nasan tabbas sai gulna da tsautsau bakinki yasa kin sanar ma Turab sirrin Abdulmajid."
Jakadiya ta zaro ido sannan ta tuno kalaman Turab a yayin da ya mike zai fita bayan ya gama mata fada " Kada ki kuskura ki nunama Magajiya munyi maganar nan dake, duk yanda taso ta bugi cikinki ki tabbatar baki bar wata hanya ba dazai sa ta fahimta, nagode da sanar dani da kikai."
Ya juya ya fita, tunowa datai da kalamansa yasa tai saurin zubewa tace " Gimbiya Magajiya ta yaya zakimin wannan shaidar? Bayan shekaru sama da ashirin ina rike da wannan sirrin? Sai yanzu ne zan tona? Inci ribar me?"
Magajiya ta kalleta tace " Amma ai kwanaki kin min birga akan sirrina da kike rike dashi sannan banida tabbas ke d'in yanzu a bangarena kike duba da abinda kikamin."
Magajiya ta daure tace " Gimbiya bani bace, me nene ma zaisa in fadamai?"
Ganin yanda Jakadiya tai yasa ta gamsu akan ba ita bace, ta kalleta tace " bani guri."
Fita Jakadiya tai, tana zuwa waje ta saki wani ajiyar zuciya.
Magajiya kam tana fita ta dafa kanga cikin tashin hankalu tace " ba wannan bane, tunda duk gidan Jakadiya ce kawai tasan wannan sirrin, tunowa tai da Hajiya, ba dai Hajiya ce ta fad'i dayan sirrin ba?"
Mikewa tai da sauri ta fito, ta sanar ma Bayinta akan zuwa bangaren Hajiya.
Tana shiga wannan baiwar ta taho gunta da gudu ta gaisheta.
Magajiya ta kalleta bata amsa mata ba tai ciki.
Mai kuka da ita wacce tafi kusanci da Magajiya ce ta kalli Baiwar tace " kina zubawa?"
Cikin tsoro tace eh, dan bazata iya cewa ta batar da maganin ba dan ta tabbata inhar ta fada to lalai kwananta ya kare.
Magajiya na shiga ciki ta rufe kofa.
Kallan d'akin tai a wulakance sannan ta toshe haccinta wai wari.
Zama tai daga nesa da Hajiya sannan ta kalleta cikin jin dadin yanda take shan jiki ba damar magana tace " Hajiya? Kin ganeni?"
Kallanta Hajiya tai, tana ganin Magajiya ta shiga yunkuri tanasan magana ta kuma kasa, Magajiya tace " Lalai Hajiya kiji da jikinki har kike wani yunkurin magana? Da nadauka ko kinsamu sauki ne harkinyi tsautsayin yin magana amma yanzu naga ba haka ba, bakya tunanin ya kamata ki sallama komai na duniya ki jira mutuwa tazo ta daukeki?"
Hajiya yunkuri take sosai, ganin ba dama yasa tai shiru sai hawaye da yake ziraro mata ta gefen ido, tunowa tai da abinda ta gani.
{
" Wasika aka ba da akawo mata tashin safiyar yau, amsar wasikar tai ta bud'e, kana kallan rubutun kaga rubutu ne na 'yan koyo, sai dai da yake bata iya karantawa ba yasa ta ajiye wasikar a tunaninta ba mai amfani bace.
Sai dai me? Kwana hudu kenan ana aiko mata da wannan wasikar sannan yaro ne yake kawowa kuma daga ya bada yake sa gudu yai waje, yau abin ya fara damunga dan da alama magana mai mahimmanci ake san sanar da ita.
Sawa tai a kira mata Rabi'a, bayan tazo sun gama gaisawa ta d'auko wasikar ta bata tace " Karantamin."
Rabi'a ta amsa tare da bud'e wa.
Na farko an rubuta "Hajiya d'anki na cikin matsala."
Na biyu " Hajiya ki yafemin sai dai ba yanda zanyi dolene na cigaba da zuba maganin nan inba haka ba Magajiya halakani zatai."
Na uku "Hajiya ki taimaken ki d'au mataki ko na samu zunubina ya tsaya anan."
Na hudu " Hajiya kiyi wani abu dan Allah."
Hajiya ta amshi takardar a taorace tace "Rabi'a kin tabbatar da abinda aka rubuta kenan?"
Rabi'a tace "Hajiya wlh abinda akace kenan amma me hakan yake nufi? Magajiya tana ba sarki magani? Akan me?"
Hajiya tace " jeki gida sannan maganar nan ta zama sirri tsakaninmu koda wani abu zai sameni kimin alkawarin bazaki taba fadan wata kalma ba."
Rabi'a tace "Na miki alkawari, nan ta mata sallama ta fita da tsananin mamaki, bazata taba iya ma Hajiya musu ba."
Tana fita Hajiya ta kona takardar sannan tai shiru tana tunani, ba wanda ta yarda dashi bare suyi maganar dashi, sannan batasan wacece tayo mata wasikar ba, gashi ita ta tsufa ba wani abu da zata iya yi.
Abu d'aya ne ya dace tai shine taje gun Magajiya dan nuna mata ba tsoronta ake ba sannan ga fadamata inhar bata daina ba zata sanarma Sarki.
Yau da safe tasa aka kira mata Magajiya, tun safe aka sanar da ita amma sai yamma liss sannan tazo.
Hajiya na zaune da charbi, zama tai akan kujera sannan tace" Hajiya kim wuni lafiya?"
Hajiya cikin takaici ta kalleta tace " me kike bawa d'ana?"
Magajiya ta kalleta cikin mamaki tace "me nake ba d'anki kamar ya kenan?"
Hajiya tace "Kamar yanda kikaji haka yake, wani tuggun kike dubgawa Abdussamad, nasan dai ba maganin mutuwa kike bashi ba tunda zamansa a mulki shine zamanki kema a mulki, sanar dani me kike masa?"
Dama Magajiya na tsananin jin haushin Hajiya dan tunda aka aureta tasan ba santa takeyi ba, fuska ta canza ta d'aure fuska tace " koma me nake bashi ai mijinane sannan bakida ikon shiga tsakanin mata da miji."
Ta mike zata fita, Hajiga abin ya bata mamaki tace " waye ya haifa miki har kika aura? Sannan ni dama tunda na fara ganinki wlh nasan ke ba alheri bace a gareshi ba kuma matar zama bace ta amana, ko kiyi gaggawar daina abinda kike bashi ko kuma wlh in sanar dashi, zakiyi mamaki inkika ganki a gidan yayanki da takardar saki, ba'a saki a gidan sarauta bari sakin uwargida wacce take sarauniya sai dai ina sanar miki za'a fara akanki."
Wata banzan dariya Magajiya tai tace " Me? Ni za'a saka?"
Hajiya ta kalleta sai dai yanda taga Magajiya tayi yasa tsoro ya d'arsu mata dana sani ya kamata me yasa bata fadama d'anta ba ta sanar ma Magajiya?"
Magajiya tazo kusa da ita ta sakar mata murmushi tace " ina jiran lokacin da za'a bani takarda, ki kuma tabbatar an bani, sannan maganar magani maganin hana d'aukan ciki ne ki tabbatar kin sanar dashi haka."
Ta juya ta fita, tana kallan Hajiya duk ta rikice jikinta ya d'auki rawa.
Bayan Magrib tanashan ruwa shikenan ta kasance ba lafiya tun daga wannan rana har yau ba baki ba zama bare tafiya."
}
Magajiya ta mike tazo saitin kunnen Hajiya tace " Kijira d'ana ya hau mulki in har kinada rai ni zan taimaka a fitar dake daga gidanan akaiki can bayan gari ki zauna kyafi jin dadin zaman duniyar, in kuma kinaso in hada da jikanki da kuma uwarsa Basira ku zauna tare acan."
Ta mike tai waje.
Tsayuwa tai a wajen gidan, me turab ya sani? Bataji akwai wanni babban sirri dazai tsoratata da ya wuce wad'an nan biyu, sauran duk sai dai tasa a aikata amma badai ita dakanta ba, inma zancen kashe yayan Basira ne ai ba ita bace tai Hisham ne.
Dolene ta nemi Turab ta kuma bihi cikinsa da jin sirrin da ya sani.
Turab zauna akan kujera yana d'an kada dan yatsansa d'aya tunani yakeyi wace hanya ce mafi sauki da kuma bakin ciki da zai sa Magajiya ta fita hayyacinta in taji Yayanta Hisham yaci amanar ta? Ya tabbata Hisham da Magajiya kowa amfani yake da dan uwansa.
Ita tana amfani dashi dan cikar burinta, shi kuma yana amfani da ita dan samun matsayin da zai wuceta nan gaba, murmushi yai yace " Badai tana tunanin in Abdulmajid ya hau mulki komai na burinta ya cika ba?"
Mikewa yai ya fito waje.
Hango Abdulmajid yai a zaune yana shan iska jiyai tausayinsa ya dan darsu mai, ya zaiji in yaji wannan sirrin? Yauce rana ta farko dayaji tausayin Abdulmajid ya kamashi.
Ya zaiyi ya sa Magajiya da Hisham su tunama junansu asiri da kansu?
Khadija!
Shiru yai jin sunan daya zo mai, tabbas itace a tsakanin mutanen biyu, ita da Abdulmajid, sai dai me? Zuciyarsa zata iya jure amfani da ita?
Juyawa yai ya koma ciki tare da furzar da iska mai zafi.......
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*58*
Duk yanda Magajiya tai akan samun mafita ta kasa, da sassafe kuwa ta aika akan a kira mata Hisham.
Ko gaisuwarsa bata amsa ba tace " Yaya inaji fa yaran can yasan wani abu namu."
Gabansa ne ya fad'i kallanta yai sannan ya tuna kawo Khadija gida da yai, ba dai wani abu ta fada mai ba?
Daurewa yai yace " bangane ba? Me ya sani?"
Ta girgiza kai tace ban sani ba sai dai daga yanda yazomin da kuma yanayin kalamansa inada tabbacin yasan wani abu wanda yafi fyaden da akama Basira."
Hisham ya sauke ajiyar zuciya jin da alama ba Khadija bace yace " amma kinsan yaran nan shegen yaro ne anya ba dan karkiyima Mahaifiyarsa wani abu bane?"
Magajiya ta girgiza kai cikin yanayin tunani tace " Yaya bakaga idanun yaran nan ba alokacin, sannan cemin fa yai in fara hada kayan lefensa yaban zuwa sati biyu, kamar ni dan karamin yaron da ko uwarsa na girma yazomin da zancen rainin hankali irin wannan?"
Hisham shi kansa yayi mamakin jin haka yace " da kuma bakinsa ya fad'a miki hakan?"
Tace " anan gun kuwa, sannan harda cemin in sa Abdulmajid ya janye auren Mairo, umarni fa yazo ya bani wanda ko ubansa bai taba ban umarni akan abinda yasan ina duk wani abu na ganin na hana wannan abun."
Hisham yace " da alama yasan wani abun to amma ta yaya?"
Magajiya ta juya kai tace " wannan shine abinda ke damuna."
Shiru sukai kafin can ta kalleshi tace " Yaya"
Kallanta yai yace " ya zakiyi?"
Murmushi ta saki tace " kamar ni? Abinda yafi damuna kenan dan jiya ko baccin kirki ban samu ba, kamar ni Magajiya ace wannan yaran zai kalla ya bani umarni?"
Hisham a ransa yace " an tabo Masifa."
Magajiya ta kalleshi cikin iza tace " zanyi abinda yace bayan na tabbatar da akwai sirri na a hannunsa, zanyi lefe zan kuma sa a sa rana, zan nuna ma jama'a Turab ma d'anane."
Hisham cikin tsananin tsoro ya kalleta dan ya tabbata wank mugun abun zata fada daga karshen abin arzikin datai, dan yasanta haka take in har aka bata mata rai sai ta nuna bakomai Sai kuma tayi abinda baki bazai fadu ba.
Magajiya ta kara wani murmushin jin dadi tace "Aure? Auren Bilkisu?" sai kuma ta sa dariya tace " lalai nayi gangancin barinka da rai."
Hisham ya kalleta yace " me kike tunanin yi?"
Kallansa tai sannan ta wani juya ido tace " sai muga ranar auransa waye zai je gun, mai makon kaga ai aure da shi a d'aura da Abdulmajid sannan su gama d'aura aure suzo su tadda angon da aka shirya za'ai dashi a kwance ba numfashi."
Hisham ya kalleta yace " ban fahimceki ba....."
Tace "Zaka fahimceni, dan kuwa kaine zakasa a kamashi a hanyarsa ta zuwa d'aurin auran, sannan musa abokinsa dole ya sanar akan bazai samu zuwa ba dan shi ba auran yake so ba, kaga ran Sarki zai b'aci matuka ya aura ma Abdulmajid Bilkisu sannan mai makon mu sakeshi lafiya sai mu juya abin a matsayin 'yan fashi ko kuma hatsarin mota, kaga mun jefi tsuntsu biyo da dutse d'aya."
Mamaki ya hana Hisham magana kawai kallanta yakeyi.
Kallansa tai tace " ya? Wasan nawa ya had'u?"
Idanunta ya kalla yace " Magajiya kenan, duk duniya Allah bai taba hadani da mai kaifin basira irinki ba, da ace Basirarki a abu mai kyau kike sa ta lalai da ancigaba a gidan nan."
Harara ta makamai tace " mai kake nufi?"
Jinjina ya mata da hannu yace " komai yayi nake nufi."
Tace " Uwata fa?"
Sai daya had'iyi yawo yace " tana gida ba lafiya."
Cikin kulawa tace " da alama sam yaya baka kula da Khadija, inaji zan dawo da ita gabana har tai aure, munyi magana da Mahaifin Saifullahi yace tunda yara sun daidaita zasu kawo kudi."
Hisham yai murmushi yace "Allah ya kaimu."
Kallansa ta kuma yi tace " Ya ake ciki a fada akan maganar auran Abdulmajid da wannan sakaryar?"
Hisham yai tsaki yace " kwana biyu dai anyi shiru da maganar dama Galadima ne uban san kawo maganar da Turaki."
Magajiya tai shiru kafin tace " Gun Abu Turab zani yanzun nan dan in tabbatar da abinda yake dashi."
Hisham ya kalleta yace " da kanki zaki? Ba gwara ki aika yazo ba?"
Murmushun jin dadi tai tace " ai tun yanzu za'a kulla abotar d'a da uwa saboda gudun zargi da zai biyu baya."
Kallanta yai sannan yai kasa dakai.
Mikewa tai ta fita sannan shima ya fito.
B'angaren Turab suka nufa, mai kula da kofarsa ne ya bud'e tsananin mamaki ya kamashi na ganin Magajiya.
Su kansu mutane duk wanda yazo wucewa alokacin sai dayai mamakin ganinsu.
Bud'e mata kofa yai tare da gaisheta.
Magajiya ta shiga tana kanta tsaye.
Garzali ne ga taho da sauri tare da gaishesu.
Magajiya ta kalleshi tace " Turab fa?"
Yace " yana d'aki."
Nan ya nuna mata hanyar falo ta shiga.
Tsayawa tai tana kallan bangaren, abinda ko bangaren Abdulmajid tunda ya tasa bata zuwa.
Garzali yai ciki dan kiran Turab.
Abu Turab ya gama sa kaya kenan yaji ana kwankwasawa, yace waye? Garzali yace "nine kayi baki ne."
Bai tambayi waye ba sai huka da ya saka ya sa turare ya fito.
A zaune ya ganta tayi zamanta na isa akan kujera.
Mamaki ne yasa ya ja ya tsaya tare da jingina kansa da bango, yace " Umma Magajiya da kanta?"
Alama tama bayin da su fita daga falon,saj da suka fita sannan ta kalleshi tace " tsayuwar anan ta menene? Abun mamaki ne in uwa tazo ganin d'anta?"
Kallanta yai sannan ya tako a hankali yana cewa " inafa abin mamaki, dama ai hakkinta ne na ta kula da d'anta."
Ya karasa maganar tare da zama.
Kallansa tai tace " nayi tunani akan maganar ka sai dai banaji kai ka isa ka bani umarni sai dai In zaka canza yanda kamin magana daga umarni zuwa roko."
Kallanta yakeyi har saida tazo karshe, gani tai ya sakar mata wani bazawarin murmushi yace " ko?"
Ranta ne ya d'an soso ta kalleshi.
Yace " kin fara had'a kayan? Ko dayake jiya mukai maganar bazai yiwu ace kin fara ba, amma ina sanar miki sati biyu na baki kacal in har kika wuce ina tausayin halin da zaki shiga dan banaji Sarki zai barki da ranki, in kuwa har ya barki to lalai a kurkuku zaki karasa rayuwa daga ke har yayanki."
Gabanta ne ya fadi, ta daure tare da kakaro dariya tace " inji wa kenan? Kai kana tunanin duk duniya akwai wanda ya isa ya hukuntani? Sarki? Hahah lalai yaro yaro ne."
Turab kallanta kawai yake, jin kalamanta yasa ya mike tsaye yace " Ba sarki bane zai hukuntaki Umma mantawa nai, nine nan d'anki wanda zai hukuntaki, ya kuma hukunta duk masu hannu a abinda kuka aikata."
"Ahhh, bansan me yasa nake tausayin mutanen da kukai amfani dasu gun cimma burinku ba, sai dai ina tunani anya zasu yafe muku? Sannan Hisham da kike takama dashi...."
Sai kuma yai shiru tare da yin kasa da kai yana dariya yace " ke kina tunanin zai cigaba da bin umarnin ki har sai sanda kika jefashi halaka?"
Kallansa tai cikin mamaki tace " mene?"
Kafada ya d'aga mata ya girgiza kai yace " Bansan komai ba."
Juyawa yai yace " in kin gama ganin gidan d'an naki kya rufomai kofa."
Ya juya yai ciki ransa a b'ace, wato bata d'auki Sarki da wani matsayi ba? Gani take tafi karfinsa.
Ba shakka ran Magajiga yakai gurin tunzura, lalai dole taga karshen yaron nan ita ganin sa ma ta tsani yi yanzu.
Haka ta fito rai a b'ace.
************
Abdulmajid kam yana tsaye a kofar gidansu Mairo sai data dade sosai dan sai da mahaifiyarsa ta tsawatar mata sannan ta fito.
Yana ganinta ya sauko yana washe baki.
Tsayawa tai tare da hard'e hannayenta ta juya mai baya a cikin soron.
Abdulmajid ya karaso ya kalleta ta baya sannan yace " Gimbiya irin wannan tsayuwa haka kamar mai shirin yin hoto?"
Juyowa tai ta kalleshi tace " Abdulmajid."
Da sauri yace " Naam."
Tace " dan Allah dan Annabi ka kyaleni, wlh wlh ni kam na gaji da wannam abun, ka sanni sarai banaso raina ya bace dan wlh xanyi abinda kaima sai kai dana sani."
Kalamanra ko a jikinsa yace " eh wlh, dan Allah Mairo kiyi abinda zanji jiki ni wlh so nake yi."
Wani banzan kallo tamai na takaici tace " wai kana d'an sarki me yasa kake abu kamar karamin yaro?"
Hannunta ya kamo, da sauri ta fizge tace " Wai Abdulmajid meke damunka ne? Na d'auka na sanar dakai banasan ka dinga tabani ko? Kaje can kun karuwan......."
Batai auni ba taji yasa hannu ya rufe bakinta.
Matsowa yai da sauri ta matsa jikin bango tana zare ido tace " meye hakan?"
Kallanta yai yace " Mairo me yasa kike tunani ni din dan iska ne?"
Harararsa tai batace komai ba.
Yace " nasan bazaki yarda da abinda zance ba amma wlh kinji na rantse ban taba sanin wata 'ya mace ba, ma sani sarai ina shafa bayin gidan mu dan jin dadi na sai dai ban taba bari abin yakai nan ba."
Kallansa tai tace " kana tunanin zina sai ka sadu da mace kawai take a matsayin zina?"
Kallanta yai yace " Mairo ni duk wannan ba sune a gabana ba, in kikace in daina taba mata zan daina nidak dan Allah ki auren, ko na aureki in kikaga dama kice sai kin amince zan kusanceki Wlh zam yarda ni dai dan Allah ki yarda ki auren, ina san......."
Katseshi tai tace " Ni dai dan Allah ka kyaleni na rokeka da Allah."
Murmushi ya sakar mata sannan yace" ma tafi yau, sai na dawo zuwa jibi."
Kafin tai magana har ya tafi, juyawa tai ta wuce gida.
*******
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*59*
Magajiya sam ta rasa yanda zatai, ganin ba mafita yasa ta nufi gun Sarki.
Yayi mamakin jin zuwanta bayan ta shigo ta zauna sannan ta gaidashi.
Kallanta yai tare da amsawa yace " Lafiya dai ko?" ya fada tare da d'aukan ruwan dake gabansa a kofi dan sha.
Fuskarta a sake kai kace cikin farin ciki take tace " dama maganar auren Turab ne, ina tunanin ya kamata in fara had'a lefe....."
Furzo da ruwan bakinsa yai tare da kwarewa, kallanta yai cikin tsananin mamaki yace " me? Me kika ce?"
Dariya tai na salo tace " me? Kana tunanin lokaci baiyi ba?"
Ido ya kura kura mata yace "Magajiya!"
Kallansa tai bata amsa ba, yace " kinsan me kike anan kuwa? Kin tabbatar a hankalinki kike ko kuwa wani tugun muguntar kika shiryo?"
Sansanyan murmushi ta sakar mai tace " ko d'aya na dai fahimci cewa aikinane wannan, sannan waye Turab? D'anka ne fa wanda daga shi baka kara samun wani ba, ta ya za'ai yara kwaya biyu ace mun kasa kula dasu? A wata masarautar sai kaga 'ya'yan sarki sunfi 30 amma mu a namu haryanzu biyu Allah ya bamu, me zaisa mu zauna muna samun sab'ani akan su?"
Wata banzar dariya yai dan ko magajiya zata dafa Al-qur'ani bayajin zai yadda da wad'annan kalaman nata, ya tabbatar da abinda take shiryawa.
Kallanta yai yace " yanzu me ake bukata?"
Nan ta fara mai bayani, yace zai bada kudi ayi komai cikin girmamawa da matsayi.
Tana fitowa yabi bayanta da kallo yana tunani, me ke faruwa? Ya tabbata Turab ko mai zai ce mata bazata taba yarda da zancen nan ba balle ma tasan sirrin mahaifiyarsa, me zai sa ta amince? Ya tabbatar akwai wani shirri da take yi.
*********
Turab zaune agun hutawar daya saba zama ya saka ledar maganin nan a gaba a hannunsa yana kallo cilla maganin yai sama kad'an sannan ya cafe yace " kai kuma aikin me kakeyi?"
Mikewa yai dan dole ne ya binciko maganin menene wannan.
Bangarensa ya nufa, yana shiga Garzali ya taso ya gaidashi sannan ya sanar dashi nemansa da mahaifiyarsa takeyi.
Mikamai maganin yai yace " so nake ka bincikomin maganin menene wannan yanzu, sannan ya zama sirri kar ka tambaya a gidan nan, kaje wajen gari"
Garzali yace " to" sannan yai waje.
Bangaren Mahaifiyarsa ya nufa, ta sa an shiryamai abinci, Turab ya zauna sannan ya gaisheta.
Kallansa tai cikin kulawa daga dawowarsa daga kano har ya d'an fada, Lantana ta kalla tace " Lantana zubamai abincin."
Turab ya kalli Lantana sannan yace " barshi zan zuba da kaina."
Nan ya jawo plate ya d'ebi fankaso guda biyu ya zuba miyar taushe wanda yaji kaza.
Hannunsa ya wanke sannan ya fara ci, sai da ya gama yasha zubo sannan ta kalleshi tace " ya kukai da Magajiyan?"
Murmushi yai mata sannan yace " karki damu Umma, sirrin nan sai dai ta tafi dashi har kabarinta badai ta sanarma wani ba."
Basira tace "me kake nufi? Kasan halin Magajiya fa?"
Yace " Nasani Umma sanin ne ma ya sani fad'in haka, sirrinki datake tunanin amfani dashi wajen hanani auren Bilkisu da kuma sa Mai Martaba yin murabus wannan sirrin ba wani abu bane akan sirrinta da nake rike dashi, ke dai kawai ki kula da lafiyar wannan shine kadai abinda nake nema daga gareki."
Kallansa tai cikin jin dadi da gamsuwa tace " maganar Mairo fa?"
Yana murmushi yace " Umman Mairo, wai ni Umma daga ni da alama ba wanda kikeso sai Mairo ko?"
Tace " Turab kenan, kasan yarinyar nan itace ta taimakeni har nakejin zaman gidan nan bai zaman min takura ba?itace ke d'ebe mana kewa daga ni har lantana, jinta nake kamar 'yata."
Turab ya jinjina kai yace " haka ne, shi yasa akoda yaushe nake godiya gareta, na sani ta kula dake wanda ni da nake d'anki ban baki wannan kulawar ba."
Basira ta kalleshi sai dai batai magana ba, sai dai yanayin kalamansa da yanda yake fitowa tasan magana ce wacce ke kwance a kasan zuciyarsa.
Turab ya d'ago sannan yace " karki damu Umma, Insha Allah ba abinda zai faru sai alheri."
Tace " Allah yasa."
Zama sukai shi da Lantana da Basira sukai hira sosai sai da yaji la'asar tayi sannan ya fito.
Yana shiga Garzali ya shigo falon, tare da mikamai maganin nan.
Turab ya kalleshi yace "Maganin menene?"
Garzali yai kasa dakai sannan yace " magani ne wanda zai halaka gab'obin jiki, ya hana mutum yin komai, ya kuma shanye mai b'arin jiki, a takaice dai guba ce mai illar gaske wanda samunta yake da matukar wahala."
Turab idanunsa ya runtse da karfin gaske dan ji yake gaba daya kamar an kwara mai ruwa.
Idanunsa a runtse yace " Ka yarda da sanin mai maganin daka tambaya?"
Garzali yace " kaf garin nan an san dashi dan nima kaini gunsa akai, shikansa yayi mamakin ganina da maganin, sannan ya sanar dani maganin a hankali yake lahanta mutum ba wai tashi d'aya ba."
Turab yace " jeka na gode."
Garzali ya mike yai waje.
Yafi minti goma idanunsa na runtse, wace irin matace wannan? Dan ya tabbatar itace tasa a ba Hajiya maganin nan, amma mahaifiyar mijinta? Wannan wace irin masifa ce?"
Jiyai kansa ya sara, ya mike yai sallah ya dade yana addu'oi kafin ya shiga bandaki ya sakar ma kansa ruwa.
Ruwa ne ke zuba a jikinsa hayi shiru yana tunani, ya dade sosai kafin ya fito.
Shiryawa yai sosai cikin wata dakakiyar shaddarsa ruwan madara, hula da takalmi ya saka sannan ua saka agoggo.
D'ankwalin khadija ya kalla ya dade yana kallan d'ankwalin kafin ya rufe kofar da karfi, takardar daya ajiye a gefen gado.
B'angaren Magajiya ya nufa yana tafe cikin isa.
Yayi sa'a Abdulmajid na zaune a gunta.
Tana jin ance yazo sai dataji gabanta ya fad'i, yauce rana ta farko data taba jin shakkar zuwan wani d'an adam gunta ba sai yau.
Ba shakka wannan abu ya kona mata rai.
Abdulmajid yace " ya shigo."
Turab ya shigo tare da sallama.
Abdulmajid ya bugamai banzan kallo yace "ina zakaje haka?"
Turab ya kalli Magajiya sannan ya kalli Abdulmajid yace " zance zanje."
Abdulmajid ya tab'e baki sai kuma ya zabura yace"badai gun Mairo ta ba ko?"
Turab ya kalleshi sannan ya maida idanunsa kan Magajiya datake kallansa yace" yau ba gunta zanje ba, gun Khadija zani."
Tashin hankalin daya bayyana a idanuwan Magajiya ba'a magana, Kallansa tai tace " me? Khadija? Ba dai Khadija wacce take 'ya ga yayana ba?"
Turab ya d'aga mata gira sannan yace " ya? Kin sanar ma Sarki akan maganar lefe na?"
Abdulmajid ya sheke da dariya yace "Lalai Turab amma kai ba karamin had'amamen mutum bane, kana tunanin soyayya da aure wata a lokaci d'aya?"
Turab yai murmushi yace " ba'ayi ne? Da farko dai ni d'in mijin mata hud'u ne banda kwarkwarori."
Abdulmajid yace " wannan damuwarka ce sai dai ka fita hanyar kanwata dan badai yar uwata ba kai ko kunya ma damu zaka had'a zuri'a?"
Magajiga kam kallansa take cikin idanunta da suka canza kala wanda bakin ciki ne karara ne d'auke a idanun.
Turab ya kalli Abdulmajid sannan ya kalli Magajiya tare da ciro ledar maganin nan. Ruwan dake gaban Andulmajid ya jawo ya zuba a kofi sannan ya zuba maganin nan.
Magajiya ta kalleshi tace " meye hakan kuma?"
Mika mata kofin yai yace " Umma sha."
Wani banzan kallo tamai tace " a gabana ka zuba magani kace insha? Nasan ko maganin halaka ne?"
Kai ya d'an langwab'e yace " kuma fa haka ne, kar in baki maganin dazai kwantar dake ya kashe miki gab'obin jiki sannan ya hanaki magana, ya kuma hana kwakwalwarki aiki yanda ya kamata."
Gabanta ne ya shiga fad'uwa, daurewa tai ta saki murmushi zatai magana Abdulmajid yace" ansha karya, yanzu kai kana tunanin akwau irin wannan maganin a duniya? Sannan in akwai ma mai zai sa ka saku?"
Turab ya kalli Abdulmajid yace " shine ai abin tambayar, Umma ya akai kika samu wannan maganin?"
Kallansa tai tare da fito da idanuwanta, daurewa tai tai wani dariya tace " Turab kenan, kanasan zolaya, yanzu ka shigo da magani kace ni na baka?"
Turab yace " kin manta? Ke kika bani a sanda muka had'u a b'angaren Hajiya?"
Magajiya tace " ni bansan wannan zancen ba, sannan mai zai sani in baka?"
Yace " shine abin tambayar? Mai zaisa ki bani? Sannan me na tare miki da zaki bani irin wannan abin? Karfa ki manta nid'in d'a ne a gunki."
Idanu suka kafama juna dan magana ce suke yinta a juye wanda su biyu ne suka san me suke nufi, ita tasan Turab sanar da ita yake abinda ta sa akeba Hajiya, shi kuma so yake yaji menene dalilinta na neman halaka kakarsa? Wacce take uwa a gareta?
Abdulmajid ne ya kallesu, kana kallan yanda suke kallan juna kasan kallo ne mai tatare da ma'anoni kala kala, hannu yasa ya daki kafadar Abu Turab yace " Turab bakada hankalu ne? Umma kakema wannan kallan?"
Magajiya ta juya kai sannan ta kalleshi tace " bansan me kake cewa ba Turab."
Yace " wasa nake yi nima, ya maganar lefen?"
Tace " na d'auka mungama wannan maganar hakki nane a matsayina na mahaifiyarka ai inyima lefe."
Yace " haka ne, yauwa bari na kira Gimbiya na tabbata ta damu da jina shiru tunda na dawo, bari nai amfani da wayar b'angarenki."
Magajiya ta gama cika fal, Abdulmajid mamaki ma ya hanashi magana, kallan sa yai harya mike yai falonta, sannan ya kalli kofin ya d'auka yana kallan ruwan ciki, yace "Umma me wannan yaran yake cewa?"
Sam bataji ma me yake cewa ba dan ta tafi dogon tunani.
Kallanta yai ganin yanda ta tafi tunani ya sa jikinsa yai sanyi, bai taba ganin ta haka ba, me ke faruwa? Me zaisa Ummansa tama Turab lefe bayan tasan yanda ta tsani auren nan?
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*60*
Abdulmajid ya kara kallan Magajiya yace " Umma wai meke faruwa?"
Tsawa yaji ta dakamai tace " Fita ka bani guri."
Tsananin mamaki ne ma ya hanashi d'auke ido daga kanta, me yai? Yauce ranar daya tabaji tamai tsawa haka balle ma akan wani Abu Turab?
Mikewa yai rai a b'ace yai waje.
Ko bi ta kansa batai ba ta sa kafa tayi ball da wannan kofin, mikewa tai ta nufi falonta.
Turab kam number Bilkisu ya danna, ta dade kafin a d'aga, gaisheshi akai sannan akace wanene?"
Turab yace " Ina Gimbiya?"
Daga can akace bari a sanar mata, waz'ace?" yace "Abu Turab."
Da sauri mai maganar ta gaisheshi sannan ta ajiye kan wayar a gefe tai cikin d'aki da sauri.
Gimbiya na Kwance rike da wani littafi tana karantawa.
Bayan yarinyar ta nemi izini ta shigo ta tsugunna sannan tace "Gimbiya, yarima ne ya kira waya."
Mikewa tai zaune da sauri tace " Turab?"
Yarinyar tace " eh Gimbiya."
Da sauri ta juya zata sauko, sai kuma ta koma ta zauna tace jekinkice ina zuwa.
Yarinyar ta amsa da to sannan ta mike.
Bilkisu sai da ta d'an dade a zaune sannan ta sauko a hankali ta fito.
Sallamar duk masu kula da ita wad'anda ke falon tai sannan ta d'auki wayar, cikin kasalaliyar murya tace " Barkanka da Warhaka."
Turab wanda yasan dolene ya jira saboda mulki, yai murmushi sannan yace " na d'au lokaci kafin na kira Gimbiya, ina fatan za'amin afuwa."
"Hmmm za'a duba uzurunka sai a maka."
Turab ya kalli kofa dan yasan tabbas Magagiya zata leko dan ganin me yake yi.
Gefen fuskarsa ya d'am shafa sannan yace " Abubuwa ne wad'anda nikaina banyi tsamanni ba suka dinga bulbulowa wad'anda suka rike tunanina."
Tace " Hmm yanzu fa? Ka warware komai?"
Yai shiru, hakan yasa tace " Karka damu nasan zaka iya, koma menene, kardai kacemin baka yarda da kanka ba?"
Turab ya kalle gefen kofa inda ya hango inuwar Magajiya, yiyai kamar bai ganta ba, murmushi yai sannan ya gyara zamansa irin mai jin shaukin nan yace " Kuma fa haka ne, ya kamata in zama mutum na farko mai yadda da kansa."
Tace " A koda yaushe ka dinga tunawa ina tare da kai akan komai, duk da ayanzu bazan iya taimaka maka ba, bazan kuma iya kula da kai ba sai dai inaso kasa a ranka akwai wacce take tare da kai a koda yaushe."
Har zuwarshi sai da yaji wani sanyi ba shakka Bilkisu macece wacce ta san kanta ya tabbata zasu zauna lafiya, sannan yana ji a jikinsa ita alheri ce a gareshi.
Jiyai tace " kayi shiru? Ba dai kalamai na......"
Katseta yai da sauri yace " wannan layin nawa ne bance ki fada ba."
Tace " layin me?"
Yace " Kalamanki sun ratsani na kuma ji dadi, ba haka zaki ce ba?"
Bata san sanda tai dariya ba, tace " mene? Haka nace ma?"
Yace " sosai ma."
Gani inuwar Magajiya yai ta juya.
Fuska ta rufe kamar yana ganinta, Turab yace " zan kiraki zuwa ko zuwa anjima ko zuwa gobe."
Tace " Karka damu dani, yanzu ma da mukai magana ya isa, duk sanda ka samu sarari ka kirani."
Yace " Nagode, ki gaida Munnira."
Bai jira ta amsa da to ba ma ya ajiye kan wayar sannan ya mike.
Magajiya kam ta gama kuluwa da alama ma soyayya suke da yarinyar, itakam duk duniya ba wanda ta tsana yanzu irin wannan dan banzan yaran, ko ganinsa batasan yi, wai kamar ita ace ta zauna yaro yana raina mata hankali? Dolene ta nemi abinda zatai amfani dashi ko da yake ai ta shirya da auransa hmmm tai kwafa tace a ranar aure ka zai kasance jana'izar ka.
Ta na kokarin shiga d'akinta yace " Umma me kike anan?"
Juyowa tai fuskarta a had'e sai kuma ta saki fuska tace " Na d'auka ka tafi ai, ashe kana ciki?"
Turab yace " na d'auka zakizo ku gaisa da sirikarki, ko zaki koma in kira miki ita?"
Idanunta ne suka canza har fuskarta sai data nuna bacin ranta, daurewa tai ta saki yake tace " Meye abin azarbabi bayan nice shugabar kai lefe?"
Kai ya jinjina sannan ya dawo gabanta, fuskarsa a hade tare da kallanta.
Kallansa tai tace " ya akai kuma?"
Wani banzan murmushi yai yace " maganinki da kika sa a dinga sama Hajiya ina tunanin sai kinsa a nemo wani."
Idanunta ne sukai rawa alamar mara gaskiya tace " me kake fada?"
Yace " ba abinda nake fada ina dai sanar dakeni duk wanda ya maida Hajiya haka wallahi wannan rantsuwa ce nai bazan taba kyaleshi ba, sai na sa anmai hukunci daidai da abinda ya aikata, ko da kuwa Umma tace Basira ta aikata hakan, duk da nasan bazata taba zalintar d'an adam ba kamar wasu."
Magajiya ta kalleshi sannan ta saki wanj banzan murmushi na rainin hankali tace " Ko nima zan tayaka d'aukan hukuncin, sai dai ka tabbatar kana da karfi na hukunta mai laifin? Ba wai karfi na jiki nake nufi ba."
Turab ya kalli kwayar idanunta yace " Ahhh to wa ya sani?" sannan ya murmusa yace " kece kika sa aka fara game d'in, sai dai ni nake da ikon tsayar dashi, sannan inaso ki tabbatar idanunki na nan a bud'e har sanda zan tsayar da wasan, zakiga inda mara karfi yake kaskantar da masu karfi."
Magajiya tama kasa magana kallansa kawai takeyi.
Turab ya juya ya fara tafiya, har yayi nisa ya juyo yace " Ahh ki gaida Khadija banaji zan iya zuwa yau ba, ko da yake bata sani ba."
Kallansa tai cikin takaici tace " Kana tunanin ita Khadijan yarda zatai dakai?"
Wata dariya ya saki yace " Khadijan? Kin tabbatar Khadijan da kika sani kike fad'a? Ahh Umma ya zakiyi? Dan Khadija ba sai na tambayeta ba dan nasan abinda ke ranta."
Ya juya.
Jiyai tace " Lalai na yarda yarinta na damunka kanka kuma na rawa, ya zakayi to? Dan kuwa an kusa sa ranarta da Saifullahi."
Bai san me yasa ba amma sai dayaji wani abu ya taba zuciyarsa.
Sai da ya daure ya juyo fuskarsa d'auke da murmushin da yake iya lab'ansa yace " ai mace sai anyi aurenta an shafa fatiha ake tabbatar da mijinta."
Ya juya ya fita.
Agogon dake manne a bangon gun tasa hannu ta fizgo sannan ta bugashi a kasa, kanta ta dafe sannan ta shiga d'akinta, da karfi ta bugo kofar.
Ji take kamar ta saki kara.
**********
Turab na fita ya dafe kansa, ba shakka matarnan bala'ice, wacce mutum zai dinga neman tsari da ita (irinsu sai a karshe zakaji suna cewa sharrin shaid'an ne)
Khadija ya hango daga nesa, tafe take kamar mara laka a jiki, da alama batajin dadi.
Me ya sameta?
Juyawa yai da sauri dan bama yasan zuciyarsa ta nemi yin rawa saboda ita.
Ganin ya juya zai wuce yasa ta tsaya cak, idanunta ne suka ciciko dan taga da alama goje mata yake sanyi, ita kanta bataso shigowa ba sai dai dolene ta fadama Magajiya akan bazata auri Saif ba, ita dai su barta ta karashi rayuwarta a haka, inta tunan mumunan abunda suka aikata ji take baxata iya kallan wata zuri'ar da sunan mutum na gari ba.
Ko me ya tuna sai kuma ya juyo, kallan kallo sukayi daga nesa.
Juyawa yai a hankali ya fara tafiya.
Bata san tana binsa ta baya ba, ji take ganinsa kamar yanasa taji abinda ke tokare a ranta na raguwa.
Yasan tana binsa sai dai ya rasa dalilinsa na nuna mata bai sani ba, sannan ya rasa dalilinsa nayin tafiya a hankali cikin saibi.
Har ya isa bangaren Hajiya.
Yarinyar nan ya gani tana shara, kallanta yai yace " ajiye tsintsiyar ki kuma biyoni."
Gabanta ne ya fadi ta kalleshi tace "Yarima laifi nai?"
Wani mugun kallo ya mata, da sauri tai kasa da kai tace "Tuba nake Yarima."
Ajiye tsintsiyar tai tabi bayansa.
B'angaren sa ya nufa da ita, suna shiga cikin falo ya d'aga hannu cikin zafin rai zai kai mata mari, idanunta ta runtse dan ta gama sadaukarwa.
Saura kiris ya mareta sai kuma ya tsaya cikin tsananin b'acin rai.
A hankali ta bud'e idanunta ta tsugunna da sauri tace " Tuba nake ranka ya dade."
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*61*
Jin bataji saukan mari ba yasa ta bud'e ido a hankali, kallansa tai sannan tai saurin zubewa a kasa ta saki wani irin kuka.
Turab idanunsa ne suka canza, kallo d'aya zakamai ka tabbatar da tsantsar b'acin rai, maganin nan ya cilla mata.
A tsorace ta d'ago jiginta ya hau karkarwa.
Cikin kakkausar murya yace " Waye ya saki?" ba wai dan baisan amsar bane, a'a yanaso yasan ko tana danasanin abinda takeyi.
Kasa ta karayi tana kuka sosai tace " Ranka ya dade ka yafe min wlh in na fad'a kasheni za'ai, sannan mahaifina karshensa yazo."
Magajiya? D'agowa tai da sauri jin abinda yace, yanayin kallan da tai yasan dama abinda yake zargi haka ne, kusa da kafaffunsa ta matso tace " Ranka ya dade wlh nima ba'a san raina nakeyi ba, mahaifina na bukatar aiki na gaggawa a asibiti shine akace in ina sa maganin nan za'a biyamai kud'in aiki, sannan komai ua faru in sanar da ita.
Fuskarsa ya shafa da hannayensa biyu a ransa yace Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.
Zama yai a kan kujera sannan yace " me ya faru tsakanin Hajiya da Magajiya?gaskiya nakeso ki fadamin, ni zan taimakeki, zan kuma bayar da kudin aikin."
Tana kuka ta girgiza kai tace " wlh ban sani ba, nadai san a ranar da Umma Rabi tazo a ranar ta aika a kira Magajiya, sannan daga ranar aka fara sani aikin."
Turab ya kalleta yace " naji, zan sa Lantana ta koma dake bangaren Hajiya da kula da ita, zan gani ko kinyi dana sanin abinda kika aikata, sannan ki jira hukuncin da zansa a yanke miki, mahaifinki ni zan taimaka mai sai dai ke dole ki fuskanci hukunci."
Kuka take sosai tace " na sani Ranka ya dade, na gode kwarai da cetoni da kai daga cikin masifa."
Turab yace ta tashi ta tafi.
Fitowa yai, ya nufi can cikin gida bangaren kannen mahaifinsa dan zuwa gun Umma Rabi.
Ko Garzali baya yarda ya biyoshi duk da kuwa ya yarda da shi.
*********
Khadija kuwa ganin Turab ya shiga bangaren Hajiya yasa ta juya.
Har zata wuce bangaren Abdulmajid sai kuma ta karkata ta shiga.
Bayan an sanar da zuwanta, Abdulmajid dake zaune abin duniya ya dameshi yace ta shigo.
Khadija ta shiga, kallan bangarensa tai sannan a ranta tace " yafi na ya Turab kyau sosai, da ban kula da hakan ba amma yanzu na gani, ya zakai in kaji kai ba toshen gidan nan bane?"
Idanu ta kura mai tana wannan tunanin, ji tai tsananin tausayinsa ya kamata.
Batasan ma ya miko yazo kusa da ita ba, sai jitai yasa kafa ya d'an harbota.
Kallansa tai tace " Yaya."
Abdulmajid ya hard'e hannayensa ya shiga zagayeta yana kallanta yace " me ya kawoki? Ba dai zuwa kikai akan rabamu da Mairo ba?"
Hannu tasa ta riko rigarsa tace " Yaya wannan zagayen fa? Ai sai jiri ya kamani."
Murmushi yai sannan ya koma ya zauna.
Kallansa ta karayi a ranta tace " ya ya zanyi? in har kaji abinda suka maka wace rayuwa zaka shiga? Alokacin ba ka da wanda zaka gani kaji dadi, komai da kake tunanin naka ne a lokacin xakaga babu abu ko d'aya daya kasance naka, dama ace Mairo na sanshi ne....."
Khadija meye hakan?
Abinda ya fadane ya dawo da ita daga tunaninta.
Fara'a ta saki sannan tazo ta zauna kusa dashi tace " Yaya."
Ya kalleta yace " menene? Nifa na fara shakkar me kikazo dashi naga sai wani kafeni da ido kikeyi."
Murmushi tai tace " yanzu ace kai ba dan sarki bane wace rayuwa kake tunanin zakai?"
Dariya ya saki sosai yace " ban taba wannan tunanin ba, dan tun ina d'an shekara uku Umma ta fara horar dani akan magajin sarki, kinga kuwa banda wannan lokacin."
Khadija ta jinjina kai tace " Haka ne, amma ka taba tunanin rasa mulki?"
Wani kallo ya mata yace "Khadija meke damunki? Kinsan tun ina dan shekara uku Umma take sanar dani ni kadai ne magajin sarki, shi kanshi Abba a lokacin nunamin yake nine magajinsa, a haka na taso har sai bayan zuwan Turab sannan na fahimci canji daga gun Mahaifina wanda hakan na kona min rai, sam ya daina wasa dani gaisuwa ce kawai ke had'amu, bayan da shi dakanshi yake aikawa a kirani."
Yai wani murmushin takaici yace " Khadija duk wani abu na rayuwata a da ina yinsa ne dan faranta ran mahaifina, burina naga ya dubeni yacemin Abdulmajid kayi daidai, sai dai inaa duk wani abu dazanyi bana birgeshi, ko jarabawa ta na kawomai banaji ma yana bud'ewa...."
Wani abu ya had'iya sannan ya kalleta, hawaye ne yaga ya zubo mata.
Harararta yai yace " tausayi na kike?"
Shiru tai batace komai ba.
Yai murmushi yace " tundaga lokacin na tsani Abu Turab tsana mai yawa sannan akoda yaushe Umma na sanar dani shi din fa makiyinane, kar na kuskura ba barshi."
Yai ajiyar zuciya yace " kinsan me?"
Kai ta girgiza alamar a'a
Ya matso alamar rad'a yace " ko kiran mata da nakeyi bangarena yi nakeyi dan in batama Sarki yai ko naki dadin rashin damuwa dani dayakeyi."
Idanu ta rufe a hankali wasu zafaffan hawaye suka biyo mata, kallanta yai yace " Karki damu Khadija, na saba da rayuwa, kinsan tunda nake a gidan nan ba wanda ya taba tambayata ya nake? Tambaya ta kulawa, ina nufin Umma na ko Abba na, ita burinta shine in zama abinda takeso, shikuma dama bana cikin shafinsa."
Hawayenta ta share tace " Yaya me yasa baka taba fad'amin ba?"
Dariya yai sannan ya mike yace " na fizan na zama bad guy, hakan ne zaisa in rage takaicin abinda ke raina, sai dai Khadija kiyi hakuri amma bazan taba ba Abu Turab Mairo ba, ya kwacemin uba, mutane, na bar masa amma banda wannan."
Jitai tama kasa magana, me yasa itama a koda yaushe takejin zafinsa? Gani take baya kyautawa sannan shidin mutumin banza ne? Ashe bakincikin dake ransa ne yake amfani dashi dan kuntatawa na kusa dashi? Ya zaiyi in yaji sirrin nan?
Daurewa tai tace " Yaya kana tunanin Mairo zata soka? Bayan kai din mutum ne wanda yake had'uwa da Magajiya su aikata abinda bai daceba na zalunci?"
Yace "Ahhh zalunci? Hmmm Khadija kenan bana tunanin kinsan Umma."
Kallansa tai tace " bansan ta ba sannan bana bukatar Saninta, sannan kaima Yaya zuciyarka na neman riked'ewa gaba d'aya ta koma ta Umma, ka gaggauta kaucewa daga sharrinta."
Murmushi yai sai dai baice komai ba, a ransa yace "hakan na nufin in bijiremata ita kuma ta yarda ni, ita kadan da nake sa rai tana sona itama ta juyamin baya."
Khadija ta mike tare da kallansa tace " Yaya zanje gurin Umma Magajiya ne, akan maganar aurena da Saif."
Yace " Ya ya? Maganar auren an kusa ne?"
Kai ta girgiza tace " a'a."
Juyawa tai ta fita, aranta tana mai fatan kub'uta daga sharrin Magajiya da Mahaifinsu."
********
Falon yai tsit kamar ba kowa a ciki, Umma Rabi tai shiru kamar ruwa ya cinyeta sannan ta d'ago ta kalleshi.
Abu Turab yace " Umma ki taimaka ki sanar dani, Hajiya na cikin wani hali."
Tace " Turab sirri ne...."
Yace "wa ke zancen Sirri rayuwar Hajiya na cikin had'ari?"
Umma Rabi tai shiru kafin can ta d'ago ta kalleshi.
Nan ta sanar da shi abinda ta sani.
Shiru yai kafin yace "ita waccan d'in wacece? Wacce ta aiko da wasikar?"
Umma Rabi tace " ban santa ba sai dai kafin Hajiya ta fara rashin lafiya da yamma na koma gunta, a lokacin ne ta sanar dani wani sirri wanda ahi nake tsoron sanar dakai."
Yace " na menene?"
Ta dade batace komai ba, yace Umma dan Allah ki fadamin.
Tace " ka tabbatar zaka iya ja da Magajiya?"
Yace " kwarai kuwa."
Yanda yai maganar ya bata kwarin gwiwa tace " Maganin da ake zubawa sarki na hana d'aukan ciki ne."
Tashin hankali.
Bakinsa ne ya shiga rawa yama rasa mai zaice.
Umma Rabi ta kalleshi sai dai itama batasan me zatace mai ba, a hankalu tace " ni kaina ina zargin ciwon Hajiya da Magajiya, sai dai banida shaida sannan bansan wa zan tara da maganar ba."
Turab mikewa yai kamar wanda bashida laka a jikinsa.
Tafiya kawai ya keyi yana tunanin wannan al'amari.
Jiyai kansa ya d'au wani zafi, tsayawa yai a jikin wata bishiya ya dafata, addu'a kawai yakeyi Dan neman sauki a zuciyarsa.
Ya dade sosai kafin ya nufi bangaren Hajiya.
Hajiya kam babu, dan jikinta ba dadi to abune da anriga an gama halakata, ba shakka bai taba ganin mutum irin Magajiya ba, kenan duk wanda yasan sirrita ajali shine zai biyoshi?
Kallo d'aya zakama Hajiya kasan inaa sai dai wani ikon Allah.
***********
Magajiya na kwance a d'aki dan tun tafiyar Turab takejinta haka, a kwance take taji sallamar Khadija.
Daurewa tai ta mike zaune, Khadija ta shigo.
Bayan ta gaisheta, Magajiya tace " Khadijata ina kika shiga? Kwana biyu sam ban ganki ba."
Khadija fuskarta a had'e tace "Ina gida."
Magajiya ta kalleta cikin kulawa ganin duk ta rame, tace " Khadija mai kike tunani akan dawowa nan da zama kafin lokacin aurenki?"
Khadija ta kalleta duk da gabanta na fad'uwa saboda tsananin kwarjini da Allah yaba Magajiya ta daure tace " Dama zuwa nai in fadamiki akan bazan auri Saifullahi ba."
Magajiya ta zaro ido tace " mene? Wace irin banzar magana ce hakan?"
Khadija tace " dama abinda nazo fadamiki kenan."
Magajiya ranta ya b'aci tace " Akan Abu Turab?"
D'agowa Khadija tai ta kalleta, Magajiya tace " ke kina tunanin zan baki Abu Turab?"
Jitai zuciyarta ta dake tace " ina fa zance Ya Turab zan aura? In ba so nake ku halakashi ba?"
Magajiya ta kalleta cikin tsananin takaici tace " in kin san da haka to kiyi gaggawar cireshi a ranki."
Khadija jitai ranta ya b'aci wato duk abinda sukeyi baya damunsu? Tace zasu halakashi amma ko a jikinta.
Sun biyu suna neman ruguza rayuwar mutane dayawa, na farko sun gama cin amanar sarki, sun jefa Abdulmajid cikin halaka, suna neman jefata sannan sun takurawa wanda yake jinin gidan, suna neman halakashi.
Ita kanta batasan tace " To ko Ya Abdulmajid zan aura."
Jitai gabanta yayi wani fad'uwa, mikewa tai tace " wani irin hauka kike fad'a, bakida hankali ne? Ko kanki me ya zare?"
Khadija tace " in har ba Ya Abdulmajid ko Ya Turab zan auraba inaso ku barni, banaji zan yi aure har karshen rayuwata dan bazan iya auren wani da hali irin na mahaifina ba."
Magajiya tace " Khadija? Me kike cewa?"
Mikewa tai saboda ta fara jin dakewar tata na neman gazawa tace " na barki lafiya."
Magajiya mamaki ma ya hanata magana sam, anya Khadija ce? Ba waccan tsinanen yaran bane ya zigata kuwa? Yace tace a aura mata Abdulmajid?
Jitai idanunta sun daina ganin komai sai duhu, baya tai lyuuu kamat zata fadi sai kuma tai saurin rike gadon tana maida numfashi.
Cikin wata sarkakiyar murha tace " *ABU TURABBBBBBBBB*"
Nima na tayata fada *ABU TURAB😂*
*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*62*
Khadija tana fita ta samu guri a waje ta xauna, jitai jikinta duk ya kaure da rawa, ba shakka wannan ce rana ta farko da tai tafa kukewa tai ma wanda ya girmeta magana irin haka, balle Magajiya mace mai tsananin kwarjini da mulki.
Mikewa tai a hankali, so take ta samu Abu Turab taji a wani mataki na aure ya d'auka tsakaninsa da Mairo? Dan ba shakka tana san d'an uwanta ya aureta ko dan ranar da wannan sirri ya bayyana ya zama akwai wanda zai gani yaji dadi, ta tabbata in tai magana gani za'ai kamar kishi ne ke damunta sai dai ko d'aya, tasan akwai kishi na wanda take tsananin so shikuma ba ita yake so ba, sai dai a yanzu burinta tai kokarin ganin ta gyara wani abu ko yaya ne na daga cikin laifukan da aka aikata.
Bangarensa ta nufa, har takai hannu zata kwankwasa ta fasa saboda batasan da wace kalmar zata fara masa magana ba, a hankali ta juya cikin damuwa.
Idanu ta zaro, kallanta yai sannan ya kalli kofar, miyau ta had'iya sannan tace " Ya Turab."
Kallanta ya sakeyi sannan yace "Lafiya?" daga bangaren Hajiya yake sam bayasan magana.
Khadija tai shiru tana wasa da hannayenta, tunanin abinda zata cemai takeyi.
Ta gefenta ya wuce zai shiga ciki ganin batada niyyar magana.
Itama ganin haka yasa tai saurin cewa "Magana nakeso muyi."
Juyowa yai ya kalleta sannan ya kauda kai yace "Banaji akwai wata magana da zamuyi."
Kasa tai da kai tare da jinjina kai cikin rashin jin dadin abinda ya fada tace " haka ne, na tabbatar ba wata magana datai saura tsakaninmu, sai dai inaso ka bani ko minti goma ne."
Harshensa ya zaro kadan ya d'an lashi lab'ansa da suka bushe yace muje.
Mai makon yai ciki sai taga ya juya ya fara tafiya.
Bata tambayi inda zasuba itama binsa kawai tai a baya.
A hankali suke tafiya yana gaba daga gefen dama, ita kuma tana bayansa daga gefen hagu, tafiya kawai yakeyi. Yana kara tattaro duk wani tugu da ya sani wanda Magajiya ta aikata ita da yayanta wanda ya kasance mahaifin yarinyar dayafiso a rayuwa.
Ta yaya zai iya zaman aure da ita ko bayan komai ya kamala? In har ya sa akama mahaifinta da Magajiya hukunci ta yaya zai iya kallanta da sunan soyayya? Itama ta yaya zata iya kallan wanda ya ruguza rayuwar gidansu da sunan soyayya? Ai duk san da takemai bai kai na iyayenta ba, shima haka, duk sanda yake mata bazai taba kwatanta shi da wanda yakema mahaifiyarsa ba.
Juyowa yai ya kalleta, ganin irin kallan da yake mata yasa jikinta yai wani irin sanyi.
Baice mata komai ba sai nuna mata inda zasu shiga dayai.
Kallan gurin tai, inda ya ke hutawa ne, sai daya shiga ta bi bayansa.
Can yaje ya zauna akan kujerar dake gun.
Rasa inda zata zauna tai dan kujerar gud'a d'aya ce a gun doguwa.
Kallanta yai sannan ya mata alama da kai akan ta zauna daga gefe.
Nan ta zauna, ta d'an kalli sararin samaniya, kasancewar yamma ce garin yayi luf abin sha'awa, bare lokacin na zafi ne, iska tana kad'awa a hankali.
Jitai yace " ina jinki."
Khadija ta kalleshi kallo na tsananin kauna, inama lokacin da suke yara ya dawo? Lokacin da suke kullum tare, cikin tsananin bege da kulawa.
Kin kafeni da ido bakice komai ba.
Khadija ta kakaro murmushi tace " Ba fara'a yanzu a tsakaninmu."
Kallanta yai sai dai baice komai ba ya maida kansa inda yake kallo da.
Murmushi ta sake yi na tausayin kanta cikin wani yanayi ta fara cewa " sa dayawa ina tunanin ina ma, ina ma ban sanka ba? Ina ma banida had'i da wannan gidan? Inama da naje kano ina karama ban dawo ba."
Tacigaba bayan ta d'an had'a hannayenta gu d'aya.
"Yaya na rasa wace irin mummunan kaddara ce tsakaninmu? Banida abinda xancema na abubuwan da mahaifana suka aikata, bani kuma da bakin baka hakuri akanshi, sai dai zam baka hakuri akan abubuwa gudan biyu."
Hawayene suka zubo mata ta sa hannu ta sharesu tace " Yaya kayi hakuri akan abinda Ya Abdulmajid ya maka, ba wai ina baka hakuri bane dan ka yafemai a'a ina baka ne saboda neman sassauci akansa, ina tsananin tausayinka sai dai ina tausayin Ya Abdulmajid."
Juyowa yai ya kalleta, da alama tasan komai, dama ranad da ta fad'o musu gaban mota tai wannan firucin ya tabbata akwai wani abu da ya sani."
Idanunsa na kanta yace " kin san komai kenan da alama."
Hawayenta ta sake sharewa tace " Yaya wancan sokon yayan nawa baisan komai ba, baisan abinda suka aikata mai ba, tunda yake bai taba keran wacce ta d'au cikinsa na wata tara da sunan uwa ba, bai taba yi mata wani abu ba wanda d'a ya kamata yama uwarsa ba, ko magana tamai gani yake matsayinsa ya wuce a nemi bashi shawara, wancan soko yaya baisan matsayin da yake takama dashiba ba nashi bane, matar da yake kokarin faran tawa rai a koda yaushe baisan amfani take dashi dan cikar burinta bawai dan so ba, Yaya Turab sannan wancan sokon ya gama mutuwa akan san wacce bata sansa, tunda yake a rayuwarsa banaji akwai mutum d'aya wanda ya kasance yana kaunarsa kauna ta yanda yake bawai dan tushensa ba ko dan halayensa ba,yaya wancan sokon d'an uwa nane jini nane wanda ni kaina......."
Kuka ne ya ci karfinta wanta take yinshi daga cikin zuciyarta kuka mai taba zuciyar mai sauraro.
Duk yanda yaso ya jure ya kasa dan kukan sosai yake taba ransa ba shakka shi kansa yana tausayin Abdulmajid, mikewa yai ya nemi hanyar fita.
Cak ya tsaya dan jiyai bazai iya fita ba tana irin wannan kukan.
Handkerchief ya zaro daga cikin aljihunsa na wando ya nufo inda take.
" Ungo." abinda ya fada kenan yana mika mata.
A hankali ta d'ago sannan tasa hannu ta amsa.
Juyawa yai zai fita, da sauri tasa hannu ta riko rigarsa.
Turab ya tsaya sai dai bai juyo ba.
Saukowa tai kasa ba tare da saninsa ba ta sanya gwiwowinta biyu a kasa.
Tace " Ya Turab."
Juyowa yai kallan mamaki ya mata gani gwiwowinta biyu a kasa.
Yace " meye hakan?"
Tace " kasa ama duk wani laifi a cikinsu hukunci sai dai dan Allah yaya ka hakura kaima da abu d'aya, kana da komai a rayuwarnan.
Mulki, uwa ta kwarai, mata, sannan dukiya da ilimi da kuma masoya, dan Allah ka sadaukarwa Ya Abdulmajid da abu d'aya na daga cikin wad'an nan abubuwan da Allah ya azurtaka dashi ka bar masa Mairo kad'ai, ita kadai, in tana tare dashi gani nake ko wani abu ne zai sameshi zai jure sannan ko wani hukunci aka mai zai yi kokarin jureshi."
A hankali ya furzo da wata iska sannan yasa hannayensa biyu ya d'agota, kallanta yai ido cikin ido, yace" bazan yi miki dogon bayani ba, ba kuma zanyi duk wani abu da kikeso ba, abu d'aya na sani shine duk wani mai laifi zan sa a hukuntashi indai da raina, akan ganin bayan Magajiya even u i will have to use u."
Ba tare da wani tunani ba tace " use me ya Turab, kayi amfani dani ta kowace hanya da kakeso, bazai damen ba, me kake tunanin zanyi?."
Wani murmushi wanda ni kaina bansan ma'anarsa ba yai sannan yace " even if i hurt u?"
Kallansa tai sannan ta ce " please yaya hurt me."
Shiru yai yana kallanta dan tabbas kalmar data fada har zuciyarsa ya jita.
Murmushi ta mai sannan tace " Yaya a koda yaushe zam kasance mai ma addu'a."
Wuceshi tai ya fara tafiya, tana tafe hawaye na zubo mata, ji take kamar yau shine rana ta karshe da zasuyi magana irin haka, itakam tasan farinciki? Bataji zata sameshi a duniya.
Idanu ya runtse dan tabbas yana bala'in san Khadija, ya tabbatar yauce rana ta karshe da zasu zauna kamar haka, Allah ka bani ikon yin abinda ya dace, abinda ya fada kenan sannan ya juya.
*********
Duk yanda taso tai bacci ta kasa, juyi kawai take a kan gado tana tunanin abinda ya cancanta.
Tabbas dolene ta gajarta rayuwar Abu Turab, a ranar auransa dolene ta kaudashi ko ta samu salama, duk sanda bacci ya d'auketa sai taga Abu Turab a gabanta ya sa hannu ya shake mata wuya, dole ta tashi daga barcin.
Wannan abu ya dameta.
Da safe ta shirya tsaf dan ta gama yanke hukuncin yin komai da Abu Turab zai umarta na lefensa har ta samu a zo bikinshi ita kuma ta sa Hisham ya aiwatar da abinda ya dace.
Sai yamma ta samu nutsuwa dan tana ta yin aike.
Ta zuba abinci zataci kenan aka sanar da ita zuwan Abu Turab.
Ta rasa dalili duk sanda taji zuwansa kwanan nan sai taji gabanta na fad'uwa.
Mikewa tai ta gyara jikinta dan batasan ya fahimci wani abun.
Zama tai irin zaman data saba.
Turab ya shigo sannan ya gaisheta.
Amsawa tai cikin isa sannan tace " ya akai?"
Murmushi ya sakar mata yace " na d'auka farin ciki zakiyi da ganina? Banji dadi ba ganin ba kiyi farincikin zuwana ba."
Tace " ina fa? Ka taba ganin inda uwa tayi bakin ciki da zuwan d'anta?"
Yace " haka ne fa kuma, ya an fara had'a lefen?"
Ta kalleshi sai dai batace komai ba.
Yace " Jiya naga Khadija ai, nan tazo ko ganina tazo yi kadai?"
Magajiya wani abu ne yazo mata ta kalleshi tace " gunka ta fara zuwa kafin tazo nan ko?"
Turab ya kalleta dan bai fahimceta ba, tace " ai na sani, dama ni nasan yarinyar nan da ba ruwanta ba yanda za'ai tazo min da wannan banzan zancen."
Turab ya fahimcu Khadija magana tai da Magajiga wanda da alama abin ya sosa ranta.
Yace " hmmm ai banyi tunanin wannan abin zai b'ata miki rai ba......"
Magajiya tai dariya kadan tace " kana tunanin in ka zugata karta auri saif zan amince dakai ne? Meye manufarka da neman had'a auran ta da Abdulmajid?"
Sai yanzu ya fahimta baisan sanda yai wata dariya ba, Khadija? He can't believe that naive girl can......
Magajiya ce ta katseshi da cewa " In har kanasan Sirrin mahaifiyarka da kuma auranka ya yiwu karka kuskura ka kara sa Khadija cikin al'amuran mu."
Turab ya kara murmusawa yace " me? Akwai wani dalili ne dazai hana auransu?"
Idanu ta zaro tace " baka da hankali ne?"
Ya dan tabe baki yace " ban fahimta ba? Akwai dalili ne?"
Magajiya ta kalleshi tace " ba wani dalili kana san ka hadasu aure bayan ba san juna suke ba?"
"Ooooo soyayya? Banaji dama a aure irin namu ana neman soyayya, kinsan da haka kike neman had'a Abdulmajid da Gimbiya? Hmm banaji kema auran so kikai."
Mikewa tai da sauri tai wani murmushi wanda yake iya lab'anta tace " in ma hakan ne ina tunanin bakada hakki akan auransu, Khadija da Abdulmajid ina tunanin duk 'ya'yanmu ne basuda had'i dakai."
Turab ya jinjina kai yace " kuma haka ne fa."
Tace " ba sai ka kara zuwa bangarena ba, in na gama had'a lefenka zan aika ma uwarka ta gani."
Ta juya tai ciki.
Turab ya bita da kallo.........
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*63*
Kallansa tai tare da yin ajiyar zuciya tace " wai ni Abdulmajid mai na tsare maka ne?"
Kallanta yai sai dai baice komai ba, tace " saboda kai yanzu ko gaida Umma Basira ba na iya yi, na fadama banaso dan Allah ko ana so dole ne?"
Kai ya rangwada gefe ya sakar mata wani lallausan murmushi yace " Mairo inaso inga kina fada, kyau yake miki."
Rasa ma mai zatace tai ta saki baki cikin takaici tace " Dan Allah nidai na rokeka ka kyaleni."
Abdulmajid ya matso hakan yasa tai baya da sauri dan ta san halinsa.
Sai da takai jikin bango sannan tace " matsa menene hakan?"
Abdulmajid fuskarsa a had'e ya sako fuskarsa saicin kuncinta.
Tsoro yasa tasa hannu biyu a kirjinsa ta turashi.
Hannayenta ya rike yace " Mairo sai yaushene zaki daina wahalar dani?"
Gabanta ne ya tsananta fad'uwa, ga dare ne soron ba haske, tace " ban fahimceka ba, wahalar dakai name?"
Jawota yai saura kiris ta had'u da jikinsa gashi ya rike mata hannaye duka, yakai bakinsa saicin kuncinta kamar wanda zai sumbata, da sauri ta runtse idonta cikin tsananin fargaba tare da sa kafa ta taka mai kafarsa.
Ko gezau baiyi ba sai dayai bakisa daf da kuncinta sai kuma ya saki dariya yace " Mairo kinganki kuwa?"
Gabanta sai wani irin fad'uwa yake ta kalleshi, hannayenta ya saki yana cigaba da dariya yace " sry, wlh ba abinda zan miki kawai so nake naga yanda zakiyi."
Lab'enta na kasa ta ciza sannan ta sa kafarta ta kara taka kafarsa da karfi.
Kara ya saki sannan yai baya da sauri yace " Mairo amma dai ke wlh da a india kike da film zakiyi, boss zaki zama."
Harararsa tai tace " Allah Abdulmajid ka kiyayeni."
Kansa ya shafa yace " ba laifi ai in namiji ya kiyayi matarsa."
Ta makamai wata hararar tace " mijin tace kawai."
Ta fada tare da juyawa zatai gaba.
Gabanta yasha da sauri yace " Sai da safe, gobe zan sake magana a fada dan na gaji da jira."
Tana kokarin bashi amsa yai gaba, tsaki taja sannan tai gaba, haushinta ma da mahaifiyarta ta sata ta fito da ai ta ce ko yazo bazata sake fitowa ba.
Tana shiga ta wuce d'akinsu ta fada kan gado.
Ummanta ce ta leko tace " kin dawo?"
Mairo tace " Umma ni dai ko yaran nan ya dawo dan Allah karki kara cewa in fita, ni wlh bana so."
Tace " Mairo shifa aure da kike gani ba wai mutum ne yake zab'awa kansa ba, babu yanda za'ai wani ya auri matar wani, haka kuma babu yanda za'ai wata ta auri mijin wani, duk wanda kika ga sunyi aure to fa dama akwai aure a rubuce a kaddarar rayuwarsu, inhar yaran nan ba mijinki bane cikin ruwan sanyi sai kiga kun rabu bawai fadanki bane zai sa ku rabu."
Mairo ta turo baki, tana san magana taga Umma tayi waje, kara komawa tai ta kwanta a fili tace " Ya Allah!"
************
Magajiya kuwa a daren yau ta tsaya sosai tayi tunanin al'amarin dake faruwa, yanzu ta fahimci Abu Turab bai san sirrinta na Abdulmajid ba, tunda a tunaninta da hankalinsa bazai yi tunanin had'a auren Abdulmajid da Khadija ba in har yasan wannan sirrin, tunda yasan ba abu bane mai yiwuwa.
To wanne ya sani? Maganin nan ta tuno da abinda ya fad'a mata a lokacin, mikewa tai zaune tace " yasan sirrin ba Hajiya magani." da alama wannan shine sirrin da ya sani.
Washegari da sassafe tasa aka kira mata wannan yarinyar, yarinyar ta shigo jikinta sai tsuma yakeyi, ta shiga ta zauna a falon da ba kowa.
Magajiya ta shigo sanye da rigar bacci dan ko wanka batai ba, karfe 6 ne na safe.
Magajiya ta kalleta tace " ina abinda aka baki?"
Da sauri tasa hannu a lalitarta ta d'auko maganin.
Magajiya ta kalleta tace " akwai wanda ya kamaki da wannan maganin?"
Kai ta girgiza alamar a'a tace "ba kowa, ina kuma zuba mata kullum."
Magajiya ta kalleta tace " kin tabbatar? Kinsan dai mahaifinki na cikin wani hali, kuskurenku d'aya zai jawo masa ajali."
Da sauri ta sunkuya tace " tuba nake rankiya dade amma ba wanda yasan maganar nan."
Magajiya ta amshi maganin sannan tace" jeki."
Mikewa tai tare da karayin godiya.
Tana fita tai ajiyar zuciya, kalan Abu Turab ta tuna sanda ya ce karta kuskura ta nuna yasan komai, sannan ya bata maganin saboda gudun zargi."
Magajiya tai shiru bayan ta fita, tace " to me yake nufi? Ta tabbatar akwai wani sirri da ya sani, sannan ko baisan maganin nan ta hannun yarinyar nan ba ta tabbatar yasan da zancen maganin, dan tabbas irin wannan ne a hannunsa.
Ajiyar zuciya tai tace " mai ya sani yaran nan?"
Tun kafin asiri ya tuno gwara ta salwantar da maganin, sannan yarinyar nan ta turata wani garin ita da mahaifinta.
*********
Abu Turab zaune kusa da Hajiya wannan yarinyar tanamai bayanin komai, ya jinjina kai yace " hakan yayi, sannan ki shirya zan canza ma mahaifinki asibiti sannan ke kuma ki koma ki kula dashi, kafin lokacin da zaki bada shaida yayi."
Tace " to."
Turab ya kalli Lantana yace " Lantana akwai wacce kika yarda da ita a gidan nan?"
Tace " eh akwai wata yaruwata da aka kawo."
Turab yace " ki dawo da ita nan sannan ke ki koma gun Umma dan kar Magajiga ta fahimci wani abin, ina tsoron kar ta ma Hajiya illa ta wani gun."
Lantana tace "to."
Mikewa yai ya wuce bangarensa, yana shiva Garzali ya sanar dashi kiran da Mahaifiyarsa take masa.
Turab ya juya.
Sai da ya gaisheta sannan yace " Umma gani."
Ta kalleshi tace " Abu Turab me yasa baka zuwa gub Mahaifinka?"
Kansa na kasa bai d'ago ba baikuma ce komai ba.
Basira tace " Mahaifinka na nemanka, yana san ganinka."
To, kawai yace, sannan ya kalleta yai murmushi yace "zanje Umma, shikenan?"
Fuska ta saku tace " ko kaifa?"
Kansa ya sunkuyar yana murmushi, tace " Ya maganar Mairo?"
Kallanta yai sannan yace " Hmmm Umma yanzu ba wannan bane matsala, sai dai insha Allah shima ba wani matsala."
Tace " to, amma Turab nidai kayi a hankali da Magajiya dan wlh wannan matar bala'i ce."
Yace " Nasani Umma, bala'in gaske ma kuwa, sharrinta ya wuce duk yanda kike tunani, zan sanar dake komai sai dai ba yanzu ba."
Tace "shikenan."
Sai yamma sannan ya nufi gun mahaifinsa, sai daya gaisheshi sannan Sarki ya kalleshi yace " Turab ina ka shiga ne haka?"
Turab yace " ina nan, abubuwan ne sukai yawa." kansa na kasa yai maganar nan.
Sarki ya kalleshu yace " kasan tunda ka shigo baka kalleni ba?"
Turab a ransa yace " ina na isa? Nima ai mai laifine tunda nima na b'oyema sirrin nan "
Katsemai Tunaninsa yai da cewa " na aika abin bukatu na lefen."
Kansa na kasa yace "to, angode."
Mamaki ya kama mai martaba yace " Umarni sarki zai baka ka d'ago ka kalleshi."
Turab ya d'an runtse ido kad'an sannan ya d'ago a hankalu ya kalli Mai Martaba.
Sarki yace " Turab menene?"
Abu Turab ya kakaro murmushi yai sannan ya girgiza kai yace " ba komai, sai dai jikin Hajiya da ba dadi, ne yasa baza'a kaita asibiti ba a kwantar da ita?"
Ajiyar zuciya yai sannan yace " Hajiya mace ce mai masifar kishin al'adarta, ko sanda za'a kaika asibiti sai datai ta fada wai akan me za'abar maganin hausa a koma maganin bature? Ita ko mutuwa zatai bata yarda a kaita wani asibiti ba."
Turab yai shiru sannan yace " Amma Abba yanayin jikinta ne ba dadi."
Yace "haka ne ni kaina har banasan zuwa dubota."
Turab yad'anyi shiru kafin yace " Ko za'a maidata cikin gari? Sai a tafi nata da masu kula da ita?"
Mai Martaba yace " Turab kenan, nan d'in ba'a kula da ita?"
Kai ya girgiza alamar a'a yace "ba haka bane kawai dai gani nake zatafi jin dadi in tana can."
Sarki ya kura mai ido ya tabbata akwai dalilinsa ma fad'ar haka, sai dai baisan menene ba, yace " shikenan, zansa a maidata a satin nan."
Turab yai saurin cewa " a maidata gobe, dan Allah."
Sarki ya kalleshi yace " Akwai abinda kake b'oyemin ko?"
Turab yai kasa dakai, Sarki yace " na sanka da taurin kai tun kana yaro, jn har bakaso fad'ar abu ba to fa bazaka tab'a fada ba, zanyi yadda kace sai dai ka tabbatar ka sanar dani abinda ke faruwa nan kusa ba da dadewa ba."
Yace "godiya nake, sannan insha Allah zan sanar dakai."
Nan ya mike ya fito.
Hakan kuwa akai washegari da safe a ka d'auke hajiya, wanda ba wanda ya sani sai Turab sai Sarki da masu d'aukan, Jakadiya kuwa sai dariyar mugunta take kasa kasa dan ta tabbata akwai wani abu da Turab yake shiryama Magajiya tunda taga ta zake tana shirya mai lefen auren da tace ko zata mutu bazata bari ayishi ba.
*"*******
A duk bayan kwana biyu Turab suna waya da Bilkisu, shakuwa ce a hankali take shiga tsakaninsu, duba da yanayin gidan da suka taso da kuma aminta ta yarda dake tsakaninsu.
Magajiya ta shiga tashin hankali, ta rasa wannan yarinyar wato Zakiyya sannan an d'auke Hajiya wanda ba wanda yasan inda aka kaita, da farko ta aika gidan cikin gari sai dai bata nan, shikansa Turab baisan inda Mai Martaba ya kai ta ba.
Sai dai yasan Sarki ya fahimci Uwarsa na cikin wani halin ga tsufa, ya san hakan ne yasa ya d'auketa.
Magajiya ta gama had'a lefe wanda ta yishi na gani na fada dan ita d'in yar kwallisa ce ta gaske, an kashe kudi kam, hankalin Magajiya a kwance take had'a kayan nan, dan itada Hisham sun gama tsara yanda zasu shirya komai.
A b'angaren Turab kuwa jira yakeyi a tsaida rana dan shima ya fara aiwatar da nasa shirin kamar yanda suma suke nasu shirin, Magajiya ta gama yanke hukunci akan Halaka Turab dan wannan ita kadai ce hanya, ganinsa ma batasanyi sam.
An tsaida lokacin biki nan da wata d'aya.
Magajiya ta sa Hisham ya hana Khadija fita, yanzu ko nan da nan ba a barinta fita.
Wannan kenan.
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*64*
Abdulmajid yau tun safe yai wanka tsaf ya shirya ya nufi bangaren Sarki, Mai Martaba ya bashi izinin shiga.
Ya dade rabon da ya keb'e da mahaifinsa irin haka, shiga yai a hankali kamar ba shi ba sannan ya gaisheshi.
Sarki ya kalleshi yace " Ya akai?"
Ba shakka har cikin ransa sai dayaji ba dadi, ya akai? Abinda uba ya kamata ya fara tambayar d'ansa kennan sannan kuma fuska a d'aure?
D'agowa yai jiki a sanyaye yace"dama maganar Mairo ne....."
Katsehi Mai Martaba yai yace " maganar Mairo a me kenan? Kana tunanin kayi daidai a zuwa cikin tsakiyar fada kace kana san auran Mairo? Bayan ni naka sameni ba?"
Abdumajid yai shiru, Sarki yacigaba " Na rasa wani irin hali ga reka, gani kake komai naka ne kamar Magajiya ko?"
Abdulmajid ya d'ago idanunsa sun ciciko sosai da kwalla yana tsananin ganin kwarjinin mahaifinsa amma ya daure yace " menene laifina? Abba ni ba d'anka bane? Me yasa komai sai dai Abu Turab? Ka samomai mata yar mulki, gashi yanzu har an tsaida rana ana ta shirye shirye, nine fa babba ba shiba, amma bance komai ba, sannan nace ga wacce nakeso itama an kasa bani, ko itama Abu Turab din za'a ba?"
Sarki ya kalleshi yace " Kana tunanin duk abinda kukeyi kai da mahaifiyarka sani ne banyi ba ko ka d'auka karfina tafi? Sanda kukama Turab sharri kana tunanin bansan ku kuka aikata ba?"
Abdulmajid yai shiru, sai dai zuciyarsa na tafasa da tsanar Abu Turab tsantsa.
Sarki yace " Maganar auren Mairo ni har yanzu ban yanke hukunci ba, zamu zauna da mahaifinta muga wanda ya dace da ita."
Abdulmajid ya d'ago sai dai baice komai ba amma kana kalla idanunsa zakaga tsantsar b'acin rai.
Mikewa yai yama mahaifinsa sallama ya fita.
Cikin tsananin takaici ya nufi bangaren Magajiya.
Tana zaune tana shan madarar shanu, wanda takesha duk safiya dan gyara mata fatarta.
Ko sallama baiyi ba ya afka ciki.
Magajiya ta kalleshi har ya zauna, baigaisheta ba yace " Umma nikam na gaji da abinda Abba yakemin, wlh zan d'au mataki a kaina."
Magajiya bata daina shan madarar ta ba ta kurb'a sannan tace " me ya faru?"
Abdulmajid ya kalleta yace " Umma ni kam na tsani yaran can, me yasa ne komai nake so a rayuwa sai ya kwacemin?"
Tace " karka damu ka kara hakuri na wasu 'yan lokuta, sannan ka shirya nan da wani satin dan zuwa ganin yar sarkin daura."
Kallanta yai yace " inganta in mata me?"
Kallansa tai tace " tambaya kake?"
Kansa ya maida kasa sannan yace " Amma Umma kinsan ai ni M......."
Kallan data masa ne yasa yai shiru, ajiye kofin tai sannan ta juyo ta kalleshi tace " me yasa kake neman canzawa? Da baka tambayata akan abinda na sharadda maka amma yanzu naga alama yar iskar yarinyar nan tana neman canza maka hali, a kanta ka fara neman canzamin."
Kansa na kasa yace " Amma Umma."
Mikewa tai tsaye tazo kusa dashi ta sa hannu a kafadarsa tace " Abdulmajid ka zama mai bin duk abinda na sharadda maka, komai da kakeso a rayuwa ni zan baka, in nace komai ina nufin komai d'in, kai dai kabi ni."
Shiru yai, ita kuma tana gama magana ta juya tai ciki, ya dade a zaune kafin ya mike ya fita.
********
Turab yau da kansa yaje fada ya dade a can sai dayaga fitowar Waziri sannan shima ya mike ya fito.
Yana kallan Hisham ya shiga mota ya wuce gida, shima ya shiga tasa motar wanda dama ya sa Garzali ya jirashi ya bi bayansa.
Hisham na kokarin shiga gida, Turab ya fito da sauri ya biyoshi.
Hisham na shiga aka cemai wai yayi bako, yayi mamaki sai dai bai yi tunanin Turab bane yace " ace ya shigo."
Turab ya shiga cikin falo ya zauna, sannan Hisham ya shigo.
Mamaki ne ya kamashi na ganin Abu Turab.
Karasawa yai ya zauna yace "Yarima lafiya?"
Turab ya gaisheshi sannan yace " biyoka nai ai daga fada."
Hisham yace " wani abin ne ya faru da baka sanar dani a can ba sai da ka biyoni gida?"
Turab yai kasa dakai yace "ai yanzu a matsayin siriki mai neman 'yarka nazo."
A zabure ya kalli Turab cikin raahin fahimta yace " me kake nufi?"
Turab ya d'ago idanunsa yace " zuwa nai maka da abinda zai taimakeka ya kuma taimakeni."
Hisham ya bishi da kallo, Turab yace " khadija zaka auramin kaga nan gaba ko da komai naka ya kare a kalla 'yarka tana da matsayin da zata kwace ka."
Ran Hisham ya b'aci yace " Ta karemin kamar ya?"
Turab ya d'an furzar da iska irin damuwar nan yace " Badai kana tunanin in Abdulmajid ya hau mulki Magajiya zata barka da matsayinka ba ko ta barka kayi yanda kakeso da d'anta ba?"
Hisham yace " wannan banaji yana daga cikin damuwarka."
Turab yace " Hake ne sai dai inaso kayi tunani sosai kaga mafakar da zata bul'ema, ka fini sanin kanwarka ka kuma san halinta, kana tunanin zata barka ko shawara ne kaba Abdulmajid? Inka bada ma shawarar kana tunanin zata bari yai aiki dashi?"
Hisham ya mike tsaye cikin takaici yace " koma menene damuwatace ba taka ba, sannan kana tunanin ni zan kai 'yata a ta biyu gidan wani? Sannan ni ban taba tunanin had'a zuri'a dakai ba kuma bazan yi ba har abada."
Turab yace "kumafa gaskiya ka fada, ni kaina bansan me yasa nazo ma da zancen ba, inaso ka sanar da 'yarka hukuncinka saboda mu hakura da juna."
Ya mike yamai sallama ya fito daga falon.
Yana fita yai wani murmushin gefe yace " nazo neman iri ne na auran 'yarka? Inji wa? Kai dai na tabbatar abinda na saka a kwakwalwarka ya shiga zai kuma fara aiki."
Ya juya, Karo suka kusa yi da Khadija wacce ta taho da tirw daga kitchen rike da tire wanda yake d'auke da juice.
Kaucewa tai saboda ganin zata bugeshi, garin kaucewa bata kula da kafarsa ba ta taka ta tafi kamar zata fadi, da sauri ya rikota ta baya.
Ajiyar zuciya tai da karfi dan tabbas ta d'auka fad'uwa zatai.
Juyowa tai a hankali, nan taga wanene idanunsu ne suka had'u da juna.
Sai da 'yan wasu dakiku suka wuce a haka kafin Turab ya daure yace " Baki bige ba?"
Gyara tsayuwarta tai sannan ta kalleshi, a hankali ta d'aga kai, kallanta ya sakeyi yaga ta rame, ita kuma tana san tambayarsa abinda ya kawoshi, a tare sukace "Nace me......"
Ganin yanda sukai maganar a tare basu san sanda sukai dariya ba, Turab yace " fara magana."
Kallansa tai tace " a'a ka fara." yana kokarin tambayarta yaji murya ance " Khadija me kikeyi anan baki kai ba?"
Juyowa tai ta kalli Ummanta tace " yanzu zan kai."
Kallan gun yai, mahaifiyarta ya gani, suna tsananin kama da Khadija sosai, da ace itace Abdulmajid to fa yasan tabbas zargi zai bayyana.
Gaisheta yai sannan ya fita, Hisham kam Turab na fita ya kumburo baki yana tunani, tabbas dolene ya fara jan d'ansa a jikinsa dan sai yanzu ya farga ya san Magajiya sarai tabbas gaba ma neman ma hanashi zuwa gidan zatai.
Ko tabin bayan Khadija data shigo baiyi ba ya shiga cikin d'aki.
**********
A can kano kuwa shiri sosai akeyi na auren Gimbiya, auren da babu kamarsa agunsu domin ita kadai ce 'yar sarki mace, shiri ake sosai wanda yasa kishiyoyin Fulani jin kishi dan komai ita keyi, Bilkisu kuwa an shiga gyara, dama ba zancen zance dan in suka fara gyaran jiki to ango bazai ga amarya ba saboda so ake inya tashi ganinta yaga kamar ba ita ba.
Turab kam na kiranta sosai suna waya.
Hisham ya gama tsarawa dan yau yana tashi daga fada ya nufi bangaren Abdulmajid........
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
_Sakon ta'aziyya gareki kawar arziki BillynAbdul Allah ubangiji ya jikan Mahaifinmu yasa Aljanna ce makomarsa.....(Ameen)_
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
_Masu san karanta Matar Fayrouz na AsyKhaleel da sauran litattafanta su duba ta a wattpad @asykhaleel.😘😘_
*65*
Hisham yana fita yai bangaren Abdulmajid, baya nan ma sai ya zauna a falo ya aika a nemoshi, yace " in an ganshi kar acemai shine yake nemansa.
Abdulmajid ya fito daga bangaren Magajiya kenan aka sanar dashi yanada bako.
Yana shiga yaga Hisham, ya karasa ya zauna sannan ya gaidashi, Hisham ya washe baki yace " Abdulmajid sai ka ganni ko?"
Kallansa yai yace " Kawu me ya kawoka? Naga baka taba zuwa bangarena ba."
Hisham yai murmushi tare da kallansa yace " yauma wucewa nazoyi sai na fahimci ban taba shigowa ba."
Kai ya d'aga kawai baice komai ba, yau ce rana ta farko da suka kebe su biyu haka shiyasa yakejin abin wani banbarakwai kamar ba kawunsa ba.
Hisham ya kalleshi yace " ya maganar auren naka da Mairo? Har yanzu Magajiya bata sauko ba?"
Hisham ya kalleshi kallan mamaki, cikin rashin fahimta yace " eh kasan halin Umma ai "
Hisham yace " karka damu inaso kome ke damunka ka dinga sanar dani, ni zan yi iya kokarina wajen ganin na taimaka maka, Magajiya bazata taba bari ka auri yarinyar ba, sai dai ni zan san yanda zanyi in har kanasanta."
Ya kasa fahimtarsa, mamaki yake na yanda yake mai, Abdulmajid yace "Nagode, amma kana tunanin Umma zata yarda?"
Hisham yace " karka damu, kai daj ka yarda dani, duk wata matsala taka ka dinga zuwa kana sanar dani, ni zan taimakeka akan komenene, kawai dai ka dage kar ka taba bari Turab ya kwacema mulkinka."
Abdulmajid kallansa kawai yakeyi, Hisham ya matso yace " inaso a sati ka dinga zuwa gidana cikin gari, zansa Maman Khadija ta dinga shiryama duk abincin da kakeso, kaga sai kazo ayi hira, hakan zai ragema kewa ya kuma kara mana zumunci."
Shekarata nawa da haihuwa? Da can ba'ai zumuncin ba sai yanzu? Abinda ya fada kenan a ransa, sai dai a fili kallan Hisham yai kawai baice komai ba.
Hisham ganin yanda Abdulmajid yake yi yasa ya mike yace " ni zan koma sai mun ganka ko ran Juma'a ko asabar,sannan karka fadama Magajiya zuwana da zancen da mukai, ka santa."
Uhm hmm, kawai yace.
Hisham yai waje.
Kallansa Abdulmajid yai sannan ya mike yai ciki.
Hisham kuwa na fita ya jinjina kai yace " a hankali zan jawoka jikina, ai tsakanin Uba da d'a sai Allah."
Yana fitowa yai wuf yai kwana ya wuce, Abu Turab wanda yana shiga bangaren aka sanar dashi zuwansa ya fito dama yana jiran fitowarsa.
Yana hangoshi ya taho kamar irin bai ganshi ba d'in nan, Hisham na hangoshi ya tsaya tare da neman inda zai b'uya, dan dai girma ya kamashi ne amma da gudu zai saka, juyawa yai da sauri dama abinda yasa ya bi ta baya saboda bangaren Magajiya ne ta gaba, yana tsoron kar aganshi.
Abu Turab yana kallan ya juya yai wani murmushin jin dadi.
Hisham ya shiga bangaren Magajiya.
Tana kishingide ta bashi izinin shigowa.
Hisham ya shiga yana dariya yace " Magajiya ikon Allah hutawa kikeyi ne?"
Wani banzan kallo tamai hakan yasa yai shiru sannan yace " Magajiya barka da yamma."
Idanu ta d'an juya bata amsa ba, zama yai sannan yace " na lekone mu gaisa."
Tace " ka sandai muna da abinda ya kamata mu shirya na ranar auren yaran nan ko? Ga lokaci yana matsowa amma sam ka ki shigowa ayi magana."
Yace " haka ne, nima ai ba mantawa nai ba, yanzu ya kikeso ayi?"
Ta bud'e baki zatai magana aka sanar da ita zuwan Abu Turab.
Fuska ta canza tare da yin wata karamar kwafa, ba shakka itakam ta gaji da jin ko sunan yaran nan.
Shigowa yai ganin batada niyyar bashi izini.
Yana shigowa yace " Umma bakiji isowar d'anki bane?"
Murmushi ta saki sannan ta koma ta gyara zamanta tace " banyi tsamannin zuwan ka bane."
Zama yai sannan ya kalli Hisham yace " da alama sirri kukeyi da Kawun namu au ko ince Babana."
Magajiya ta had'e fuska, shima Hisham yaci mazu, Turab ya d'aga hannayensa yace " Tuba nake Babana kar in bata ma sirikin nawa rai kafin abani Khadija."
Magajiya ta kalleshi cikin takaici tace " kai dai ka nutsu akan auranka da Bilkisu ka daina wata banzan magana wacce bazata amfaneka ba."
Turab yace "Haka ne Umma, nayi..." yai alamar zip a bakinsa.
Kallan Hisham yai yace "Amma waziri kamar daga bangaren Abdulmajid na ganka ko?"
Hisham ya zaro ido, da sauri ya kauda kai gefe irin mara gaskiyar nan yace " a'a wucewa nai ba shiga nai ba."
Turab ya jinjina kai yace " kayi kokari sai naga kamar tacan yafi nisa."
Hisham yace "Hmm." da sauri ya kuma cewa " bari nikam na koma." ya fada dan kawar da zancen.
Turab yace " a'a bari ni na tafi da alama Umma akwai abinda zata cema, da na d'auka ma d'anka kazo ba gun Umma ba shiyasa na shigo."
A tare gabansu ya amsa da rass, Magajiya cikin tsananin tsoro tace " D'ansa?"
Hisham kam har zufa ta fara afko masa, Turab yasa dariya yace " menene hakan? Da ba d'ansa bane?"
Ai tuni Hisham kansa zuwa wuyansa ya cika da zufa, Magajiya kam a ranta tace "shikenan ta faru ta kare."
Turab ya karayin dariya yace " lalai Umma ba kara? Na d'auka d'anki a ka'ida d'an Waziri ne saboda jininku d'aya."
Bakin Hisham har rawa yake gurin cewa " sosai ma haka ne."
Magajiya kam idanu ta bud'e ta kurama Turab tana kokarin ganu abinda ke b'oye a ransa da gaske abinda yake nufi kenan?"
Turab ya kalleta yace " Umma lafiya? Naga kinata kallo na."
Idanu ta d'auke tare da cewa " ba komai, ya shirye shiryen biki?"
Yace "Thanks to you, komai na tafiya daidai."
Kai ta d'aga tace " yayi kyau."
Turab yace " Ayi hira lafiya."
Ya juya ya fita, yana fita ya kara kallan kofarsu ta gefe, "Haka ne nima ba mantawa nai ba, yanzu ya kikeso ayi?" kalaman Hisham da yaji sanda ya iso gun ne ya kara dawo mai, tabbas akwai wani mugun abu da suke kara shiryawa, ya tabbatar.
Juyawa yai ya fita.
Yana fita Hisham ya saki wata ajiyar zuciya ya kalli Basira yace " kinji hanjin cikina?"
Magajiya ta kurama kasa ido kafin tace " Inaji ya kamata mu maida Khadija kano."
Yace " Kano? Kamar ya?"
Tace "kasan Mahaifiyar Saifullahi ta kirani jiya da daddare tace wai Khadija tace ma Saif akwai wanda takeso, dolene mu maidata kano in taga bata gani yarancan sai ai auren, inba haka ba intaga mutuwarsa abin zai baci, ka san dagar da akai da ita sanda tana karama ma bare yanzu."
A ransa yace " ni da 'ya'yana sai dai a dinga sharada min abu, da girmana amma a dinga kaskantar dani"
A fili yace " hakan yayi."
Nan suka cigaba da tsarinsu.....
*********
Basira zaune a falonta, gabanta kuma leda ce irin mai karfin nan, da alama kaya ne a ciki.
Amsa sallamar Turab tai sannan ta kalli kofar da ganin shigowarsa.
Turab ha shigo sannan ya zauna yace "Umma gani."
Kallansa tai tace " Dama aikenka zanyi."
Kallanta yai sannan ya kalli ledar gabanta, sai kuma yar murmushi yace "Gun 'yarki?"
Tace " eh, Mairo zaka kaimawa, sa wa nai a d'inka mata na bikinka."
Murmushi yai yace "Umma kenan."
Kallansa tai tace " Amma baka tunanin hakan yazo da kamar wulakanci ko?"
Turab yace "wulakancin me?"
Tace " Na kaimata kayan da zata sa a bikinka bayan akwai wata a kasa."
Turab yace " Lalai Umma, ni bansan wannan ba ki tambayi Lanta....."
Da sauri yai shiru tare da kallanta, Kallansa tai itama tace " Turab har yanzu ba labarin inda Hajiya take? Bare Lantana?"
Kai ya d'aga alamar eh.
shiru sukai ganin haka yasa ya jawo ledar yace " Zanje in anyi Magrib."
*********
Garzali ne ya kaishi, yana cikin mota Garzali ya fito ya aika a kirata.
Ta gama kunce lale kenan wanda tayi a hannunta, aka sanar da ita zuwan Turab.
Wankewa tai dama ba sallah zatai ba ta saka hijab ta dan murza hoda sannan ta fito.
Tanaji 'yayan kishiyar babarsu na mata habaici, ko ta kansu bata biba tai waje.
A jikin soro ta tsaya dan bata fita waje zance, ka'idar gidansu ne haka.
Turab sai da ya hangota sannan ya bud'e motar ya fito, rike da ledar.
Tundaga nesa take murmushi har ya iso, Kallanta yai sannan ya karasa cikin soro yace " Hajiya Maryam an fito?"
Kallansa tai tace " Yaya ina wuni?"
Bai amsa ba sai cewa dayai " kwana dayawa?kin bata bat."
Fuska ta d'an rufe tace " wlh inasan zuwa gaida Umma magana ce banaso."
Leda ya mika mata yace " ga sakonki inji Ummanki."
Amsa tai tana murmushi tace " oh ni, me na samu?"
Yace " kayan bikin yayanki ta d'inka miki."
Gani yai ta d'ago da sauri, sannan yanayinta ya canza, yace " Badai Umma tayi lefi ba?"
Ya ke tai tace " a'a."
Kallanta yai zai yi magana aka dallesu da fitilar mota.
A tare suka kalli motar, Turab ya sa hannu ya rufe idanunsa dan sam bayasan a haskashi irin haka saboda idanunsa.
Mairo ta juya kai tare da jan tsaki.
Turab ta kalla ganin yanda ya rufe idanunsa yasa ta taho dan nufo mai motar.
Har ta iso sannan ya kashe, tare da fitowa daga motar.
Kallansa tai tace " Abdulmajid me ke nan?"
Kallanta yai fuskarsa a d'aure yace "me kike a can?"
Tace " ko ma me nakeyi banaji ya shafeka amma wannan dallenin da kai da fitila fa?"
Kallan inda Turab yake yai bai amsa mata ba taga ya nufi inda Turab yake.
Abdulmajid na zuwa ya d'aga hannu zai naushi Turab, Abu Turab ya sa hannu ya tareshi.
Kallo kallo sukai kafin turab ya sakar mai hannu sannan yace " ka kiyayi kanka da san duka, sannan ka kiyayi kanka da saurin hawa Da kuma kishi "
Abdulmajid yace " Kai waye da zaka bani shawara?"
Turab ya kalleshi ba shakka yana tausayamai alokacin da yasan sirrinsa shiyasa baya neman fada dashi a wannan lokacin.
Mairo ce ta karaso ta kalli Abdulmajid, zatai magana Turab yace " Bari na wuce."
Ya karasa maganar tare da wucewa ta gaban Abdulmajid.
Biyoshi tai tace"Yaya kama Umma godiya."
Juyowa yai ya kalleta sannan ya kalli Abdulmajid dake tsaye yace " Mairo."
Kallansa tai bata amsa ba, yace " karki dinga zafaffama Abdulmajid."
Tace " Yaya na fadamai ba so nake ba, na rasa dalilin takurar."
Shiru yai tare da cigaba da kallan Abdulmajid yace " ba yanda za'ai?"
Kallan mamaki tamai tace " yanda za'ai me?"
Kai ya girgiza da sauri yace "ba komai."
Ya karasa mota ya shiga.
Shiru tai tana kallansa har sukai gaba, ba yanda za'ai? Me yake nufi?"
Karasawa tai inda Abdulmajid yake.
Kallanta yai yace " Mairo mai ya kawoshi?"
Ledarta ta nuna mai tace " abu ya kawomin, ko da wani abun?"
Abdulmajid yai murmushi yace " Mairo lalen ki yayi kyau sai kika fito kamar amarya."
Harararsa tai tace " kamar Ango ne ba amarya ba."
Dariya yai yace " in kika zama kamar ni Angon ki ai ba wani abin bane."
Baki ta d'an murguda tace " Ka manta."
*********
Turab kam kansa ya kama a cikin mota wanda yaji yana sarawa, yace " Ya Allah! Ka kawo komai da sauki, kada ka bani ikon cutar da wanda bashida hakki akan al'amarin nan, ka bani ikon aiwatar da komai yanda ya kamata.
Nace Ameen
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
_Haly(Mom Farhan) Allah ya kara lafiya yasa kaffara ne....Wish u quick recovery_
*66*
Abu Turab idanunsa ya bud'e a hankali ya shiga kallan d'akinsa kafin a hankali ya furzar da wata yar karamar iska daga bakinsa.
Sannan yasa hannu ya dafa gadon ya mike ya zauna, idanunsa ya rufe ya shiga karanto addu'oin safiya, kafin ya sauko daga kan gado.
Yau saura sati 3 bikinsa, dayake gidan maza ne ba wani abu special ake aikatawa ba, an dai kammala ginin bangaren da zasu zauna da gimbiya.
Saukowa yai daga kan gadon sannan ya nufi bandaki dan kama ruwa da yin alwala.
Bayan ya dawo daga masallaci ya zauna yai ta tilawar al-qur'ani har sai da gari yai haske, wannan al'adar haka yake yinta dan koyar wace ta ma'aiki S.A.W.
Sai wajen karfe goma yaci abincin safe sannan ya fito.
B'angaren Mahaifiyarsa yaje sukai 'yar hira kafin ya fito.
Yana kokarin komawa bangarensa ya hango Baiwar da take kula da bangaren Abdulmajid wanda ya shine ya sakata a bangaren dan kawomai rahoto akan Hisham.
Karasowa tai cikin hanzari sannan ta gaisheshi, tana yi tana kalle kalle.
Turab ya kalleta yace " lafiya da safen nan?"
Tace "banga d'an aike bane, dama Waziri ne ya zo yanzun nan, sannan rike yake da lefa katuwa, da ya shiga ciki na amshi laidar sai naga kula ce sannan ga kamshin abinci nan."
Turab yace " yayi kyau, koma bakin aikin ki."
Tace "Yarima Abdulmajid ya......"
Dakatar da ita yai yace " na tambayeki rayuwar Abdulmajid? Ko kuwa a sanda na baki aikin nan nace ki dinga kawon zancensa? A iya sanina ce miki nai kawai in Waziri yazo ki sanar dani."
Tace " Tuba nake ranka ya dade."
Turab ya sallameta sannan shikuma ya shiga ciki.
A bakin kofa ya tadda Garzali da alama fita zaiyi.
Turab ya kalleshi yace " in zaka fita ka biya bangaren Sarki gub Jakadiya."
Garzali ya kalleshi yace " Jakadiya?"
Turab yace " ka sanar da ita Hisham na bangaren Abdulmajid."
Garzali cikin rashin fahimta yace " to." dan bazai iya tambayarsa dakili ba.
Garzali ya garzaya yaba Jakadiya sako.
Ita kanta kallab Garzalin tai tace " abinda yace kawai ka fadamin kenan?"
"iya kacinsa kenan."
Ya juya.
Jakadiya tai shiru tana kara maimaita kalmar kafin daga baya ta fito.
Bangaren Magajiya ta nufa, Magajiya na karyawa ta shigo.
Sama sama ta amsa gaisuwarta tanayi kamar bataso.
Sannan tace " me ya kawoki?"
Jakadiya ta miko mata leda tace " maganine aka kawo na gyaran fata."
Magajiya ta kalli maganin dake cikin farar leda sannan ta kalleta tace " ni ce miki akai ko wani kare da doki ya bani magani amsa nake?"
Jakadiya tace "badai haryanzu baki hakura ba?haba Hajiya Magajiya, matar sarki, uwar sarki, kakar sarki."
Magajiya ta wani juya kai sannan tace " Me ya kawo ki? Dan na tabbata ba wannan bane kadai abinda ya kawoki."
Jakadiya ta dan shafi fuska sannan ta matso tace " hmm dama na kasa fahimtar wani abu ne, Na rasa me yasa nake ganin Waziri yanzu yana zirya bangaren yarima Abdulmajid."
Magajiya ta kalleta tace " ban gane ba.."
Jakadiya tace " Tuba nake Ranki ya dade amma nifa hankali ya kasa kwanciya da zuwansa."
Ruwan da ta gama sha ragowar cikin kofun tai kamar zata zubo mata har ta rufe idonta ta d'auka ita zata zuba ma.
Magajiya ta ajiye cup din sannan ta kalleta tace " najiki inaso kuma ki fita."
Jakadiya ta had'iyi yawu sannan ta mike tai waje.
Magajiya tai shiru tana tunani, dama kwanaki Turab ya sanar da ita ya ganshi amma shi ha musa, sannan an fada mata rannan an ganshi, sannan yau Jakadiya ta fada mata, me Hisham yake tunani? Tamai magana akan kai Khadija Kano ma ya mata burus sannan yanzu ya fara kewayewa yana zuwa gun D'anta?
Turab kam zama yai a falo yai zama cin abinci sannan ya rufe idanunsa, yana kada 'yan yatsun hannunsa, Magajiya! Ki jira juyawar bayan duk wani na kusa dake, a hankali zan ruguza miki duk wani abu da kike takama dashi....Slowly ya saki murmushi sannan ya bud'e idanunsa, ta ya zakuyi kisa ku cigaba da zama kamar wad'anda basuyi komai ba? Kun halaka rayuwar mutane dayawa amma ko tunawa bakwayi.
Hannunsa ya dunkuke sannan ya kalli bakin kofa cikin tsananin kunar rai.
********
Abdulmajid na mikewa daga kan gado aka sanar dashi zuwan Hisham, baiyi mamaki ba dan ya kula yanzu wata gulma ce take damunsa, inba haka ba da can me yasa bai mai haka?
Sai dayai wanka sannan ya fito.
Hisham ya sa an jeramai abincin dayasa matarsa tai, ita kuwa tanayi tana farinciki dan yauce rana ta farko da zatai abinci domin d'anta Shikadai.
Kallan abincin yai sannan ya karasa ya zauna, ya gaisheshi.
Hisham ya amsa fuskarsa a washe yace "Ashe bacci kake?"
Abdulmajid yace " eh wlh, kayi hakuri na barka kai kadai kawu."
Hisham yace ba komai, zauna kaci abinci, goggonka ce ta dafa ma.
Abdulmajid ya kalleshi sannan ya kalli abinci yace "Kawu me kakeso?"
Hisham yace " name kenan?"
"na tabbatar abu kakeso a gareni shiyasa kake nunamin kulawar da baka nunamin da, badai so kake in auri Khadija ba ko wani abun ba?"
Da sauri Hisham ya zaro ido yace "ka auri khadija kuma? Wannan wani irin shirmene? Auzubillah."
Abdulmajid yayi mamaki yanda yaga yayi, sai dai bai kawo wani abu ba yace " to inba shiba menene? Na tabbata akwai dalilinka na yin haka balle ma kace kar na dinga sanar da Umma zuwanka."
Hisham yai shiru yana tunani kafin yace " ko d'aya kawai dai ina ganin ya kamata mu saba da juna ne, na ga ko aboki baka dashi."
Abdulmajid ya kalleshi baice komai ba ya fara cin abincin.
*******
Magajiya kam Jakadiya na fita hankalinta ya kasa kwanciya, mikewa tai ta shirya ta fito ta nufi bangaren Abdulmajid.
Da yake ta baya ne bata wani dadeba ta isa.
Ana kokarin sanar da isowarta tace ayi shiru.
Kai tasa tare da tura kofar a hankali.
Hisham taji yana cewa " Na d'auka wancan sati zaka zo, sai naga baka zo ba."
Abdulmajid wanda ya gama cin abinci ya kalleshi tare da wanke hannu yace " ya su Umman da Khadija?"
Hisham yace " suna lafiya, zakazo ran juma'ar?"
"Yaje ina?" abinda sukaji kenan da ga bayansu.
A tsorace suka mike, Abdulmajid ya kalleta yace " Umma."
Kallansa tai sannan ta kalli abincin da ya gama ci tana gani tasan Hisham ne ya kawo dan ga kuka nan a gabasa, sannan ita ba irin abincin da aka kawo mata ba kenan.
Ba shakka ranta ya baci sosai, dan idanunsa sun canza fuskar nan tata ta had'e ta tamau.
Kallan Hisham tai tace " Yaje ina?"
Hisham ya kalleta sannan ya kallu Abdulmajid, kallan Abdulmajid tai tace " ina zaka?"
Abdulmajid yace " Umma."
Kallan abincin tai sannan ta kallu Hisham tace " me kenan? Waye ya baka ikon kawomai abinci?"
Hisham ya kalleta yace " dan na kawo mai abinci wani abin ne?"
Cikin d'aga murya wanda ni kaina sak dana razana tace " wani abin ne babba ma kuwa, yaya me ke damunka?"
Abdulmajid wanda ransa ya dan sosu ya daure yace " Umma dan ya kawomin abinci wani abun ne? Kawu nane fa na tabbata bazai cutar dani ba."
Kallan Abdulmajid tai tace " ta ya kasan bazai cutar dakai ba? Dan yana kawunka kawai?"
Hisham yace " mene? Kina nufin ni zan cutar dashi?"
Cikin bacin rai tace " yaya biyoni inasan magana dakai."
Tai gaba.
Abdulmajid ya dafa kai, sannan ya kalli Hisham wanda yama rasa mai zaiyi.
Yana kallan Hisham yai waje.
Komawa yai ya zauna jiki a sanyaye.
Ita kuma suna shiga d'akinta ta juyo cikin tsananin bacin rai zatai magana.
Hisham ne yai saurin cewa me kike nufi da zan cutar da abinda na haifa?
Wata irin dariya ta saki mai razanarwa, sannan ta tsuke bakinta lokacin d'aya ta matso kusa dashi tace " me? Abinda ka haifa? Inji wa kenan?"
Hisham yace " mene?"
Tace " ahhh dalilin kenan da yasa kake neman kula dashi yanzu? Saboda d'anka ne? Ko saboda kanasan amfani dashi nan gaba?"
Hisham yai kasa dakai.
Tace " idan har kana san kanka da arziki ka fita harkar d'ana, shine magajin sarki banasan wani abu ya faru har sai ya hau mulki, in kuma har kana tunanin wani abu kama daina dan zan iya sa Abdulmajid ya daina ko gaidaka ne kai kasani."
Kallanta kawai yake yama rasa mai zaice.
Hannu tasa ta shafi fuskarta sannan Tace " Yaya banaso muna fada akan abinda bai kai ya kawoba, ban hanaka kula Abdulmajid ba amma bance ka shishigemai ba, d'ana ne banasan wani abu na shakuwa ko sama da haka ya shiga tsakaninku."
Sam yama kasa magana, sai mamaki kawai da yake na kalamanta.
Magajiya tace " Yaya na aika da kayayyakin bikin Abdulmajid gida, sannan karka manta da shirin mu na ranar d'aurin aure, wannan shine abinda ya kamata muyi ba fada ba."
Ta karasa maganar tana murmushi kamar ba abinda ya faru.
Hisham " to." kawai yace ya mata sallama ya fita.
Tabbas daga Abu Turab sai ke zakisan ni kikama haka, ba uwa d'aya uba d'aya ba ko 'yatace ke wlh sai kinsan nikikama haka.
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
_I sincerely apologize to u 😌_
*67*
Basira ce ta kalli mai martaba tace " Barden ya amince ne?"
Takawa yai shiru alamar tunani sannan ya kalleta yace " Basira kiyi hakuri, nasan yanda kika d'auki Mairo na kuma san halin Abdulmajid, yanda Magajiya ta raineshi a haka yake, yaro ne wanda bai yarda da babu ba, sannan duk abinda yakeso gani yake dolene sai ya samu, hakan ne yasa nake nunamai ba haka ba, nake kuma janyeshi daga jikina saboda banaso yai tunanin komai nasa ne kamar yanda Uwarsa ke koyar dashi, sai dai nayi tunani dakyau yaran yanasan yarinyar sannan Mahaifiyarsa ba so take ba, ko dan Magajiya taji ciwon bijire mata da d'anta yai ina tunanin Amincewa."
Basira tace " ba wai naki aminta da kai bane sai dai meyasa nakeji kamar kanasan had'a auren ne bawai dan farincikin d'anka ba ko dan karfafa zumunta da Barde ba, ya nakeji kamar dan cikar burinka na kuntatama Magajiya kake san had'a su?"
Sarki ya kalleta yace " wannan tunanin shine babban dalilin dayasa na dage akan auren Turab da Bilkisu."
Tace " bangane ba."
Yace " a masarauta dolene ka sadaukar da wani abu dan samun wani abun, bazai yiwu ka samu komai ba, inhar inaso Turab ya zama Sarkin da naso na zama dolene na samarmai mace jinin sarauta wacce tasan sadaukarwa."
Basira ta kalleshi tai murmushi dan ta fahimcu a fakaice magana ya gwab'a mata, tace " Allah ya baka hakuri."
Hannunta ya kamo duka biyun yace " inaso ki zama mai karfafamin gwiwa akan al'amurana, bawai dan Magajiya ba kawai nake san had'asu, inaji a jikina zata zama mata ta gari agareshi."
Shiru tai dan batasan me ma zatace ba, amma itakam dan ba yanda zatai ne, bataso Magajiya ta zama sirika a gun Mairo.
************
Yau kwanan Abdulmajid biyu kenan Magajiya bata kulashi, gaisuwarsa kawai take amsawa.
Yau dai abin ya dameshi bayan ya gaisheta yaki tashi.
Ya dade a zaune kafin yace "Umma nikam sai yaushe zaki huce ne?"
Bata kalleshi ba bare yasa ran amsawa, yace " kema kinsan ba ji nace ya kawomin abinci ba, sannan gani nai Kawu Hisham yaya yake a gunki kinga kuwa Uba yake a gurina......"
A gun wa yake uba?"
Kallan mamaki ya mata yace " Umma kinsan kwanan nan kin canza kuwa?"
Kallansa tai tace " na canza ko ka canza?"
Yace " Umma yanzu na kula kamar akwai abinda ke damunki, abinda bai kai ya kawoba sai inga kinji haushi, a da kuwa kina dadewa kafin inga b'acin ranki."
Shiru tai ita kanta tasan haka ta rasa me yasa takejin ta akoda yaushe kamar intai sake Abu Turab zai ruguza mata rayuwa.
Abdulmajid ya taso yazo gabanta yace " Umma meke damunki?"
Murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace " Abdulmajid."
Naam Umma.
"inaso kamin alkawari a koda yaushe cikin ko wani hali zaka zama a bayana, bazaka taba juyamun baya ba."
Murmushi yai wanda sainda hakoransa suka bayyana yace " bakyasan indinga shiga jikin Kawu?"
Kai ta girgiza alamar a'a tace " kawai dai banasan inga wani yana neman janye min kai ne."
Yace " Umma kenan, wa ya isa ya janye miki d'anki? Nifa d'anki ne ba kuma wanda ya fimin ke duk duniyar nan."
Tace"ka tabbatar ka ajiye wannan kalmar a kasan zuciyarka."
Kallanta yai yace " Umma na kasa fahimtar dalilinki na yin hidimar bikin Turab, akan me wacce ta haifeshi bazatai ba sai ke?"
Magajiya tai shiru a ranta tace" kwalliya zata biya ai kud'in sabulu."
Amma a fili tace " karka damu nice uwargidan Sarki, hakkinane na kula da hidimar bikin 'ya'yansa."
Abdulmajid ya dai kalleta ne kawai amma zuciyarshi bata gamsu da wannan sharhin nata ba.
Haka ya taso ya fito.
Da yake juma'a ce massalaci ya wuce, bayan an idar da sallah Abu Turab na cikin mutane suna ta gaigaisawa ana tsokanarsa akan ya kusa zama ango.
Abdulmajid na zaune yana hangoshi, shi kansa Abu Turab baya minti biyu sai ya kalli inda Abdulmajid yake saboda yanasan ganin Hisham kusa dashi.
Abdulmajid ya miko yazo shima aka fara gaisawa dashi.
Hisham ne ya karaso gun, yana zuwa Abdulmajid na gaisheshi ya juya zai yi tafiyarsa.
Hisham ganin haka yabishi da sauri tare da kiransa, tsayawa yai tare da juyowa, Hisham ya iso yace " gida zaka?"
Abdulmajid ya kalleshi yace " eh, da wani abun ne?"
Zaiyi magana Abu Turab ya karaso yace " Abba barka da juma'a."
A tare suka juya suka kalleshi, Hisham yace " ni?"
Turab yace " Kai Abba, zumunci akeyi shine kuka taho gefe?"
Abdulmajid yace " a yaushe ya zama Abbanka?"
Turab ya kalli Hisham irin jin kunyar nan yace " Waziri baka sanae dashi ba?"
Hisham ya had'e rai yace " me zan sanar dashi?"
Turab yai murmushi yace " Abdulmajid ai munkusa zama surukai."
Kallan Hisham yai cikin mamaki, yace " me? Sirikai? Badai Khadija ba?"
Turab yai kasa dakai yace " da alama kuna bukatar keb'ewa ko kwa zanta na maganar, ko gun Khadijan zaka kaji komai?"
Abdulmajid ya cika yai fam, yace " Kawu me kenan?"
Hisham ya kasa magana.
Turab ya kalli Abdulmajid yace " ka tambayi kanwarka."
Ya juya yai gaba, sai dai hankalinsa na kansu.
Baisan me sukace ba sai dai yaga sun juya a tare sunyi hanyar fita.
Turab ya kalli Garzali yace " dubamin ko gida sukai."
Yace to.
Bai dade ba ya dawo yace " ya gansu sum shiga mota a tare."
Murmushi Turab yai yace " Bari muje muga Hajiya Umma Magajiya."
Yai gaba.
Tanaji an sanar da ita zuwan Turab sai da gabanta ya sake fad'uwa.
Mike wa tai ta shiga cikin d'aki, gyara kanta tai sosai, sannan ta fito.
A zaune ta ganshi yana cin ayaba.
Karasowa tai ta zauna, Turab ya kalleta yace " Umma barka da rana."
Ta amsa cikin izzarta sannan tace " banyi tsammanin ganinka ba."
Yace " nima bansan zanzo ba sai dai kinsan Juma'a dole ne d'a ya kwashi gaisuwar iyaye."
Baki tad'an tabe, jujuyawa yai kamar yana neman wani abu yace " Banga Abdulmajid da Waziri ba, na d'auka nan sukazo."
Kallansa tai tace " baka gansu ba anan kuma ka d'auka nan suka zo? Wace irim tambaya da amsa ce wannan?"
Turab yace " naga sun fita tare da aka idar da Sallah shiyasa na garzayo saboda ingaida Baban namu."
Shiru tai sun fita tare? Me kenan? Badai Hisham baiji fadanta ba?
Turab yace " Hala sun shiga garine zumunci, abinka da d'a da mahaifi."
A hankali ya karasa maganar.
Kallansa tai tace " me kace?"
Turab yace " me nace? Nikaina na manta."
Idanu ta kafa mai tace "kamar zance d'a da mahaifi kai...."
Dariya yasa yace " d'a da mahaifi kuma? Wa? Abdulmajid da Waziri? Ta yaya?"
Kallansa tai tsoro ya gama kamata, duk yanda taso ta b'oye sai da Turab ya gano hakan, yace " Umma?"
Kallansa tai tace " wani shirme kake fad'a, kai da Sarki nake magana ai."
Yace "Ahhh ni da Abba? Ko Abba da Abdulmajid?"
Magajiya ta makamai harara, yace "Au ashefa ni Abban nawa sun zama biyu tunda akwai Waziri."
Magajiya tai murmushi tace " Wai kana shirye shiryen bikin kuwa? Ko kuwa kana nan kana neman auren wacce ba baka za'ai ba?
Turab ya mike yace " Umma ki tabbatar komai na bikina ya tafi lafiya yanda ake so, in har kinaso bakina yai shiru kenan, sannan auran Khadija sai dai in ni ince bazanyi ba badai ku ba, daga ke har Wazirin saboda......."
Sai kuma yai wani murmushi yace " a bar dai maganar ko Umma? Banasan ciwo ya kamamin ke kafin bikin d'an naki."
Kallansa tai idanunta sun kasa d'aukewa daga kallansa tace " ko? Zamu gani ai."
Gira ya d'aga yace " ya kamata mu gani kam."
Ya juya yai waje.
Yana fita ta fara maimaita kalamansa, ta rasa me suke nufi, tabbas dole ne tasan me dan iskan yaran nan ya sani.
Mikewa tai tace "Hisham dani zakaja?"
A can gidan kuwa, sun isa gidan Waziri, khadija ta fito daga wanka kenan, mai kawai ta shafa ta saka doguwad riga ta zauna a bakin gado, ita yanzu komai ma baya mata dadi, in har ta tuno da kazanta da kuna rashin imanin da suka aikata.
Muryar Umma taji tana kiranta, fitowa tai tare da amsawa, ganin Umma tai bakinta yaki rufuwa saboda tsantan farinciki.
Umma tace mata " Khadija yarima ne yazo, yana nemanki."
Sam bata kawi Abdulmajid ba dan bai taba zuwa gidansu ba, ta d'auka masoyin ranta ne.
Da sauri ta koma d'aki ta shafa hoda da turare sannan ta yafa mayafi ta fito.
Sallama tai a falon, muryar data amsa ne yasa tasan ba muryar masoyin nata bane, bud'e labulen tai tare da cewa "Yaya?"
Abdulmajid ya kalleta sannan ya kallu Umma wacce ta taho rike da tire.
Matsa mata khadija tai Umma ta mikama Khadija tire mai dauke da lemon zobo, sannan tace " a kawo abinci?"
Khadija ta kalli Abdulmajid tace " Yaya wai a kawo abinci?"
Murmushi yai dan shi ya rasa me yasa Goggo take kunyarsa, sam Bata iya tsayawa suyi magana ko zuwa can tai, yace " na koshi khadija, zobon ya isa."
Umma ta juya, kallo d'aya zaka mata kasan tana cikin tsantsar farin ciki.
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*68*
Khadija ce ta karasa ciki ta zauna sannan ta gaisheshi.
Kallanta yai yace " Khadija meye tsakaninku da yaran can?"
Kallansa tai sannan tai kasa da kai.
Yace " Khadija me kike tunani? Kinaso kicemin yaran da na tsana shi kike so? A ma bar maganar so tunda nasan dama Kina sanshi amma me kike nufi da aurensa?"
Khadija a ranta tace " abinda nasan bazai taba yiwuwa ba kenan."
Amma a fili tace " Ya Abdulmajid."
Cikin fada yace " kinaso ki je gidan sarauta a matsayin kishiyar Gimbiya? Sannan a matsayin matar wancan yaran?"
Khadija ta kalleshi tace " Yaya wai me yasa ka tsaneshi da ya wa haka?bayan bai taba yima komai ba?"
Abdulmajid ya kalleta cikin b'acin rai yace " na tsaneshi, kallansa ma ba san yi nake ba, duk duniya shine mutum na farko dana tsana."
Khadija batasan sanda tace " bayan shine ya kamata ya maka wannan tsanar?"
Yace " mene?" khadija ta kalleshi tace "Yaya please ka dinga sa ruwan sanyi a ranka, in har wannan karamar maganar ta b'ata ma rai ya zakayi in babbar magana ta doki kunenka?"
Yace " babbar magana? Wacce iri kenan?"
Juya kai tai da sauri tace " ina dai fada ne saboda ni banga abin jin haushi a maganar ba."
Abdulmajid ya mike a zuciye yai waje ko zobon baisha ba.
Kanta ta dafe tare da rufe idanunta.
Hisham kam yana d'aki yana cire Babbar riga Umma ta shigo bakin nan nata a washe, tace "wai ya akai ya biyoka?"
Yace " sai ki rufe bakin ai, kin wani baje baki kamar yau kika taba ganinsa.
Kasa tai da kai tana murmushi.
Hisham ya shiga band'aku dan kama ruwa, yana fitowa yai falo inda Abdulmajid yake.
Me zai gani?"
Ba kowa a falon, da sauri ya fito yana kiran Khadija.
Fitowa tai daga d'aki tace " gani."
Cikin tsawa yace " ina Abdulmajid?"
Tace ya tafi.
Yace " ban gane ba?"
Shiru tai dan batasan me zata ce ba.
Waje yai da sauri cikin tashin hankali.
Umma ce ta karaso gunta tace " Me kika ce masa da har zai tafi ba ko sallama? Yanzu khadija bawan Allahn nan bai taba zuwa fa gidan nan ba sai yau, amma ki koreshi? Ta ya ya zaki......"
Kasa karasawa tai, Khadija cikin tausaya mata tace "kiyi hakuri Umma amma ba korarsa nai ba."
Umma tai shiru kafin tai ciki.
Khadija ta bita da kallo cikin tausayawa.
Abdulmajid yana fita yai gida.
Har zaiyi bangarensa aka sanar dashi kiran Magajiya.
Yana shiga ya taddata a tsaye da alama yawo take a tsakar falon.
Shiga yai ya kalleta yace "Umma ga......"
Wani wawan mari da ta sakar mai ne yasa ya kasa karasawa, tace " Uban me kaje yi gidan Waziri?"
Kasa magana yai sai kuncinsa kawai daya rike yana kallanta.
Magajiya ta kara hasala tace " wato bakajin maganata ko? Na d'auka na sanar dakai ba kai ba keb'ewa da yaya? Wato shine har da zuwa gidansa ko? Ka nunamin yafini matsayi a gunka ko?"
Abdulmajid yai shiru, tace " fitarmin daga falo, sannan wlh karka kuskura inkarama magana akan wannan zancen, na fadama."
Abdulmajid yai waje jiki a sanyaye, mota ya fada ya ja ta da gudu yai waje.
Abu Turab na kallan sanda ya fita, ba shakka yasan Magajiya ta haushi da fada ne, a fili yace " am sry, sai dai kaima kayi abubuwa marasa dacewa wanda dolene kaima kaji ba dadi."
Juyawa yai ya koma b'angaren sa.
Har zai zauna ya fito ya nufi bangaren Umma.
Tana zaune tana ta raba cingam ya shiga.
Yace " Umma amma dai harda 'yan katsina zaki aikama ko?"
Tace " kanaso kenan bikinka ya lalace daga biki zuwa gulma, gulmar da zata zama silar rugujewar komai."
Turab ya kalleta yace " Kina tunanin zasuyi zancen anan?"
Tace " Abu Turab kenan, bakasan mutane ba, kai a ido ne zaka ga kamar 'yan uwa ne amma a zahiri ba haka bane."
Kallanta yai sai dai baice komai ba, a kasan ransa shikansa yana san yaga 'yan uwansa.
Basira ta cigaba, kun had'u da Mai Martaba?
Yace " a'a."
Tace shikenan.
Kallanta yai cikin kulawa yace " lafiya dai ko?"
Tace bakomai.
********
Abdulmajid kam bai tsayar da motarsa ba sai a kofar gidansu Mairo, kallan kansa yai a madubi yace " baka da inda zaka sai nan?"
Kofar gidansu ya kalla sannan ya kwantar da kansa jikin sityarin motar ya dade a haka kafin ya tada motar yai gaba.
Yayanta ne ya shigo lokacin taba tsinke alayahu.
Yace " Yauma kin fita kikai?"
Mairo tace " infita zuwa ina?"
Harararta yai yace " wlh ki kiyayi kanki da wulakanta mutum, mutum ma irin Yarima wanda kalma d'aya zai iya sa rayuwar gidan nan ta ruguje, tun dazu bawan Allahn nan yake waje har ya gaji yai gaba."
Baki ta tabe tace " ni bai aikomin ba dan bansan yazo ba."
Ciki yai tare da yin kwafa.
Mairo ta cigaba da tsinke alayahunta, can tace " me ya kawoshi da ranar nan? Sannan bai aiko ba?" tsaki tai tace " damuwarsa ce."
************
Washegari kuwa Magajiya tasa aka kira mata Hisham, yana shiga ta rufeshi da fada kai kace itace uwarsa ba ma yayarsa ba balle kuma kanwa.
Ganin abin ya zo mai wuya yasa yace " Wai Magajiya inada tambaya."
Yaran nan da kike fada akansa na waye?"
Tashin hankalin da ba'a misaltawa.
Idanunta kadai sun isa su nuna maka tsantsan tashin hankalin da take ciki, tace " Yaya?"
Yace " kwarai ni yayanki ne, sai dai abun ya isa haka, akan yaran nan yaje gidana zaki sani a gaba da fada haka? Cinyeshi nai a gidan nawa ko me?"
Kallan mamaki takemai yanzu, yauce rana ta farko da Hisham yake maida mata murtani.
Tace " yaya ni kake fadawa magana?"
Yace " an fada miki d'in, duk yanda naso in kyautata miki na kula bakya gani, yanzu kwata kwata kin zama sai a hankali komai fada, ina Magajiyar da na sani wacce tsoro baya cikin zuciyarta?"
Tace " nikaina bansan meke damuna ba Yaya, sai dai tundaga sanda yaran can ya ce yasan sirrina nakejin kamar komai na rayuwata xai ruguje, yaya ka taimakeni ka kashe yaran nan da uwarsa, ni har itama banasan gani ba shi ba."
Hisham yace " in taimakeki? Duk abinda kike min?"
Tace " amma ai kai kasab burina ko? Dolene mu kawar da duk wata matsala da zata kawo mana kai akan nad'a yaran nan mulki."
Hisham ya kalleta a ransa yace "Magajiya kenan, zanyi duk abinda kikeso saboda d'ana, sai ya hau mulki in shekaki kema barzaho."
Hannu ya saka zai murd'a kofar shiga, abinda yaji ne yasa ya tsaya cak sai jikinsa da hau tsuma saboda tsananin tsoro da razana.
Magajiya ce ta katseshi tare da cewa " yaya."
Kallanta yai bai amsa ba.
Tace " na fasa kashe basira, mai kake gani in muka haukatata?"
Hisham yace " hauka?"
Tace kwarai " idan muka halaka Turab a ranar auransa ita kuma sai musa a haukatata kaga sai ace rashin d'anta ne yasata yin haukar."
Hisham ya sheke da dariya yace " gaskiya Magajiya ba digon imani a ranki, duk duniya kece mutum ta farko danasan yasan salan mugunta, ko shed'an sai dai ya sara miki."
Murmushi tai tace " ni dai yaya ka taimaken ka kyalemun yarona, wannan shi kadai ne abinda nakeson ka dashi, mu samu komai ya kammala, banasan wani abu ya tare mai hawa mulki."
Kafafunsa ne suka kasa d'aukansa da sauri ya dafa bango, dan gaba d'aya jikinsa kaurewa yake da rawa......
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*69*
D'aki ya koma da sauri ya shige cikin d'aki shi kadai, labulayen d'akin ya rufe duka, ya shige lungun gado ya kankame kafafunsa.
Kalaman dayaji ne suke dawo masa, a haukata Basira? A kashe Turab ranar auransa?
Me ke faruwa? Me kunensa yakeji haka? Tsoro da fargaba sun hanashi fita, adaren ranar kuwa da zazzabi ya kwana.
Cikin dare kuwa yayi mafarkin wannan abu yakai sau nawa.
A zabure ya mike ya shiga cikin bargo, me Umma da kawu suke shirin yi? Kisa? Duk yanda yaso ya daure ko fitowa yai ya kasa.
Kwanan Abdulmajid biyu ko kofar gidansa bai fita ba, ya rasa menene abinyi dan abin duniya ya dameshi.
*****
Biki na ta matsowa, Gimbiya ansha gyara, gyaran da fadarsa ma bata lokaci ne, kullum Abu Turab na kiranta su gaisa.
Yau ma tsokanarta yai tayi a waya wai bata gajiya da killaceta da akai? Ba dama ko fita tai?
Sai dai tai murmushi tace " itakam bata ga wani abu ba."
Suna gama waya ya ajiye kan wayar sannan ya kalli Sabi'u yace " ya ya irin wannan sa ido haka? Ko kishi kake ne?"
Sabi'u yace " Gaskiya Turab da alama kanasan Gimbiya."
Turab yai murmushi yace " bai kamata in so ta ba?"
Sabi'u yace " ina na isa? Kawai dai da na d'auka kamar tursasa ma akai, amma yanzu naga kamar san ranka ne."
Turab yai murmushi tare da mikewa tsaye yace " Sabi'u kasan menene abinda ke halaka rayuwar zaman aure?"
"a'a."
Turab yace " nunama mace kiyayya."
Sabi'u ya kwashe da dariya yace " lalai Ango da alama ka fara shirye shiryen canza rayuwa."
Turab a ransa yace ina zaka gane abinda hakan ya jawo? Jiya da daddare ya dade yana tunanin wani abu, idan ya duba menene ya sa Magajiya ta zama tsantsar muguwa ba shakka rashin nuna mata damuwa da Sarki yai ne tun farko, wannan shine yasa take neman ta kwatarma kanta 'yanci na samun duk abinda takeso, tare da sashi ya so ta ya kuma kaskanta a gunta, wanda hakan ne ya jawo tai ta tafka kura kurai tare da kauce hanya, gashi yanzu tayi nisa wanda ta manta ma da dalilin dayasa ta cikin wannan halin tun farko.
Ajiyar zuciya yai tare da kallansa yace " Sabi'u kenan."
************
Gobe ne ake sa ran tafiya kano dan d'aurin auren Abu Turab, shirye shirye ake sosai da sosai, dan ma masu shirin suna Kano, masarautar kano kam ta cika ta batse da 'yan uwa na jini, na mulki da kuna na siyasa, Sarkin kano sosai yake cikin farinciki.
Dan ana sauran kwana hudu daurin aure yasa aka kiramai Turab ya kara bashi amanar 'yar tilon 'yar tasa da yake ji da ita kamar nama d'aya a cikin miya, yayyinta ma haka sukai ta bashi amanar ta, ba shakka ya fahimci tsantsar gata da ji da Gimbiya Bilkisu da akeyi, sai dai ko ina kalma d'aya yake fad'a _Baiyi alkawarin santa ba kamar yanda suke santa ba, sai dai ya musu alkawarin kula da ita, da kuma kaucema duk abinda zai sata dana sanin auransa._
Magajiya kuwa da Hisham sun gama shirinsu tsaf, ta rasa gane kan Abdulmajid dan sai yai kwana biyu kafin yazo gaisheta, inyazo kuwa gaisheta kawai yakeyi ya mike ya tafi, sai dai batasa wannan a ranta ba dan tana ta faman shirin yanda zasuyi gun halala Turab.
A ranar d'aurin auransa ne Abdulmajid sai zarya yake a d'aki, mai ya kamata yai?
Duk yanda yaso ya cire abin a ransa ya kasa, shi gani yake menene nashi a ciki? Sannan shima ai ba san Turab yake ba, sai dai gani yake kamar duk saboda shi Magajiya da Hisham suke neman halaka Turab, dan ya hau mulki ya kuma auri gimbiya, sannan su salwantar da mahaifiyarsa wanda take tushensa.
Har wajen karfe takwas yana ta zarya, gashi a lokacin mutane duk sun shirya ma sunyi gaba.
Magajiya ce ta aiko akan yai wanka yai shiri sosai na gani na fada.
Bai musa ba kuwa ya je yai wanka, kayan data aiko mai ya saka, kaya ne masu tsananin kyau da tsada, wanda ya tabbata ankashe kudi sosai a kansu.
Harya fita ya koma ciki tare da yanko yar takarda ya rubuta kamar haka _Ka tabbatar ka sanar ma mahaifiyarka kar taci komai yau, in har ba ita tai da kanta ba, kar kuma tasha komai._
Fitowa yai ya samu wata baiwarsa wacce take kurmiya, ya mika mata yace taje waje ta ba yaro ya kaima Abu Turab, sannan ta tabbatar bata fadama kowa ba wanda ya aikota sannan karta bari a ganta.
Hakan tayi kuwa, dan kurma Allah ya bashi iya rike sirri da kuma alkawari.
Turab yana zaune, Sabi'u na ta wani fesa mai turare kamar zai juyemai kulbar a jikinsa.
Turab yayi kyau na ban mamaki, Magajiya ta aikomai had'adun kaya sai dai bai sa ba, dan wannan Mahaifinsa ne ya aikomai.
Dole ne in ya wuce sai ka kalleshi saboda tsantsar kyan da yai, kwarjininsa da zatinsa kadai xai sa ka kalleshi ta baya.
Turab ya fizge turaren dake hannun Sabi'u yace " Ka bari in akazo naka auren sai ka fesa turare har a cikin bakinka ma, ba damuna zaiyi ba, amma ba ni ba."
Sabi'u yai dariya.
Shigowar Garzali ne yasa Turab ya kalleshi yace " Garzali ba na baka kaya nace ka saka ba?"
Kansa ya sunkuyar yace " Ranka ya dade kayan ai sunfi karfina."
Sabi'u ne yace " Gaskiya Turab ka d'au mataki da alama Garzali ya fara daina jin maganarka."
Da sauri Garzali yai kasa yace " Tuba nake ranka ya dade, yanzu zan saka."
Mikamai takarda yai yace " gashi inji wani yaro."
Turab ya amsa tare da bud'ewa.
Abinda ya ganine yatada masa hankali, yace " Garzali ina yaran yake?"
Yace " ya tafi."
Turab da sauri yai hanyar waje, dafashi Sabi'u yai yace " Lafiya?"
Turab yace " ina zuwa."
Waje yai da sauri sai dau ba yaran ba kuma alamunsa.
Fitowa yai ya nufi bangaren Mahaifiyarsa tana zaune kasanta mutane ne suna ta kukula Kayan robobi da su dubulan da zasu raba.
Mairo ya gani a gefenta, alama ya mata da hannu akan tazo.
Mairo ta mike ta fito.
Waje suka fita sannan ya kalleta yace " Mairo kina nan ai yau cir anan ko?"
Tace " a'a anjima nakesan tafiya."
Tai maganar fuskarta a had'e, irin wai kishin nan, balle yanda taga yasha kyau, haka kawai tana sanshi ba tun yanzu ba amma wata can a sama tazo zata aureshi...(😂nace Mairo ai dama haka rayuwa take, Matar mutum...Lol) dan itakam dan Basira ma ta aika tazone amma da bazata zo ba.
Turab ya mika mafa takardar nan, tana karantawa ta d'ago cikin tsananin tsoro tace "Yaya mekenan?"
Yace " ban san meke faruwa ba, sai dai na tabbatar akwai abinda ake shirin yi, ki tabbatar Umma bataci komai na gidan nan ba, ko ruwa in zatasha ki sa a kawo kara daga gidanku."
Tace " ko ruwa?"
Yace " bazai yiwu haka ba, yanzu bari nasa amaida ta kawai gidan Abba dake cikin gari, inaji hakan zaifi sauki."
Tace " mutanen da zasu nemeta fa?"
Kai ya dafa sannan yace " ko waye ma yazo nemanta ace batada lafiya tana asibiti."
Mairo tace "to."
Yace " ta fito yanzu ba sai kin fada mata ba, kawai kice wani guri nace a rakata ta gani, zan turo garzali, in yaso in kukaje gidan kya fada mata."
Tace to
Nan tai ciki, sai dayaga fitar Mahaifiyarsa sannan hankalinsa ya kwanta.
Haka suka kammala komai suka fito, sai dai jikinsa gaba daya yayi sanyi, inhar Magajiya zata cutar da Mahaifiyarsa ya tabbata ta kanshi zata fara, ya tabbatar akwai abinda take shirin yi masa.
Kansa ya dafe, da alama yayi sakaki da sharrin Magajiya, ya yi sake dayai tunanin bata isa yi masa komai yanzu ba.
Abdulmajid yana kallansa a tsaye, cikin mutane suna ta gaigaisawa, sai dai ya tabbatar shima abin na damunsa, dan murmushin da yakeyi inka kula da kyau iya l'abansa suke basu kai har zuciyarsa ba.
Ya tsani yaran can, amma me yasa yakeji bazai iya bari a kashe shi ba?
Kai ya girgiza yace " ba wai saboda shi bane, ni raine bazan iya gani a d'auka ba, Allah ne kadai ya isa yin wannan."
Cikin isa yazo ya wuce ta gun Abu Turab ko kallansa baiyi ba, shima Abu Turab ganin haka ya juya mai baya, Abdulmajid na zuwa ya bud'e had'adiyar motar Sarki wanda ya bada dan tafiyar Ango ya shiga.
Sannan ya kallu mai tukawar yace " mu tafi."
Kallansa yai yace " Ranka ya dade amma ai....."
Katseshi yai cikin fada yace " ina sasa dakai? Ko kanasan yanzu insa a kulleka?"
Da sauri ya shiga motar ya tada.
Yai gaba, Turab yana kallan sanda Abdulmajid ya shiga sai dai bai d'auka tafiya zaiyi ba.
Ganin sunyi gaba ya bi motar da kallo, lalai Abdulmajid, wannan kuma wani sabon wulakanci ne?"
Sabi'u ne ya kalleshi yace " kaga mai ya faru?"
Turab yamai alama da hannu yace " yai shiru kar aji, ba komai shi ya tafi a motar sa."
Sabi'u yai kwafa yace " amma wancan anyi mara mutunci wallahi."
Turab ya wuce ya shiga motarsa sukai gaba.
Tafiya suke sai dai gaba d'aya hankalinsa ya kasa kwanciya.
Me Magajiya take shirin yi? Yayi niyyar zuwa gunta kafin ya fito sai dai bangarenta taf yake da mutane.
Abdulmajid kam tafiya kawai sukeyi su biyu a mota, ya tabbatar duk wani abu da zatayi daga kan hanya zata yishi.
Sunyi nisa da tafiya wajen jeji kawai sukaga an tare gabansu.......
*TURAB😌*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*70*
Motar suka kalla da kyau da yanda aka nuna musu suka tabbatar itace, tsaida motar sukai ta hanyar tsayawa agaban titin tare da manyan sanduna da makamai.
Tsoro ne ya shiga jikin Abdulmajid l, shikansa driver din ya tsorata sosai.
Katon cikinsu ne ya bud'e motar ya cillo da driver din waje shikuma ya shige ciki.
Nan yaja motar sukai gaba, can cikin wani daji suka shiga dashi.
Abdulmajid ya kasa magana sai tsantsar fargaba dake damunsa, me ya kaishi? Amma dagaske su Umma abinda sukai shirin yima Abu Turab kenan? Lalai shikam yasan kwanansa ya kare, ashe bazasuyi sallama da Maironsa ba zai tafi kabari, dan tunda yaji wannan maganar a d'akin magajiya bai ko kara zuwa yaga Mairo ba.
Sai da sukai tafiya mai nisa sosai, wani gida ne kwaya d'aya a tsakiyar dajin, gida ne karami, mutumin ya tsaida mota ya bud'e bayar motar ya fizgo Abdulmajid.
Yana shiga ya cillashi ciki da karfi, jikake gum, ya buge, jikinsa ne ya shiga rawa ganin ba imani ko kadan a idan wannan mutumin, jawo kofa yai ya rufe, bai dade da fita ba yaji karar wata mota da alama ragowar ne suka iso dan ihu yaji sunayi kamar tab'abu.
Tsoro ne ya kara shigarsa, idanunsa sun firfito da tsananin tsoro.
Jiyai an banko kofa da karfi suka shigo.
Ogan cikinsu ne yazo inda yaje ya d'aga sanda ya makamai a kafa da karfinsa.
Wani mugun kara Abdulmajid ya saka wanda sai da dajin yai kara, tsananin azabar dayaji je yasa yasan anma kafarsa illa babba.
Zufa ta ko ina take ketomai, hawaye ne ke zubomai sosai saboda rad'adi so yake ma yace musu su kira wanda yasasu aikin dan ba shi bane amma ina...Azaba ta hanashi magana sam.
Murkususu yakeyi, ogan yasa dariya yace " ance mu wahalar dakai kafin mu shekaka bar zaho."
Suka tuntsire da dariya......
**********
A motar Abu Turab kuwa tafiya suke amma gaba d'aya hankalinsa ya kasa kwanciya, sai dayaga sun isa kano sannan yaji ya d'an samu sauki kadan a ransa.
Yana isa ya tadda masallacin masarautar nan taf take da jama'a, sai kiranshi ake suna gaisawa da mutane.
Har Saif ya gani a gun taron, sai dai kallo d'aya yamai ya d'auke kai yai kamar bai ganshi ba.
Yanda Hisham yai a sanda yaganshi yasa yasan da wani abu, kusa da Hisham ya karasa yace " Waziri lafiya?"
Shidai Hisham yana bayan motar sarki kadan, saboda dama anyi daga zarar motar ta fito tayi gaba sai ya bisu a baya, yana kallan aka cilar da driver din sannan wanj ya shiga yaja motar, sannan yayo gaba.
Kallan Turab yai a razane yace " motar Sarki ba a ciki ya kamata kazo ba?"
Turab yace " a ciki ne amma Abdulmajid.........."
Yanda yaga idanun Waziri sunyi ne yasa ma ya kasa karasawa, kallansa yai yace " ya akai kasan a motar sarki zanzo?"
Hisham kam baimasan me yake cewa ba shidai juyawa yai da sauri zai fita.
Turab yasa hannu da sauri ya riko rigarsa yace " ina Abdulmajid?"
Hisham ya gama rikicewa kai kawai yake girgizawa.
Turab yace " ina Abdulmajid?"
Hisham ya fizge rigarsa yai waje da gudu.
Sabi'u ya taba yace " yi sauri kabi Waziri kaga ina zaije." nan sabi'u yai waje.
Turab nan ya dunga kutsawa cikin mutane yana neman Abdulmajid sai dai bashi ba labarinsa.
An d'auran Auren Gimbiya Bilkisu da Yarima Abu Turab a ranar Asabar da misalin karfe goma sha d'aya na safe, a massalacin dake gidan sarki na kano.
Abu Turab kawai dai yake yakeyi amma gaba d'aya hankalinsa baya jikinsa, meke faruwa?
Hisham kam mota ya shiga ya dinga zabga gudu, sabi'u na bayansa yana ta binsa, a ransa yace " ko dai zariya zai koma?"
Har yai tunanin juyowa ganin suna ta tafiya ba tsayawa, gani yai ya gangara ya sauka daga kan titi ya nufi wani lungu cikin daji.
Tsayawa yai yana tunani kafin ya ajiye motar ya fito yabi bayansa cikin dajin, dan ya tabbatar inyashiga da mota hisham zai ganshi.
Hisham na isa wannan d'an gidan ko kofar motar bai rufe ba ya fito cikin hanzari.
Buga musu kofa yai tayi da karfi sai dai ba alamar kowa a ciki.
Ya gama rikicewa gaba d'aya dan ya gama sadaukarwa an gama kashe mishi d'a, zama yai a waje kawai yasa wani irin kuka.
Sabi'u ne ya karaso duk ya gama gajiya, hango gidan dayai ne yasa ya tsaya, Hisham ya gani a zaune yana baza wani irin kuka.
Boyewa yai jin shewar mutane, Hisham na jinsu ya taso a zabure ya cakumi wuyan ogan cikin su yace " ka kasheshi ko? Ka kashemin d'ana ko?"
Ogan ya kwace rigarsa yace " Malam me kenan? Kai kabamu kwangila sannan yanzu meye na zuwa mana da wannan zancen?"
Hisham cikin karaji yace " Abdulmajid kuka kama ba Abu Turab ba."
Kallansa sukai sukace " anma ai shine a cikin motar."
Hisham a rikice yace " bud'e min kofar, kun kasheshi ko?"
Bud'e kofar sukai, da sauri ya shiga ciki, yanda yaga Abdulmajid a yashe yasa ya gama rikicewa, cikin tsoro ya karasa gunsa, durkushewa yai a gub yana kuka sosai yace " najama kaina masifa, na kashe d'ana na cikina da kaina saboda wani buri nawa na shirme, nikam na shiga uku na...."
Oga ne ya matso yace " tab amma Allah ne ya kiyaye dan har naso mazgemai wuya nai tunanin barinsa zuwa anjima, ba shakka da anyi tsiya."
Hisham ya kalleshi a tsorace yace "kana nufin yanada rai"
Sosai ma sai dai kafarsa d'aya banaji zatai aiki.
Abdulmajid dake kwance yana fitar da numfashi sama sama kalaman Hisham suka daki kunuwansu, d'ansa?na cikinsa? Sai dai ba wani abu da zai iya yi dan ko magana ya kasa yi saboda dukan da sukai tamai da kafa.
Hisham ya d'ago Abdulmajid ganin yana numfashi yasa yace su taimaka mai ya sashi a mota.
Nan suka fito.
Ogan yace " Kayi hakuri yallabai, yanzu ya za'ai mu kama d'ayan?"
Hisham ya buga musu kallo yace " ku tabbatar kun bar garin nan kafin wani abu ya faru, ai dama na gama biyanku kudinku.
Nan ya shiga mota.
Sabi'u na kallansu, Abu Turab sukaso kamawa kenan su halaka? To ya akai Abdulmajid ya shiga motar? Da alama yasan da shirinsu kenan?
Lalai mutanen nan basuda imani.
Sai da Hisham yai gaba sannan shima ya fito, ya fita ya shiga mota, har zaiyi Zariya sai ya koma Kano.
Abu Turab yana cikin jama'a bayan an gama aka shiga cikin gida dan yin walima wacce yayun amarya suka shirya musu.
Suna gamawa ya fito kenan sai ga Sabi'u.
Da sauri ya matsa gunsa yace " ya ya?"
Sabi'u yace " Abdulmajid suka kama sun d'auka kaine, da alama Waziri ne yasa a kamaka."
Turab ya shaka fuskarsa da hannu biyu, ji yai idanunsa sun ciciko, mai yai wa mutanen nan, mai ya tsole musu a duniyar nan, duk abinda yaji game dasu, mahaifin Khadija? Magajiya? He will never forgive them, kallan Sabi'u yai yace " ya jikin Abdulmajid din?"
Sabi'u ya girgiza kai yace " da alama ba dadi abin dan naga kaishi mota akai."
Turab ya d'aga kansa sama saboda hawaye dake neman zubomai, sannan ya kalli Sabi'u yace " Da alama yasan abinda suke neman aikatawa, how can i forgive those people?"
Duk yanda yaso ya kore abin saj da hawaye ya zubomai ta kwaryar idanunsa, Sabi'u ya dafashi yace "Amma dama haka kake rayuwa cikinsu?"
Turab yai wani murmushin takaici sannan ya cije lab'ansa, wato su sukai su kasheshi sai su ba Basira magani suce hauka take saboda na mutu? Tabbas sai yanzu ya had'e puzzle din.
Hannunsa ya dunkule kai kace wani zai kaima naushi...........
Nikam ina ganin haka nai waje da gudu dan na d'auka ni za a make dan yanda naga idanun turab? Ba sauki......
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*71*
Magajiya kam tana zaune cikin mutane anata hidima, sai dai ta rasa gane kan dalilin dayasa akace mata wai Basira bata gidan, aikenta uku amma duk maganar d'ayace wai bata nan, ba haka taso ba lalai d'an iskan yaran can ne ya d'auke ta, to menene dalili? Inta tuna haka sai tai dariya tace " bakasan gani na karshe zaka mata ba.
Kowa yazo sai ya yaba kyan datai, saboda tsananin kyan datai, ga wani annashuwa da jin dadi dake fita daga fuskarta, tasha kwalliya, tasha lalle,hmmm abin ba a magana farinciki biyu take jira a kawo mata, na mutuwar Turab dana auran Abdulmajid da Gimbiya, taga uban da zai nemi kwace mulkin d'anta.
Aikowa akai akan Waziri nasan magana da ita, tace " a sanar dashi ina cikin taro, dan itakam ta san me zai sanar mata. Dama kuma abinda take jira kenan."
Sau biyu yana aikowa akan yana nemanta daga karshe tace " wai akan me tana cikin taron mutane zai dinga aikawa tazo?"
Murmushi tai a ranta tace " nafisan in zan fita anjima infita da kukan mutuwar d'ana Turab.
Jin haka ne yasa Waziri yaga in ya biyema jiran Magajiya d'ansa zai karasa, fitowa yai ya ja mota ya wuce asibitin ABU Gun abokin Mai Martaba.
Cikin tashin hankali da tausayawa aka shiga dashi cikin emergency.
*********
Tana zaune akan kujerarta
Sai da sukai ta sallama da mutane sannan aka barshi ya taho.
A hanya addu'a kawai yake akan Allah yasa ciwon Abdulmajid ba mai lahani bane, motar tasu tsit har suka isa kamar ba motar Ango.
Suna isa ya fito bai bi takan masu mai busa ba yai bangaren Magajiya.
Yana shiga aka fara gaisheshi, ganin gidan a cike taf yasa ya rasa yanda zaiyi, ga shi mata ne fal, juyawa yai ya fita tare da dafe kansa.
Kallan Sabi'u yai yace " muje gidansa, da alama ba nan yayo ba, dan ba alamar sun san wani abu."
Nan yai waje, sunje gidan Waziri tare da sanar da masu kula da kofa akan neman sa da suke yi, nan suka sanar dasu ai baizo ba.
Turab yace " muje gun Umma in sanar da ita sai mu shiga duba asibiti, dan na tabbatar tunda aka kaita wannan gidan a tsorace take."
Nan sukai gidan Mai martaba na cikin gari.
Mairo tana cire mata lalen data mata suna yar hirarsu sama sama, sukaji sallamar Turab.
Wani lallausan murmushi ne ya bayyana a fuskar Umma dan ba shakka zuciyarta a d'arare take, Mairo ma ta mike tare da d'auke robar lalen.
Turab ne ya shigo ya kalli Mairo cikin jin dadi yace " kanwata ina godiya sosai."
Murmushi tai tare da sunkuyar da kai.
Umma ta kalleshi tace " Alhamdulila, sai yanzu hankalina ya kwanta."
Turab ya zauna tare da cewa " umma ke sai yanzu kikai lalen bikin?" ya fada yana kallan Mairo ta gefe.
Fuska ta hade tace " itadai Umma lalle tai ba wai na biki ba, ko Umma?"
Basira ta d'aga kai tace " ina na isa yin lalle abikin Turab ai ni bikinki ne kadai zanyi Lalle Mairo."
Mairo tace " yauwa Umma." ta juya tai waje.
Turab ya kalli Umma yace " Umma kin tsorata ko?"
Kai ta girgiza alamar a'a tace " Turab taya zan tsorata akan abinda nasan kana da dalili na aikata shi?"
Murmushi yai sannan yace " Umma da matsala Amma."
Tace " tame kenan?"
Mairo ce ta d'auko mai lemon zubo da tai tare da abinci, tana kokarin shiga taji yana cewa " Abdulmajid inaji yana asibiti."
Basira tace " mene?"
Turab ya kwashe komai ya sanar da ita.
Idanu ta runtse tashiga fadin Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.
Mairo kam jikinta ne ya shiga kakkarwa, daurewa tai tai sallama.
Turab ya amsa tare da juyowa.
Ajiye tiren tai ta mike zata fita.
Turab ya kalleta, yana kallanta ya fahimci taji me yace, nan yace mata "Abdulmajid na asibiti."
Kanta na kasa tace " Me ya dameni Yaya? Fatan sauki ne namai Allah ya bashi lafiya."
Mikewa tai ta fita.
Turab ya mike ya biyota tana kokarin shiga kitchen yace " kin tabbatar bai dameki ba?"
Kai ta d'aga mai sannan ta shiga ciki.
Kallan Umma yai wacce gaba d'aya komai ya mata zafi yace " Umma karki damu yanzu zanje mu duba inda yake."
Basira tace " ka cire babbar rigar."
Nan ya zareta sannan yasa akan kujera."
Tace " abincin fa?"
Kai ya girgiza yai waje.
A kofar kitchen din ya tsaya, Mairo ya kalla tana tsaye ta juya baya, ba abinda take a kitchen din, da alama tunani take.
Yace " Mairo zo ki rakani."
Kallansa tai tace " ina?"
Yace " neman Abdulmajid."
Tace "ni kuma meye nawa?"
Turab yai murmushi yace " wai dole ne sai an nunamin akwai dakakkiyar zuciya? Bayan ni ina ganin rauninta?"
Mairo ta juya kai, yace "wuce muje."
Fitowa tai tasa takalmi suka fita.
Sabi'u na cikin motar turab ya shiga gaba.
Ita kuma ta bud'e baya ta shiga.
Sabi'u ya kalli Turab ya kuma kalli Mairo ta madubi sai dai baice komai ba.
Turab yace " mu fara da asibiti babba ko?"
Sabi'u yace " ni nasan ma yana ABU dan shikadai ne asibitin da zasu(😂nace da wannan lokacin ne da bakace haka ba, yanda asibitoci sukai yawa.)"
Turab ya jinjina kai.
Sun isa asibitin ABU, suka nufi emergency, Mairo tana tsaye bakin kofar shiga, gabanta ne kawai ke faduwa, wanda ita kanta batasan dalili ba.
Can suka hango Hisham, Sabi'u ya taba Turab tare da nunamai Hisham.
Nan suka nufi gun.
A kwance yake kamar mai baccu sai kafarsa da aka gewaye da katako, kallo d'aya zaka ma gun ka fahimci karayace a gwiwarsa sannan ga bandage da aka nad'e kasan gwiwar dashi alamar ciwo, duk fuskarsa ma an masa dressing guri guri.
Hisham kam kallan Abdulmajid kawai yake ya baza tagumi.
Turab na isa gun ya kalli Hisham cikin b'acin rai.
Baimai magana ba ya kalli wani nurse dake gun yace " ya jikin shi?"
Yace "duk an gyara ciwokan da kuma karayar yanzu ma d'aki za'a maidashi dan neman samun sauki, saboda Director yace kar a barshi anan."
Turab yace " to."
Nan suka turo gadon.
Ta gabanta sukazo suka wuce, gaba d'aya jitai komai na jikinta ya dena aiki, kana kallansa kasan yana jin jiki sosai.
Binsu kawai take har suka isa d'akin, a baya ta tsaya ganin d'akin da suka shiga.
Hisham na kokarin shiga turab ya tare kofa tare da kallansa.
Yace " Waziri mai kake anan?"
Hisham ya bishi da kallan mamaki, wannan wace irin tambaya ce? Ya kawo yaro asibiti amma a tambayeshi me yakeyi anan?"
Turab ya kara cewa " waziri mai kake yi anan?"
Hisham yace " bam gane ba?"
Turab yace " saboda tsaro da kuma yin bincike na ke sanar dakai abu d'aya in har kanasan kaga Abdulmajid sai ka bi abinda nace."
Mamaki ya hana Hisham magana, Turab yai wani murmushi yace " ko kana tunanin bansan ni kukaso a ma illa ba?"
Gaban Hisham ya yanke ya fadi.
Turab yace " kaje gidanka yanzu, ka jirani zuwa gobe."
Hisham samun kansa yai da cewa to, ya juya yai gaba jikinsa a sanyaye, yanayi yana waiwayen kofar.
Kallan Abdulmajid Turab yai, ya dade yana kallansa, tsananin tausayinsa ne ke ratsashi gashi duk jikinsa ciwuka banda karaya, kamar ba shiba sam.
Turab ya kalli Sabi'u yace " zo muje gun likitan."
Sabi'u yace " karkuma abarshi shi kadai."
Kallan Mairo Turab yai da take rakube a gefe yace " akwai wanda ahi kansa mara lafiyar yafisan ya gani."
Bai fahimta ba sai dai ya gane akwai wanda zai zauna har suje su dawo.
Sai da sukazo inda taks Turab yace "ki shiga ki duba shi."
Sukai gaba.
Mairo a hankali ta tura kofar d'akin ta shiga.
Jikin gadon ta karasa sannan ta kalli fuskarsa, gaba d'aya an mata faci.
Fuskar ta kurama ido tana tuno abubuwan da suka dinga shiga tsakaninsu.
Sam bata san sanda hawaye suka ciciko a idanunta ba, a hankali wasu siraren hawaye suka gangaro kan fuskarsa.
Jin ruwa a fuskarsa ne yasa ya dan motsa idanunsa kadan, a hankali ya bud'e idanunsa da suka kumbura idanunta a rufe suke, yana kallanta ya maida idanunsa ya rufe.
Ina ya isa ya kalleta a cikin wannan halin? Ba ma wannan halin ba, ina ya isa yi mata magana bayan bai gama sanin wanene shi ba? Menene matsayinsa?
Idanunta ta bud'e a hankali sannan ta juya baya, tare da zama akan kujera, itadai so take ta karyata zuciyarta akan kukan nan tayine saboda tausayin d'an Adam ba wai saboda wani Abdulmajid ba.
Shikam ji yake inama ba wani babban sirri agabsa yaga Mairo tana nuna damuwa haka a gabansa? Meke shirin faruwa dashi?
Wasu zafafan hawayene suka gangaro ta gefe idanunsa.
********
A can kuwa Magajiya takaici ya isheta, har yanzu busa takeji da wasanni a gidan sarauta bata fara jin koke koke ba.
_TURAB_
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*72*
Turab ne ya kalli likitan sannan yace " kana nufin kafarsa bazata dawo dai dai ba?"
Kansa ya girgiza alamar a'a yace " ba wai bazata dawo daidai gaba d'aya ba, sai dai dawowarta daidai din abu ne mai wahala, a yanzu inya warke zamu had'ashi da sanduna dan taimaka masa gun tafiya, idan har Allah yayi sai kaga a hankali kafar ta warke in yana samun kulawa."
Turab yai godiya suka mike, kallan Sabi'u yai bayan sun fito yace " Sabi'u muje ka kaini gida, sai ka d'auko Khadija ka kawo asibitin ta zauna jinyarsa, ni akwai abinda zanyi."
Sabi'u yace " wacce muka kaifa?"
Turab yai murmushi yace " kana tunanin zai sake a gun yarinyar da yake so?"
Gaba yai daga fadar haka, mota suka shiga ya kaishi gida, akan inya d'auko Khadija sai ya maida Mairo.
Magajiya kam ana zaune a waje dan an fito waje wajen wani had'aden kwalliya ta sarauta da aka zagayen gun dashi, matane manya ke ta kid'an kwarya na ruwa, sai gaishe gaishe akeyi.
Turab yana shiga ya wuce bangarensa wanda yanzu komai nashi an kwashe daga bangaren, wanka yai sannan ya bud'e drawer da ya ajiye wata shadda a ciki dan dama ya ajiye ne saboda zuwa bangaren Amarya da ita, jawota yai tare da kallan d'ankwalin daya biyo bayan shaddar.
D'ankwalin Khadija ne, sawa yai a aljihunsa dan yau zai maida mata d'ankwalinta, inhar ya maida mata kuwa to yana nufin komai na alakar dake tsakaninsu ta tsaya kenan.
Fitowa yai daga bangaren, rawani yasa akamai, sannan yasa a d'aukomai dokin da Sarki ya bashi.
Had'aden dokin da mai martaba ya bashi ya hau, yasha ado na ban mamaki, Turab ya hau kai sannan ya nufi inda ake ta mai hawan dawakai.
Yana Isa masu busa suka canza salan busarsu aka saki wani kiraki.
Magajiya tana zaune labari ya iso mata na hawan da Ango yake yi.
Kallan yan aiken tai tace " Turab ne?"
Sukace sosai ma, duk da dai rawanun dayai bazai bari mu tabbatar shi bane amma ai kowa yasan Ango ne.
Tsaki tai a ranta tace " zancen banza kenan, Ango? Ai Abdulmajid ne angon."
Yana gama hawa dan ba dadewa yai ba ya nufi inda Magajiya take.
Aiko mata akai akan d'anta yazo kwasar gaisuwa.
Murmushi ta saki tace " ace ya shiga ciki ina shigowa."
Nan aka sanar ma Turab.
Ciki ya shiga ya samu guri ya zauna.
Magajiya ta mike cikin yauki ta nufi ciki.
Murd'a kofar tai ba tare da ta kula ba saboda bayansa ya juya tace " Ango kasha kamshi, dafatan yanzu ka hakura da aura........."
Juyowar da Turab yai tare da cuge rawanin ne yasa ta tsaya cak da maganar, jitai wani abu tundaga tsakiyar kanta har kafarta.
Turab ya tako cikin isa ya karaso inda take, hannu yasa ya tura kofar d'akin data rike da karfi bai cire hannunsa daga kai ba yace " Kina mamakin ganin wanda ya kamata ya mutu ne a tsaye a gabanki?"
Magajiya ta kakaro murmushi tace " me kake nufi? Kaine Angon mana, ko akwai wani aure da akai da ban sani ba?"
Turab ya girgiza kai yace " ina fa? Ai ni kadai ne a gidan nan aka d'aurama aure yau sannan aka Wani asibiti."
Magajiya tace "asibiti kuma? Me kake nufi?"
Turab idanunsa ne suka canza kala ya juyo ya kalleta yace " sa mayafi mu fita."
Tace " mene?"
Yace " abinda kikaji shi zakiyi."
Wata muguwar dariya ta saki tace " mene?kai harka isa ka sani nayi abinda banyi ra'ayi ba?"
Murmushi ya mata yace " daya wannan lokacin kuwa duk wani abu danai ra'ayi shi xakiyi."
Ranta ne ya baci matuka ta d'aga hannu zata wanka mai mari.
Jitai yace " Ya Abdulmajid zai ji in yasan kece kika sa aka kusa kashe shi?"
Hannunta ta tsayar kusa da fuskarsa, tace " Abdulmajid? Me ya sameshi?"
Turab yace " me ya sameshi? Yana kan gadon asibiti numfashi ma banaji yanayi, ko kin manta ke kika sa a kasheni? "
A rikice tace " to meya kawo Abdulmajid ciki?"
Turab yace " wannan kuma ke zan tambaya, ya zakiyi? D'an da kike gwagwarmaya a kansa gashican nufashinsa na neman d'aukewa."
Wani irin ihu ta saka ta kama kwalar rigar Turab tace " kana nufin d'an nawa ba ma tabbas ko yana da rai?"
Turab yace " ke nake jira muje ki ganshi kafin mu mikashi gidansa."
Wani irin ihu ta kara sakawa tace " kai har ka isa? Waye ya baka damar cewa d'ana numfashinsa na neman yankewa? Amma ban taba ganin mutum mara imani irinka ba, d'an nawa ka tura a ka kusa kashewa?"
Turab yai dariya yace " mara imani? Na tura? Magajiya na kasa fahimtar wa kikema inkiya a wannan maganar, ko kinaso kicemin Waziri shi kadai yai abin ba tare da kin sani ba?"
Magajiya ta kalleshi tace " Hisham? Eh shine yasa akai komai, ni meye nawa na neman ganin bayan rayuwarka?"
Turab yai wata dariya yace " dama ta ina zaki yadda kece sila bayan ni nasan wacce ke? Duk abinda Hisham ya miki kenan kanki kawai kika sani?"
Fuska ta had'e tace " bugar cikina kazoyi kenan?"
Turab ya bi kwayar idanunta da kallo, tace " me? Akwai wasu daka b'oye a d'akin nan? So kake kaji me zan fada?"
Turab yace " me kike san kice?"
Tafin hannunfa ta d'aga tace " ka san me yasa muke da zane kala kala a hannun mu?"
Yace " kwarai, kissa ta biyo akan mata ne lokacin Annabi Yusuf......"
Ta matso kusa dashi sosai yanda shikadai zai iya jin ke take cewa tace " mata ko? Amma tunda kasan wannan kissar kasan me matar da ta sasu tai ko?"
Kallanta kawai Turab yake, tace " mace aka ce, ni kuma a matan ma dabamce. Sharri na da sanin duniya da nai ko rabinta bakai ba, kai baka isa ka shiryamin ramin da zan afka ba."
Hannu tasa ta ture hannunsa ta bud'e kofa tai waje.
Turab ya ciji lab'anbansa.
Mahaifinsa dake jikin d'ayan d'akin ne ya fito.
Bazaka taba cewa sarki bane dan Shadda ya saka ba rawani a kansa sai hula, shida Sabi'u ne.
Abdussamad ya matso ya dan daku kafadar Turab yace " ya kafadar jarumin d'ana zata yi kasa?kana tunanin daga bugun farko zakasa magajya tai kasa? Da daddare naje naga jikin nasa, sannan mayi maganar abinda ke faruwa a hankali, yanzu in aka kula na dade bama fada za'ai zargin wani abu."
Turab yace " Tuba nake."
Sarki yai murmushi yace sannan yai waje.
Turab ya tuno plan dinsa.
Sanda Sabi'u zai tafi d'auko Khadija ya sanar dashi akan in har yanasan ganin d'ansa to yaje ya sanar da Sarki akan Magajiya na san ganinsa ganin gaggawa dan da matsala, saboda shi a ka'ida bai isa yaje fada yasa mahaifinsa tasowa.
Idan mahaifinsa yaji haka ya tabbatar ransa zai baci, sai dai bai isa nunawa ba saboda girmama matarsa kuma uwar gida.
To in ya fito sai Jakadiya ta sanar dashi shigar burtu.
To yasan mahaifinsa inyaji haka yasan Turab ne ya shirya wani abu.
Ita Jakadiya zatazo bangaren magajiya ta tabbatar ta sa mutane sun fita gun kida da wayau, shikuma Sabi'u yana dawowa sai ya taho raka sarki yanda ganinsu tare bazai sa mutane susan sarki bane.
Turab ya kalli Sabi'u yace " da alama nayi gaggawa akan yin plan dina, bazata taba yarda ta a sake fooling dinta twice ba."
Sabi'u ya girgiza kai yace " wacce kake yi da ita ne tafi karfin plan din bawai kayu gaggawa ba."
Turab ya shafi kansa yace " ka kai khadijan?"
Yace " eh, na kuma maida Mairo gun Umma."
Turab yace " nagode."
Sabi'u yace " gobe fa Amarya zatazo haka zaka tarbeta jiki a sanyaye?"
Turab yai murmushi yai waje.
*********
Magajiya na fita tai bangaren Abdulmajid tasa a kira mata Hisham.
Gabanta sai faduwa yake ba kakkautawa, inka kula da hannunta ma rawa suke yi.
Yana shigowa ta taso a rikice tace " Me ya samu Abdulmajid?"
Hisham yace " tun yaushe nake aikawa kizo?"
Tace " meya sameshi?"
Hisham yace " yana asibiti gun Turab."
A rikice tace "wani irin hauka nakeji haka?"
Ganin baiyi magana ba cikin tsawa tace " uban waye ya dakarmib d'a? A kuma wani dalili ne zai kasance gun Turab??"
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*73*
Ta gabansa ta wuce a zuciye tai waje.
B'angaren Turab ta nufa, ba kowa a bangaren sai mai kula da kofa, gaisheta yai ya sanar da ita ai ba kowa a nan.
Juyawa tai hankalinta a tashe, ina ya kaimata d'anta? Itakam mai makon wannan ranar ta zama ranar farin ciki yau kam wannan ranar ta gama zame mata ranar bakin ciki.
Ga magrib ta kawo kai.....
***********
Duk yanda Khadija taso da ya bud'e ido amma inaaa, ya kasa,yana kwance idanunsa a rufe, itakam gani take kamar baya haccinsa, sai dai shikam bayaji zai iya bud'e idanunsa yaga maike faruwa a wannan duniyar, bayasan ya bud'e idanunsa yaji abinda kwakwalwarsa bazata iya d'auka ba.
Khadija zama tai a gabansa duk ta rame a 'yan kwanakin nan dan itakam sam yanzu rayuwar bata mata dadi, tace " Yaya ka taimaka ka farka."
A can gidan Barde kuwa kwance take a kan gado banda juyi ba abinda takeyi, ta rasa menene ya hanata bacci, ta dade tanata juyi ta gaji ta mike zaune tare dayin dogon tsaki tace " Allah ya isa? Wannan wace irin muguntace? Haka kawai ku samu mutum ku hau dukansa ba gaira ba dalili?"
Ahh ashe fa akwai dalili tunda Ya Turab akaje daka shi kuma ya shiga motar?
Hannu tasa akan kirjinta tare da turo baki gaba tace " Allah sarki, ashe mutumin nan nada tausayi, sannan zuciyarsa ba wai mara kyau bace duka, me yasa muka kasa gani?"
Ajiyar zuciya tai ta tuno sanda take mai rashin mutunci shi kuma yake nuna ba komai, batasan sanda ta sa murmushi ba, tunowa datai yanda ta ganshi a kan gado yasa jikinta yai sanyi.
Idanunta ne taji ya ciciko, da sauri ta kwanta taja bargo ta rufe duka har kanta.
***********
Mai Martaba ne ya kalli Turab yace " ya akai Abdulmajid ya kasance cikin wannan halin?"
Turab ya kalli Abdulmajid da ke kwance yana bacci, karfe shida da rabi ne na safe dan ana sallar asuba suka taho shida Mai Martaba.
Khadija na kwance akan sallaya rike da karamin kur'ani izu biyu da alama tana karatu bacci yai gaba da ita.
Yace " Tuba nake ranka ya dade amma ni akaso halakawa."
Sarki ya kalleshi yace "Shi kuma yaji kenan?"
Turab ya d'aga mai kyai.
Idansa ya runtse kadan sannan ya juya.
Turab yace " Abba bazaka shiga ba?"
Kai ya girgiza yace " kana tunanin zaiso gani na? Ko kana tunanin zai so ganin kowa? Bayan yaji da kunnensa mahaifiyarsa na neman yin kisan kai? Me kake tunanin yana ayyana wa a kwancen nan da yake?"
Turab ya kalli Andulmajid cikin tausayawa.
Sarki ya kamo hannun Turab yace " Abu Turab!"
Turab ya kalleshi sai dai bai amsa ba.
Sarki cikin wata irin murya yace " na girma, sannan ko ban girma ba haka na taso a rayuwar auranmu da barin Magajiya taci galaba akan dukkan lamuranta, saboda bata taba barin evidence dazai nuna tabbas itace ta aikata abu, sannan inba wanda ya san halinta ba ba wanda zai yanda akan abin da zata iya aikatawa, ina rokonka daka taimakama wannan mahaifin naka ya aiwatar da babban harkar shari'a ta gaskiya na karshe akan gadon mulkinsa, ka kawomin hujjojin da zasusa Magajiya ta fuskanci hukunci akan mayyan laifukan da ta aikata, wannan shine babban burina da ya ragemin a duniya in hakan ta faru inaso inyi murabus in baka mulkin nan, in d'auki mahaifiyata da matata mu ziyarci ka'aba dan ziyarar d'akin ma'aiki sannan mu jira sanda in karasa rayuwata cikin al'umma ina kallan yanda kake tafiyar da naka mulkin wanda shine abinda nafisan gani."
Turab yai shiru yanajin kalaman mahaifinsa,can ya d'ago yace " Abba insha Allah wannan d'an naka bazai baka kunya ba, sai dai maganar murabus mayi daga baya in komai ya kamalla."
Sarki yai murmushi sannan ya kara kallan Abdulmajid cikin tausayawa sannan yai waje.
Turab ne ya murd'a d'akin jinshi a kulle ya kai hannu zai kwankwasa.
Yanda yaga khadija tana bacci ne yasa ya sauke hannu tare da fasawa, ya tabbatar tana bukatar hutu.
Maida kayan mota yai ya zauna a cikin motar tare da kwantar da kansa jikin kujera.
Garzali ya saukemai glass, a hankali shima bacci ya zareshi.
*********
Magajiya kam wannan rana a zaune digirgir ta mata, babban tashib hankalinta duk inda ta aika a nemomata Turab sai ace baya nan, a wani hali Abdulmajid yake ciki? Dan itakam batasan wani abu ya sameshi, yanzu in matsala ta sameshi ta tabbatar shikenan ba shi ba hawa mulki, in hakan ta faru kuwa to wallahi sai dai kowa ya mutu dan Abu Turab bai isa hawa mulki ba sai dai su mutu tare.
Karfe bakwai tai wanka tai kwalliya tsaf kai kace ba matsalar dake damunta ta kintsa ta fito.
Masu kula da ita mutum biyu tace " su biyota."
Wajen karfe takwas tasa driver dinta akan ya wuce da ita ABU, manta wa ma tai ta tsaya tunanin ina aka kaishi.
Suna isa asibitin cikin sa'a ta hango motar Turab a waje.
Driver dinta ta kalla tace " je ka kiramin Garzali."
Nan yai waje, bai dade ba sai gasunan tare, Magajiya ta kalli Garzali tace " me kuke a waje haka?"
Yace " Yallabai ne ya samu bacci."
Tace " ayya, gashi shi yace inzo asibitin mu shiga tare gun Abdulmajid, kuma ba dadi yana bacci a tasheshi, ga ba wanda yasan gun, da alama sai dai ka taso shi din ko?"
Garzali yace "gun Yarima zaku?"
Tace " eh, kasan jiya ina cikin taro ban samu nazo ba sai yanzu."
Sunkuyawa yai yace " nasan d'akin in ba damuwa sai na kaiku kafin ya tashi."
Tace " shikenan."
Ta fada tare da fitowa.
Sun isa har d'akin, ta sa aka kwankwasa kofar.
Khadija dake kwance ta mike tare da zuwa bakin kofar tace waye?"
Magajiya tace " Bud'e."
Kallan masu kula da ita tai a Garzali tace "su juya."
Gaban Khadija ne ya fadi dan Turab ko Ummansu bai bari tazo ba, a hankali ta bud'e kofar
Suna juyawa ta d'aga hannu ta wankama Khadija wani gigitacen mari.
Kuncinta ta rike saboda azabar da taji, shikanshi Abdulmajid sai daya farka daga baccin, dukda dai bai bud'e ido ba amma yana jinsu.
Magajiya tace " Wato ke kin zama rikakiya ko? D'ana bashida lafiya dan tsabar rashin mutinci baki aikomin ba, bare insa ran zaki sanar dani inda yake."
A yanzu ji take zata iya yin komai dan kare d'anta, duk kuwa da yanda takesan Khadija.
Wucewa tai ta kusa da ita ta nufi gadon da Abdulmajid ke kwance.
Kallansa ta shiga yi sannan ta sa hannu kan kafarsa tace " wa ya saka? Wayace ka shiga motar da ba taka ba? Da kai nake magana, ka bud'e ido ka bani amsa ko sai ranka ya b'aci?"
Gaban Abdulmajid ne ke ta faduwa.
Muryar Khadija taji tace " Haka Uwar kirki ya kamata ta fada ma d'anta dake kwance ba lafiya?"
Magajiya ta juyo ta kalleta tace "mene?"
Khadija tace " girma ana bawa wanda yasan darajarsa ne sai dai wanda baisan darajar ba banaji ya cancanceshi, bansan me kike nufi ba da cewa Wayace ya shiga mota ba amma banaji haka ya kamata uwar da danta ke kwance ta fadama d'anta."
Magajiya cikin gadara ta fara takowa inda Khadija take, ba shakka yarinyar nan Turab ya gama lalatata.
Kusa da ita tazo ta d'aga hannu zata kara wanka mata mari.
Har Khadija ta runtse ido jin bataji saukar mari ba yasa ta bud'e idanunta a hankali.
Magajiya ce ta kalleshi tace " me kakeyi hakan?"
Turab ya kalli Khadija yace " bamu guri ko?"
Khadija tai waje.
Turab ya sauke mata hannunta yace " me kike anan?"
Tace " kaine kasa d'ana a cikin motar daya kamata ka tafi ko?"
Turab yace " mene?"
D'anki?
Hannu yasa akasan hancinsa yace " a da banso kisan abinda na sani ba sai dai kunnuwana sun gaji dajin muryarki tana cewa d'an da batasan zafinsa ba da sunan d'anta."
Idanu Magajiya ta zaro, a tsorace tad'anyi taku biyu baya.
Turab yace " me? Kina mamaki ne? Wato kinaso ki halaka asalin d'an sarki ki saka d'an d'anuwanki akan mulki shiyasa kika sa a kasheni?"
Magajiya bakinta ya fara rawa tace " bansan me kake cewa ba, sannan zance kasheka bansan wannan maganar ba, sai dai ka tambayi Hisham."
Turab ya kalleta yace " banyi mamaki ba, dan dama nasan cewa zakiyi shine ya aikata hakan."
Shiyasa ana sanar dani zuwanki nasa Garzali ya kirashi, bari yazo sai muji wanene yasa a kasheni, daga nan sai mu nufi turakar Sarki."
Magajiya tsoro da fargaba ne suka dinga ratsata, inza'asan komai nata bazai dameta ba amma banda sirrin Abdulmajid, komai zata iya kwatar kanta inhar d'anta nada matsayinsa.
Abdulmajid dake kwance a kan gado a hankali wasu zafafan hawaye suka gangaro mai.
Turab ne ya kalli kan gadon, ko tunanin me yai sai ya kalli Magajiya yace "ahhh yau Gimbiya zatazo banaji ya kamata in zauna anan, ina tunanin maganar a gida ya kamata muyi."
Ya juya da sauri yai waje.
A can gefe ya hango Khadija, gunta ya nufa fuskarnan a d'aure yace " Abdulmajid ya farka bayan na tafi?
Tace "a'a."
Bai jira mai zata kara cew ba yai gaba.
Dawowa yai inda take, kallansa tai, hannu yasa a aljihunsa ya ciro d'ankwalinta ya mika mata.
Ya juya yai gaba, bakinta ta saki tana kallansa.
Kallan bayansa tai har sai da ya bace mata, kwallar data zubo mata ta share.
Sannan ta kurama d'ankwalin ido, ita kanta dan dai ya bata d'ankwalin ne yasa tasan nata ne, amma ita kanta ta manta dashi.
Hawaye ne suka shiga zubo mata, in har Turab zai ajiye abinda ita kanta ta manta dashi to ba shakka yana santa.
Amma meye amfanin san da bata tashi sani ba sai lokacin da bazai mata amfani ba, ko da yaks da can ma ko ta sani ma ba zai musu amfani ba.
Jingina tai da bango tanajin zuciyarta na mata wani irin rad'ad'i na azaba........
*******
Magajiya kuwa Turab na fita ta rufe kofa da makulli ta zauna kusa da Abdulmajid tace " Uban waye ya isa ya ce ba ni na haifeka ba?"
Inhar kana tare dani ba abinda ba zan iya ba, dan haka ka gaggauta mikewa, Mairo kake so ko? Ka farka zan baka ita, mulki? wannan dama dole ne, sai me? Turab? Karka damu ko me zai faru sai naga bayansa, bazan taba bari yafadama wani sirrin nan nawa ba.
Ko mai zai faru banaso kasan komai, ni dai kawai ka tashi.
Sam hankalinta ya kasa kwanciya ganin Abdulmajid ko motsi baya yi.
Shi kuwa Abdulmajid samun kansa yai da Addu'a mara amfani, baisan sanda yace " Allah ka d'auki raina......"
*******
A can kano kuwa anata shirin zuwa kawo amarya, dan wasu ma yau da wuri suka taho dan kara gyara gidan Amarya da kara duba jeren da akai, Amarya Gimbiya Bilkisu kuwa yau tun safe ake ta gyarata, gyara mai sunan gyara na gargajiya bawai irin na xamani ba......
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*74*
Turab gidan Umma ya wuce inda take, yana isa ya tadda ta shiryamai abinci, nan yaci sannan ya kwanta akan kujerar falo.
Fitowa tai daga d'aki ta kalleshi tace " Turab meye hakan? Ta ya zakaci abinci ka kwanta?"
Mikewa zaune yai yace "Wlh Umma kaina kemin ciwo."
Zama tai gefensa tace " Ba dole kanka yai ciwo ba, tun da ka tafi d'aurin aure har yanzu banaji ka samu isasshen hutu na awa biyu cikake, ni na kasa gane me kake tayi a waje haka, gashi ni kace in zauna anan."
Turab ya kalli falon sannan yace "Umma ni dama ki dawo nan da zama."
Kallansa tai tace "akwai abinda kake b'oyemin ko?"
Turab yai kasa dakai yace " Ni Umma haryanzu Abba bai fad'amiki inda Hajiya dasu Lantana suke ba?"
Umma tace " Bai fad'amin ba, sai dai inaji kamar fa har yanzu jikin Hajiya ba sauki."
Turab yace "dama nayi tunanin haka, dan da ta warke da ta sanar dashi wani abu."
Basira ta kalleshi tace " me kenan?"
Kai Turab ya girgiza sannan yace " In kawo miki masu aiki daga can? Naga waccan kamar aikin zai mata yawa."
Tace " karka damu, ni ma zaman haka kawai damuna yakeyi, yanzu kai haka zaka zauna har a kawo Amaryar?"
Turab yace " name?"
Tace " ko ma dai menene, ka samu ka huta sosai kafin suzo, kar suzo suganka a haka."
Murmushi yai yace " a haka kamar ya?"
Tace " oho dai nidai na fad'ama in ba so kake su juya da ita suce dama Ashe Angon ba shida jini a jika."
Dariya ya saka sosai, yace " lalai Umma, kawai kice kinaso in huta amma wannan sharhin babu shi."
Tace " haka kace?"
Yace " hmm, ni kam Umma akwai abinda nakesan sanar dake."
Tace " name kenan?"
Yace " Umma so nake idan komai ya kammala in d'aukeki da Bilkisu muje kauyen da na taso."
Umma ta kalleshi cikin jin dadi, tace " Ni kaina inasan zuwa sai dai ina tunanin me zance ma Sarki."
Yace " ki jira in gama abinda nakeyi, sannan ki kara min addu'a akan Allah ya bani ikon gurfanar da masu laifi, ya kuma kareni daga sharrinsu, sannan karya bani ikon cutar da wasu saboda wani buri nawa."
Basira cikin kulawa take kallansa tace " Insha Allahu Allah na tare dakai, sannan muma bazamu daina maka addu'a ba."
Haka sukai ta dan hira sama sama kafin daga baya ya kwanta.
Bacci sosai ne ya d'aukeshi wanda shi kansa bai san jikinshi ya gaji haka ba.
Bai tashi ba sai karfe biyu na rana.
*********
A can gida kuwa Magajiya ce zaune a kuryar d'aki ita da Hisham ta kalleshi tace " Yaya Yaran can yasan komai."
Hisham yace " name kenan?"
Magajiya tace " yasan Abdulmajid ba d'ana bane."
Hisham yai kasa dakai wato shiyasa ya ce mai haka? Sanda ya koreshi daga asibiti?"
Magajiya ta kalli Hisham tace " yaya duk yanda za'ai inaso ka tabbatar baka bari an san nice na sa a kama Turab ba, inaso ka yarda akan kaine kai komai, ni zan san yanda zanyi karyai magana akan Abdulmajid."
Tsananin mamaki ne ya kama Hisham ya kalleta yace " ban gane ba?"
Tace " inaso ka ce kaine kasa a kama Turab in Sarki ya tambayeka, ni zansan yanda zanyi kar a hukuntaka."
Tsananin mamaki yama hanashi magana sai kallanta kawaj da yakeyi.
Magajiya tace " Sannan inaso a maida Khadija Kano, duk sauran matsalar daga baya ni zan san yanda zanyi, kai dai kai wannan abun guda biyu."
Ta mike ba tare da ta jira amsarsa ba tace " bari naje na kara shiryawa asibiti zan koma, dan bazan iya barin D'ana a can ba."
Hisham yabi bayanta kawai da kallo Baki a bud'e.
Ya dade a zaune kafin ya mike yai waje cikin tsananin takaici.
Gida ya wuce, ya shiga d'aki ya baza uban tagumi.
***********
Mairo kuwa tana gama aikin gida da takeyi tai wanka ta shirya ta cema Ummanta zataje gun Umma Basira, nan ta fito, sai dai me? Asibiti ta fara wucewa.
A jikin windown d'akin ta tsaya, ba kowa a d'akin, batai niyyar shiga ba dama, gani tai yana kokarin motsi da hannunsa da alama idanunsa a bud'e yake kuma abu yakesan d'auka.
Da sauri ta shiga ciki, yana jin motsi ya koma ya kwanta tare da rufe ido.
Mairo ta karasa gunsa da sauri tace " me kakesan d'auka?"
Ta fad'a tana kallan gefe, ruwa ta gani a jarka da alama shi yakesan d'auka.
Tace "Ruwa zaka sha?"
Jin shiru yasa ta matsa daf dashi tace " nice bakasan gani?"
Ganin bashida niyyar bud'e ido yasa haushi ya kamata ta juya zata tafi, jitai an riko hannunta.
Tsayawa tai ba tare da ta juya ba, Abdulmajid a hankali yace "Karki fad'awa kowa na farfado, na rokeki."
Cikin mamaki ta juyo ta kalleshi, gani tai yayi wani mugun fadawa, tace " bakasan asan ka farfado?"
Kai ya d'aga mata, tace "ban gane ba? Abinci fa? Ruwa fa? Kashe kanka kake sanyi?"
Maimakon taga ya bata amsa gani tai yana murmushi, tace " murmushi ma kake?"
Yace "in kina fada kyau kikeyi."
Kallan mamaki tamai, sannan ta d'auko ruwa a cup ta mikamai tace ungo.
Sam ya ma manta abinda ke gabansa ganin Mairo, yace " bazan iya tashi ba."
Harararsa tai sannan tace " ta ya ya ma zaka sha ruwa? Ai kullema ciki zaiyi."
Ta karasa tare da ajiye ruwan.
Inda kayayyakinsu yake ta shiga dubawa, kular abinci ta bude ta zubo shinkafa miya wacce taji naman kaji.
Abdulmajid yace " so kike inaci wani ya shigo?"
Tace " wai me ke faruwa?"
Idanunsa nd suka kada yace " ban cancanci cin abinci ba, magana ma bancancanci yimiki ba, Mairo."
Mairo ta kalleshi tace " nima ce maka akai ina san yi maka magana?"
Yace " haka ne, amma yanzu in wani ya shigo fa? Dan Khadija ma fita tai taje ta dawo."
Bata amsa mai ba kawai yaga ta kukule window ta sa sakata a kofa, sannan tazo ta taimaka mai ya zauna ta mikamai abinci.
Hannunsa ya nuna mata tace " to me kakeso ai?"
Yace " shiyasa nace bazan ci........"
Abincin data samai a baki ne ya hanashi karasa abinda zai fada.
Haka ta shiga bashi abinci, tana bashi ruwa, daga zaiyi magana zata ballamai harara.
**********
Turab na farkawa yaga Sabi'u a kujerar gabansa.
Kallansa yai yace " kai kuma fa?"
Sabi'u yace "gaskiya ban taba ganin ango irinka ba, ana can ana ta hidima a gidan sarauta amma kai baka nan, Ummanka bata nan, yayanka bayanan, nikam yau an ka wahalar dani."
Turab yai murmushi yace " dama ko muna nan ai jama'a ne masu hidimar ba mu ba."
Sabi'u yace " ka tashi ka shirya mu tafi, 'yan uwan Amarya sun fara zuwa.
Yace" to ni mai kake nufi inje?"
Sabi'u yace " au bazaka ku gaisa ba?"
Turab yace "amma lalai kafi kowa, a ina aka taba haka?"
Sabi'u yace " haba? Ba haka ake ba?"
Turab ya girgiza kai yace " kai in anzo naka kayi, yanzu ina Umma?"
Ya fada tare da mikewa.
Sabi'u yace "ta tafi gun 'yan uwan Amarya, tace in fadama inka tashi, insun watse ta taho."
Turab ya d'aga kai alamar gamsuwa.
Sabi'u ya kalleshi yace " dazu waziri ya aiko inje."
Turab yace " me yace?"
"yace zaiyi tunani akan abinda kace mai."
Turab yai murmushi a ransa yace " ko kayi tunani dolene ka amince da abinda nace dan nasan halin magajiya maida komai kanka zatai, in har kanasan taimakon d'anka da kuma kanka dolene kabi abinda nace."
Sabi'u ne ya kalleshi yace "me kace mai wai?"
Turab yace " ba komai."
Yai ciki.
Wanka yai ya saka kayan da Sarki ya aikomai.
Yadi ne mai masifar kyau, kallo d'aya zaka mata kasan tsadarsa.
Farin yadi ne, ya saka aikin babbar rigar kayan, yasa hula da takalmi ya fito.
Tafi Sabi'u ya saka yana ganinsa yace "kai Ango, yaufa ba dama, da alama Gimbiya yau sai an tausaya mata."
Turab ya kalleshi yace " yo ai dole a tausaya mata tunda Amaryar Sabi'u aka kai."
Sabi'u yace "anma kafadamin magana."
Haka suka taso suka fito.
""********
Zaune take a cikin mota, sai kuka takeyi, kanwar Fulani na gefenta da kishiyar Fulani.
Wani had'ad'an leshi na da mai nauyi da tsada, ta sanya, tayi kyau sosai da sosai sai dai kukan da takeyi yasa duk kwalliyar fuskar tata ta tafi.
Haka har suka isa garin na zazzagawa.
Suna isa gidan aka saki wani busa na sarauta.
Su Magajiya dama sun shirya dan tarbar ta, tana isowa suma suka fito suka zo inda suka tsaya.
Magajiya ta dafa ta saboda fuskarta a lulube take ruf.
Nan suka shiga har bangarenta, ana tafe ana zabga guda.
Magajiya na ajiyesu ta tabbatar komai ya kammala ta fito.
Tana san ganin fuskar Amarya amma hankalinta na gun Abdulmajid.
********
A asibiti kuwa Mairo tana gama bashi abinci, tana bashi ruwa aka fara kwankwasawa.
Nan ta tattare kwanukan ta ajiye a kasa, shikuma ya kwanta.
Kofar ta bude tana addu'a Allah yasa ba Magajiya bace.
Ajiyar zuciya tai ganin Hisham ne da Khadija.
Khadija ta kalleta tace " saukar yaushe?"
Mairo tace " d'azu, har abinci ma naci, dan sanda ma taho ban tsaya naci abinci ba."
Hisham ta gaida, jiki a sanyaye ya amsa ya shiga ciki ya duba Abdulmajid sannan yai waje.
Mairo ta kalli Khadija tace " are u okay?"
Khadija tace " name kenan?"
Mairo tai murmushi tace " yau ake tariyar ya Turab."
Khadija kanta ta sunkuyar sannan ta d'ago tace " ke zan tambaya ai duba da yanayin dake tsakaninku na shakuwa, ni dama mun dade a haka."
Mairo ta kamo hannunta cikin tausayawa ganin yanda idanun Khadija suka ciciko, tace " Khadija ya Turab na bala'in sanki, in nace so tofa so d'in gaske nake nufi, tun kina karama yake sanki sai dai da alama har zuwa wannan lokacin bai bayyana miki ba."
Kallanta khadija kawai takeyi, idanunta na zubo da kwalla.
Mairo tace " Ya Turab a matsayin kanwa ya d'aukeni, kece zabin ransa ban san me yasa soyayyar ku ta koma haka ba."
Khadija ta runtse ido tare da share kwallar ta tace " Mairo inaji dama can Allah baiyi akwai wata rayuwar jin dadi ta soyayya ba a tsakaninmu, soyayya ta zamantakewa bazata taba shiga tsakanina da yaya ba, mahaifina da Kanwarsa sun zalunceshi sunmai abinda na tabbatar bazai iya mantawa ba (nace wanda ma kika sani kenan), ta ina kuwa zamu iya zaman aure dashi?"
Mairo tace " to amma ai ba ke bace kikai, kuma laifin wani ai baha shafar wani."
Khadija tai murmushi tace " haka ne sai dai........."
Kallan Abdulmajid dake kwance tai, a lokacin ta tuno da kalaman Turab, a sanda take juyawa zata tafi d'azu daya ce ta fita.
Kamar Magajiya yake tambaya akan ciwon yaya.
Mikewa tai da sauri tai waje da gudu, Mairo cikin mamaki ta kalleta.
Abdulmajid na kwance duk yana jinsu, hawayen tausayin kansa dana kanwarsa ne ya ziraro mai ta gefe.
Khadija can ta hango mahaifinta da karfi ta kwalla mai kira, ko takalmi babu a kafarta.
Tsayawa yai yana kallanta, da gudu ta karaso tana hakki tace " Baba kai da Umma Magajiya kuna da hannu a ciwon Yaya?"
Kallanta yai sai dai baisan me zaicw ba, tace " Ya Turab kukaso ama haka, amma Ya Abdulmajid ya tare?"
Hisham ya kalleta yace " Khadija..." ya fada tare da kokarin kai hannu ya riko ta, da sauri tai baya tana zare ido tare da girgiza kai, dan yanda ya kira sunanta ta ya bata amsar tambayarta.....
0 comments:
Post a Comment