Kofar ya maida ya rufe sannan ya ya tako zuwa inda take.
Kallansa tai tace "har ka gama cin abincin?"
Hannu yasa a kugunta ya dan jawota a hankalu yace "ta ina zan iya ci?"
Idanu tadan raba tace "dalili?"
Dan fuska yadan gimtse kadan yana kara jawota jikinsa.
Kikace kin gama.
Ido tadan zaro tace "na gama me?"
Kallan mamaki ya mata yace "me kike nufi?"
Tace "cewa mai ka gama, cin abincinka nake nufi."
Saketa yai fuskarsa a daure yace "ka gama? Haka kika ce kenan?"
Eh da kai mai kake tunani?
Haushi ne ya kuleshi ya kalleta yace "ba sai kinji ba."
Dariyarta ta guntse tace "ina zaka?" Ganin ya juya.
Baiko kalleta ba ya shiga toilet, yana fitowa ya ganta akan gado tana bude wasu takardu, ransa ne ya kara baci ya nufota zai wuce ya koma falo.
Har yadan wuceta yaji an riko rigarsa, bai kalleta ba ya kwace rigarsa zai wuce.
Ji yai ta riko hannunsa, juyowa yai ya kalleta, tace "ina zaka?"
Kin amsa mata yai sai dai kallanta da yai, tace "azahar tayi? Dan wani sa'in banjin kiran sallah da rana, kar na makara banyi sallah ba."
Wani murmushi ya saki yace "are you playing with me?"
Murmushi tai itama ta daga kai tace "eh, sai dai da alama nayi winning."
Baisan sanda ya sake yin wani murmushin ba yace "ramawa kikai kenan?"
Sakeshi tai tana cewa "at least ka sani, me? Zaka ajiyeni kaje gunta? Nima a kalla na rama rabi."
Hannu yasa ya riketa yai baya da ita ta kwanta sannan ya kwanto yace "ba laifi at least for me ina san mace tai kishi na."
Fuska ta hade tana kallansa tace "yaushe nace kishi nake?"
Hannunyasa yana shafa gefen fuskarta yace "inje gunta? Ko in nuna miki kira nawa tamin?"
Wata harara tamai tace "sai ka dawo." Ta dan sa hannu tana neman tureshi, hannunsa ya rike yai baya dashi kan gado sannan yace "fadamin me kika ce dazu?"
Fuska ta daure tace "kaji meye na tambaya?"
Murmushi yai a hankali ya karaso yakai bakinsa cikin nata..............to dai an lula🤪
Yanda take fitar da numfashi a hankali idanunta a lumshe tana jin wani irin shauki na ratsata, bata taba tunanin abinda ake ji yakai haka ba, ita da Adam iya kaci ayi abu wani sa'in ko minti goma baiyi ake gamawa, dan ita abin ma sam baya kanta daga anyi an wuce gun take shiga wata sabgar.
Jin hannun Khalid ya jawota ya kwantar a kan bayansa yasa ta kwantar da kanta idanunta har yanzu a lumshe suke, tana fitar da numfashi a hankali ta dan ja bargo ta rufesu.
A hankali taji muryarsa yace "ashe shi yasa naji bazan iya cin indomie din ba."
Hannu tasa tadan mintsineshi kadan tace "wai ni haka kake ko yanzu ne ka zama haka?"
Murmushi yai baiyi magana ba, wani irin dadi ne ke ratsa shi.
Zainab kam tuno yanda al'amarin ya kasance dazu tai, dole gobe ta shiga makota gun Maman Al'amin.
Khalid ne taji yace "Ina so zamu hadu da Adam zamuje Naibawa ne."
"Adam? Me zakuyi?"
Tai tambayar cikin mamaki, yace "Gidan su Raziyya ina tsoron kar mahaifiyarta ko mahaifinta wani ya rasu Adam be nemi yafiyarsu ba?"
Me ya musu?
Juyowa yai ta kwanta a kafadarsa, yasa hannu a tata kafadar yana dan shafawa ya fara bata labarin abinda ya faru.
Hawaye ne ya shiga zubo mata yana diga akan kirjinsa, tadan dago ta kalleshi tace "Da alama ni......."
Dan dagowa yai ya sumbaceta hakan yasata yin shiru sai hawaye daya gangaro.
Ya kalleta yace "ba laifinki bane, san zuciya ce ta Adam tasa hakan ya faru, kuma alhakinta ne ke binsa."
Idanu tadan runtse, kallanta yai yace "ki daina dorawa kanki laifin wani, bake kika sanshi yai ba, sannan baki san da ita ba."
Kallansa tai sannan ta daga kai a hankali alamar gamsuwa.
Murmushi yai itama ta saki murmushi........
*************
Masha Allah Khalid anje Zenith an kuma turashi bank na Zenith dake ka titi zoo road wajen Sahad store, duk da daga kasa zai fara amma Alhamdulila shikam dadi yakeji kwarai da gaske.
Zainab kam yau da aiki ta tashi sai data gyara ko ina na gidan ta shige gidan Maman Al'amin, sunyi hira nan taga suna ta hade hade, ana ta hidima, itama ta sai nata ta zauna tana mata bayanin yanda ake amfani dashi.
Zainab kam kunya take in taji Maman Al'amin na mata sharhi, nan ta tambayeta kananan kaya tace "ai gobe ma zata kasuwa."l
Zainab ta ce itama zata kawo kudi a siyo mata, tayi mamaki ganin awanta daya da rabi a gidan ita da sam bata zuwa makota gidan yan uwa ma ya aka kare.
*******^^
Karfe 2 Khalid ya fito, dan sai gobe zai fara aikin full, ga shigar da zasu dinga yi ma a kayyada take.
Ajiyar zuciya yai sannan ya dau wayarsa ya kira Adam wanda yana kaance cikin bargo takaici ya gama isarsa.
Yana ganin kiransa ya daga jin muryar Khalid yai yace "ka fito mu hadu."
Adam zai yi magana yaji karar katse layi, wani kululun takaici ne ya kamashi, a kufule ya mike yana neman abinda zaisa, ransa bai gama baci ba sai daya ga ba kayan dazaisa a dakin, sai wata riga da wando na jeans haka yasa ya fito.
Aljihunsa ya duba naira hamsin ce dashi, haka ya hau bus yana tafe rai a bace dan bus din an cika ga sai kwaraf kwaraf take.
A titi aka saukeshi ya fara tafiya.
Kusa da gidan ya tsaya rai a bace yana duba Khalid, kenan nama rigashi zuwa ko me?
Daga nesa ya hango Khalid, ji yake kamar ya ruga ya bishi ya danneshi yai ta naushinsa har sai ya ji dalilin daya sashi auran matarsa.
Har Khalid ya iso gun idanun Adam na kansa kamar zai cinyeshi.
Khalid ne ya kalleshi yace "Sorry ban iso da wuri ba."
Adam ne ya karaso kusa dashi ya dunkule hannu yana kallansa rai a tsananin bace yana huci.
Khalid ya kalleshi yace "menene?"
Tambaya kake?
"A'a amsa nake."
Ya fada yana kallan gidansu Razy.
Haushi ya kara tuke Adam ya dan bugi kafadar Khalid yace "banda cin amana ka rasa wanda zaka yaudara sai matata? Hannu ya dunkule ya naushi Khalid wanda sai daya fadi gefen bakinsa ya fashe, wani murmushin jin dadi yai.
Muryar Khalid yaji yace "tunanin me kake?"
Kallansa yai da sauri kenan ba naushin yai ba?
Khalid ne yace "muje?"
Adam a kufule yace "da gaske Honey ka aura?"
Honey? Wa kenan?
Adam ya hade rai sosai yace "Da gaske Zainab ka aura?"
Kallansa yai sannan yasa hadu yadan daki kafadarsa yace "meye naka na tambayar matar wani bayan ba saka akai ba?"
Baijira yace wani abu ba yace "muje."
Adam ji yai kamar yai ihu dan bakin ciki, kofar gidan Khalid yadan buga daga cikin dattijon ya fito ya bude yana tace "waya rufe kofar."
Khalid ya kalla cikin jin dadi yace "oh saurayin nan kaine?"
Khalid yadanyi kasa dakai yana cewa "nine baba."
Cikin farin ciki yace "bismillah."
Nan ya koma ciki Khalid ya kalli Adam sannan yai ciki, shikuma ya bishi rai a bace.
Baba na shiga ya fara kiran Raziyya wacce ke kwance tana daddana waya, bakin cikin gidan duk ya isheta.
Baki ta saki ganin Khalid, kallan Adam tai, shima ya kalleta.
Fuska ta hade tace "me kake anan?" Tai tambayar tana kallan Adam.
Baba ne yace "Ah kinsan shi ne?" Yai tambayar yana cewa "Bismillah kuzo ku zauna."
Khalid ne ya fara zama sannan Adam ya zauna a darare.
Khalid ya ajiye ledar lemo da ayaba daya siyo yace "Ina wuni?"
Baba ya amsa, Adam be ya gaisheshi ya amsa sannan ya kuramai ido yace "kamar na san......."
Muryar Razy ce ta tabbatar da tunaninsa datace "Baba baka ganeshi ba? Kalleshi da kyau."
Shiru Baba yai yace "ya isa haka nan."
Kallan Adam yai yace "me kake anan gidan?"
Adam yai shiru jiki a sanyaye.
Baba yace "me ya kawo ka?"
Adam ne ya kalli Khalid gani yai Khalid din bai ko kallan sa, hakan yasa yace "kuyi hakuri abinda ya faru."
Muyi hakuri? Me dame ka mana?
Adam yai shiru, muryar Baba yaji yace "ka san rayuwar daka jefamu? Kasan halin da muka shiga a tsawon shekarun nan?"
Adam ya kalli Baba jikinsa ne ya fara sanyi.
Baba yai dan gyaran murya yace "mun dauke ka kamar d'a amma ka saka mana da butulci, sai dai kaddara ta riga fata Allah yayi ta wannan hanyar ajalinta zaizo, sai dai mahaifiyarta dake kwance tun faruwar abin, da kanwarta data sadaukar da rayuwarta saboda mu........"
Shiru yadanyi yana kallan kofar dakin da maman take.
Adam kam jiyai idanunsa ya ciciko da kwalla, Baba ya kalleshi yace "idan aka fara cewa da ace bata sanka ba, da ace ka taimaka kazo, da ace da ace da ace...... to magana ta baci dan in abu ya faru ya riga ya faru."
Razy ce ta juya ciki da gudu tasa wani wahalalen kuka wanda su kansu suna jiyo kukanta.
Jin yanda take kuka ne yasa Adam zubar da hawaye, tabbas yanzu ne ya fahimci ya tafka babban laifi, ya dau alhakin su.
Gwiwowinsa yasa a kasa, yace "Baba ka yafemin, dan Allah......." yai maganar murya a raunane.
Baba ya kalli Khalid yace "mun gode sosai, ko dan darajar ka zan yafe masa, sai dai bansan mahaifiyarta da kanwarta ba.
Ni dai ma yafe mai, Allah ya yfe mana gaba daya."
Adam ne ya kara share hawaye yace "nagode sosai."
Khalid ne ya kalli Baba yace "zamu iya ganin ta?"
Eh tana dakincan.
Nan ya rakasu, ganinta yasa Khalid duk dauriyarsa sai da idanunsa suka ciki.
Gaba daya ta rame ta yamushe duk da baisanta ba amma kana ganinta zaka gane.
Tana dan jingine dan tana jin maganarsu a waje, bakinta a dan karkace yake maganar bata yinta yanda ya kamata sai dai tanayi wanda ke zaune da ita zai gane.
Khalid ya gaisheta ta amsa, Adam yasa gwiwowinsa a kasa yana gaisheta.
Tana ganinshi ta fara zubar da kwalla tai saurin kauda kainta.
Adam ya nemi yafiyarta, Baba yace "ki yafe masa tunda ya fahimci laifinsa."
Tadanyi shiru kafin cikin maganar ta tace "Allah ya yafe mana gaba daya, na yafemai."
Kuka Adam yasa yana kara basu hakuri, wanda hakan ya raunana zuciyarsu duka.
Haka suka fito daga dakin, Dakin Razy Baba ya kalla yace "Raziyya fito."
Ya dan murda kofar, jin kofar yai a garkame.
Raziyya? Fito ko?
Kuka kawai takeyi.
Khalid ne ya matso yace "Baba a barta daga baya ya dawo, da alama abin ya dawo mata, in ta dan huce ya dawo."
Baba ya jinjina kai sannan yai ma Khalid godiya.
Adam kam sai kara neman yafiya yake yana godiya har suka fito.
******
Allah ya yafe mana laifukanmu😪
Ameen
*****
Ayusher🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
The believers are those who spend in charity during ease and hardship and who restrain their anger and pardon the people, for Allah loves the doers of good.
Surat Ali Imran 3:134
{63}
Ajiyar zuciyar data sakeyi a karo na ba adadi ta sakeyi, wayar ta data rabe gida biyu ta kalla, dan tana jin Zainab tai auri kuma wai drivernta ta saki wayar kasa ta fadi, tagumi ta sake bazawa ta sake yin ajiyar zuciya.
Haka zata cigaba da zama anan damuwa ta mata illa, yanzu taya Zainab zata musu haka?
Tuno abinda Adam yai tai ta baza tagumi dan ba shakka tun daga nan komai ya tarwatse, ajiyar zuciya ta sakeyi, tana tuno yanda tai rayuwa cikin jin dadi da walwala, yanzu gata a wani dan dakin da ake ajiye abincin tumakai, sai shi ta gyara take lalabawa.
Mikewa tai ta fito, tana kallansu suna surfe suna hira, Sadiya na gefe tana ta fama yin abincin saidawa.
Kusa da ita taje tace "Sadiya zuban shinkafar a kwana yunwa nakeji."
Kallanta Sadiya tai tace "Goggo taya zan baki ribar? Kina gani yanda nake ta faman hada kudin nan saboda bikina."
Shikenan karki bani ki bari yunwa ta kasheni.
Ta juya a kufule, da kallo Sadiya ta bita sannan ta dau plate ta dan zuba kadan ta kai mata.
Goggo ta amshi kwanan tace "Sadiya ko zaki taimakan da dari biyar? So nake na koma kano."
Dari biyar? Bandashi gaskiya, haba Goggo yanzu dan Allah bakiji kunyar ma tambayata kudi ba? Ki tafi ki barni a gidan nan banda gori ba abinda naie sha har na dage na fara neman na kaina shine yanzu zakizo ki dauran wahala.
Cikin mamaki Goggo tace "sau nawa ina bada kudi daga can a baki? Sau nawa ina sa Zainab ta ba Adam kudi ya turo miki?"
Shiru tai kafin tace "amma daga baya ai daina turowa kukai."
To ko mun daina dai a kalla ai kinci rabanki kema, dari biyar shine kike fadan magana haka?
Jikin Sadiya ne yai sanyi tace "zan kawo miki anjima."
Ta juya ta fita.
Goggo ta sa hannu tana cin abincin........
*********
Khalid na fitowa ya nufi titi, Adam na binshi a baya, gaba daya jikin Adam yai sanyi har suka isa titi ba wanda yama wa wani magana a cikinsu.
A bakin titi suka tsaya, Adam ya dan matso kusa da Khalid a hankali yace "nagode."
Shiru Khalid yai bai kalleshi ba, Adam ya juya kai cikin kuluwar yanda ya manna mai, jiyai yace "ka san rayuwar da Raziyy tai a asibiti?"
Kallan Khalid yai, wanda idanunsa ke kan titi bai jiyo ba, yace "likitan saboda rashin kudi duk sanda zai duba Firdausi sai yayi amfani da ita, can you imagine how much she suffered?"
Hankalin Adam ne yai matukar tashi yace "wani irin bala'i ne wannan?"
Khalid ya kalleshi yace "a lokacin da kake can kana jin dadin rayuwa a kasan mace, su suna can suna cikin tashin hankali, a lokacin da kake can kana baccin asara su suna can suna zaman makoki, ko da wasa ka taba tunanin kaje ka ga ya suke rayuwar su?"
Adam ne ya hadiyi wani abu yana kallan Khalid, sai yanzu Khalid ya kalleshi yace "ka dawo gobe ka nemi yafiyar ta, dan duk wannan abin dake samunka alhakin su ne ke yawo dakai, nasan dama can kana da naka issue din amma abin bai kai haka ba.
Yana kai nan yaga adaidaita ya tsayar, ganin Adam yai ya nufo adaidaitar, ya kalleshi yace "ina zaka?"
Adam ya kalleshi yace "gidanka."
Kai me?
Kallansa yai yace "Kai kace in na shirya ganinta zaka kaini."
Khalid yai wani murmushi yace "yanzun ka shirya?"
Adam yai shiru.
Khalid ya matsamai ya fara shiga sannan ya shiga suka nufi gidanshi.
A bakin gate din dan karamin gidan suka sauka Khalid ya bashi kudi sannan yai gaba Adam nabinsa a baya.
Kallan gidan yai anan Zainab ke zaune?
Khalid yace “muyi sallah tukun.” Ya fada tare da dan gangarawa hanyar masallacin da ake ta kiran sallah.”
Sai da sukai sallah sannan suka fito Khalid ya kalleshi yace “yanzu me kakeyi?”
Aiki nake nema.
Aiki? Ina da ina ka ciki?
Adam adan kufule yace “Khalid wai ni kai abokina ne ko babana?”
Khalid ya kalleshi yace “kai ai ba a maganar abokantaka dakai, sai dai ai magana kai tsaye.”
Me ka dauken?
Ya tambayeshi yana kallansa, Khalid ya shareshi suka nufi gidan.
Gidan Adam ya kara kallo da gaske nan Zainab take?
Danne tunaninsa yai yabi bayan Khalid.
*******
Zainab kam tana dawowa daga gun Maman Al'amin ta bubude abubuwan da aka bata, tunawa tai tace yawan shan fruit shine zata dinga yi musamman ma kankana da ayaba in ta hadasu ta barkada da madara, murmushi tai ta boyesu a drawer a kitchen sannan ta sa abinci tanayi ita kadai tana murmushi, fitowa tai ta hada turaren wuta ta turara kanta, tana yi tana kunyar kanta, batasan meke damunta ba, ta dade da sanin ana turara jiki dan Aunty tasha yi a gabanta ma amma sam rashin lokaci bai taba sa tayi tunanin yi ba sai yau.
Sai data gama ta fito ta zauna a falo tana duba aikinta, jefi jefi ita kadai sai ta saki murmushi, agoggo ta kalla a karo na uku, haryanzu?
Ta fada a ranta tana kallan wayarta, jin ana kiran sallar magrib yasa ta mike tai alwala, tai sallah, tana nade sallaya taji alamar sallama ana neman shigowa.
Wani irin farin ciki ne ya kamata sallayar ta ajiye ta fito da sauri, daga bakin kofa ta tsaya tana kallanshi.
Shima a bakin kofar ya tsaya yana kallanta, a tare suka sakarwa juna murmushi sannan cikin dan salo da ita kanta bata san tana da shi ba tace “sai yanzu?”
Dan taku biyu yai, ya bar Adam daga gefen kofa ta waje hannu ya bude mata, kafad’a ta noke tace “bayan kayi late dayawa.”
Hannu ya kafa nuna mata da kansa, ta kara noke kafada, dan fuska ya hade yace “shikenan.”
Ya fada yana neman zama, takowa tai a hankali ta rungumeshi.
Juyowa yai ya kara rungumeta cikin rada a kunne yace “I miss u baby.”
Murmushi tai ta kara dan kankameshi.
Kamshin turaren wuta mai sanyi take yi, idanu ya lumshe a hankali yace “do u wanna kill me?”
Tace “in ka mutu wa zai kula dani?”
Tai maganar ne a ranta sam batasan a fili tai ba sai jitai yace “I........”
Dagata yai da sauri yace “bani kadai nake ba, na manta sam.”
Kallan mamaki tamai tace “kai da waye?”
Kallanta yai da yake hijab din datai sallah yana jikinta, yace “Adam ne”
Adam? Wani Ad....Adam dai?
Yace “eh”
Me zaiyi anan?
Murmushi yai yace “matar abokinsa zai gani.”
Fuska ta daure, yace “Adam.”
Juyawa tai yasa hannu ya riko kugunta, matso da ita yai yana kallanta.
Kallansa tai, yace “bakon mijinki ne, tafiya zakiyi baku gaisa ba?”
Daidai nan Adam ya shigo, zuru yai yana kallansu, basu ma san ya shigo ba.
Zainab ce tace “am sorry, bansan me zai cemin ko nace mai bane.”
Kome zai ce ko me zakici wannan abu ne daga baya? But at least ku gaisa.”
Okay ta fada, sannan ta mai murmushi.
Juyowa tai kawai sukaga Adam a tsaye zuri, kallansa tai duk ya rame yai baki, Khalid ne ya ja hannunta ya zauna sannan ya zaunar da ita kusa dashi, ya kalli Adam yace “Adam zauna mana.”
Adam ya zauna a takure, baki na dan rawa yace “Ho......”
Mugun kallon da Khalid yamai ne yasa yace “Zainab!”
Kallansa tai tace “kana lafiya?”
Idanunsa ne suka ciciko yadan takure yace “lafiya kalau ya gida?”
Lafiya ta fada tana kallan Khalid.
Adam ya kara kallansu, ya hadiye wani abu, duk sai yaji ya raina kansa, Khalid ne yace “dan kawo mai ruwa”
Cikin dan rada tace “nayi Abinci.”
Murmushi yai yace “thanks dear.”
Kallansa tai yace “kawo mana please.”
Mikewa tai Adam na zaune na kallan ikon Allah yana ganin Zainab ta tashi ta kawo musu abinci abinda har suka gama zama a shekara 4 da sukai bata taba kawo mai abinci ba, ajiye wa tai sannan ta kalli Adam tace “Goggo fa?”
Yadan daure yace “tana kauye.”
Kauye?
Cikin dakewa yace “eh ta koma can kafin na samu aiki.”
Kai ga daga Khalid ne ya kalleta, ta koma ta zauna kusa dashi, yace “Baby ko zaki shiga ciki muci abinci tukun?”
Baby? Wa? Ni? Ganin tana ta aune aune ya kanta yasa ya ciro waya yace “kidan samin a charge.”
Amsa tai tace “okay ku gama.”
Ta wuce daki.
Tana shiga daki ta zauna a bakin gado tare da sa hannu a saitin zuciyarta dake bugawa da sauri, kwanciya tai tasa pillow ta rufe fuskarta, nice baby?
Ahhh wannan Khalid din ko? Ta fada sai kuma tai murmushi,.....
Nace ke kadai dai🤪
A falo kam Khalid ne ya zuba abinci ya kalli Adam yace “Adam Bismillah.”
Adam ya kalleshi dan dai yana jin yunwa ne amma yanayin daya samu kanshi a ciki bayaji zaiso cin wani abu.
Haka suka zuba abinci, suna ci Khalid yace “yanzu meye plan dinka?”
Plan? Bandashi ina dai fatan samun aiki.
Ka tabbatar ma ni kana neman aikin?
Kunya ce ta kama Adam ya kalleshi, cikin jin haushin kansa yace “Afreey na tambaya.”
Wani kallo yamai yace “meyasa kake so a rayuwarka ka dogara da wani? Bazaka gwada abu da kanka ba sai dai kai tabi kana neman a taimaka ma? Tundaga fara karatunka haryau baka kula komai wani bane yake maka? Haka kake so rayuwarka ta kare?”
Shiru yai jikinsa ya kara mutuwa yace “Khalid kai dani ba daya bane.”
Ba wani ni dakai ba daya bane, duk dan Adam daya ake haifarsu, kai dai kasawa kanka ka biye zuciyarka banda san jikinka baka san komai ba.”
Shiru yadanyi yanajin rashin Zainab a ransa, ga yazo yaga yanda suke rayuwarsu gaba daya ba kalar tashi ba, jiyai hawaye ya zubo mai.
Khalid ya kalleshi yace “ka zama mai kokarin neman naka wannan zaisa ka rage biye shirmen da zuciyarka ke raya maka a koda yaushe.”
Dan shiru sukai Adam ya daure ya kalli Khalid yace “Khalid da gaske Zainab dina kake aure? Gata dai na ganta naga kamarta amma gaba daya ba ita bace.”
Khalid ya kalleshi yace “Wace Zainab dinka?”
Da sauri yace “oh”
Khalid ya dan sha ruwa yace “ka duba ka nemi abinyi, karka dogara da Afreey kasan halinta sarai, in har zata taimaka ma to ko kuwa komenene dole kabi abinda take so, sannan maganar matata bana san menene dalilinka na tambayar matar da ba muharramarka ba.”
Adam yai shiru yana cin abincin, har saida suka gama ba wanda ya sake magana, Adam yasha ruwa Khalid ya kalleshi yace “kafin ka samu aiki zaka gwada wanda nai da?”
“Wanene? Zan iya ko wani aiki ne indai ba aikin karfi bane.”
Khalid ya kalleshi, kamar zaiyi magana ma sai ya fasa.
Adam yace “kayi shiru.”
“Kafi kowa sanin aikin karfi nake to cewa ba aikin karfi ba kana nufin baka so kenan.”
Adam yadanyi shiru dan shikam bashi da karfin yin aiki gaskiya.
Mikewa yai ya shiga daki, Zainab na kwance akan gado tana searching a google.
Khalid ne ya kalli wayarta ganin harya shigo bataji ba, hannu yasa ya fizge wayar.
Mikewa gai da sauri tana neman kwacewa.
Dariya yai ya daga wayar sama, hannunsa ta shiga jawowa tana san kamo wayar.
Kafada ya daga mata sannan ya dan karkace kai kadan yana kallanta.
Tace “bani please.”
Kai ya daga wayar na sama ya fara karantawa.
Love name to call your husband?
Fuska ta rufe da sauri cikin jin kunya, dariya yai ya kalleta yace “abinda kike nema kenan?”
Fuska ta dauri ta kalleshi tace “Wata ke so shine zan tura mata.”
Wata? Wannan? Ya nunata ta cikin madubi.
Tace “ce maka akai nice?”
Mika mata wayar yai yana cewa “in ni ake nemarwa ma na yafe, dan Sweet din nan nakeso, a taimaka a kirani da hakan.”
Wayar ta amsa tace “na dauka baka so, tsokana ta kake.”
“Ah a taimaka a kirani da sunan nan nidai”
Dan baya ta juya dan haka kawai taji dan kunya, tana mamakin yanda akai wai ita ke kunyar abu in yace, bayan shi sauray.......
Kansa ya sako takan kafadarta dan juyowa tai ta saitin daya sa kansa, kuncinta ya sumbata yace “muje mun gama.”
Kai ta daga, sannan ya kalleta, kallansa tai, ya kara kallanta, itama kallansa ta sake cikin rashin fahimta, kallanta yai yana nuna mata gefenta da kansa.
Kallan kan gadan tai, hikab din data cire ta kalla, kallan kanta tai yane yake da mayafi.
Yace “sa”
Dauka tai ta zura suka fito.
Adam tunda suka fito yake kallansu, har suka zauna sannan ya daure ya dauke kai.
Khalid ne ya matsa gefe yana daddana waya alamar ya barsu suyi magana.
Zainab tai murmushi in barinsu za’ai suyi magana ai sai ya tashi.
Kallan Adam tai tace “yanzu a ina kake?”
Ina gidan wani abokina ne ina neman aiki kafin a dace.
A gun wa kake nema?
Dan kallan inda Khalid yake yai sannan yai shiru, kallanshi tai tace “in kansan aikin nepa ka turo takardunka na turawa Dady, amma sai dai ka fara daga can kasa kamar yanda na fadama.”
Adam yai shiru,wato dai ko wani aiki sai aikin karfi, harga Allah shikam baisan aikin karfin nan.
Nepa din ma in daga can kasa ne ai yasan wahala suke sha, daurewa yai yace “nagode Zainab zan turo, sannan....”
Ya dan yi shiru yana kallanta, yace “dan Allah Zainab ki yafemin, abinda nazo roka kenan.”
Kallansa tai tace “nice zan nemi yafiyarka ka yafemin Adam.”
Kai ya gitgiza yana dan share kwala yace “ba abinda kika min nine na miki laifi”
Tace “na yafe maka, kaima ka yafemin.”
Cikin dan rawar murya yace “na yafe miki.”
Mikewa yai ya kalli Khalid yace “Khalid zan wuce.”
Khalid ne ya mike yace “muje na rakaka.”
Zainab ta shiga daki a kudin nan ta ciro 10k sai kuma ta rage ta dauko 5k dan tasan halin Adam a kwana daya ma sai ya cinye kudin.
Fitowa tai ta mika mai tace “ka rage wani abin ba yawa.”
Harzai amsa sai kuma yace “ta ina zan amshi kudinki?”
Tace “karka damu ba wani abin.”
Shiru yadanyi kafin ya amsa, Khalid ne yace “muje?”
Nan suka fito, Adam kam gaba daya jikinsa yayi sanyi, harya hau adaidaita bai ce kala ba, a ciki ma zugum yai.
Khalid kam na komawa gida yaga Zainab na kwashe kwanuka, murmushi yai tana dawowa daga kitchen ya kalleta yace “Baby dan dubamin daki kiban wayata.”
Kallansa tadanyi, Khalid fa akwai sa aike, haka ta wuce daki tana shiga ta ganshi shima ya shigo.
Kallansa tai cikin mamaki, matsowa ya farayi yanda taga yanayi da idanunsa ne yasa ta gane nufinsa, kallansa tai tace “sai kace ba wayarka zan dako ma ba.”
Ba kirana kikai ba?
Kallansa tai sannan tai yar dariya tace “yaushe akai hakan kenan?”
Yanzu, na tabbatar naji ance Sweet zo kaga.
Baki ta bude tace “har haka nace?”
Kai ya daga yace “sosai dan haka kunnena yaji.”
Haka dai kunnenka ke san ji.
Karasowa yai inda take yace “fadamin yanda kunne na ke san ji to.”
Tace “Sweet ga wayarka.”
Murmushi yai yace “okay, ai kece wayar tawa na gane irin juya maganan nan ne.”
Dariya tai tace “oh ni wai dama haka kake? Anya su Umma sun san..........”
Jin ya jawota ne yasata yin shiru, kallansa tai cikin wani yanayi, hannunsa yasa ya riko fuskarta a hankali ya kai bakinsa ya sumbaci saman goshinta, ya sako ya sumbashi karan hancinta, ya sumbaci idanunta dake lumshe, sannan ya sumbaci kucinta.
Idanunsa ya lumshe sannan yakai kan labanta ya sumbata, dagowa yai a hankalu ta bude idanunta, kara kallan bakinta yai sannan ya nufeshi................
********
Afreey tashi kici abinci nace ko?
Bargo ta sake ja tace “banaci.”
Afreey wai wani irin abu ne haka? So kike hankalinmu ya tashi?
Cikin kuluwa tace “ki kyaleni banaci, in har kuna so naci abinci ku kawon Khalid.”
Tace “mene?”
Bargo ta kara ja ta rufe kanta gaba daya.
Mumy haka ta mike ranta a bace ta fito.
Nace cikin wa?🤪
*************
Yau da safe tana tashi sakon shugaban gun aikinsu Abubakar ta gani, mamaki ne ya kamata dan tambayarta yake sanda take available yana san ya kira akwai maganar da yakeso suyi.
Shiru Zainab tai tana kallan text din, tare da tunanin me yake san yace mata........
^******
Ayusher🏌🏻♀
********
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
{65}
Ganin kira ya shigo cikin wayarta ne yasa ta daga “Assalamu Alaikum Sir”
Daga can Abubakar ya amsa yace “Zainab inata cigiyarki shiru bake ba labari.”
Shiru tai batace komai ba, yace “Zainab me zai haka ki taimaka ki dawo aiki? Wlh akwai matsala rashinki a nan yasa komai na neman tarwatsewa.”
Murmushi tai tace “Yallabai am sorry amma bazan koma ba.”
Yace “na sani an bata miki rai amma kiyi hakuri Zainab ki taimaki gun da kika bunkasa da hannunki karya ruguje.”
Shiru tadanyi kafin tace “An sorry yallabai amma i can’t do that.”
Yana kokarin magana tace “nagode.”
Ta kashe wayar, shiru tai tara da dafa kanta, sannan a hankali tadan sauke ajiyar zuciya.
Rubutun da take a takarda ta cigaba, har sai da azahar tai sannan ta mike tasha tea tai sallah sannan ta sa abinci.
Daki ta shiga dubawa tana neman flash dinta data ba Khalid sanda zai mata printing.
Wandan dayasa jiya ta jawo tana dubawa, takardar data ji a ciki ne yasa ta cirota tana dubawa, list din kayan da zai dinga sawa ne daga sun gama training kenan wani satin zai fara sasu?
Shiru tai tana tunanin kila bashi da ko dubu daya ma ina yaga kudin siyo wadan nan kayayyakin?
Zama tai a bakin gado tana tunani, ya zatai da Khalid?
Ganin tunani na mata yawa yasa kawai ta cigaba da abinda take tana duba abinci.
^**********
Sakon daya shigo wayarsa ne yasa ya kara kallan sakon baya ya gama karantawa.
“Khalid wannan shine magana fa karshe da zan ma in har bakazo ba to lalai zakaji sallahun mutuwa ta gobe.”
Ajiye wayar yai ya rufata ta baya ya cigaba da abinda sukeyi, har sai 5 da suka tashi sannan ya dagota.
Kallan text din ya sake kawai ya danna kira.
Afreey na kwance cikin bargo taga kiran Khalid, cikin sauri ta yays bargo ta daga tace “Khalid!” Tai maganar da sauri cikin zumudi.
Yace “Safiyya sai yaushe zaki daina abu na marasa tunani?”
Cikin mamaki tace “Khalid?”
Yace “Bansan me kika dau kanki kika dau rayuwa ba sai dai daga wannan lokaci zan canza numberta sannan zan sanar dake abu daya, kiyi kokarin daraja rayuwarki da wad’anda ke tare dake, ki nemi wanda ke sanki ki aura wannan shirmen da kike kira da sunan so ba shine so ba, ina miki fatan alkairi.”
Kha....... karar kashe wayar dataji ne yasa tace “khalid! Khalid.....”
Ganin da gaske ya kashe ta shiga sake kiransa sai dai ana tace mata wayar a kashe take, haushi ya isheta ta cilar da wayar.
*******
Khalid kam yana kashe wayar ya fito ya nufi gida.
Zainab na zaune ganin an kawo wuta ta dawo falo, harta fara aiki taji hankalinta nakan kofar waje, tana yi tana kallan time, tv ta kunna ta zauna tana kallan shirin da akeyi, gaba daya shirin dake gudana a gidan tv din ga rainashi, daga masu shirin har yanda shirin ke tafiya, tsaki tai wai a hakan plan dinta ake bi, tasha ga canza ganin ana wani indian film ta tsaya tana kallo, shigowar gate taji a hankali ta mike ta leka kofa, murmushi tai sannan ta koma da sauri ta zauna sai kuma ta girgiza kai tai saurin kwanciya akan kujerar, nan ma taga baiyi ba tai saurin daukan littafin datagama rubutu dazu ta rike wai a dole karatu take.
Khalid ne yadan kwankwasa tare da murda kofar falan, yi tai kamar bataji ba, sallama yai sannan ya kalleta, kallansa tai tadan basar ta amsa sallamar sannan tace “sannu da zuwa.”
Ta cigaba da kallan littafin, kallanta yai sannan ya shigo har ya zauna kusa da ita bata kalleshi ba, sa fuskarsa yai cikin littafin yace “ya naga kamar a juye?”
Kallan littafin tai sam batama san ta yanda ta rike ba saboda hankalinta bai wajen, kallansa tai tace “practicing din karatu a juye nakeyi.”
Practicing? Kai ta daga tace “eh.”
Ohhhh ba laifi amma..... ya jawota jikinsa, kallansa tai ya daure fuska tace “karatu fa nake”
Nima wani karatun zan zuba miki, tadan kauda kai tace “karatu?”
Yace “eh na tabbatar karatuna yafi wannan saurin shiga.”
Kallansa tai tace “shine tunda ka tafi ba ko yar text, balle waya.”
Kallanta yai cikin mamaki wanda hakan yasa tai saurin runtse idanta tare da jin haushin kanta, murmushi Khalid yai mai fadi wanda hakoransa suka fito yace “au fishin kenan?”
Kanta tasa a cinyarsa da sauri cikin jin haushin kanta, murmushi ya sakeyi ya kwanta akan bayanta yace “but i like it, i wish za’a cigaba da yin fushi dani indai akan haka ne.”
Ya dan dago yana cewa “Baby in miki text yanzu?”
Dagowa tai tace “kana gida me.....”
Sai kuma tai shiru tana murmushi ganin tunda ta fara murmushi yakeyi, tace “menene?”
Yace “i just feel like i need it now.”
Tace “me kenan?”
Hannu yasa akan cinyarta yana tahowa dashi, ture hannunshi tai, dariya yai yace “raguwa.”
Wace?
Nidai banfadi suna ba.
Ah to nidai mutum bazaicemin raguwa ba.
A gwada?
Tureshi tai tace “dama nasan juya maganar zakai.”
Yace “tunda kin sani ya akai kika biyemun?”
Dan laban bakinta ta hade sannan ta wadd tace “fanshewa kake yi ne?”
Me?
Ta matso kusa da kunnensa tace “gaurantakar da akai da?”
Ta mike da sauri tana neman guduwa, hannu yasa ya jawota, fadowa kan cinyarsa tai yace “fanshewa kike?”
Kallan sa tace “ni kuma name?”
Bakinsa yakai saitin kunnenta sai yace “na fasa fada.”
Yasa dariya, sauketa yai ya mike yana dariya, tace “fadamin name?”
Ciki ya wuce ya fada toilet, tana biyoshi taga baya dakin.
Shiru tai tana tunani name?
Falo ta dawo ta kashe tv ta kawo kai abinci falan.
Khalid na fitowa faga wanka yasa yar riga da wando ya fito.
Kallan abincin yai sannan yace “Ur sweet na godiya.”
Tace “in Sweet na godiya ya fadamun me yake nufi.”
“Ayya am sorry baby amma da alama Sweet dinki bai shirya sanar dake yanzu ba.”
Fuska ta daure tace “shikenan.”
Zama yai ya kalleta yace “bani abinci.”
Kallansa tai wannan sakalci? Haka ta zuba kai ta sa spoon ya sau spoon din yana cin jellof din shinkafa da wake datai.
Wayarta ta mikomai? Ya amsa yana kallan email din da Adam ya turo na result dinsa, result ne da kana gani kasan wanda yasha dakyar ya wuce, duk da sake jarabawar dayai dayawa.
Kallansa tai tace “Bari na turawa Dady.” Tai maganar tana neman amsar wayar, hannunta ya hade da wayar ya juyo yana kallanta, yace “ba yanzu ba.”
Cikin mamaki tace “jiya nace mai zan tura inya turo.”
Yace “haka kika ce, sai dai daga alamun maganar Adam haryanzu baisan kanshi ba, in har aka nemomai a tsukukun nan mutuncin Dady zai zubar ba komai ba.”
Kallansa tai tace “me kake tunanin yi kenan?”
Ya dan murmusa yace “barshi yai aikin gini danai na wata biyu am sure zai dawo hankalinsa.”
Okay shikenan ta fada cikin gamsuwa.
Abinci ya gama ci yasha ruwa, sai data maida kwanukan sannan ta zauna a dan gefensa, hannu ya nuna mata alamar ta matso, dawowa tai kusa dashi.
Kwanciya yai akan kunjerar ya kwantar da kansa a kan cinyarta, sannan ya sa hannunta acikin sumarsa.
A hankali ta shiga shafawa yana dan lumshe ido, kallansa tai cikin tsantsan san da batasan sanda yai mata kamu haka ba tace “dazu Shugaban gun aikina nada ya kirani.”
Idanunsa yadan bude ya kalleta, nan ta fadamai yanda sukai, kallan idanunta yai yace “kin tabbatar hakan kikeso?”
Kallansa tai tace “ta ina zan manta abinda suka ma?”
Murmushi yai yace “dan bugamin nan.” Ya nuna mata kafarsa.
Matsawa ta shiga yi, tsabar yanda ya aikatu kwanakin nan yasa har yanzu jikinsa ciwo yake.
Can tace “ya zamuyi da kayan da zaka siya?”
Bai kalleta ba yace “zan yi aiki da weekends din nan zan san yanda za’ai insha Allah.”
Shiru tai tana kallansa idanunsmta sukai rau rau tace “Sweet idan naga tanasa ba mijin kyautar abu ya zatayi?”
Yanzun ma bai kalleta ba idanunsa na lumshe yace “indai kyautar batai yawa ba ai bakomai, amma menene?”
Shiru tai wanda hakan yasa ya bude idansa yace “menene?”
Kallansa tai tace “please!” Tai maganar cikin rauni idanunga na digo da hawaye.
Mikewa yai yace “menene?”
Ta kalleshi tace “please ka barni na saima kayan.”
Kallanta yai yace “nace za......”
Rungumeshi tai kam wanda hakan yasa jikinsa yin sanyi, tace “bakasan yanda nakeji ba in ka je gun aikin gini din nan, dan Allah kayi hakuri ka bari nasaima kyautar abu nake san ma amma nasan bazaka taba amsa ba, shiyasa na fadama kar ranka ya baci.”
Ta kara kankameshi, kanta ya shiga shafawa, duk da ba mace bace kai gashi sosai a kallantana da nata daidai gwargwado dan in ta gyara shi yana kwanciya luf.
Dagota yai ya sa hannu yana share mata kwallarta, yace “ana kiran sallah muyi sallah ko?”
Kai ta daga tana kallanshi.
Alwala tai sukai sallah tare, yace ta dauko qur’ani nan tamai karatu yaji, ya mata gyara sannan ya dan daura mata kadan.
***********
Adam kam sai duba waya yake yana jiran sakon Zainab na cewar ta tura komai ya kammala sai dai har dare yai bai ga komai ba, wajen karfe 9 sako ya shigo wayarsa da sauri ya dauka ganin numberce yasa ya bude a dan zuciye.
Number aka turo mai a kasa akasa ka kirashi, namai bayani zakazo gobe, sunanshi Gaddafi.
Sannan kaje gidan su Raziyyan?
Daga Khalid!
Zanzo gobe? Har aikin ya samu?
Shiru yai sannan ya tuna yau yaso zuwa gidansu Raziyyan amma baisamu ya fita ba saboda jiya kasa bacci yai in ya tuno abinda ya faru a gidan Zainab sai yaji sam baccin yaki zuwa.
Jiya itace rana ta farko da ya taba kasa bacci arayuwarsa,
********
Salmanu ne ya shigo bayan an mai izini, hannunsa dauke da bakar leda.
Umma tace “Salmanu sannu da zuwa”
Shigowa yai yana dariya yace “Umma kinjini shiru ko?”
Tace “ai da bakazo yau ba sawa zanyi Asiya ta kiramin kai a waya naji ko lafiya.”
Dariya yai yana karasowa, Abba yace “nikaina nace wannan d’a lafiya?”
Kusa da Abba ya zauna yace “wlh munje dutse ne neman aiki Abba.”
Umma tace “masha Allah, Allah yasa a dace.”
Ameen yace ya ajie ledar gaban Umma yace “Umma ga tsarabar zuwa dutse.”
Budewa taj tana cewa “mungode, Abban Khalid gashi an kawo mana dankalin hausa.”
Mungode sosai.
Asiya ce ta fito gaisheshi tai sannan tai hanyar komawa ciki.
Umma tace “Asiya zo ajiye wannan, yanzu yayanki Salmanu ya kawo.”
Kusa da Umma tazo ta dauka, tana dagowa suka hada ido da Salmanu, murmushi ya mata ta dauka ta ajiye.
Zata koma ciki Umma tace “zo ki kawo mai abinci, Salmanu alale ne nasan kana so.”
Kallan Asiya yai yace “Asiya zubomin alale.”
Ya kalli Umma yace “ashe raban zanci alale ne yasa na rike yunwata.”
Umma tai dariya, kallan Asiya yai harta zubo ta kawo mai sannan ta juya ciki.
*********
Ayusher🏌🏻♀
***********
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
{65}
Ganin kira ya shigo cikin wayarta ne yasa ta daga “Assalamu Alaikum Sir”
Daga can Abubakar ya amsa yace “Zainab inata cigiyarki shiru bake ba labari.”
Shiru tai batace komai ba, yace “Zainab me zai haka ki taimaka ki dawo aiki? Wlh akwai matsala rashinki a nan yasa komai na neman tarwatsewa.”
Murmushi tai tace “Yallabai am sorry amma bazan koma ba.”
Yace “na sani an bata miki rai amma kiyi hakuri Zainab ki taimaki gun da kika bunkasa da hannunki karya ruguje.”
Shiru tadanyi kafin tace “An sorry yallabai amma i can’t do that.”
Yana kokarin magana tace “nagode.”
Ta kashe wayar, shiru tai tara da dafa kanta, sannan a hankali tadan sauke ajiyar zuciya.
Rubutun da take a takarda ta cigaba, har sai da azahar tai sannan ta mike tasha tea tai sallah sannan ta sa abinci.
Daki ta shiga dubawa tana neman flash dinta data ba Khalid sanda zai mata printing.
Wandan dayasa jiya ta jawo tana dubawa, takardar data ji a ciki ne yasa ta cirota tana dubawa, list din kayan da zai dinga sawa ne daga sun gama training kenan wani satin zai fara sasu?
Shiru tai tana tunanin kila bashi da ko dubu daya ma ina yaga kudin siyo wadan nan kayayyakin?
Zama tai a bakin gado tana tunani, ya zatai da Khalid?
Ganin tunani na mata yawa yasa kawai ta cigaba da abinda take tana duba abinci.
^**********
Sakon daya shigo wayarsa ne yasa ya kara kallan sakon baya ya gama karantawa.
“Khalid wannan shine magana fa karshe da zan ma in har bakazo ba to lalai zakaji sallahun mutuwa ta gobe.”
Ajiye wayar yai ya rufata ta baya ya cigaba da abinda sukeyi, har sai 5 da suka tashi sannan ya dagota.
Kallan text din ya sake kawai ya danna kira.
Afreey na kwance cikin bargo taga kiran Khalid, cikin sauri ta yays bargo ta daga tace “Khalid!” Tai maganar da sauri cikin zumudi.
Yace “Safiyya sai yaushe zaki daina abu na marasa tunani?”
Cikin mamaki tace “Khalid?”
Yace “Bansan me kika dau kanki kika dau rayuwa ba sai dai daga wannan lokaci zan canza numberta sannan zan sanar dake abu daya, kiyi kokarin daraja rayuwarki da wad’anda ke tare dake, ki nemi wanda ke sanki ki aura wannan shirmen da kike kira da sunan so ba shine so ba, ina miki fatan alkairi.”
Kha....... karar kashe wayar dataji ne yasa tace “khalid! Khalid.....”
Ganin da gaske ya kashe ta shiga sake kiransa sai dai ana tace mata wayar a kashe take, haushi ya isheta ta cilar da wayar.
*******
Khalid kam yana kashe wayar ya fito ya nufi gida.
Zainab na zaune ganin an kawo wuta ta dawo falo, harta fara aiki taji hankalinta nakan kofar waje, tana yi tana kallan time, tv ta kunna ta zauna tana kallan shirin da akeyi, gaba daya shirin dake gudana a gidan tv din ga rainashi, daga masu shirin har yanda shirin ke tafiya, tsaki tai wai a hakan plan dinta ake bi, tasha ga canza ganin ana wani indian film ta tsaya tana kallo, shigowar gate taji a hankali ta mike ta leka kofa, murmushi tai sannan ta koma da sauri ta zauna sai kuma ta girgiza kai tai saurin kwanciya akan kujerar, nan ma taga baiyi ba tai saurin daukan littafin datagama rubutu dazu ta rike wai a dole karatu take.
Khalid ne yadan kwankwasa tare da murda kofar falan, yi tai kamar bataji ba, sallama yai sannan ya kalleta, kallansa tai tadan basar ta amsa sallamar sannan tace “sannu da zuwa.”
Ta cigaba da kallan littafin, kallanta yai sannan ya shigo har ya zauna kusa da ita bata kalleshi ba, sa fuskarsa yai cikin littafin yace “ya naga kamar a juye?”
Kallan littafin tai sam batama san ta yanda ta rike ba saboda hankalinta bai wajen, kallansa tai tace “practicing din karatu a juye nakeyi.”
Practicing? Kai ta daga tace “eh.”
Ohhhh ba laifi amma..... ya jawota jikinsa, kallansa tai ya daure fuska tace “karatu fa nake”
Nima wani karatun zan zuba miki, tadan kauda kai tace “karatu?”
Yace “eh na tabbatar karatuna yafi wannan saurin shiga.”
Kallansa tai tace “shine tunda ka tafi ba ko yar text, balle waya.”
Kallanta yai cikin mamaki wanda hakan yasa tai saurin runtse idanta tare da jin haushin kanta, murmushi Khalid yai mai fadi wanda hakoransa suka fito yace “au fishin kenan?”
Kanta tasa a cinyarsa da sauri cikin jin haushin kanta, murmushi ya sakeyi ya kwanta akan bayanta yace “but i like it, i wish za’a cigaba da yin fushi dani indai akan haka ne.”
Ya dan dago yana cewa “Baby in miki text yanzu?”
Dagowa tai tace “kana gida me.....”
Sai kuma tai shiru tana murmushi ganin tunda ta fara murmushi yakeyi, tace “menene?”
Yace “i just feel like i need it now.”
Tace “me kenan?”
Hannu yasa akan cinyarta yana tahowa dashi, ture hannunshi tai, dariya yai yace “raguwa.”
Wace?
Nidai banfadi suna ba.
Ah to nidai mutum bazaicemin raguwa ba.
A gwada?
Tureshi tai tace “dama nasan juya maganar zakai.”
Yace “tunda kin sani ya akai kika biyemun?”
Dan laban bakinta ta hade sannan ta wadd tace “fanshewa kake yi ne?”
Me?
Ta matso kusa da kunnensa tace “gaurantakar da akai da?”
Ta mike da sauri tana neman guduwa, hannu yasa ya jawota, fadowa kan cinyarsa tai yace “fanshewa kike?”
Kallan sa tace “ni kuma name?”
Bakinsa yakai saitin kunnenta sai yace “na fasa fada.”
Yasa dariya, sauketa yai ya mike yana dariya, tace “fadamin name?”
Ciki ya wuce ya fada toilet, tana biyoshi taga baya dakin.
Shiru tai tana tunani name?
Falo ta dawo ta kashe tv ta kawo kai abinci falan.
Khalid na fitowa faga wanka yasa yar riga da wando ya fito.
Kallan abincin yai sannan yace “Ur sweet na godiya.”
Tace “in Sweet na godiya ya fadamun me yake nufi.”
“Ayya am sorry baby amma da alama Sweet dinki bai shirya sanar dake yanzu ba.”
Fuska ta daure tace “shikenan.”
Zama yai ya kalleta yace “bani abinci.”
Kallansa tai wannan sakalci? Haka ta zuba kai ta sa spoon ya sau spoon din yana cin jellof din shinkafa da wake datai.
Wayarta ta mikomai? Ya amsa yana kallan email din da Adam ya turo na result dinsa, result ne da kana gani kasan wanda yasha dakyar ya wuce, duk da sake jarabawar dayai dayawa.
Kallansa tai tace “Bari na turawa Dady.” Tai maganar tana neman amsar wayar, hannunta ya hade da wayar ya juyo yana kallanta, yace “ba yanzu ba.”
Cikin mamaki tace “jiya nace mai zan tura inya turo.”
Yace “haka kika ce, sai dai daga alamun maganar Adam haryanzu baisan kanshi ba, in har aka nemomai a tsukukun nan mutuncin Dady zai zubar ba komai ba.”
Kallansa tai tace “me kake tunanin yi kenan?”
Ya dan murmusa yace “barshi yai aikin gini danai na wata biyu am sure zai dawo hankalinsa.”
Okay shikenan ta fada cikin gamsuwa.
Abinci ya gama ci yasha ruwa, sai data maida kwanukan sannan ta zauna a dan gefensa, hannu ya nuna mata alamar ta matso, dawowa tai kusa dashi.
Kwanciya yai akan kunjerar ya kwantar da kansa a kan cinyarta, sannan ya sa hannunta acikin sumarsa.
A hankali ta shiga shafawa yana dan lumshe ido, kallansa tai cikin tsantsan san da batasan sanda yai mata kamu haka ba tace “dazu Shugaban gun aikina nada ya kirani.”
Idanunsa yadan bude ya kalleta, nan ta fadamai yanda sukai, kallan idanunta yai yace “kin tabbatar hakan kikeso?”
Kallansa tai tace “ta ina zan manta abinda suka ma?”
Murmushi yai yace “dan bugamin nan.” Ya nuna mata kafarsa.
Matsawa ta shiga yi, tsabar yanda ya aikatu kwanakin nan yasa har yanzu jikinsa ciwo yake.
Can tace “ya zamuyi da kayan da zaka siya?”
Bai kalleta ba yace “zan yi aiki da weekends din nan zan san yanda za’ai insha Allah.”
Shiru tai tana kallansa idanunsmta sukai rau rau tace “Sweet idan naga tanasa ba mijin kyautar abu ya zatayi?”
Yanzun ma bai kalleta ba idanunsa na lumshe yace “indai kyautar batai yawa ba ai bakomai, amma menene?”
Shiru tai wanda hakan yasa ya bude idansa yace “menene?”
Kallansa tai tace “please!” Tai maganar cikin rauni idanunga na digo da hawaye.
Mikewa yai yace “menene?”
Ta kalleshi tace “please ka barni na saima kayan.”
Kallanta yai yace “nace za......”
Rungumeshi tai kam wanda hakan yasa jikinsa yin sanyi, tace “bakasan yanda nakeji ba in ka je gun aikin gini din nan, dan Allah kayi hakuri ka bari nasaima kyautar abu nake san ma amma nasan bazaka taba amsa ba, shiyasa na fadama kar ranka ya baci.”
Ta kara kankameshi, kanta ya shiga shafawa, duk da ba mace bace kai gashi sosai a kallantana da nata daidai gwargwado dan in ta gyara shi yana kwanciya luf.
Dagota yai ya sa hannu yana share mata kwallarta, yace “ana kiran sallah muyi sallah ko?”
Kai ta daga tana kallanshi.
Alwala tai sukai sallah tare, yace ta dauko qur’ani nan tamai karatu yaji, ya mata gyara sannan ya dan daura mata kadan.
***********
Adam kam sai duba waya yake yana jiran sakon Zainab na cewar ta tura komai ya kammala sai dai har dare yai bai ga komai ba, wajen karfe 9 sako ya shigo wayarsa da sauri ya dauka ganin numberce yasa ya bude a dan zuciye.
Number aka turo mai a kasa akasa ka kirashi, namai bayani zakazo gobe, sunanshi Gaddafi.
Sannan kaje gidan su Raziyyan?
Daga Khalid!
Zanzo gobe? Har aikin ya samu?
Shiru yai sannan ya tuna yau yaso zuwa gidansu Raziyyan amma baisamu ya fita ba saboda jiya kasa bacci yai in ya tuno abinda ya faru a gidan Zainab sai yaji sam baccin yaki zuwa.
Jiya itace rana ta farko da ya taba kasa bacci arayuwarsa,
********
Salmanu ne ya shigo bayan an mai izini, hannunsa dauke da bakar leda.
Umma tace “Salmanu sannu da zuwa”
Shigowa yai yana dariya yace “Umma kinjini shiru ko?”
Tace “ai da bakazo yau ba sawa zanyi Asiya ta kiramin kai a waya naji ko lafiya.”
Dariya yai yana karasowa, Abba yace “nikaina nace wannan d’a lafiya?”
Kusa da Abba ya zauna yace “wlh munje dutse ne neman aiki Abba.”
Umma tace “masha Allah, Allah yasa a dace.”
Ameen yace ya ajie ledar gaban Umma yace “Umma ga tsarabar zuwa dutse.”
Budewa taj tana cewa “mungode, Abban Khalid gashi an kawo mana dankalin hausa.”
Mungode sosai.
Asiya ce ta fito gaisheshi tai sannan tai hanyar komawa ciki.
Umma tace “Asiya zo ajiye wannan, yanzu yayanki Salmanu ya kawo.”
Kusa da Umma tazo ta dauka, tana dagowa suka hada ido da Salmanu, murmushi ya mata ta dauka ta ajiye.
Zata koma ciki Umma tace “zo ki kawo mai abinci, Salmanu alale ne nasan kana so.”
Kallan Asiya yai yace “Asiya zubomin alale.”
Ya kalli Umma yace “ashe raban zanci alale ne yasa na rike yunwata.”
Umma tai dariya, kallan Asiya yai harta zubo ta kawo mai sannan ta juya ciki.
*********
Ayusher🏌🏻♀
***********
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
{66}
Kwance take akan kirjinsa kamar me bacci, yana dan shafa kafadarta zuwa bayanta.
Shima yana kwance ne sun luluba da bargo, a hankali tace “Dady dazu yamin text yana san jin sanda kake dawowa gida, yana san kiranka.”
Kin fadamai?
Hmm tace kafin tafan yi ajiyar zuciya kadan tace “na san maganar aiki ne, in na fara aiki ya kake gani zamuyi?”
Ba tare da dogon nazari ba yace “kafin ki tafi sai kin gama komai na gida kinyi abinci kin ajiye sannan ki fita”
Da sauri ta dago tace “da safen?”
Yace “eh haka duk mata masu aiki sukeyi.”
Amma ni da nake fita da wuri fa?
“Sai ki tashi tsakar dare.”
Baki ta bude tana kallansa, kallanta yai yace “menene?”
Tace “wani sa’in sai na kasa gane wanene kai”
Kara jawota jikinsa yai yace “so kike nace ki fita aiki sanda kikeso ba tare da kinyi komai ba?”
Tace “ba haka ba amma ta ina zai iya aikin gida nai abinci kafin na fita?”
Kafada yadan daga sannan ya dan sumbaci goshinta yace “zaki iya tunda kina san aikinki kina kuma san Sweet dinki.”
Bata san sanda tasa dariya ba sannan ta kalleshi tace “mekace?”
Yace “kina san aikinki kina kuma san mijinki, ba haka bane?”
Dan ido ta dan kikifta tace “ko haka ne sai ka fada kai tsaye? Sai a bari na fada da kaina.”
Ko baki fada ba jikinki ya fadamin me zai sa na jira sai kin fada?
Dariya ta sake ta sa hannu ta dan tureshi ya dan murgina kadan tace “Allah nikam na rasa irinka.”
Ta juya mai baya tana kunshe dariyarta, juyowa yai ya rungumeta ta baya, hannunsa ya sako saman kirjinta yasa kansa a bayanta yace “Allah in na tuno shekararki hudu da shi sai naji kamar......”
Dan yawon bakinta ta hadiya sannan ta dan lashi kasan lebanta kadan, batace komai ba, shiru yadanyi jiyai tace “kasan meyasa banji haushin yimai magana ba balle harnai tunanin taimakon shi?”
Meyasa? Ya tambaya yana dan kara gyara kansa dake wajen wuyanta.
Juyowa tai suna fuskartar juna, daf suke da juna, tasa hannu akan fuskarsa tana dan shafawa kadan tace “ta hanyarsa na hadu dakai, sannan ta hanyarsa muka kai inda muke yanzu, da ban aureshi ba kila bazan sanka ba, da bai ci amana ta kila bazamu kai wannan stage din ba.”
Tadan yi wani lalausan murmushi tace “shiyasa ko haushinshi banaji.”
A hankali wani murmushi ya bayyana a fuskar Khalid, matso da fuskarsa yai ya sumbaci lebanta yace “That’s why nima nake yafemai duk sanda na tuno hakan.”
A tare sukai murmushi sai kuma ta canza fuska, tace “gwara ni dama haka ka ganni dashi kaifa?”
Nifa?
“Eh yarinyar da har gun aiki a manne kuke kai da ita.”
Wa? Ya tambaya yana kallanta, tayi kicin kicin da fuska yace “wai Safiya?”
Oho koma wa sunanta ni bai damenba.
Murmushi yai yace “Karki tsaneta please yanda ta taso ne yasa take ganin duk abinda take so kamar kayan shago ne da zataje ta siya haka take ji, sannan ni ba komai tsakaninmu da ita, ita tana tunanin so na take ni kuma nasan ba sona take ba, duk sanda hankali ya shigeta am sure zata fahimci hakan.”
Dan baki ta tabe tace “naji da alama kamafi saninta akaina.” Ta karasa maganar tana dan harararsa.
Murmushi yai ya kara kankameta tare da lumshe idanunsa.
A hankali tace “maganar dazu? In fita gobe?”
Murmushi yadanyi idanunsa na rufe yace “abu daya sannan please banda mai tsada.”
Shiru tadanyi tana tunani, itakam ya zatai da Khalid?
A hankali bacci ya daukesu.......
************
Kabir ne ya kara kiran number a karo na goma sha biyar, yanzun ma harta katse bata dauka ba, Mumy ce ta shigo dakun kawai ta ja akwati ta fara zuba kayan Afreey a ciki.
Afreey dake kwance ce tadan leko kallan Mumy tai cikin mamaki ta mike zaune da sauri tace “Mumy me kikeyi hakan?”
Tace “Gun yayarki zaki tafi yau”
Da sauri tace “yanzun Paris xan tafi? Ban shirya ba?”
Gashinan ina shirya miki ai, sannan in kinje shekara biyu zakiyi acan.
Ido ta zaro ta mike zaune da sauri tace “me kike nufi Mumy?”
Tace “badai taurin kai kike mana akan wani fakiri ba? Mahaifinki ne ya yanke hukuncin nan sannan nima na amince dashi, nan da awa biyu jirgin ku zai tashi.”
Awa biyu? Ta fada tare da mikewa tsaye da sauri ina zata san ma inda yake? Ga ya canza number.
Ranta ne ya baci ta kalli Mumy tace “mumy ki barni plz bansan zuwa wlh.”
Mumy bata kula taba ta cigaba da hada kaya.
Afreey haka ta shirya dan dole Abbi da kanshi yai shirin yi mata rakiya suka tafi kasar Paris suna tafe tana hawaye har jirgi ya tashi bata daina kiran Khalid ba.
*********
Kayanta ta jawo bayan motarsu ta sauka ta nufi gidansu Kamalu, cikinta sai uban karar yunwa yakeyi.
Haka ta isa gidan sai dai Kamalu yace mata Adam ya fita tun safe.
Ganin yanda iyayen Kamalu ke mata wani kallo yasa ta nemi bashin dari biyu agun Kamalu ta nufi gidan Hajiya bilki.
Kallanta sosai mai gadin ya shiga yin dan ya kasa gasgata idanunsa kan Goggo ce.
Sai datace “Nuhu bude min mana.”
Yace “hajiyar bata nan.”
Tace “ina taje?”
Yace “wlh ban sani ba dazu ta fita.”
Bari na shiga na jirata.
Sai dai ki jirata a harabar gidan dan ba kowa a ciki.
Cikin takaici ta wuce harabar gidan ta zauna, sanyi sai busawa yake sai rakubewa takeyi.
Adam kam cikin farinciki ya isa inda mutumin yace su hadu.
Tunda ya iso yaga sunata aikin gini, cikin mamaki yace “oh aikin fad’ad’a gun aikin nepa din sukeyi?”
Haka ya isa can ciki inda mutumin yake yana zaune suna cin abinci shinkafa da wake da suka siya yanzu.
Kallan Adam yai yace “oh harka iso?”
Ya kalleshi cikin mamaki yace “eh amma me kuke anan?”
Ya tambaya yana kallan yanda suke cin shinkafar tundaga yanayin jikinsu.
Gaddafi ya kalleshi yace “kaci abinci ne?”
A’a Adam yace yana kallanshi.
Alama yamai daya zauna, Adam ya zauna ya kalli plate din da aka turo mai, loma daya yaci yace “a ina zan yi aikin? Naga nan kamar ba aikin kuke ba.”
Dariya Gaddafi yai yace “lokacin cin abinci ne daga mun gama zakaga kowa ya d’au harama.”
Cikin rashin fahimta yake cin abincin, kafin ya gama yaga ragowar sun gama kowa ya mike, gani yai suna ta aiki kowa da abinda yakeyi.
Adam ya kalla yace “kai tunda farkon zuwa ne sannan yace baka taba yi ba ka fara da kwaso kasa.”
Shinkafar daya firzo ne yasa ya kalleshe, kallansa yai yace “kasa?”
Gaddafi ya kalli inda ya farzo shinkafar yace “eh ko kafinsan farawa da hada siminti?”
Baki Adam ya bude yana kallansa yace “aikin gini nazo yi?”
Eh da me ka dauka?
Kallansa Adam yai ya mike da sauri zai tafi, sai dai tunawa dayai kudin da Zainab ma ta bashi a biyan bashi ya kare dakyar ya samu na mota yau, yazaiyi ya koma?
Haka ya nufi gun yashi yana gamawa akasashi hadin siminti, awa biyu jinta ya dingayi kamar wanda ya wuni, jikinsa duk yadau ciwo.
Gun Gaddafi yaje yace kansa na ciwo.
Gaddafi ya duba awa hudu kawai yai yace ga kudinka nayau ya mika mai dubu daya Adam ya kalleshi yace “kullum nai dubu daya zan samu?”
Yace eh, amma kaga Khalid dake aikin mutum biyu dubu biyu yake samu kullum, wani sa’in ma na mutum uku yake.
Baki Adam ya bude shiva Khalid bane bazai kashe kanshi da aiki ba amma dubu daya kullum? Kwana goma dubu goma?
Murmushin jin dadi yai tunda bazai samu waccan ba gwara ya lalaba dama yanata mamaki ace abinda yama Zainab bai dameta ba harta bashi aiki?
Amsa yai ya fito cikin jin dadi.
Har zai hau motar unguwarsu ya canza ya hau ta Naibawa.
Tsayawa yasai lemo da ayaba na dari da hamsin yana tuno Khalid hk yai.
A kofar gidan ya tsaya yana tunani, zata kulashi yau? Yai tambayar jiki a sanyaye sannan yai sallama.
Baba na rubutu da alkalami a alo a waje ya amsa tare da bada izini.
Adam ne ya shigo ya karasa kusa dashi ya tsugunna yana gaisuwa.
Baba wanda tun shigowarshi yake kallansa harya karaso.
Amsawa yai yace “sannu da zuwa.”
Adam yace “yauwa Baba yamai jiki?”
Kallansa yai haryanzu yana jin zafinsa kadan yace “ gun Raziyya kazo?”
Kasa yai dakai yace “Babs ku kara yafemin bansan haukar danai haka ta ruguza rayuwarku ba.”
Kallansa yai yace “Mun yafema dan abinda ya faru yasa na rufe ido na toshe kunena har sai da abokinka ya farkar dani na fahimci lalai nima na tafka babban kuskure, nikaina dana sanin abinda na aikata nakeyi wanda yanzu idan duniya suka gama sani bansan yanda rayuwarta zata kare ba.”
Jikin Adam ne ya sake mutuwa tausayinsu dajin haushin kanshi ya sake kamashi, kwalla ta zubomai yace “kuyi hakuri Baba.”
Murmushi Baba yai ya girgiza kai yana kokarin wanke rubutun yace “duk abinda ya faru laifi nane ina neman Allah ya yfemin, ya bata miji na gari itama.”
Fitowar Raziyya daga bandaki ne yasa ya kalleta, buta ta ajiye ta bugamai wani banzan kallo tana neman wucewa ciki.
Baba ne yace “Raziya dawo nan.”
Dawowa tai inda ya nuna mata fuskarta a daure tamau.
Baba ya mike ya dau rubutun ya nufi dakin mama ya barsu.
Adam ne ya kalleta, cikin dauriya yace “Sa....Au Raziya.”
Bata ko kalleshi ba balle yasa ran zata bashi amsa.
Yacigaba “Raziya ki yafemun dan Allah, nayi kuskure na sani nine silar jifawar rayuwarki haka, amma ki yafemun ba dan halina ba.”
Idanunta ne suka ciko tana kallanshi, a hankali hawaye suka gangaro kan fuskarta.
Daurewa yai yace “kiyi hakuri dan Allah.” Yai maganar cikin rawar murya.
Kallansa tai sannan ta mike, da sauri yace “Raziyya!”
Tsayawa tai batare da ta kalleshi ba, yace “dan Allah kiyi hakuri.”
Daki ta shiga ta rufo kofar yana daga waje yana jin kukanta, sai dai itakam wannan karan kukan tausayin kanta take dan ko yanzu a dole take zaune a gidan nan amma ta riga ta saba da namiji batasan yanda zata kare rayuwarta ba.
Haka ya musu sallama ya fito jiki a sanyaye.
********
Sakonsa data gani ne ya sata sakin murmushi mai sanyi, kallan kayan data amso daga gun Maman Al’amin tai, sannan ta sake karanta sakon.
Baby i miss u.....
Fuska tadan rufe sannan ta kara kallan kayan dake kan kujera wanda ta fita ta siyo yanzu, dan tana dawowa ta tsaya a gidan Maman Al’amin ta amso kayanta.
Murmushi tai sannan ta mike ta shiga dasu daki, budesu ta dingayi tana gwadawa, kunya duk ta rufeta ganin kayan duk kamar kayan ‘yan iskan titi.
Wata riga tasa wacce gaba daya rabin kirjinta a waje yake ga rigar iyakarta gwiwa, da sauri ta hau cirewa tana cewa “ina na isa sa wannan?”
Wayarta ce tai kara ta dauka tare da cewa “Hello Yallabai”
Abubakar yace “Zainab da gaske bazaki dawo ba?”
“eh!” Ta fada kai tsaye, ajiyar zuciya yai yace “na fahimceki shikenan ni kuma zan saida broadcasting station din nan dan dama solution dina kece in har bazaki dawo ba zan sashi a kasuwa.
Cikin sauri tace “ma’aikatan ciki fa?”
Wannan sai su nemi wani aikin dan dama na ba Kabir kwana daya tunda bai samo solution ba yu din nan na koreshi.
Shiru tai kafin tace “wa zaka saidawa?”
Ban sani ba sai wanda yake so naga kuma zai siya yanda nake so.
Shiru tadanyi kafin tace “ka saidamin.”
Fuskarsa dauke da mamaki yace “in saida miki?”
Tace “eh, in har saidawa zakai ka saidamun.”
Shiru yadanyi yace “kizo mu tattauna, kiji ko zaki iya siya.
Okay kasa time ka turon, nan sukai sallama.
Shiru tadanyi, kafin ta kalli kayan, murmushi ta sake, jin fitsari ne yasa ta shiga toilet, tana fitowa ta shiga kitchen tana tafe tana wa kanta dariya tare da cewa “ai baya nan kafin ya dawo na cire.”
Jellof din taliya datai ta zuba ta fito falo tana ci tana duduba abu a laptop dinta, tana gamawa ta cigaba da abinda take ko plate din bata maida ba, jin ta buga mata ba charge yasa tai ajiyar zuciya sannan ta dau plate din zata wuce kitchen.
Karar gate taji, wani murmushi ta saki sam ta manta shigar dake jikinta, dan window ta leka ta sake sakin murmushi tana kallansa har ya kusa bude kofar, kallan kanta tai ido ta zaro sannan tai hanyar daki da sauri, sai dai ko kusa da kofar bata je ba ya bude kofar.
Baki ya saki yana kallanta, idanunsa kuwa ya bude su sosai tun daga kanta yake kallanta, ta tufke gashinta a tsakiyar kai? Sakowa yai rigar kalar ash ce wato kalar ruwan toka, ta zauna dam a jikinta, a hankali ya sauko kasan cinyoyinta dake waje, da alama ma bata jin sanyi.
Wani irin abu ne ya taso mai, a hankali ya fara takowa, jin alamar yana tahowa yasa ta taka kafafunta tai daku da sauri, tana shiga yana turo kofar, kallansa tai ya kalli yanda rigar ta mata ta gaba.
“Wow da alama Baby so kike ki kasheni” ya fada yana dan jingina kansa da jikin kofa.
Kallansa tai sannan ta juya da sauri zata shige toilet, cikin hanzari ya karaso ya kamo kugunta ya jata suka fada kan gado.
Kallansa tai tace “dan Allah barni na cire kayan kunya nake.”
Kunya? Ya tambaya yana kara kallan jikinta yace “ina kunya ana neman zautar dani? An samu hanya?”
Dan idanunta ta juya tace “ni dai karka fassarani, nasan ai basumin kyau ba kamar wata.....” sai kuma tai shiru tana kunyar yanda yake kallanta.
Murmushi yai a hankali yace “i like it, i like it soo much.”
Kunyace ta rufeta ta ja pillow ta rufe fuskarta dashi.
Hannu yasa yana kokarin jan pillow din itama tana kara rikeshi, yana ja ya fizge kallansa tai tace “dagani.”
Um um
Allah nauyi gareka
Dan murginawa kusa da ita yai yace “in nauyi gareni kiyi maza ki koyi yi a sama.”
Baki ta bude da sauri ta dau wani pillow din ta makamai tace “Laaaaa, Allah da alama ba karatu kawai kai a daki ba.”
Dariya yai yace “me nai?”
Tace “Kafi karfina wlh” ta fara kokarin mikewa, riko hannunta yai yace “Baby i miss u.”
Juyowa tai a hankali tana kallanshi, murmushi ya mata, samun kanta tai da kwanciya kusa dashi, hakan yasa suka kwanta a rigingine hannunsu na rike da juna.
Yace “ina kika samo kayan rudani?”
Tace “makota”
“Ahhh lalai na amince da zuwa gunta.”
Murmushi tai tace “I like it.”
Yace “me?”
Tace “inkace you miss me.”
Murmushi yai yadan juyo da fuskarsa yace “in nace I luv you fa?”
Kallansa tai zuciyarta na bugawa da sauri cikin wata murya da ita kanta batasan tana da ita ba tace “i really want to ask you, yaushe ka fara sona?”
Yana kallanta yace “I can’t say, na dai san before ki bar aiki.”
Murmushi tai tace “kenan sanda kaje Abuja ka....” sai kuma tai shiru jin nauyin maganar.
Kai yadan daga mata yace “Umm shiyasa it hurt danaji kina min wani zancen aiki”
Murmushi tai tace “meyasa bakai tunanin me yasa ban nemi kowa ba sai kai?”
Kallanta yai yace “bansan wannan tunanin at that time I feel like zakicemin saboda ni talaka ne.”
Kallansa tai, a hankali ya kai ido kan saman rigarta.
Bakinsa ya sa cikin nata..........
*************
Uwar hamma ta saki sannan tai mika tana kokarin mikewa, kallan Hajiya Bilki dake kanta tai, tace “Bilki kin dawo?”
Hajiya Bilki ta kalleta tace “inalilahi wai da gaske kece? Adama?”
Goggo tai dan yake tace “Bilki nice”
Kallan mamaki ta shiga mata har suka shiga ciki.....
Goggo ta daure tace “Bilki duniya ce ta juya dani nazo dan Allah ko aikatau ki nema min.”
Shiru tai tana kallanta tace “me ya juya haka lokaci daya? Ina sirikarki?”
Shiru tai kafin tace “sun rabu.”
Kuka ta sa mata, Hajiya Bilki tausayinta ya kamata tace “ki kwana anan gobe mayi magana.”
Dadi kamar ya kashe Goggo balle an bata abinci tashi ga falansu ana ta kallo ta rakube a kasa tana yi, har yaran suka kaji suka kwanta tana ta uban kallo, sai da Hajiya Bilki tace su kwanciya ake in dare yayi haka.
Dole ta tafi dan dakin da aka ce ta kwanta, kallan dakin tai tace da Hajiya bilki katan daki take ban amma yau???
Haka ta kwanta.
******
Ayusher🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
*Sweet din Baby na gaisuwa 😉😉*
{67}
Kwanciya sukai bayan sunyi sallar asuba alarm dinsa ne ya buga ya bude idanunsa tare da kashewa, a hankali ya janyeta daga jikinsa, har ya cire kaya zai shiga toilet ya kalleta, hannu yasa ya dan tab'ata cikin bacci ta gyara kwanciyarta.
Kara tabata yai yace "Baby tashi."
Idanunta ta bude a hankali ta budesu da kyar cikin bacci tace "ya akai?"
Yace "breakfast."
Idanunta ta maida ta rufe tace "anjima zanci in na tashi."
Yace "bake ba ni."
Idanunta tasake budewa dakyar tace "baga haka kake tafiya."
Yace "hmm haka nake tafiya amma daga jiya na daina, tashi ki samun wani abun kafin na fito daga wanka."
Bata san sanda ta ware idanunta ba tace "yanzu wai zan sama?"
Kai ya daga alamar eh yace "kidan yi sauri kinsan bama late."
Tana kokarin magana ya shiga toilet, tsananin mamaki ne ya rufeta, wayarta ta jawo ta duba time 6:20am? Haka ta mike kamar zatai kuka tai kitchen, tama rasa me ake ci da sassafen Allah, sannan me zatamai kafin ya fito daga wanka? Kwai ta soya ta dafa ruwan tea ta dauko bread ta fito dashi falo, murmushi tai tana tuno yanda Aunty ke tsananin san tea da bread da kwai ashe yau zai mata rana.
Tana ajiye cup yana fitowa, kallansa tai hamma ce ta zo mata dan bacci takeji sosai, zama yai ta kalleshi, tea din ya hada ya fara sha, kallanta yai yace "kije ki kwanta."
Mikewa tai zata wuce, hannu yasa ya riko hannunta ta koma ta zauna.
Kallanta yai sannan ya nuna mata kuncinsa, murmushi tai sannan tace "bayan an hanani bacci?"
Yace "yanzu aka fara hanaki, dan kullum a gida zan dinga break."
Kallansa tai cikin mamaki tace "a gida?"
Kuncinsa ya kara nuna mata yace "Sweet na jira."
Sumbatarsa tai ya saketa ya cigaba dacin abincinsa, mikewa tai ta wuce ciki ta kwanta, sai dai duk yanda taso tai bacci ta kasa sai juye take, jiya har sha biyu basuyi bacci ba dan bayan sun kwanta hira sukai cikin nishadi da kauna sukai bacci, yau me ya faru haka?
Daki ya shigo ya dau agoggonsa tana kwance tana kallansa, kallanta yai ya sakar mata murmushi sannan ya matso kusa da ita ya sumbaceta a hankali yace "See u baby"
Samun kanta tai da mai murmushi itama, fitowa yai shiru tai a daki a hankali ta sauko ta bude waje ta tsaya a baranda tana jin yanda sanyi ke busawa, hanzu a haka ya fita da kafa?
Shiru tai tana kallan motarta, juyawa tai ciki.
*********
Goggo cikin jin dadi take cin soyayyen dankali da kwai, loma takeyi kai kace bata taba ci ba.
Hajiya Bilki ce ta turo kofar dakin, Goggo tai saurin zuba na hannunta cikin plate din ganin yanda ta cika hannu, kallanta tai tace "Bilki!"
Hajiya Bilki ta na tsaye a jikin kofa ta kalleta tace "inkin gama cin abincin kizo ki tafi."
Kallan ta tai da sauri tace "in tafi ina?"
Murmushi Hajiya Bilki tai tace "ina na sani? Ina fada miki ne bana bukatar mai aiki balle kuma ke dana san hallinki"
Hankalin Goggo ya tashi tace "Bilki na canza yanzu sam ba haka nake ba, ba ruwana wlh ba zan kushe komai ba zan kuma kular miki......"
Katseta tai da cewa "Ko kin canza ko baki canzs ba maganar dai guda daya ce kiyi hakuri ki nemi wani gun."
Goggo ta kalleta tace "yanzu Bilki ina neman alfarma gunki duk yanda muke amma ki kasa min?"
Kallanta tai a kule tace "yanda muke? A yaya muke? Ke da kika sa dana ya fada soyayyar Nabila kikace zaki hadasu aure, yaran nan ya kamu da santa amma dame kika sakamin? Ko cewa nai zaije sai ki fara kame kame, ko duk daga baya kina tunanin ban fahimceki bane?"
Goggo ta kalleta tace "kindai san banda iko akanta ko kin manta kanwar Zainab ce?"
Haushi ya kama Bilki tace "kinsan haka kika kawo mai hotonta?"
Sum sum tai dakai Bilki tace "ni wannan ma abarshi ya wuce ga wannan, ta ajiye mata dubu biyu tace "kiyi na mota, sannan in har baki kara dawowa gidan nan ba zanfi kowa farin ciki xan kuma fahimci kin san darajar kanki."
Ta juya ta fita.
Baki Goggo ta bude tana kallan ikon Allah, wannan dankalin kasa karasa ci tai, ta dau kayanta dake leda ta dau dubu biyun ta fito, tana tambayar 'yarta ma inda Bilkin take suyi sallama amma sam taki ko kulata.
Haka ta fita gaba daya ranta ba dadi, ta koma gidansu Kamalu tana fatan samun Adam.
********
Adam ne ya shirya ai dole ya koma gun aikin nan, dan yama Khalid text ma bai ko mai reply ba, kenan bashida wani zabi.
Ya fito tana tace yana hamma sai jerota yakeyi dan ya saba baccin safe yau kuwa gashi karfe tara wai zai fita.
Yana shawo kwana Goggo na saukowa daga cikin adaidaita, kamar da wasa ya kara kallanta.
Kallansa tai cikin jin dadi tace "Adam!"
Kallanta yai ya karaso yace "Goggo? Me kike anan?"
Kallansa tai tace "da Kamalu baicema nazo ba?"
Kinzo me?
Ya tambaya yana kallan kayanta a leda.
Tace “Adam na gaji da zama a kauye wlh, ga bani da waya gaba daya komai ya tsaya min cak.”
A kufule yace “kina gani nima a dosane nake ina kike so na saki?”
Tace “bazamu rasa na Allah ba.”
Kallanta yai yace “wlh komawa zakiyi yanzu.”
Ina zan koma?
Kauyen kije can ki lalaba kafin Allah ya sa nadan tara, kinsan yanzu aikin da nakeyi ne? Gini fa nakeyi? Duk yanda nake tunda kikaga na dage kema ai sai kiyi hakuri da yanda Allah yai dake.”
Kallansa tai ranta a matukar bace, yace “Allah Goggo komawa zakiyi yanzu.”
Fuskarta ta hade tace “na maka rana dole kamin dare, duk inda nake kai kadai nake tunanin halin da kake amma abinda zaka cemin kenan?”
Yace “Goggo dan Allah ki barni da abinda ke damuwa, idan na tuno abinda nama mutanen can ji nake gaba daya na tsani kaina, ki barni da wannan bazan kuma kara da rokon karaki a gidan mutane ba.”
Lalai Adam ni kake fadawa haka? Akainane bazakai roko ba? Sanda na haifeka tsabar san da na dorama tun kana ciki yasa mahaifinka ya tsokaneni ya sama Adam wai ni Adama kai Adamu, mutane akanka kasan irin zagin dana sha? Na saida duk abubuwa na saboda kai amma haka zaka cemin?
Ransa a matukar bace yace “me na miki? Dan nace kawai Goggo ki koma ki kira ma zauna da kafata? Ke ba abin alfahari bane kiga ina aiki?”
Ido ta zubamai ranta a matukar bace adaidaita ya tara suka shiga, ranta duk a bace, shiru sukai har suka je tasha kallanta yai yace “kiyi hakuri Goggo zanzo da zaran na samu dan kudi.”
Kallansa tai tace “ka aikon da waya.”
Yace “zan aiko da zaran na hada kudi.”
Haka ya shiga mota ranta duk ba dadi, me zata ce ma yan gidan?
Sai da suka tafi sannan ya juya ya tafi gun ginin, kallan gun yai shikam wlh baisan aikin nan amma ya zaiyi? Yanzu Kamalu ma ba magana yake mai sosai ba ya kuma tabbatar ya gaji da zamanshi ne, dole ya shiga ciki.
*******
Har ya iso gate din gidan yana waya da Dady kafin suyi sallama ya kashe wayar.
Zainab wacce ke kwance akan gado rike da wayarta gefe kuna takarda da biro ne tana duba abu a wayarta tana rubutawa a takardar, sam bataji alamar shigowarsa ba, lokaci ta kalla a wayarta taga har shida saura.
Mikewa tai ta fito falo dan shan ruwa, zaune ta ganshi ya jingina kansa da kujera idanunsa a rufe.
Kallansa tai cikin mamaki, sannan ta tako har inda yake, kallansa samun kanta tai da kasa dauke ido daga kansa, idanunsa a rufe yace “Baby in kin gama kallan nawa zan bude ido.”
Kanta ta dauke ds sauri tana cewa “yaushe ka shigo?”
Idanunsa yadan bude sannsn yasa hannu ya jawota ta dan zaune a karkace akan cinyarsa.
Kansa ya kwantar akan kafadarta yace “jira nake ki fito.”
Kallansa tai tace “in ban fito bafa?”
“Nasan zaki fito ma tunda Sweet dinki bai dawo ba, ina kika ga nutsuwa?”
Wani murmushi tai tace “taya akai kasan banda ita?”
Dagowa yai ya kalleta yace “I know it, you don’t have to tell me.”
Wai why are you so confidence?
Kansa ya maida yace “me zai sa na jira sai kin fadi abinda na sani?”
Murmushi tai, kin samu cinya kin ki tashi, gashi ni kuma ina san mikewa.
Kallan mamaki tamai tace “waye ya sani akan cinyar?”
Nine sannan yanzu kuma nace a dagani.
Mikewa tai rai a bace, ta daure fuska tamau, kallanta yai bayan ya mike yace “bari nadan watsa ruwa muyi sallah sai muci abinci”
Kai ta daga kawai fuskarta haryanzu a tsuke, baiko bi takanta ba ya wuce yana murmushi shi kadai.
Haushi ya isheta, kallan atamfar data sa tai tace ko in sa kananan kaya? In kuma nasa ai sai yafi fadam abinda yaso tunda ba dashi ya ganni ba.
Zama tai a bakin kujera, meya sameshi?
Kofar daki aka bude, ya leko kai yace “Baby ina towel dina?”
Dan kallansa tai tace “yana inda ka ajiye.”
Zo ki daukomin.
Banfa dauka.......
Maida kofar yai ya rufe, a kufule ta mike, tana shiga taga towel daure a jikinsa.
Kallansa tai tace “Sweet kace baka ganshi ba?”
Murmushi ya sakar mata yace “so nake kawai naga kinzo.”
Kallansa tai tace “fadamin gaskiya so kake kaga raina ya baci ko?”
Bingo ya akai kika sani?
Baki ta bude tace “dalili?”tai tambayar cikin mamaki.
Sirri nane ni kadai but i like it.
U like it?
Bai bata amsa ba ya shiga toilet yana kokarin rufewa yace “ko za’a tayani wankan?”
Juyawa tai ta fita daga dakin tana ajiyar zuciya, wai meke kan Khalid? Sam baya kunyar fadar abu? Ta dauka shine zai dinga ma jin kunyarta amma yanzu taga alama ita ma ke jin kunyarsa.
*******
Abincin data ajiye mai ya kalla sannan ya zauna ya kalleta, saukowa tai ta zubamai, ta samai spoon kallanta yai ta kalleshi mamaki ne ya kamata dataga fuskarsa a daure gam.
Mikewa tai ta zauna tana kallan ikon Allah, harya gama cin abincin be ce mata komai ba, ruwa yasha yace “kwashe kwanukan.”
Kwashewa tai gaba daya mamaki ya rufeta, tana dawowa taga ya bar falan.
Daki ta nufa, ganin baya nan ta tsaya a jikin dakin, jin karan gen ne yasa tasan yana waje.
Yana shigowa ya xauna akan kujera baiko kalli inda take ba, gaba daya hankalinta ya tashi, kallansa tai a hankali ta dan zauna daga gefensa tace “menene?”
Kallanta yai yanayin sa gaba daya ta kasa fahimta, tace “menene?”
Next time in abu ya shafeki ya kuma shafeni ina san jinshi daga bakinki.
Kallan mamaki tamai tace “wani abin nai?”
Murmushi yai.
Kallansa tai ta riko hannunsa tace “Kanasan hankalin Baby ya tashi?”
Kallanta yai sannan ya kalli hannunsa data rike murmushi yai yace “Meyasa baki fadan kina tunanin siyan gidan Tv dincan ba?”
Kallansa tai kana ganin yanayin da fuskarta ta bayyanar zakasan dana sani ne tace “Allah I thought na fadama, sannan abin bai tabbata ba.”
Duk abinda ya shafeki ya kuma shafeni ina san ko ban xama na farko ba ya zama na sani daga bakinki, ni bai zama dole sai na fada miki komai ba but i want you to tell me, zaki iya kiranshi selfishness........
Rungume shi tai wanda hakan yasashi yin shiru, am sorry nayi laifi, amma dan sankai sai kace na fadama kai kuma ba komai ba.
Murmushi yai yace “eh am a man akwai abinda dole ni kadai zan iya rikeshi.”
Dagowa tai tana kallansa tace “selfishness”
Yace “eh dana bakiji nace ki kirashi da hakan ba?”
Dan harararsa tai tace “haushi kaji maganar kajita daga gun Dady?”
Yace “a’a matsayina da yardar da kikamin nake san na duba.”
Murmhshi tai tace “Allah bansan yanda zanyi dakai ba.”
Ta fada tana dan matsawa, kara jawota yai yace “akwai matsala kenan”
Tame? Ta tambaya tana dan yin baya a kan kujera ganin yanda yake kwantowa.
Sai da suka karasa jikin kujera sannan ya nufi fuskarta kamar mai shirin sumbata dan harta rufe idanunta sai jitai yace “saboda ke kadaice a yanzu kike da yanda zakiyi dani.”
Ido ta bude ta kalleshi, murmushi yai yace “yau ke nakeso kiyi.”
Ya fada yana dan motsa bakinsa, kallansa tai tace ka danne ni.
Baki gane yaran ba kenan?
Dan sumbatar lebansa tai tace “gashinan nayi.”
Kallanta yai dan yanda ya kankance ido yana kallanta har ya bata kunya tace “menene kuma?”
Yace “ina tunanin yanda zanyi dake ne.”
Dariya tai tace “yanda zakai dani?”
Yace “eh”
Mikewa yai ya zauna yace “Dady yace cikin weekend din nan zaizo, zakuje gun Abubakar din.”
Zamuje dai bazaka rakani ba?
Eh ya fada kai tsaye.
Tace “ba ko yar kara?”
Yace “so kike nace eh?”
Dan fuska ta kauda, murmushi yai yace “am sorry amma no.” Ya karasa maganar da murmushi.
Shiru tai jin kansa tai akan kafadarta ya kwanta sannan ya jasu suka jingina da kujerar, ya sa hannunsa ya zagayo da ita ta cikinta.
Idanu ta lumshe a hankali.
*******
Ayusher🏌🏻♀
********
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
{68}
Alhamdulila Dady ya zo an sai broadcasting station, sunje danbatta Khalid ya kai Abba asibiti dan kwana ma sukai a can sai washegari suka dawo, ba karamin dadi Khalid yaji ba dayaji Salmanu yacemai yar gida yake san ayi, sai dai Khalid yace mai tunda tana shirin fara exams na waec da neco ya bari sai ta gama.
Sun dawo kano cikin kewa da jiran lokacin hutu dan Asiya tazo dan itama tasan su Nabila zasuzo.
*******
Yau wata biyu da sati biyu da aure, sati uku kenan da fara aikinta.
Khalid ne ya fito daga wanka harya gama shiryawa bata shigo dakin ba, sanye yake cikin suit wanda a koda yaushe inya saka kyansa da kyan zatinsa ke kara fitowa agoggonsa ya daura a ahannunsa sannan ya dau jakarsa ta aiki da wayarsa ya fito daga dakin.
Abincinsa ya gani a falo hakan yasa kawai ya zauna ya bude, soyayyiyar indomie ce, kadan yaci dan tun daren jiya yake jin cikinsa a cunkushe.
Daga waje yaji tada mota hakan yasa yasan tana waje, tea ya hada yadan kurba, yana sha yana kallan gidan mikewa yai ya dau plates da cup din ya wuce kitchen, kallan kitchen din yai ga kwanukan datai amfani dasu nan a sink, ajiyewa yai kawai ya fito.
Tana gani ya fito ta fito daga cikin motarta tace “Sweet kai nake ta jira sauri nake yi.”
Ko kallanta baiyi ba yacigaba da sa takalminsa, da sauri ta tuno hakan yasa tace “Oh ina kwana?”
Ta fada tana tahowa inda yake.
Bai kalleta ba sai dai ya amsa gaisuwarta.
Hannunsa tadan riko tace “muje?”
Kallanta yai yace “ina?”
“Gun aiki na akiyeka na wuce”
Dan kallanta yai yace “no ki wuce.”
Tace “dan Allah Sweet ka daina min haka kazo mu wuce tare plz”
Hannunsa ya dan zare yace “sai na dawo.”
Ya fito daga gidan bayan ya bude mata gate, bin bayansa da kallo tai sannan tai ajiyar zuciya agoggo ta kalla sannan ta juya cikin sauri ta shiga mota, tana kallansa yana tafiyarsa, haka ta wuceshi ta tafi gun aikinta.
Gaba daya komai ya cabe mata dan tana aikatuwa saboda komai na gun ya durkushe sai faman saita komai takeyi, meeting ta wuce direct ranta a matukar bace take magana, tana gamawa ta fito ta wuce office dinta, tea dinta tasha sannan ta fito tana duduba abinda akeyi.
Sai data tabbatar komai na tafiya yanda takeso sannan ta koma office dinta ta cigaba da aikinta.
Secretary dinta ce ta shigo tace “Hajiya ta gama yin aikin.”
Kallanta tai tace “tabi duk wanda zai dauko rahoto yanzu ta taimaka musu da aikin rike kaya.”
Kallanta tai cikin mamaki ganin yanda kullum Ramlatu a wahala take karewa, Zainab tace “menene? Kice in bazata iya ba tabar aikin.”
Haka ta juya ta sanar mata, Ramlatu tace “to” sannan ta juya.
Kanta tadan dafa dake mata ciwo sannan ta kalli wayarta, kan sunan Sweet ta bude ta zubawa sunan ido ajiyar zuciya tai sannan ta kifa wayar ga cigaba da aikinta.
Sai yamma lis sannan ya dawo, yauma ya rigata dawowa, yanda ya tafi dama haka ya dawo yaga gidan, yana tunanin raban da gidan nan yaga shara yakai sati biyu, kitchen ya shiga shiru yai, tunanin gyarawa dakansa yai sai kuma yai tunanin daga sanda ya fara ya tabbatar bazata sake yi da kanta ba.
Juyawa yai ya shiga toilet yai wanka, akan gado ya dan mike yana waya da Salmanu.
Suna sallama yaji shigowar motarta, kayanta ta kwaso ta shigo ciki, ajiyewa tai a falo sannan ta shiga daki, yana zaune yana dane dane a waya kallansa tai tace “Sweet ka dawo?”
Eh kawai yace ba tare da ya kalleta ba, kallansa tai sannan ta matso ta zauna dan kusa dashi tace “sai yaushe zaka dinga kallona in ina ma magana?”
Kallanta yai yace “dan matsa zan wuce masallaci.”
Jiki a sanyaye ta mike ya sauko ya fito ya wuce masallaci.
Kanta tadan shafa sannan ta shiga toilet, wanka tai sannan ta sa kayan bacci sai datai sallah sannan ta fito falo, gen aka tada dayake ya canzo musu gen karshen watan daya wuce.
Zama tai ta jawo takardun ta tana dudubawa, Khalid ne ya shigo baiko kalli inda take ba yai hanyar daki.
“Sweet abinci fa?”
Sai nayi isha’i yace kawai ya wuce ciki.
Shiru tai ganin ta kasa maida hankalinta kan abinda takeyi hannunta tasa a gefen kanta tana dan murzawa tana cigaba da abinda takeyi.
Har ya fito zai fita masallaci sallar isha’i tana nan yanda ya barta tana ta hidima.
Kallo daya yama inda take ya wuce, sai dayaje kofa ta lura ya fito da kallo ta bishi ganin ya wuce bai ko bita kanta ba.
Idanu ta rufe sati daya kenan da canzawar Khalid sam yanzu ko magana baya bari suke mai tsawo, ita kuma ga abubuwa sun cude mata bata san ya zatai ba.
Tana nan tana tunani harya dawo, mikewa tai tana kallansa, zama yai akan kujera a falan ta wuce kitchen ta kawo mai abinci sannan ta zubamai, zama tai kusa da inda ta ajiye abincin tace “ko na baka?”
Kallanta yai yace “kina da time din?”
Kallan takardunta tai tace “oh am sry.”
Mikamai tai ya kalleta jiyai wani abu ya tsayamai a wuya, ruwa ya kurba sannan ya dan ci abincin kadan dan haryanzu cikinsa bai ware ba, mikewa yai ya maidashi kitchen ya kara kallan kitchen din kawai ya wuce daki.
Tana nan a zaune dai sai 11 ma tai sallah, ta danci abinci sannan ta kara komawa ta zauna sai karfe 1 ta kashe komai ta shiga daki.
Khalid ta kalla dake kwance yana bacci, kusa dashi taje ta sa hannu ta ratsin cikinsa ta keantar da kanta kusa da kanshi, tabashin datai ne yasa ya dan farka.
Sha’awa ke cinta kwanan nan dan harmamakin kanta takeyi duk sanda zata kwanta sai taji Khalid take bukata, shiru tai tana tunanin yanda da ya nuna mata kulawa, a haka har bacci ya dauketa.
juyowa yai tare da dan haskata, bacci take hankalinta a kwance.
Ido ya zuba maga kafin ya juya ya koma baccinsa.
Karfe biyar da rabi ta farka, ganin baya dakin ba kuma ya toilet yasa ta fito falo da sauri, zaune ta ganshi akan sallaya yana karatun alqur’ani.
Ruwan shinkafa ta saka sannan ta dawo falo inda yake, kusa dashi ta zauna ta dan sa kanta akan kafadarsa.
Ganin ya rufe qur’anin yasa tace “Sweet me kake tunani yau in muka dawo mu taho tare muyi siyayyar abinda babu a gida?”
No kimin list zan taho dashi in na dawo.
Kallansa tai tace “wai haka zamu cigaba da zama?l
Yanayin muryarta ne ya canza cikin rauni ta cigaba da ba haka kake ba meyasa lokaci daya kake neman canzamin? Bayan kasaba min da kai?in nama wani abin ka fadamin please amma ka daina nisanta kanka dani.
Kallanta yai kallan dayasa tasha jinin jikinta, yace “ni haryanzu Zainab yarinyace yar shekara 10?”
Kallansa tai tace “Sweet”
Idanunsa yadan runtse yace “i just don’t know what to do next, na gaji da miki uzuri na kuma gaji da nuna kamar raina bai baci ba.”
Cikin shakka tace “me nai?”
Yace “haryanzu tambaya kike?”
Tace “in ban tambaya ba ta ina zan sani? Gaba daya kasa na rasa yanda xanyi bansan menama ba amma duk ka canzamin.”
Kallanta yai yace “indai wacce ke gabana yar shekara 10 ce zan dane komai na sanar da ita.”
Kallansa tai bakinta na rawa tace “Ka san bansan......”
Katseta yai cikin zafi yace “can you please stop saying that? Komai kice baki sani ba? A koda yaushe ina miki uzurin rashin sanin abu sai yaushe ne zakisan abinda ya dace dake? Naji laifinane danai tunanin san da kikemin zai canzaki, sai dai da alama san da kikemin bai kai rabin wanda kike ma aikinki ba, nabaki dama kiyi yanda kikeso harzuwa sanda limit dina na hakuri dake zai kare daga lokacin kuma....”
Hannu tasa ta rufe mai baki, tana kallan kwayar idanunsa hawaye na zubowa kuncinta.
Idanu ya runtse, ganin yanda hawaye ke zubo mata, ganin ya kasa jurewa ne yasa hannu ya jawota jikinsa.
Cikin kuka tace “Am sorry, na sani tunda na koma aiki na kasa baka mahimmanci kamar da amma Allah komai nakeyi kana raina abubuwan ne sun.......”
Muryarta ce ta sarke saboda kukan dake neman kwace mata, bayanta kawai yake shafawa dan ba shikadai ne matsalar da suke fuskanta ba.
Dagota yai yana share mata hawayenta, hannunsa dake kan fuskarta ta rike tace “am sorry.”
Kallanta yai yace “ban hanaki aikinki ba but at least respect your marriage, na sani naso kaina in nace ina san ki bani full attention dinki sai dai in kina cikin gida i need your attention, bakisan meke going dani ba, bakisan a ya na dawo ba, bakisan wani hali nake ciki ba, kawai aikin da kikeyi shine abinda ke gabanki, wani irin so ne da zama da muke?”
Wasu hawayen ne suka digo saman hannunsa tace “kayi hakuri na daina, nima please ka daina janye jikinka daga gareni.”
Shiru yai yana kallanta, ba ruwa kika sa ba?
Da sauri ta mike ta shiga kitchen, kusa dashi ta dawo tana murmushi tace “kasan yaushe raban dana taho naga idanka akaina?”
Ko ban kalleki ta ido ba ina ganinki.
Kusa dashi ta zauna ta kamo hannunsa tace “Please ka dawo Sweet din dana sani.”
Yaushe raban da a share gidan nan?
Kallansa tai tare da dan sauke ido kasa tana kallan falan, duk da ba datti yai sosai ba amma kana gani kasan an dade bai ga kulawa ba.
kitchen fa?
Kallansa tai cikin jin kunya tace “Na na....” sai kuma tai shiru, yace “toilet fa?”
Sweet abubuwa sun min yawa wlh.
Kallanta yai yace “kina tunanin akanki mata suka fara aiki? In har bazaki iya ba zan taimaka na samo mai min.”
Mai aiki zaka samo mana?
Tai maganar kai tsaye, yace “a’a wace zata kula dani nake nema.”
Wani mugun kallo tamai tace “mata kake nufi?”
Yace “eh tunda kin auri aikinki ni zan auri mai kula.........”
Katseshi tai tace “naji ai ba cewa nai banda hannun yi ba.”
Oh I thought hannunki na aiki ne kawai.
Kallansa tai tace “da can da nakeyi fa?”
Da can yaushe?
Tadan kauda kai tace “kafin na fara aiki.”
Mikewa yai yana neman shiga daki, mikewa tai ta bishi ta rungumeshi ta baya.
Tsayawa yai yana jin abu na tsirgamai, tace “Ko sunana baka kira ba.”cikin sanyi tai maganar
Dan murmushi yai sannan ya juyo da ita murmushi yai yana kallanta, dan ido ta juya kadan sannan ta dago dakanta ta sumbaci bakinsa.
Kallansa tai tace “I miss you.”
Murmushi ya sake tana neman sakeshi ya sa hannu ya rikota, yace “haka ake missing?”
Kallansa tai tace “eh mana.”
Jeki rage gas kizo na fada miki wani abu.
Sakeshi tai ta shiga cikin kitchen, kallan kitchen din tai me takeyi tabar kitchen din ta haka? Ita da batasan kazanta?
Dole Khalid ransa ya baci, zuma ta dauko tadan diga kadan a auduga sannan ta riga almiskh ta dan yi matsi dashi na dan minti biyu sannan ta cire ta fito.
Yana zaune a kujera ta dawo, hannu ya mika mata ta karaso ya jawota jikinsa, kallansa tai tana murmushi, yace “kafin mu fita aiki mu dinga gyara ko ina? Zan tayaki da gyara gado.”
Zama tai akan cinyarsa tace “am sorry bansan me nakeyi har abin yakai haka ba, sannan gyaran gado ai ba aiki bane.”
To ko bakyaso?
Cikin dan shagwaba tace “ina so, amma Allah karka sakemin zancen wata mai taimako.”
In har kema kin ajiye aiki a office kin ba mijinki kulawa a gida.
Dan kwanciya tai akan jikinsa dagota yai yakai bakinshi cikin nata, yau kam anji jiki dan an dade ba’a gamu ba abin ba’a cewa komai.
Saboda lokacin aiki ya kusa tare sukai wanka tana fitowa ta wuce kitchen ta fara gyarawa, tana fitowa taga ya gyara daki, kallansa tai harya shirya, tace “thanks.”
Murmushi yai sannan yace “Thank god mun shirya abin bai zo ba.”
Kallansa tai sannan a ranta tace oh ya haka? Ya kamata yazo tun last week.
Kallanta yai tana sa kaya yace “menene?”
Kai ta girgiza tace “bakomai.”
Fitowa sukai tare suka sha tea da bread da butter, suka fito.
Sai dadi takeji kana ganin fuskarsu zakasan suna cikin farin ciki tun balle Zainab fuskarta wasai sai murmushi take.
Kallansa tai tace “please!”
Yace “no kije plz karki late.”
Ka manta nice shugaba inada damar yin late please mu tafi tare.
Murmushi yai ya matso kusa da kunnenta yace “bakyasan rabuwa dani?”
Murmushi tai tace “yanzun ma baza’a barni na fada ba?”
Haryanzu kansa na kusa da kunnenta yace “dazu an nunamin anyi missing dina sosai.”
Dadinta nima nasan anyi.
Kallanta yai yace “inyeee”
Tace “me? Kana mamaki? Ai naga alama nima daina shiru ya kamata nai”
A tare sukai murmushi ta ja hannunshi jikin mota ta sake cewa “please.” Tai maganar cikin jan ra’ayi.
Haka suka shiga a tare dadi ya kamata suka fito.
**********
Sai yaushe zaka daina zuwa?
Kallanta yai yace “ungo.”
Ya mika mata leda, kallan ledar tai tace “menene?”
Kara mika mata yai, amsa tai ta bude, magungunan da Mama ke sha ne a ciki.
Kallansa tai tace “na meye?”
Yace “shekaranjiya naji Baba na cewa zai siyo, ki bashi wannan.”
Dan harararsa tai tace “waya saka?”
Murmushi yadanyi yace “shima laifi ne?”
Juyawa tai zata wuce.
Yace “Raziyya!”
Tsayawa tai a inda take sannan tadan juyo kadan, yace “dan Allah ki yafemin, yau zuwana na 12 kenan.”
Kallansa tai tace “na dauka a zuwanka na 5 na cema na yafema.”
Yace “naji wannan amma nasan baikai zuciya ba.”
Kallansa tai batace komai ba, murmushi yake yai yace “shikenan.”
Dan maganin dake leda ta daga tace “angode.”
Ta wuce, murmushi ya saki yabita da kallo harta shiga cikin gida.
Yana tafe a hanya mazan dake gabanshi yana ji suna gulmar Su Raziya, jikinshi ne ya sake yin sanyi dayaji dayan yace “ah dama ta ina namiji zai gama amfani da mace yace zai aureta?”
Dariya dayan yai yace “gatanan a jibge a gidan duk wadanda suka dana ba wanda ya kawo tayi.”
Ransa ne ya kara baci haka ya wucesu ya wuce gun aikinsa.
Babban shagon da yake zaman jira ya shiga, yana aiki yana tunani, murmushi yai ganin sakon Khalid dayace “In ka gama dawowa hankalinka ka min magana na fada mata.”
Reply yamai yace “Hankalin nawa bace wa yai?”
“Oh na dauka haka kacemin.”
“Haka kace?” Ya tura yana dariya yai sannan ya cigaba da aikinsa.
Sai shida ya taso a hanya ya tsaya yasai bread da kayan tea dan sachet sannan ya wuce gida.
Dan karamin dakin daya kama.
**********
Tana zaune a cikin dan kitchen din tana ta murza gyada, sai uban gumi takeyi tana yin mai.
Kafadarta ce ta shiga amsawa, ta saki wata uwar hamma sannan ta dan gutsiri gwaibar dake gefenta.
Hanne ce ta kalleta ta dan tabe baki dan tana kishin yanda Adam ya turo mata kudi ta fara sana’ar man gyadar nan.
Goggo ce ta gama ta fito tana mika, jaraba ta fada tare da daukan wayar.
Kin gama?
Na gama, wai Adam haka zaka sani a gaba kullum sai kaji abinda nai?
Kudina na baki kike aiki dashi ko kinsan wahalar danasha kafin na samesu?
Daukan hotunan na yau na gani.
Wata uban kwafa tai sannan ta dau hoton tace “in Umaru yazo ya turama.”
Yace “eh zan fadamai.”
Cikin takaici ta kashe wayarta, kwafa ta sakeyi gaba daya ta kasa gane kan Adam dan har tunani take Adam dinta ne wai?
Nace duba dai🤪
*****
Ayusher🏌🏻♀
*****
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
“It is not a lack of love, but a lack of friendship that makes unhappy marriages.”
{69}
Bayan Kwana biyu....
Lokacin lunch time dinsu ne yai, Khalid ya zaro wayarsa dake cikin dan safe din desk dinsa, murmushi yai akan sunan Zainab wanda a jikin alan wayar aka rubuta Babylove, wani sansanyan murmushi ya sake bayan wayar ta fara ringing, ganin harta katse bata dauka ba yasa ya ajiye wayar.
Sako ne ya shigo wayarsa, dauka yai ganin Nazifi ne yasa ya bude.
“Khalid in da hali zaka iya zuwa plx?”
Hankalinsa ne ya tashi dan ya tabbatar abin ya shafi Zainab, fitowa yai ya hau adaidaita sai dai gani yake kamar bata gudu saboda hankalinsa dake tashe.
Yana isa Station din nasu ya kira Nazifi, da sauri Nazifi ya fito ya sameshi, Khalid cikin tashin hankalin daya kasa boyuwa yace “Nazifi ya akai?”
Nazifi yace “in ba damuwa ko zaka shiga ciki?”
Me ya faru da ita?
Nazifi ya kalleshi yace “ita da directors da producers ne, ta sasu a meeting room tun safe ta koma office dinta ta zauna”
What?
Nazifi yadan girgiza kai kadan yace bansan me ya faru ba.
Cikin hanzari Khalid ya shiga ciki, office dinta ya wuce direct tana zaune tana ta aikinta sanye take da glass saboda yawan kallan screen yasa take sawa.
Secretary dinta na kokarin sanar da zuwansa Nazifi ya girgiza mata kai, Khalid na shiga ta kalleshi tace “waye?”
Yace oganta.
Oganta? Sai kuma tai dariya tace “ohhh na gane.”
Zainab ta dago zatai magana jin shiru bayan kuma an shigo.
Ganin Khalid yasa cikin mamaki ta zare glass dinta, murmushi ya sakar mata sannan ya nufi inda take.
Mikewa tai tace “Sweet me kake a.....”
Rungumetan dayai ne ya sata yin shiru a hankali ta dago tana kallansa, fuskarta yadan taba yace “ya isa haka nan, okay?”
Tace “me?”
“Na sani haryanzu kina jin haushinsu saboda abinda ya faru da ne, kin nuna musu matsayinki ya isa haka nan”
Kallansa tai tace “Allah saboda kai ne ban koresh ba duk ba abinda suka sani sai zaman kashe wando da gulma”
Yace “i know amma in kin duba manya ne su sannan sunada iyalai, zaki iya korarsu amma a hankali sannan ki sanarda kowa 2years before saboda ya shirya.”
Fuska tadan hade tana kallansa tace “dan Allah ka dawo nan da aiki, canfa wahala kawai kake sha.”
Harararta yai yace “me suke a meeting room din?”
Tadan kauda kai tace “punishment na basu na aiki, dan nasan ko zasu kwana acan bazasu iya samo mafitarba.”
Ohhhhh ya fada yana hada goshinsu.
Murmushi tai tace “naji zan ce su barshi.”
Ummmm thanks.
Saketa yai yace “zan koma.”
Dan rikeshi tai tana dai jujuya kai, murmushi yai sannan ya sumbaceta ya juya ya fita.
Nazifi ta kira ta bashi izinin su barshi sannan tacemai ya shirya tana so ya rakata yin signing din contract da zasuyi da masu company na detergent.
Nan ya juya cikin jin dadi.
Tare suka fito driver dinta na gun aiki ne ya shiga motar Nazifi ya zauna a gaba ita kuma ta zauna a baya tana tambayarsa abu yana bata amsa har suka isa.
C.E.O din na jin isowarta ya kalli magidancin dake durkushe gabanshi yace “tashi ka fita dan Allah, bana san in samu matsala ta harkar business dina.”
Kabir ne ya kalleshi yace “ka taimaka ka fadawa abokinka ya dauken aiki a gidan Tv dinsa, inada experience sosai akan harkar.”
Zainab ganin haryanzu ba’a basu izini ba yasa ta watsama secretary dinsa kallo, nan ta juya ta kara shiga, daidai nan Kabir ya mike saboda jin yacemai ya tashi ya fita kafin yasa a koreshi.
Haka ya fito jiki a sanyaye, idanu suka hada, kallansa ta sakeyi sosai, tadan shafi saman kanta tana kara kallansa.
Da kyar yace “Zainab?”
Wani kallo tamai sannan ta mike ba tare da ta kulashi ba ta nufi hanyar ciki.
Bakinsa na rawa yace “Zainab?”
Kofar ta bude, CEO din ya taso da sauri yace “Hajiya barka da zuwa.”
Kallansu yai da sauri, Zainab ta kalleshi tana murmushi tace “Yallabai barka.”
Kabir na tsaye kamar hoto aka rufe kofar, kasa ko daga kafarsa yai sai da secretary din yace “in baka fita ba zan kira security.
Kabir haka yaja kafarsa dakyar yabar gun.
*******
Karfe Biyar da rabi Khalid ya dawo, tsayawa yai ya siyo ‘yan abubuwan bukata sannan ya karaso gida, ya san bata nan hakan yasa ya wuce kitchen ya ajiyesu, murmushi yai ganin kitchen din a gyare, yana fitowa ya wuce toilet yai wanka tare da alwala, yana fitowa tana turo kofar dakin.
Salama tai kamar mai shirin yin kuka, amsawa yai yana goge jikinsa da karamin towel yace “An dawo?”
Kusa dashi tazo tace “Allah kaina ciwo.” Tai maganar tana zama akan gado.
Kallanta yai sannan yace “kinsha Magani?”
Kai ta girgiza mai alamar a’a tana neman kwantar da kanta akan pillow, da sauri yasa hannu ya tare kan nata.
Kallansa tai tadan lumshe ido, maida ta yai ta zauna daidai yace “magrib ta kusa karki kwanta.”
Hannu tasa ta riko hannunshi tasa a kanta tace “kama min kaina.”
Stress ne ya miki yawa, kiyi kokarin rage aiki kina barin na kasa dake suna yin nasu aikin, amma komai kice sai kinyi da kanki ko sai kin duba da kanki abin zai miki yawa.
“Ka dawo gurina ka tayani in ka damu dani.”
Murmushi yai ya dau mai yana shafawa baice komai ba.
Kan kafadarsa ta kwantar da kanta tace “nima zanyi magana.”
Uhm ina ji.
Tace “Sweet please daga yanzu duk abinda nai karka dinga dauremin fuska kaki kalona ko kuma kaki kulani, please ka dinga fadamin.”
Dan juyowa yai hakan yasa fuskarsu tai daf da juna, dan kansa ya kwantar kadan saman kanta.
Tace “nima zaka iya daukan magana ta selfishness amma banasan zamanmu ya cigaba in nama abu ka dinga dauremin fuska ba tare da na sani ba, Allah baka san yanda nakeji bane.”
Kusa da kunnenta ya kai bakinsa yace “a ina kika samo point din?”
Dan dago da kanta tai saboda abinda ya dan ratsata, bugemai fuska tai hakan yasa yai dan kara kadan, da sauri ta mike tace “na bige ka sosai?”
Hancinsa ya rike yace “da saninki ko?”
Ni da kaina ke ciwo ina zan bugashi da sanina?
Da zafi? Ta tambaya tana dan neman zare hannunsa.
Ina budewa jini zaki gani.
Ido ta zaro tace “sosai ne?”
Hannunsa ya sake yana murmushi, harararsa tai sannan ta mike.
Hannunsa ya sakalo ta kugunta yasa kansa akan kasan bayanta cikin sanyin murya yace “dazu dan ban zo ba me kike shirin yi musu?”
Shiru tadanyi, yace “umm?”
Tace “sai sanda da tashi in basuyi abinda nake so ba, duk da manyane ai basusan aikinsu ba, tunda abinda nace suyi akan aikinsu ne kaga ba wai ramuwa nai ta hanyar da basuda mafita ba.”
Dan dagawa yai ya juyota saitinshi yace “ya isa haka nan kinji?”
Kallansa tai saboda yanda yai maganar ta sigar lalashi, tace “uhm na kyalesu amma in suka cigaba da yin abinda bai daceba zanyi replacing dinsu.”
Kai ya daga mata, tace “maganar dazu baka ban amsa ba.”
Tai maganar cikin dan salo.
Saketa yai ya mike ya dau farar vest dinsa yasa yace “shikenan.”
Tace “in ka sake min fa?”
Yace “in na sake zan ma kaina hukunci.”
Murmushi tai tace “ka bari ni nai hukunci.”
No ni zanyi da kaina.
Fadamin wani iri zakai?
Ummm ya ce tare da zura riga yace “kamar na hana kaina shan ruwa na awa uku?
Baki ta bude tace “shine hukuncin?”
Turare ya fesa sannan yace “da alama kanki ya daina ciwo.”
Tace “Allah yanayi kawai dai ba kamar da bane.”
“To kiyi alwala muyi sallah sai kisha magani.”
Kallansa tai sannan ta wuce toilet, shiru tai tana kara dubawa haryanzu fa ba abinda yazo, kwana 10 kenan, meke faruwa? Dan jiya ta duba taga stress ma nasa period yai late amma ai nata ya wuce 7 days.
Alwala tai ta fito sukai sallah, shiru tai akan sallaya taba tunani, ganin haka yace “akwai paracetamol a gidan?”
Kallansa tai tare da girgizamai kai alamar a’a.
Mikewa yai yace “bari na siyo.”
Shiru tai dan ba paracetamol take bukata ba test take san yi, ba kuma tasan ta fadamai karyasa rai akan abinda ba haka ba, ta ina ma zata samu ciki? Bayan shekararta 4 da Adam ko bari bata taba yi ba? Gwara da farko tasan tai planning amma daga baya tana so amma ba alamarshi.
Yana fita ta dau waya tana duba abinda ke sa period yaki zuwa har tsawon 10days, sai dai duk inda ta duba zancen test ne gaba in har negative ne to sai ta duba ragowar matsalolin.
Mikewa tai ta fito falo tadan zauna a kasa, ta jawo laptop dinta tana duba wasu report da za’ai program dinsu gobe.
Kofar da Khalid ya bude ne yasa ta kalleshi, mika mata ledar yai ta amsa ta mike tai kitchen, hadiyan maganin tai sannan ta dauko abincinsu ta fito.
Kallanta yai harta kawo ta ajiye yace “ke da bakida lafiya?”
Murmushi kawai tai batace komai ba, zubawa yai da kansa, yace “yaushe zaki dan share dakincan? Naga an kusa hutu su Nabila na zuwa.”
Kallansa tai tace “sai yanzu za’a budeshi?”
Dan kansa ya shafa yana dariya yace “ai saboda ke na rufeshi, haka kawai nasan in dashi shareni zakiyi ki koma daki daya kina aikinki.”
Ahhhh d’an Umman nan
Murmushi yai sannan yace “taho muci abinci.”
Harzatace bari na gama sai kuma ta fasa, mikewa tai ta matso ta zauna sukaci tare, yana shan ruwa tace “Sweet ko mu koma can gidan in sunzo hutu? Nan kamar zai dan matsemana, dan Asiya ma zatazo, nasan su Amir ma nasan zuwa.”
Kallanta yai yace “hardasu Amir?”
Tace “basu sukace ba nice dai naga hakan, tunda ga Nabila da Asiya nasan zasu kula dasu.”
Shiru yai yana dan nazari, tadan sa hannu kan cinyarsa tace “sati biyu ne in suka tafi sai mu dawo.”
Kallanta yai yace “Nusaiba fa?”
Shiru tadanyi tare da kallansa tana neman abin cewa.
Yace “naga tare suke zuwa.”
Cikin saurin magana dan karya gane tace “ita a dole sanka takeyi fushi take dani nasan ba zuwa zatai ba.”
Kallanta yai kawai ya sa dariya yace “sannu wannan maganar fa?”
Tace “wace?”
Murmushi yai yace “yarintace ke damunta in ta dawo ki hadani da ita a waya.”
Da sauri tace “me zakace mata?”
Dan gefen kunnensa ya sosa yace “yayanta zai mata fada?”
Aww ta fada tana dan jin kunyar kanta.
Har suka kwanta tana tunanin wannan lamari ko wani abun ne ya sameta? Bada menopause din data karanta yana hana period ba shine da ita ba? Ai bata girma ba batakai 50 ba, sai kuma tai ajiyar zuciya cikin damuwa, karfe biyar da rabi ta farka.
Tana tashi ta wuce kitchen miyarta ta duba ganin akwai ragowa yasa ta daura ruwa akan tukunya sannan ta fara wanke wanke, tana gamawa ta sa mai ta hau dan fere dankali.
Khalid dake kwance tun fitarta ya farka, mikewa yai ya gyara dakin tas sannan ya shiga toilet yai wanka tare da alwala, yana fitowa ta shigo dakin itama ta shiga wanka.
Cikin sauri tai wankan ta fito sannan ta sa kaya, falo ta fito inda ya dan gyara throw pillows din.
Tsintsiya ta dauko yana kallanta ta fara shara, cikin sauri ta gama, break dinsa ta kawo mai ta dau flask din tea dinta ta hada, tana fitowa daga kitchen ta kalli agoggo gani bakwai saura minti biyar yasa tai hanyar daki.
Khalid ne yace “Baby.”
Naam ta fada tare da kallansa.
Alama ya mata da hannu, hakan yasa ta nufoshi alama ya mata data zauna kusa dashi zama tai tana kallansa.
Fork dinsa yasa a gabanta yace “ci”
Cikin shakka tace “gishiri yayi yawa?”
Ci ya maimaita yana kallanta.
Tace “sorry ina sauri ne bansani ba.”
Kallanta yai ya kalli abincin, hakan yasa ta debo tai spoon daya, kallansa tai da sauri tace “ba abinda yai ko bakina ne?”
Yace “no ci, karki kara fita bakici abinci ba, wannan shan shayin ya isa haka nan.”
Wuyanta ta dan shafa sannan tadanci.
Yauma tare suka fito sai dai yau bai bita ba a titi ya sauka haka ta tafi zuciyarta duk ba dadi.
*******
Yau su Nabila aka dawo hutu zuciyar nan fal take da zumudin zata gun Aunty, dan sam wannan term din haka tayishi ba dadi saboda Nusaiba haryanzu a kule take da ita, da batada kawaye amma wannan term din sai datai friends dayawa.
Abin nasu ma sai ya koma gasa, in Nusaiba taga Nabila da kawaye biyu itama sai ta nemo nata kawayen biyu, haka sukai ta wannan shirmen har sukai hutu.
********
Zainab kam yau tun safe takejinta ba daidai ba, ga abubuwa sunsha kanta ta kasa ma samun nutsuwan zuwa gun likita, ga tsoron yin test takeyi saboda tasan ba ciki bane.
Dayake yau asabar tana kwance har karfe 11, Khalid ne ya shigo cikin dakin, ya zauna kusa da ita yace “lafiya kuwa?”
Kallansa tai tace “bakomai gaba daya karfine bandashi tun jiya.”
Mikar da ita zaune yai yace “muje asibiti?”
Kai tadan girgiza tace “ko mu bari sai gobe?”
A’a muje yau.
Shiru tai tana kallansa, kallanta yai shima yace “me kike tsoro?”
Shiru tai tana kallansa yanzun ma.
Are you that scared? Kar suce miki ciki ne?”
Kallansa tai da sauri tace “ya akai ka san abinda ke raina?”
Dan yake yai yace “tun yaushe ya kamata period dinki yazo baizo ba? Kusan 3-4weeks kenan taya bazan gane ba?”
Kanta ta sunkuyar, yace “bakyasan haihuwa?”
Kallansa tai da sauri, yace “kina dana sanin bakiyi planning ba abi yazo da haka?”
Hannunta ta fixge daga hannunsa tana kallanshi, yace “ba haka bane?”
Ranta a bace tace “wani zance kale yi haka?”
Yace “ke kike sani yin wadannan tunanukan, nasan shekarun da kukai da Adam na yadda bakyasan wani abu ya kawo miki cikas a aikinki, shiyasa ban ce miki komai ba haryanzu.”
Ido ta zubamai jitai hawaye ya gangaro mata, a kufule taja bargo ta koma ta kwanta.
Baby? Ya fada yana neman juyo da ita, ganin taki juyowa yasa ya dan rukufo kanta yace “meye hakan?”
Kallansa tai tace “taya zaka fadan kalaman nan?”
Yace “tunanin dayazomin kenan nake fada miki.”
Tace “ka san sau nawa nake fatan samun ciki? Kasan yanzu tsoron kar inje acemin ba shi bane shine ya hanani zuwa? Ka san yanda nake ji.......”
Muryarta ce ta sarke, dagota yai ya rungumeta yace “am sorry baby.”
Zare jikinta tai tana kallansa, yace “ya isa haka nan”
Tace “ran laraba dady yace zasuzo, in mun fita zuwa asibitin sai na kira Nusaiban.”
Kai ya daga alamar to, tace “zamu koma can din?”
Muje mu dawo tukun.
Kai ta daga alamar to tace “amma Allah naji haushi.”
Yace “na sani, sry”
Tana shiga toilet zuciyarta ta fara tashi saboda kamshin sabulun, jin amai ne yasa Khalid shiga toilet din da sauri, amai take sosai ga ba abincin a cikinta aman sai wahala yake bata.
Bayanta ya shiga dan bugawa har ta gama.
Kallansa tai idanunta sunyi jaa, ruwa ya mika mata ta kuskure baki, dagota yai suka fito yace muje asibitin in kin dawo kyayi wankan.
Kai ta daga mai alamar to sannan suka fito.
A hanya ta kira Nusaiba, har sai data kusa katsewa ta daga murya a dakile tace “Aunty.”
Khalid ya ce “Yaran makaranta an dawo?”
Da sauri ta mike tsaye tace “Uncle?”
Yace “yan makaranta an dawo lafiya?”
Tace “lafiya kalau.”
Yace “yaushe zakizo yayarki tana san ganinku.”
Shiru tadanyi hakan yasa yace “yanzun ma fushi tai nina lalabata taya kina kanwarta bazaki nemeta ba?”
Shiru tasake yi dan batasan me xatace ba, yace “in kinzo lalai sai kin ba yayarki hakuri dan ranta ya baci “
Cikin sakalci tace “nima ai Aunty bata neman ba.”
Inji wa yace miki? Bayan tunda kuma dawo take zumudin xakuxo?”
Tace “da gaske?”
Yace “ki shirya inkunxo kya bata hakuri kinsanta in tai fishi.”
Nusaiba tace “to Uncle zan bata xan hada kayana yau.”
Haka suka kara magana kadan kafin suyi sallama.
Zainab dake kwance a jikin kujera ya kalla, yace “sannu.”
Murmushi tai tace “Thanks da alama Nusaiba xatazo.
Kallanta yai yadanyi murmushi.
**********
Kallan Dr din ta sakeyi bayan anyi test tace “me kikace?”
Tace “Bakiyi test a gida bane?”
Shiru tadanyi kafin tace “Banyi ba.”
Murmushi tai tace “abu harya kau 2mnt ya akai bakiyi ba?”
Shiru Zainab tai, ta bata shawarwari kafin ta fito.
Khalid na ganin ta fito ya taho da sauri yace “ya akai?”
Kallanta yai yaga yanda duk tai wani iri, hanyar waje tai ya bita har suka isa gaban mota.
Budewa tai ta shiga, shiga yai shima yace “Baby?”
Hannunsa ta kamo takai saman cikinta tace “Sweet tace baby ce a ciki.”
Kallanta yai da sauri, idanunta ne suka ciciko tace “I never never.......”
Rungumeta yai hawaye ne suka zubo tace “ a duk sanda nai tunanin baby sai naga kamar na shiga hakkin wanda nake aure saboda bana haihuwa, ban taba yadda da gaske nima Allah zai dubeni ba.”
Tai maganar cikin rauni, shikanshi idanunsa sai da suka dan canza saboda abu biyu na jin dadi da tausayin ta.
Haka suka taho gida hannunta rike cikin nasa.
*******
*******
Ayusher 🏌🏻♀
0 comments:
Post a Comment