Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka.
Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce da bata da tarbiya.
Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba.
Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan ta.
Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona
Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani.
Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta duk da naji tsoran yanayin shi.
Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi don ni mace bata kawo min raini nace dashi.
Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai.
Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , ,
Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni.
Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan .
Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu kama bakin nawa ba.
A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi.
Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ?
May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ?
Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri Abdul.
Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ?
Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da sauri nace zagina yayi na rama.
Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka karata ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Ina shiga ruwa na saukowa daga sama da karfi dama hadarin da ya gama haduwa a lokacin kiris yake jira ya fara zuban ruwa.
Ruwa ake sosai a lokacin na kuma san basu kai gidajen su ba duk da ba zan iya cewa ga nisan gidajen su ba a lokacin.
Na fara cire kayan jikina aka turo kofan dakin nawa da na saya da sauri na juya don ganin wanda ya shigo min a wanan lokacin haka.
Maryam yace sabuwar kawar da nayi a cikin hostel din namu tana rike da wani warmer dain abinci na silver mai marika tashigo tana dauke da murmushi a fuskanta nima murmushin na mayar mata a lokacin nace cikin ruwan nan kika fito.
Tana aje kulan tace tun dazun nake dakon dawowar ki ai sai yanzu na ga wuta a dakin ki na san kin dawo gami da yi min sannu da dawowa na amsa ta.
Na karasa cire kayan na daura zani a jikina tace abinci na kawo muci don yanzu na samu yar uwa na huta zaman kadaici hakana murmushi nayi ina zama a saman katifan nace fitan nan nawa har kikai girki haka ?
Tace dama akwai miyan a fridge sai shinkafa ne kawai na girka muna yanzu nayi mamakin jin har da fridge a dakin ta don ban taba shiga ba sai ita ce mai zuwa dakin nawa.
Ido na ta kai ga ledan da na shigo dasu dakin yanzu na dauko na fara budewa kayan mata ne a ciki irin doganyen rigunan nan har kala biyar sai takalma da jakka biyu.
Sai dayan ledan mai dauke da kayan drinks da su packed din sweet irin mai tsadan nan tace woow duk wanda yayi sayayan nan yasa kansa wanan rigunan duk letes ne fa don anty na business din da take yi ke nan wanan dawowan da tayi daga dubai naga ta dawo dasu har nace taban guda daga ciki tace sai dai in saya.
Nace uhmm kyautar maya ne haka maryam wasu yan yan gari mu ne da suka zo yanzu muka fita tare suka saya min su.
Maryam tayi dariya tace manya ko ba nawa sa ba nerbough don wanan wawan kyautar sai da wata a kasa kin san ko ba karamin kudi aka kashe wurin nan ba.
Nace kuma kin ga ba wani abu a tsakanin mu sun dai ce ne mudan fita in rakasu wani wuri ni ban ma shiga shagon ba Yusuf kadai ya shiga sai gashi da wa yan nan kayan haka ya fito.
Tace haka abin yake ai don masu kudi basu jin zafin fitar da kudin su, ga abinda suke so don wanan kyauta ai ta maya ne daganin su duniya na damawa dasu Allah.
Nace sam ban san yayi min wanan mahaukacin sayayya ba da na dakatar dashi wallahi ni na dauka ko irin dan drink's din nane da sweet fa.
Maryam tace may ye na damuwan kan ki tunda bake kikace su saya maki ba sai dai gaskiya kyauta yana nuna alama ga abinda ake so ne.
Nace so kuma ai sun san ban da lokacin wani so a yanzu kawai dai raayin su ne yin hakan sai dai zan dakatar dashi ga yi min haka nan gaba.
Abinci ta fara zuba muna muna hira na kwashe kayan na kawar gefe guda ina ce mata kinga yanzu sai dai mu canza tsari ba wai kullun kita dafawa kina kawo min muna ci ba haka.
Dariya tayi tace kin manta da rana naki mukaci shiyasa nima na dafa muna yanzu muci ai ko hakan kuma laifi ne nerbough ?
Muna ci muna hiran makaranta da ita har mun kusa gamawa wayana dake gefe yayi kara da sauri na mika hannu na dauko don kada ya tsunke.
Daddyn mune akan layin na dauka da sauri ina hadiye abincin da ke a bakina yace may kike ci haka khadja ko dadi kuke ci a makarantar mu muna nan gida muna hadiyan shikafa da mai ya fada cikin zolaya .
Nace daddy Allah ya nuna muna mun samu kuma kuji dadin da iyayye ke ji ga diyan su watarana indai zakuyi farin ciki da hakan.
Yace ko yanzun ma mun gode maku don muna cin moriyan ku a haka yaushe yaushe kika turo muna da kudin hannun ki wai mu kara nayi fada ai da yar uwarki nace ke da kike makaranta kin fimu bukata a yanzu ai.
Burin mu daya shine muga kin tsayar da miji da wuri kiyi koyi da yar uwar ki kema kiyi aure basai kin yi dogon karatun nan dakike so ba.
Dariya nayi nace kai daddy aure yanzu kuma nida nake son in zama babban lauya kafin in aure amma tunda naga raayin ka ke nan ba damuwa .
Daddy da izzinin Allah zan cika maku burin ku daddy na karasa fadi cikin sanyin murya daddy yace da sauri .
Dear kada ki sa wanan a rai yanzu buri na fada maki kawai shi aure ai dan lokaci ne indan lokacin yayi ko da shiri ko ba shiri zakiyi ne ai nafison in ganku cikin farin ciki a koda yaushe bana son bacin ranku kada magana na ya kara maki zuciyar ki akan karatun ki.
Ya kara da fadin Allah dai yayi maku albarka dake da yan uwanki don baku taba bata muna rai ba da halin ku.
A hankali na goge hawayen da ya zubo min a idona nace mukai sallama dashi bayan ya gama kwatar min da hankali na.
Maryam ido ta tsura min ina aje wayan tace dani ina son nima inga ina haka da iyayyena wallahi sai dai hakan bai samu ba a gare ni don na taso ne ba tare da iyayyena a wuri daya ba.
Mahaifiyar mu sun rabu da babban tun muna kanana sai dai idan naje inkai masu ziyara dukkan su tunda riko na yadawo hannun yayata.
Nace Allah sarki lalai dole kiji sha, awan hakan gaskiya don iri haka babu daddy ni kinga iyayyena sun fi son suga nayi aure ko yaushe maganan su ke nan a kaina.
Sai dai ko yaushe auren nawa zai zo ban sani ba tunda ko sauriyi tsayayye ban kai ga tsayarwa ba a yanzu haka.
Tace to ina ga dai yazo din ne tunda ga wanan yanzu da ya fito ya fara nuna maki son shi dariya nayi nace maryam ke nan baki ganewa ne ke.
Bandai fada mata komai ba mukaci gaba da hiran mu sai goma ta koma dakin ta nima na gama abinda nakeyi na kwata.
Har na kawanta naji wayana na verviration a gefena nasa hannu na dauko wayar nace salamu alaikum.
Yar mama kina lafiya yaya ruwa , ?
Na sauke lafiyayyen murmushi nace lafiya kalau yaya Yusuf yace kina kara fasa min kai fa da yayan nan da kike kirana dashi nace kai ka saya a kira ka da sunan.
Nace yaya kuka isa gida kuma yace lafiya kalau sai yanzu na kai mutumin ki gida yanzu haka ina hanyan gidana ne na kiraki mu gaisa.
Yace bayan mun rabu dazu mun dade muna maganan ki da mutumi na nasan zai kiraki yau din na shiya na kira ki in fada maki don naga ya yarda sosai da shawarana.
Nace anya kuwa zan iya cika maka alkawarin da na dauka don mutumin naka akwai zuciya sosai wallahi ni kuma ban iya daukan haka don nice zan taimake shi ba shi zai taimake ni ba.
Dariya yayi yace a yadds kuke yi din nan shakuwa zaizo ya shiga tsakanin ku sosai zakice na fada maki watarana bagashi yanzu ya fara saukowa ba.
Idan ba ta haka na fito mashi ba da wuya yayarda mu aiwatar da komai yadda muke so amma ki daure don Allah mubi abin sannu ni dai buri na shine ki san yadda kikayi kika kara ma wanan buzuwar kadarin ta a gurin jamma,a.
Abin ne da kamar wuya yaya na sai dai zan yi kokari inga nayi yadda kuke so din yace good girl Allah ya taimaka ya bada sa,a nace amin.
Shine kuma ka yi min dawainiya haka mai yawa don Allah nan gaba kada ka kara min irin haka don hakan zai yi maida ni cikin wani yanayi daba shi nazo yi a gatin ba.
Dariya yayi yace Khadija kin san dai sutura shine mutum yanzu don haka farawa akayi don ina son ki goge sosai ki fito a cikin classes ladies ta yadda zamuji dadin aiwatar da komai a cikin sauki nace to na gode sai dai a rage don Allah.
Kada kiji komai mana lokacin kine yayi kawai ki kwantar da hankaki kici arzikin ki a saukake wanan ba komai ba kada ki damu da hakan don har motan shiga ba dadewan nan ba zaki samu in komai ya tafi daidai.
Zanyi magana ya katse ni da cewa na iso gida zan shi sai dai indan mun kara waya don yanzu zamu rage haduwa sosai kada a zargi wani abu a gare ni.
Mun gama wayan ina mamakin su kudi kamar na sata haka nikan ban cika amincewa da irin haka ba azo ba a daidaita ba shirin mu ya watse abarni cikin wahala daga baya.
A hankali ya shigo gidan babban falon su ya samu su hidaya da sauran yan su zaune suna shan bakin shayin su na buzaye.
Gaisuwa sukayi bai tsaya ta kansu ba ya shige ciki bai jin dadin yadda suke cika mashi gida a ko wani lokaci haka.
Duk da wani lokaci abin yana taba mashi zuciya ganin yanzu babu wani nashi da yake zuwa wurin shi kamar lokacin da suke zaune kano da fati .
Yan uwan shi na yawan ziyarar su maza da mata amma tunda abin ya juye haka sai dai kulun idan ya dawo gidan ace mai akwai bakin da suka zo daga kauyen maradi.
Dakin ya nufa ya tura kofa a hankali dakin na nan a yarda ya barshi da safe ba a gyara shi ba in zai iya tunawa yau kwana uku ke nan bai samu lokacin da zai tsaya ya gyara dakin ba.
Don cikin yan kwana kin nan suna zirga zirgan filin da suke son saya a kubuwa ga kuma wanan shirin da Yusuf yake son yi a kan shi.
Rigar shi ta sama ya jefar a saman gado ya kara bin dakin da kallo ya ja tsuki ya nufi yanyar bathroom din shi wani zarni ne ya daki hancin shi da sauri ya fito ya nufi hanya wajen dakin.
Dakin Nafisa ya shiga don yana kyautata zoton tana ciki tunda bai ganta falo ba kuma bai ganta a nan dakin shi ba.
Yana shiga nan ma wani tsami ya tare shi mai kama da karni karni yabi dakin da kallo ga kaya a ko ina watse a dakin tana kwance saman godon dake tule da kayan da bai san ko na maynene ba.
Nafisa na ganin shi tace ka dawo ashe yanzu nake tunanen ka fa a raina nace ko ina ka shiga tunda ka fita da safe baku dawo ba.
Haushine ya kamashi yadda take kwance ta mike kafa sai kadasu take yi tana magana kamar wata basaraka da ita.
Kallon da yake mata ne yasa ta tsargu yace Nafisa wai ke dadin may kike ji ga kazantar nan naki ne haka don Allah dubi dakin da mutun ke rayuwa wai a cikin sa.
Kina mace kice ba zaki iya gyaran muhalin ki ba sai wasu sunyi maki wai ma ina masu aikin da kikace kin dauka ban ga wani abinda suke a yi a gidan nan ba.
Tace Samad yan uwana ne fa ko kuma yanzu kana bakin ciki da zaman su ne a gidan ko suyi aiki ko kada suyi zasu dai zauna anan tare dani ne ko ?
Nasan wanan munufakin kila yaka su hadiye a falo ya zuga kwanan nan sai nayi maganin shi wallahi ni banga dalili da zai sa yayi ta shigo min gida ba haka ba gaira ba dalili yana sa muna ido.
Ke na fada maki duk abinda zakiyi idon ki ya fita ga Yusuf don idan kikace zakiyi kokarin raba ni dashi kan ki zakiyi wa kin dai san halina and kuma ki tashi kije ki pulloshing din rubish din da kikayi min a bandaki tunda ba dakin ki bane.
May nayi kuma kewayawa fa kawai nayi a ciki na fito yace zaki tashi ko sai na bata maki rai yanzu ya fadi yana dan zare mata idon shi.
Mikewa tayi da kyar tazo ta wuce shi zuwa dakin ya bita da harara ya mara mata baya yana sa kai warin bayin ya ji har cikin dakin da sauri yafita zuwa dakin hutun shi tare da rufo kofan da key don bai son damuwa.
Anan ya cire kayan shi ya yi wanka ya fito sallah ya gabatar ya dade zaune a wurin yana tunanen halin Nafisa ga gida da ta cika mai da yan uwanta babu halin ya zauna a tsararen falon shi ya sha iska a ciki.
Tsuki yaja ya mike don ya kwanta nan yaga wayan shi da ya jefar saman gadon daya shigo dakin kafin ya kewaya dauko wayan yayi yana duba lokacin maganan Yusuf ya fado mashi a rai.
Da yake ce mashi kabi yarinyar nan a sanun har mu cin ma manufar mu a kan hajiya ba wai nace kaso ta bane dole a a wanan wani dama ne da muka samu zamuyi amfani dashi.
Nomba na ya bida a wayan da ya rubuta ma tsoturburn girl ya danna kira sai ko kiran ya shiga tunanen ya fara yi idan na dauka may zai ce min sai yaji na dauki wayan da sallama a bakina.
Queen yar matsala yaya kika shiga gida yaya kuma ruwa i hope bai taba ki ba dai ?
Murmushi nayi sai da yaji shi cikin zuciyar shi nace au mijin buzuwa ne a layi lallai kana son aikin nan da zan maka ke nan ?
Yace to yaya na iya tunda Yusuf yace ke ce maganin matsalata yanzu indai har zaki min hakan ai ya zama dole in koyi zama dake da halin ki .
Nace ashe shiyasa na samu queen din yan matsala yace idan akwai abinda yafi queen din su kinci a baki wanan muka min.
Murmushi na sake yi nace nace nako gode da wanan sunan da aka rada min sai dai ina ganin bada ni sunan ya dace ba yanzu ai.
Da sauri yace dawa ya dace nace kaida buzuwar matarka mana fara yar dagwas mai gashi har baya sai dai kassh kuma gashin sai naga kamar bai samun gyaran da ya dace dashi balle har kaji dadin shakan shi dakyau.
Ke kada fa kiga na kiraki ki nemi tozarta min matata don kin san tafi komai da kike takama don wanan banzan dalilin na Yusuf da yakawo bashi ne zai sa ki samu daman fada min maganan banza ba.
Wanan kuma fadi kayi mijin buzuwa don yanzun haka ma nasan tunanen yar asaline ya hana ka shakat sai da ka kirani kaji yaya nake sai dai kana tsoron buzuwar ka nasan ma yanzu haka wani wuri ka samu ka labe kake wanan waya dani.
Idiout stupied girl kawai ya fada ya ja tsuki ya kashe wayan yana huci wai may yarinyar nan take takama dashi ne wai zuciyar shi tace kyau ilimi tsabta da fadin gaskiya.
Idon shi ya lumshe yana tunane sai kuma ya sake guntun murmshi a yadda yake rigingine a kwace taba kofan da Nafisa keyi yasa shi bude idon yana jin ta har ta soma bugun kofan bai tashi ya bude mata ba sai gyara kwanciyar shi yayi dakyau ya fara adduan barci haka har barcin ya dauke shi yana tunane.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Ina isa na fara bude kofana na lokacin yarinyar ta iso da kayan da Yusuf ya bata tana mika min kallon kayan nayi sai na karba ta karasa min da sauran a cikin daki na.
Godiya nayi mata tace babu komai ai ana tare bayan na aje kayan na fada saman katifa na wasu hawaye masu zafi ne suke silalo min a fuska na.
Idan na tunana da maganganun da ya fada min masu zafi duk da nima din nayi karfin halin ramawa a lokacin sai nake ganin ya kwaraini da yawa.
Na dade a wurin ina neman hanyan da zan rama abinda yayi mun din don yaji zafin da naji ban kai ga samun mafita ba wayana yayi kara a lokacin.
Yusuf ne ya kirani sai da ta kusa tsukewa na dauka na kara a kunne na ina sauraron shi yace har yanzu kina fushi ne yar mama.
Daurewa nayi nace ai ban fushi dakai don bakai min komai ba yaya na yace dakyau ina son ki saurare ni dakyau magana nake so muyi dake yanzu.
Ina jinka nace mai.
Khadija don Allah ina son ki bani hankalin ki ki fahinci abinda zan fada maki yanzu naji na kara furtawa.
Don Allah ina son in rokeki wata alfarma wani aiki zaki nake son ki min a kan aboki na amma aikin yana da wahala sosai sai dai indan kin daure ba wani wahala a cikin sa.
To ina jinka Allah yasa zan iya kuma Allah yasa dai aikin bai fi karfina ba, murmushi yayi yana fadin bai fi karfin ki ba ma insha Allahu don zaki iya.
Nace fada min inji aikin idan ba zai shafe karatuna ba da rayuwa na zan iya insha Allahu yace good girl dama na dade ina neman mace irin ki mai gaskiya da zan saka.
Ba wani abu zan saki ba sai taimako rayuwan abakina Samad nake son in danka a hannun ki don kice a yanzu kadai nake da ita da zatayi min wanan kokari.
Nace ni kuma yayana yace kwarai kuwa ke khadija don ko zaki iya idan munyi laakari da irin halin ki na san zaki iya shiyasa na zabo ki.
Tun ranan da muka shiga dakin hajiya mama na fara ganin ki da kuma abinda yafaru dake da Nafisa matar shi kika tsaya min a rai.
Ban kuma gaskanta hakan ba sai da naga kin iya biyu su a motar su zuwa nan Abuja kuma komai bai faru ba yasa na kara yarda da abinda nake shirin yi din .
Sai gashi kuma yanzu abubuwa suna wakana a yadda nake son su tafi a tsakanin ku cikin hukuncin Allah komai yana tafiya daidai.
Khadija ko kin san ba macen da ta isa ta tsaya kusa da Samad tun lokacin da ya auri Nafisa buzuwar matar shi kuwa.
Nasan kin san matar shi Fati da akai masu auren gida har suka haifi yaya biyu shigowan buzuwa gidan ya sa suka rabu da ita badon basu son junan su ba.
Khadija kin san abinda ya daure min kai nace a a yace yadda Yusuf ya aminta dake a lokaci daya duk da nasan ba abu bane mai wuya a wurin Allah idan ya tashi yin ikon sa akan abu.
Don haka nake son ki taimaka muna ki sake jiki da shi tayadda zai aminta dake idan haka ya samu gare mu na tabbatar da sheri buzuwa yana gap da karyewa.
Da sauri nace ba zan iya ba gaskiya ku nemi wata wanan miskilin mara mutunci ai buzuwar ne daidai dashi yace khadija zaki iya zaki iya komai.
Kyau dai Allah ya baki shi ilimin addini da na boko duk kina dasu a wadace to may zai saki ce bazaki iya ba ai ko ba don niba ko don hajiya mama da fati da yaran ta zaki iya.
Nace yanzu may kaka son in yi wai yace shina ke son in fada maki da farko dai idan ki bi labari na zaki gane Samad bai iya ssoyayya ba shine matsalaan farko da aka samu gare shi.
Murmushi nayi nace bai iya soyayya ba ta yaya ya auri matan shi har suka zauna Fati har ta haihu dashi biyu shima din murmushi naji ya dan yi yace.
Bamu tare ke nan kin manta na fada maki ita fadi hadin iyayyene auren su ita kuma buzuwa abu biyu muke zaton shine silar auren su na farko dai ta rude shi da kyaun ta na biyu kuma ta hanyar sihiri da sauri nace sihiri kuma bada ni ba gaskiya.
Yace da zata iya maki komai da tayi tuntuni ai shine ya bani daman sakaki wanan aiki a yanzu.
Nace a takaice dai kana son in bata lokaci na a kan shi abinda ya kawo ni in barshi inje taimakon wani wanin ma wanda bai san darajan mutane ba.
Aikin da zaki muna ke nan dama ki koya mashi zama da mutane da sauran abubuwan da ya watsar a baya ki dawo muna dashi Abdulsamad din shi na baya.
Babban magana ke nan yayana yace ba wani babba bane a matsayin ki na mace zaki amfani da daman ki taimaka muna ki tai maki hajiya dake cikin halin bakin ciki a kashi.
Shiru nayi ina tunane ko badon Yusuf ba ko don hajiya da yaran Fati zan iya kasadan yin wanan gwajin da suke sona dashi yanzu.
Nace to shike nan naji zan yi matukar hakan ba zai shafi mutunci na ba dai yayi saurin cewa idan nasan zai zubar maki da kiman ki ba zan saka ki ba ai.
Nace amma fa in ya nemi keta min mutunci ba zan kyale shi ba zan dauki mataki da kaina yace wanan ba halin shi bane don nasan halin shi tare muka taso tun muna yara dashi.
Nace Allah bamu sa,a yace amin na godd da kika fahince ni yanzu zan samu lokaci in shigo inji mai kike bukata don kin san dole sai kin koma ke ma babban yarinya sosai.
Kada ka damu zanyi amfani da wanda nake dashi yace kin wuce wanan yanzu khadija zaki zama budurwan mayan garin abuja ne fa.
Yace ina son ki fara daga yau nace yau din nan ina zanganshi yace zai bugo maki waya ba yana da layin ki ba nace eh zaki kaga ya kiraki kan abinda yayi maki.
Amma sai dai please ki bishi a hankali yana da izza da saurin fushi da zuciya bai son yawan magana idan ba yaso ba amma banda wanan baida komai da zaki damu.
Ni kuwa nasan haka nida ya fada ma magana yau sun ranshi sai dai zan jure kamar yadda kuke so inyi din.
Ajiyan zuciya naji ya sauke yace ban san irun godiyan da zanma maki ba ga wanan haracin da kikai muna wanda nasan insha Allahu zai zamo maki alheri ke ma nan gaba.
To Allah yasa hakan alheri ne a gare ni dai fatana in ga ya koma da iyalin shi normal sai naji ya sauke ajiyan zuciya yace final shine dama bukatan mu .
Mukai sallama ya barni ina tunanen yadda abin namu zai kaya tsakanina da miskilin mijin buzuwa ta ina zamu fara nace anya ban daukar wa kaina abinda ba zan iya ba kuwa.
Gashi kuma Yusuf yace sirine ne tsakani na dashi sai Allah sai ko nan gaba da zai fada ma hajiya mama shirin shi.
A raina nace zan iya insha Allahu indai iyalin shi zasu dawo gare shi sai dai ban taba zaton abin zai zo a kaina haka ba amma ba komai wahala bata kissa ai.
Nan dai nayi ta tunanen ta yadda zan fara deal din akan shi amma dai Yusuf yace shi zai fara aiwatar da komai kamar yadda yake yi da farko.
Safiyan lahadi wanki nayi sai wanan bakuwar yarinyar da ta shigo min da kaya don dai han san ta a gidan ba tazo min hira dakina ina gugan kayan da suka bushe min.
Nan take fada min ai ita yar jos ne amma tana zaune ne da yayanta a nan cikin gari ta dawo hostel ne don ta samu yin karatu da kyau naji dasin haduwa na da ita ko banza zan rage zaman kadaici ni kadai da nakeyi ni kadai.
Waya na yai kara na daga Yusuf ne bayan mun gaisa yace fito gamu kofan hostel din ku dam naji gaba ya bada na kalli maryam dake gefe na nace ina zuwa ta mike ita tace zata je ta gyara daki don gobe akwai classes.
Ba wani dogon kwalliya nayi na dan yafa gyale na na fito tun fitowa idon su yana kaina har na iso inda suke a cikin motar su.
Na gaida Yusuf din yace ga abokina ogana baki gaida shi ba na dan juya wurin shi a yatsune nace oh ashe tare kuke ina wuni.
Haushi da takaici ya kama shi ya rasa ma zai yi sai da Yusuf yace khadija na gaishe ka fa cikin yanayi da alama na ko in kula yace lafiya kawai ya kawar da kanshi gefe.
A ranshi yace i hate dis girl wallahi Yusuf ya katse shi da cewa oga gata nan ta fito fa ya fada cikin tsigar tsokana ya juyo da sauri yace wa wurin na tazo dama.
Yace bakai kace muzo kabata hakkuri ba abinda kai mata jiya kasa ta kuka ya damay ka da sauri na tare Yusuf da cewa ai nice zan bashi hakuri nida na bata mashi rai jiya.
Don fadin gaskiya ni kuma nasan gaskiya na fada duk cikkaken namiji da yasan ciwon kanshi ba zai tsaya mace na juya shi macen ma kuma buzuwa wai.
Yusuf dama ka kawo ni nan ne don ta kara ci min mutunci ko may haushi ya ishe shi yarasa may zai ce min wallahi na tsani wanan yarinyar ya fada a hasale .
Cikin ko in kula nace i hate you too dama abinda yasa kuka zo ke nan daga ganin ka nasan ba yin kanka bane buzuwa ta hasala ka ka koma ma matar ka kawai ta asali ko mutuncin ka zai dawo ga idon jamma, a.
Yusuf yace kai oga fitina khadija ko rigima nace bai son gaskiya ne gadai mutum har mutum amma bai kai ga cikan kamala ba har yanzu ga idon jamma a.
Oh stop it gara ku fito fili kununa ma duniya soyayyan ku da wanan sallon soyayyan naku da kuke yi kullun u don't need to pretend garama ku fara tun yau.
Wai Yusuf may kake nufi dani akan wanan yarinyar ne da kullun kake kawo ni wurin ta taci min mutunci hakane.
Ni dramar kuce take burgeni wallahi don naga idan na kawo ka wurin khadija tana saka magana kana rage damuwa ko yaushe kuma tana ma tuni da abinda ka manta.
Gyara zama yayi a motar ya kwantar da kai tare da harde hanaye shi wuri daya yana kallon bakin hostel din mu yadda mutane ke ta shiga da fita ciki.
Nima kallon Yusuf nayi nace yayana wani wuri zaku ne yace muna dan yawata wane muka zo duba ki kin san ke amanan hajiyan mu ce gare mu yajuya wurin shi yana fadin ko ba haka ba aboki na ?
Tsaki yaja ya kara kawar da kanshi gefe nace sai dai tsiyan abin indan yayi fushi fushin bai mashi kyau sai ma ya kara mai muni sosai.
Murmushin dole ya sake yace kai Yusuf muje don Allah wanan na gane zata iya haukatani in banyi da gaske ba.
Kaiko daukanta zamuyi mutafi da ita adan sawo mata wani abin mana kaga sai ta kara hucewa ko tunda gashi har ta baka hakkuri yanzu ai komai ya wuce kenan.
Kinga ba sai kin fada ma hajiya mama dukan bakin ki da yayi ba jiya ai yanzu kun zama friends kuma ko fada ya kare ke khadija ba yayaki hakkuri don Allah.
Da sauri ya juyo inda nake sai na dan durkusa nace ya Samad kayi hakkuri don Allah idan na maka laifi.
Oh baki san ma kin min laifi ba ke nan Yusuf yace shigo mota sai mu karasa magana a hanya yamma nayi kwarai.
Banki ba tunda nasan plain ne na shiga motar a hankali ya harba titi ina harara dan iska a inda nake zaune Yusuf ne ya shiga aiwatar da nashi shirin a lokacin cikin motar yana dan muna nasiha.
Yace kar kuji komai indan nine take a deep breath and confess your love to each other wani irin dogon nunfashi yaja tare da lumshe idanuwan shi.
Da sauri nace yayana love kuma a ina kataba jin anyiwa mutum dole haka akan abinda yaki jini yace don't say dat again just say yes to each other don kuna bukatan hakan.
Khadija ina son ki rike min oga na tsakani da Allah ko babu soyayya ku zama aminan juna muna son ki gyara tsakanin shi da hajiyan mu ta fahince shi ta bar hushi dashi.
Sai lokacin ya kallo Yusuf ya sauke wani ajiyan zuciya don ya zaci Yusuf yana son hakane don gyara tsakanin shi da mahaifiyar shi.
Nace yaya zanyi in gyara mashi laifin dashi yayi da kan shi har kake tunanen nice zan gyara hakan yace yes idan hajiya taji kuna tare nasan zata ji dadin yin hakan da kuka kin ga zata fitar ma abokina da zargin da suke mashi na buzuwa bata bari ya rabi wata mace sai ita.
Sai yanzu na gane nufin ka abokina ya danyi gyaran murya sai kuma yayi shiru can yace da farko dai na gane manufan ka yanzu Yusuf .
Yace zamu shirya dake idan har zakiyi min wanan taimakon iyayyena su fahince ni a hankali nace idan ka shirya yin hakan a shirye nake in taimaka ma in har zaka koma masu da zuciya daya.
Maganan ta dan soshi ranshi amma haka ya dake yace na gode a hankali ai lokacin gode min baiyi ba nace mashi.
Tsayar da motar yayi a bakin wani babban sai da kayan sawa irin na mata da maza ga motoci birjit a wurin an paka su a haraban wurin.
Bissimilah yace muna kallon shi yayi yace wa wai ni kake nufi kowa yace daku duka nake magana ai yace may zanyi a wanan gurin yace kaunar mu zamu ma sayayya mana.
No kuje kawai yace yana gyara zaman shi a yadda yake nace da ka barshi ma ban bukatan komai a yanzu yace tunda nayi niyar yin haka barin in fita induba zaku iya jira a mota yana bude motar zai fita yake wannan magana.
Da sauri nace dashi barin fito mu shiga tare yace No ki zauna abinki yanzu zan fito ba dadewa zanyi a ciki ba.
Yana wuce na koma na zauna bayan na bishi da kallo wayana na dauko ina dubawa shiru motar babu mai maga a cikin mu sai can naji yaja guntun tsuki wai da bai harka da kananan mata sai manya masu aji ko su sai a waje idan yafita duk da ba wai yana yawan hurda dasu bane yanzun ga Yusuf yana son ya dauko mashi wani aiki ga wanan yar karamar yarinyar dako sa,an kannen shi batakai ba sosai.
Nima tsakin naja ina gyara zama cikin tunanen da nakeyi nashi.
Ga dai mutum har mutum kudi kwaliya kwarjini duk Allah ya bashi sai dai yawan miskilanci da girman kai da jan aji din yayi yawa kamar ba mace ce ke juta shi ba a gida.
Ke ni kike wa tsuki ko kowa ya juyo tare da zuba min kyawawan idanuwan shi a kaina na ma mance kana cikin motar nan murmushi mai kama da takaici yayi yaci gaba da zuba min kyawawan idanuwan shi can ya koma ya lumshe su tare da komawa saman kujera ya zauna.
Ya sake cewa kina aji nawa ne yanzu ba tare da ya juyo ya kalle ni ba shiru nayi ina game da wayana batare da na nuna mai dani yake magana ba.
Dake nake magana ko bakiji bane nace wa ni ai na dauka da kurma nake a motar a hankali ya kada kanshi ta dan sake murmushi yace ke dai ba zaki bar wanan halin naki ba ke nan.
Nace ba halina bane hakan a ra nayi don in kare kai na daga masu raina ma tallaka hankali ya fido ido waje yace haka kika dauke ni ke nan .
Hakan na gani kamar kana tsoron talaka a kusa da kai sai dai ba abun mamaki bane don ko a gida haka naga kanayi masu wanan daure fuskan.
Kin san nayi ma aboki na alkawarin ban kara fada dake yanzu don haka ki kama min bakin ki tunkan in hasala da wa yan nan maganganun naki.
Kai ashe kasan girman alkawari haka ne nakoji dadin jin hakan saidai kamar yadda kai mashi alkawari ka cika nima ada hakana naiwa kaina alkawarin ba zan tsaya da wani namiji ba sai gashi a sanidin taimako ina son karya alkawarin da na dauka ma kaina.
Yaja numfashi tare da cewa wanan deal ne a tsakanin na dan wani lokaci banga abinda zai sa ki dauke shi kamar serious ba.
Nayi dariya tare da cewa wasa mai kamar wahala ba indan buzuwa ta sanda hakan akwai matsala babba ashe sai na kwashe da wanni irin dariya mai ban haushi dake wa yayi bai ce komai ba cikin kuluwa.
Yusuf ya fito da manyan jakkuna a hannun shi yana kokarin bude motar ta kofar baya ya saka jin dariya yasa shi cewa abin ya fara tafiya ke nan dai.
Ya dai kusa na bashi amsa a takaice kai a fasa wanan deal din nace a fasa gaskiya zai fi don wanan ba zai kai ko ina ba.
Zai kai mana yace yana rufe kofan motan ya zagaya ya shiga kallon Samad dake dafe da kan shi yayi muka kama hanya a lokacin hadari ya hadu sosai a garin ruwa na iya zuba a ko wani lokaci.
Mun iso Yusuf ya tsayar da motar yace khadija mun gode sai mun kara haduwa yanzun ba time hadari ya hade gari ta ko ina nace nagode kwarai.
Ka kula min da mijin buzuwa don Allah na bude motar zan fita yace ga kayan ki nan ki kwasa duka naki ne godiya na sake mai karo na biyu na fice daga motar.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Zaman da maryam yana min dadi sosai don itama bata da wasa da karatun ta gashi musan mutuncin junar mu kamar mun dade da haduwa da ita.
Ita ta tilasta min fara amfani da kayan da Yusuf ya saya min tace may ye amfanin ajesu da nakeyi gara dai a fara gani a jikina zai fi.
Ban sake bi takan su Yusuf din ba na mayar da hankalina ga abinda ya kawo ni garin sosai sai dai muna waya da kowanin su har yanzu wanda wayana da Samad duk ya kira fada ne da zolayan junan mu har ai fada a kai ga kashe wayan.
Munyi jerabawan karshen zango na farko inda muna gap da gamawa Yusuf ya kirani nake ce mai sati mai zuwa zan tafi minna don ba zan leka kaduna ba wanan hutun saboda hutun ba mai yawa bane .
Nan yake ce min suna tafe gurina kafin in wuce gida don suma zasu shiga kaduna don Samad ya dade bai je gida yana kokari yaga ya shawo kan shi su tafi.
Nace ka barni dashi in gwada in gani idan zamuyi sa, a da nawa dabaran yace ya gode muka kashe wayan suna zaune tare aiki suke a wani file.
Yusuf yayi mamakin jin ya tambaye shi khadija yace tana nan lafiya kasan jerabawa suke yi kwanan nan wayan shi ne yai kara baiyi saurin dubawa sai da ya gama abinda yake ya dago wayan.
Kallon Yusuf yayi da mamaki tare da fadin Yusuf yarinyar nan ko mutum ce jifa itace ke kirana yanzu muna maganan ta.
Yusuf ya kalle shi yace mutum ce mana kamar kowa kaima kana ranta kamar yadda take a ranka ke nan .
Ya dauka ciki daure fuska kafin in magana ya fara fadin lafiyan kirana ina aikina nace lafiyan ya kawo haka ai .
Ya sake kiran suna na a zuce da karfi yace matsala na amsa mai da cewa may ye ne haka zaka fasa min kunne da kira haka kamar makaho.
Kai na tsani wanan yarinya ya fada a hasale na amsa mai da nima haka wallahi cikin yanayin na bashi amsa.
Nace dama abinda yasa na kiraka don in fada ma ya kamata kaje gida ka duba tsofin ka don gudun su da kakeyi ba shine mafita ba gare ka.
Yace what da karfi don bai yi tsammanin jin wanan magana haka ba a baki na
Duk wani da mai neman albarkan iyayyen shi yana tare da su a kullun suna saka mai albarka da fatan gamawa da duniya lafiya don samun haske a gare shi.
Kai kana ganin kudi da girman kai da suke rudin ka zasu iya sama ma farin ciki haka ne a gare su, sunyi ciwo sun yi rashi amma bakai tunanen zuwa ka duba su ba har yau.
Who dear you are da zaki fada min abinda zanyi akan iyayyena, nace ni bakowa bace sai mai neman albarka iyayyena don haka kai ma na tunar da kai akan hakan.
Kuma kada ka manta da su Affan don sun fi kowa bukatan ka a wanan lokacin don nasan zaka iya zuwa masu hannu sake kai ba abin kunya bane a wurin ka.
Don haka oga aje a duba su kada a shagala da yawa wataran sune masu duba mu you are stupid kece zaki tunatar dani komai kike nufi wai ke wacece wai waya baki wanan right din da zaki min wanan magana haka.
Nace gani kamar kowa na tsoron fada maka gaskiya don suna ganin kana da kudi niko kudin ka ba damuna sukayi ba wallahi gaskiya komai dacin ta dole ne in fada ma mutum shi.
Amma gani nayi buzuwan ka kamar kanta kawai ta sani sai yan uwanta ai don haka nima dan uwa na na sani a yanzu.
Kit na kashe wayan ina dariyan keta shima Yusuf dake zaune yana jin yadda mukayi dashi sai murmushi yake yi yana huci yabi wayan da kallo.
You see abinda nake fada maka kenan gashi yarinyar nan har ta hango tunda kaji ta fadi haka akwai abinda taji ya faru a gida may be.
May yarinyar nan ta dauki kanta ne wai zanyi fa maganin ta a garin nan Yusuf da sauri Yusuf din yace kunfi kusa ai ni dan kallo ne a tsakanin ku sai dai ya kamata ka bincika idan ba wani taji bai da lafiya a gidan ba.
Tsaki yaja yana rufe file din da suke aiki akai alaman rashi ya baci sosai ya dafe kai da hannun shi daya tunane ya shiga yi yaya akayi yayi sake rainin da bai taba shiga tsakanin shi da kowa ba har shiga tsakanin mu haka wai abinda nake mai zakace ko mu din cousin ne.
Kan shi yana dafe da hannu shi daya Yusuf yace muci gaba mana yace kana iya tafiya yanzu makarasa next yanzu matsala ya shiga .
Dariya yayi yana mikewa yace matsalan khadija ke nan ko hararan shi yayi da idanuwan shi da sukai mashi ja shidai ya fice bai yi magana ba.
Ya dade zaune a gurin a karshe ya jawo wayan shi yana neman layin mommy don ita kadai ce zai tsaya yayi magana na fahinta da ita ya gane komay ke guda.
Kira biyu ta dauki wayan da sallama a bakin ta ya amsa mata tare da fadin mommy kowa na lafiya ko kwana biyu ban kira waya ba.
Tace lafiya kalau muke sai dai Alhaji ne jikin nasa ba dadi wallahi wanan matsalar tashi dai ta kwanaki ke damu shi kuma sai kuma Affan da suka kwanta asibiti amma dai yaji sauki sosai yanzu.
Wanan yarinyar takai shu,uma wallahi mommu tace wace yarinyar ke nan kuma yace da sauri No magana mukeyi a nan bayan ya gama waya da mommy sai ya kira hajiya mama.
Sun gaisa ta fara mai korafin rashin kula da kyautatawan da bai yi take mai fadan ga mahaifin shi nan ba lafiya yan uwan shi na kai da komo akan sa amma ace shi yayi biris dasu badon suraj da yazo ya kai shi asibiti ba may yake son mutane su fada a kan shi.
Hakkuri ya fara bata yana fadin in Allah ya yarda jumma,an nan mai zuwa zai shigo ya tabayi jikin Affan sai bata bashi amsa ba.
Bayan sun gama waya ya dade zaune a wurin kafin ya mike ya nufi hanyar fita office din ya rasa abinda ke yawan shagaltar dashi yanzu gamay da iyayyen shi haka.
Zuciyar shi ne tayi mashi zafi don haka ya nufi gidan shi dan ya dan sarara batare da ya sanar da kowa ba ya fice a ma,aikatar nasu sai gida.
Tun a kofa yake jin suruntun yana shiga Nafisa tana zaune a tsakiyan falon tana shan bakin shayi a dan karamin cup tana lumshe idanuwanta.
Ganin shi a wanan lokacin tayi mamakin dawowan shi gida yanzu rigar da ya barta dashi na barci ne saye a jikin ta har wanan lokacin ga su hadiye na busa shisha duk falon ya gauraye ta ko ina kamar ba falon da ya narka ma makudan kudi ba haka.
Batare da yabi ta kansu ba ya haye sama zuwa part din shi har ya kama hanyan da zai kaishi dakin shi sai kuma ya juys ya shige dakin hutun shi ya rufo kofan.
Sai da ta gama shan attayen ta ta mike zuwa wurin mijin nata ba tare da damuwa da irin shigar dake jikin ta ba bata samay shi a dakin ba don haka tasan yana dayan dakin da yakan kebe kan shi wani lokaci.
Can ta nufa duk da tasan ba lalle bane ta samu kofan a bude sai dai tayi mamakin da ta tura taji kofan a bude ta sa kai ta shiga yana kwance yayi rub da ciki a saman gado ta iso gare shi tana fadin.
Samad yau lafiya ka dawo irin wanan lokacin tana kokarin hawa saman gadon ta zauna a kusa dashi juyowa yayi yana fuskantar ta wani irin karni da bashi kanta da jikin ta ke sakewa da kyat ya daure yace banjin dadi jikina ne tace oho ba sannu ba Allah sauwaka.
Samad dama ina son in fada maka satin nan akwai bukin da zamu maradi sai kuma wayan nan kannen nawa maza da suka zo zasu koma gida.
Gashi kuma ina son ka canza min mato don wanan naje dashi har sau biyu an sani dashi sai kuma su hadiye da nake son inyi wa sayayya kafin mu tafi dakuma, , , ,
Ke enough ya ishe ni don Allah duk wanan abin a cikin sati daya kike son inyishi ko kay wai may yasa ke baki da tunane ne wai ?
Tsayawa tayi tana kallon shi galala tana mamaki yadda a dan lokaci yake son juya mata baya haka a lokaci guda tace Samad ni kake dakawa tsawa haka.
Kallon ta yayi yace an daka maki ke baki da aiki sai na abaki dai a naki ai ma yan uwanki kaza ai masu kaza sam baki damu da na wa yan uwan ba da damuwar su.
Tace amma kasan ina da yan uwa da ka aure ni ko yace wa kika fi yan uwa da bukatu ni nawa yan uwan basu son ai masu ne komay.
Tace wanan kai ya shafa matsalar kace kuma ni dai nawa yan uwan na sani kuma dole kai masu don dani sula dagora.
Mamaki da karfin halinta yaji yadda take fadin magana son ranta kai tsaye ta nuna mashi nata kawai ta sani shi yaji da nashi.
Queen matsala kinyi gaskiya yace a ranshi ya ta tunar dani wani abu mai nauyi da na manta a rayuwana shiru yayi taci gaba da masifan ta akan shi bai iya furta komai ba a lokacin.
Tashi yayi ya fada bathroom ya rufo kofan da karfi ruwa ya watsa a jikin shi yai wanka tare da yin alwala don yayi sallah la,asar don har lokaci ya dan gwauta da mintoci.
Har ya fito tana zaune a wirin inda ya barta ya dauki room fresh ya fesa a dakin don bashin da dakin ya dauka ganin zai ta da sallah ya sa ta fita daga dakin ta barshi.
Gyaran kai da jiki mukayi na zuwa gida don haka agajiye muka shigo hostel din mu maryam ta zauna dafa muna abinci ni wanka nashiga don zafi nake ji jikina ina ganin yayi min dauda.
Tsab na fito nayi sallah a wirin na jawo ledan ice cream din da maryam ta sayo muna na fara sha a hankali maryam tace wallahi ji jake kamar kada ai hutun nan da za ayi.
Da sauri na juyo ina ce mata saboda may maryam kika fadi haka tace ban son rabuwar mu wallahi yanzu ko ja koma gida banda wata abokiyar hira a kusa dani don anty na ba zama takeyi ba tana da yawan tafiye tafiye kullon don ita business woman ce .
Nace ko dai ai koya nene kyayi kewan gida mana ni banki ba yanzun haka in bude ido in gani a cikin garin minna ma.
Tace kin ji dadin ki wallahi khadija na yarda ba jin dadi bane farin ciki don ko dashi ne da bazan fadi haka ba farin ciki yana ga inda kake da sukunin aiwatar da komai.
Kafin in magana wayana yayi kara na dauka kina ina nace maynene yace ki ban amsa kada ki min halin ku na yan African don Allah .
Katambayi mutum ya mayar ma da tambaya shi kuma nace ina hostel mana yace ok kawai ya kashe wayan shi dip bin wayan nayi da kallo nace miskilin banza kawai.
Maryam ta gama abinci wanda indomei da kwai ta dafa muna wanda yaji danyen attarudu mai yaji a ciki zubawa tayi a plate guda ta dauko muna lemon kwali a cikin fridge din ta wanda muke ajewa yanzu a ciki ida mun samu.
Na fara cin abincin ke nan cibi biyu kawai nayi wayana yayi ringing na duba yaya Samad nagani a layin kamar kada in dauka dai na dauka kuma gani a kofan ku ya fada kawai.
Kofan mu na maimaita da mamaki nace may kazo yi a nan kuma ban sani ba yace idan zaki fito ki fito sai ya kashe wayan kawai.
Tsaki nayi na wurgar da wayan tare da fadin dan wahala kawai maryam dake zaune ta tsura min ido tana kallo na murmushi tayi tace.
Uhm wani lucky guy din ne yazo haka ake ja mashi aji kuma abinda wasu ke nema ido rufe a zo gurin su anzo kike wanan masifa haka ?
Nace sister kin faye bin kwakwafi wanan fa ba masoyi na bane zuwa kawai yayi ya bata min lokaci na ina zaune kalau.
Don Allah ko may ya kawo shi kije ki saurare shi ba dadi mutum yazo wurin don ka ka wullakanta shi haka muje in zaba maki kayan da zaki saka in maki rakiya.
Dole na mike muka tafi dakina ita da kanta ta zaba mi wani dogon riga mai ruwan ganye da dan karamin gyale shi sai da na shirya tsab a cikin rigan tabi jikina ta feshe da turararuka masu kamshi muka rufo kofan muka fito tare.
Yana zaune a cikin motar shi riga da wandon shadace mai guntun hannu rigar ma iya ciya dinkin yake light green kayan su matukar karban jikin shi da dinkin .
Wurin dirkekiyar motar shi da ke fake a kofan can dan nesa kadan damu muka nufa ko ganin maryam ya hana shi fada ban sani ba sai cewan da yayi.
Ita ko maryam tunane take a ranta ina tasan fuskan nan nashi ne ya katse mu da cewa kin san ina waje zaki shanyani a wanan wurin naku mai kazantar tsiya haka ?
Nayi dan dariya tare da cewa cikin wayance abinda yafa da nace ga kawata maryam tazo gaida kai don ma ita ta matsa min in fito yanzun haka.
Anyway maryam ga yayan mu Abdulsamad Abdulrahim nan ku gaisa tace dama nace kamar nasan fuskan nan ai tace ina wuni yayan mu anzo lafiya yaya iyali.
Yace lafiya kalau yaya karatu koda yake exam kukeyi yanzu ko yana wani kauda kai yana basarwa .
Tace karatu Alhamdullahi mun kusa cin ma karshen shi da yardan Allah ai a huta gajiya dama nace barin zo mu gaisa ne kawai yace to na gode kwarai da alama kin fi kawar taki kirki sosai.
Dariya tayi tace a a wallahi ai kirkin khadija na daban ne wallahi tana da kiki matuka shiyasa ma nake jin dadin zama da ita wallahi.
Baki ya tabe ta juya ta tafi tana mashi a huta gajiya ta nufi hanyan shiga hostel din namu sai lokacin na sauke ajiyan zuciya bayan tafiyan ta.
Katse ni yayi da fadin tsaye zaki min sai kace wanda tazo tadi da buduruwar shi haka bude kofan motar shi yayi na zagaya na shiga sai naji ya rufe motar.
Shiru daga ni harshi ba wanda ya iya magana a lokacin sai ma gyara kwanciya yayi a motar bansan lokacin da nace dashi baka da lafiya ne Yaya Samad.
Shiru yayi kamar baiji ni ba sai can yace may kika gani a tare da ni nace yau na ganka so weak ne ba miskilancin nan naka yasa na gane bakajin dadi ko baka cikin good mode.
Wai ke aljana ce ko may dazun kin fada min magana akan ahalina ya zama gaskiya yanzu kuma waya fada maki banjin dadin jikina ?
Nace yanayin ka ya nuna min haka sai ya dago da sauri ya na kallo na nima kallon shi nake yi sai dai ba zan iya jimirin kallon nashi ba a lokacin saboda kwarjin shi da ya cika min fuska a lokaci daya dukar da kaina nayi kasa ina wasa da yan tsun hannu na.
Yau ina bakin naki ya shiga nace ko don Yusuf ne dama kike da bakin a gaban shi nace da sauri ko daya wallahi gani nayi yau kana bukatan kulawa don baka cikin hayacin ka sosai.
Don jikina ya bani baka da lafiya sai naga ya koma ya kwanta kamar yadda yake da farko ya fadi a kasalance cewa kaina kamar zai rabe biyu nake jin shi khadija.
Kasha magani na tambaye shi da sauri yace ban sha ba wani magani kake sha yace panadol extra nakan sha wani lokaci.
Wayana na fara dannawa ina neman layin maryam ta dauka nace fito min da panadol extra din nan da goran ruwa don Allah yaya Samad bai jin dadin jikin shi tace to da sauri na kashe wayan.
Motar shiru ba a dauki lokaci ba sai ga maryam ta iso da maganin ta kwankwasa glass din motar ya bude mata karba nayi ina mata godiya tace babu komai mana Allah ya bashi lafiya.
Maida marfin motar nayi na rufe na fara kokarin bare mashi maganin tare da bude goran ruwan nace mai gashi ka sha.
Ya dago kanshi da kyat ya kalleni ya kalli maganin da ruwan da nake mika mai sai naga ya bude min bakin shi alaman in bashi da kaina .
Dan rankwafawa nayi ina saka mashi maganin a baki na kawo goran ruwan na bashi ya hadiye da kyat yana wani lumshe idonun shi yana bata fuska.
Komawa yayi ya kwanta tare da fadin thanks nace Allah ya baka lafiya amin yace da kyat ni dai komawa nayi na zauna na zuba mai ido.
Wasu irin jijiyoyi naga sun fito rada rada saman goshin nashi wanda ban taba kula ko yana dasu bane dama tsoro ne ya kamani kada wani abu yazo ya samay shi fa a nan wurina nawa ya samay ni kuma.
Shiru daga ni har shi ba wanda yayi magana a cikin mu har mintina na shudewa a hakan suna batun zama awa daya muna nan a hakan dashi kamar mai barci.
Abu daya ne yasa hankalina dan kwantawa ganin yana numfashin shi normal a lokacin yasa nayi shiru tare da zuba mashi ido kawai ina kallon ikon Allah.
Wayan shi dake aje a motan ne ke ringing ganin anata kira bai dauka ba yasa na daga kiran don ba suna batare da na saurari mai magana ba nace mai wayan bai da lafiya please.
Naji muryan mace tana fadin ke wacece da sauri ya dago ya kwace wayan a hannu na ya katse kiran yace akan may zaki daga min waya waya baki wanan damar da ikon daga min kira a wayana.
Zanyi magana yace get out tunda ka samu lafiya yanzu zaka iya ci min mutunci sai dai ka sani ba zan ce ma komai a yanzu ba don yanayin da kake ciki na bukatan natsuwa.
Get out i said na bude motar na fita ba tare da na juya na kalle shi ba naji ya tayar da motar ya jata da karfi yabar gurin nashige ciki abina.
Dakina na shiga na wurgar da sauran maganin saman katifana na fara kokarin cire kaya a jikina sai ga maryam ta shigo tace ashe kin dawo.
Eh ya tafi ya samu lafiya ai nace mata ina daura zanin a jikina na nike kayan na za saman jakkunan kayana dake gefe daya a dakin.
Shiko tunda ya kama hanya yake jin wani bacin rai da bakin ciki a ranshi yana fadin wanan aljanan yarinyar sai ta kasheni wata rana.
Yarinya yanzu ta sauke min bacin raina yanzu kuma ta kara sakani a wani anya ma mutnce kuwa dai , ?
Yana shiga gidan a hargitse ya samay su duk kan su Nafisa ta haukace masu daga ita sai dan buje a jikin ta tana fadin yaushe samad ya fara cin amana na haka ?
Yaushe samad ya canza ban sani ba nayi sakaci da yawa har na bari haka ya faru a yau da ban dauki mataki ba.
Haka ya shigo ya samay ta tana wanan sambatun a cikin yan uwanta da suke ririke da ita kamar sabuwar mahaukaciya.
Nan ya shigo baice da kowa kalaba cikin fushi ya shigo gidan don haka basu ga fuskan wani magana a gareshi ba.
Tayo cikin shi da zagi tana fadin macuci mayaudari sai Allah ya isar min a gare ka har zaka dauki waya kabawa wata mace ta fada min wai baka da lafiya a wurin ta.
Da karfi ya banbare hannun ta da ta rike mai wuyan rigar jikin shi ya fisge ya shige dakin shi a hasale.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Maryam kamar jirana take in gama debe kayan a jikina ina zama tace amma friend zurinfin cikin ki yayi maki yawa wallahi.
Ashe wanan guy din da ake nema ruwa a jallo dan uwan ki ne ban sani ba saurin kallon Maryam nayi nace ruwa a jallo ake nemas may yayi.
Tace tsadan ganin gare shi mana gashi dai matashi ne amma Allah ya kai shi ga babban matsayi nace wani matsayi ne gare shi wanda kike zuzutawa haka wai ?
Kai haba friend zakice baki san koshi waye ba kina tare dashi haka mutumin nan fa na hango tsatsan son ki a kwayar idon shi.
Nace baki hango gaskiya ba idon ki bai hango maki gaskiyan alamarin ba kuma koda kin hango ma bai taba zama gaskiyan magana.
Mutumin da gidan shi yafi karfin shi a karskashin mulkin ki mace yake wanda baida mutucin duban yan uwan shi tunda na fara magana ta kafe ni da idanuwan ta.
Shiru nayi don na farga na fara sakin layi dariya tayi tace min kin dakata kuma mana nace barni da abin haushi don Allah kwantawa nayi rigingine ina tune a raina sai kuma na bushe da dariya ni kadai.
Kallo na tayi tana mamakin abinda nakewa dariya haka ni kadai nace yau akwai bura uba a gida Samad tace akan may kuma nace ke dai bari.
Buzuwar matarshi ta bugo waya tana tambayan shi na dauki wayan nace mata gashi nan wuri na baida lafiya.
Ido ta zaro waje tace kika amsa kiran matar tashi khadija nace kwarai kuwa ina dariya nace zata gane shayi ruwa ne maryam.
Ba gani take ta mallake shi ba ba macen da ta isa tazo kusa da shi hatta uwar shi ta raba shi dasu duk yan uwa ganin su take muggaine bata yarda dasu ba.
Kirikiri ta hana matar shi zama a dakin ta dole yanzu saida ta koma gida take zaune ba ruwan shi da yaran da ya haifa da cikin shi.
Tace khadija kina nufin wanan guy din yana da iyali haka dama idan ka ganshi sai ka dauka ko auren farko baiyi ba a rayuwan shi.
Nace wa mai iyali ne da kike ganin shi wurin nan auren gata ya samu ga iyayyen su shine kuma bai iya riko ba saboda buzuwar matar shi.
Nace Wasa farin girki yanzu muka fara wasan da ita sai na manna mata karamin hauka a zuciyar ta tunda tace bata son hurdan shi da ko wace mace.
Haduwa goma zamuyi dashi sako goma zan tura mata muje zuwa indai nice ko wace mace da dabaranta ake haihuwan ta sai dai na wata yafi na wata kissan.
Khadija kin ko san kisan macen buzuwa macen buzuwa fa duk inda take shu,uma ce bata bari miji ya zauna da matar shi lafiya sai ita.
Nace maryam kin san ko matan minna ko waye su ba buzuwa ba ko tsakiyan matan maradi za a kaini na shirya mata indai akwai ayar Allah.
Zan bi dare in bi rana sai na nuna mata muma matan Nigeria akwai shu,umai cikin mu ai banda matsala tunda na san lagonta ta .
Allah ya bamu saa tace nace amin sai na girgiza kai nace bawai da manufar yaso ni har cikin ranshi nake wanan abin ba yi dai nake in nuna mata boka da malam karya ne.
Tace yanzu yaya kuka kare dashi nace korata yayi daga motar shi kai tsaye dariya ta kwashe dashi tace ai ba zaki kara ganin shi ba ko.
Nace gobe ma yayi nesa ki gan shi nan ai ni abin har mamaki nake ji wallahi tace don dai kince buzuwa ce matar shi amma da sai in ce wani namiji zai samay ki ya bari ki kufce mashi khadija.
Kyau Allah ya baki tsayi da gashi ga ilimi addini dana boko kin tara ranan da naji kina karatu wallahi har rudewa nayi na raya a raina da naje gida komawa zanyi makaranta ni ma na samu in sauke.
Tun ina karama fa na sauke maryam yanzun haka ban bar karatu ba don ina nan ne bana zuwa amma a gida ban wasa da karatu ko kadan kinga yayata malama ce sosai wallahi.
Tace ai naga alama tun haduwa na dake idan kuna waya da ita zata tana makaranta ko gata tana shiri fita makaranta may yafi wanan dadi ga mace.
Nace kinga mu zama yakawo kakannin mu zama garin minna amma aslin mu yan wani gari ne da ake kira ka,oje tun ana hade da sokoto da Niger yanzun haka mu bamu san gida ba mu filani ne na asali wallahi.
Mahaifiyar mu ce kwarin minna amma saboda zama muka juye muka zama mutanen minna baki sanin mu baki ne idan ba mun fada ma ba.
Haba nature din ki yayi kama sosai da na fulani ashe ma ke ruwan su ne nace ada ke nan ina so zuwa garin mu sosai inga yan uwana wallahi.
Don ance har yanzu yan uwan mu suna garin don daddy din mu shi yasan gari har yakan je lokacin da bai tara iyali haka ba.
Tace ya kamata ku nemi gida su san ku fa nace muna da burin haka nida ya Amina ai sai dai kin san abin sai an shirya ne .
Dakin shi ya nufa ya fara cire kayan shi zuciyar shi yana mai soya yana jin kamar ya ganin a gaban shi ya shake ni don haushi da takaicina da yake ji.
Nafisa ce tazo dakin har lokacin a hasale take daidai ya fito daga wanka ta yi mai wani mugun kallo tace yau sai ka fada min gurin wace kaje har ta dauki wayan ka ta kirani dashi.
Baiyi magana ba sai kokarin saka jallabiyan da yake yi a jikin shi ta karaso tana ce mai wata yar iska yar kasada ke son shiga rayuwan ka Samad ?
Ido kawai ya tsura mata yana kallon ta batare da yayi mata magana ba ta sake maimaita tambayan shi samad ka fada min wa cece kaje wurin ta har ta dauki wayan ka ?
Ta karaso tana rike mai kwalar dogon rigan da ya a jikin shi yanzu kama hannuwan nata yayi ya murde ya wurgata saman goda ya nufi inda turaren shi suke ya dauko yana fesawa jikin shi.
Ta kara juyowa ta nufo shi a hasale tana cewa kunji kun gama iskancin ku shine ka dawo gidana kana min wankan tsarki anan.
Da mamaki yake kallon ta ya bude baki da kyar yace Nafisa yau ni kike wa zargin aikata zina da wata kace tace dole in maka samad may ye hadin ka da wata mace , ?
Yace dani mazanaci da akan ki zan fara tunda dashi kika gabatar min da soyayyan ki farkon haduwan mu dake.
Haushin maganan shi taji sai ko ta haushi da duka da yakusa tana ture shi tsayawa yayi yana kallon ta da mamaki.
Jayeta ya kara yi ya hakadata gefe ya fice daga dakin ta biyo shi tana zagi ta uwa ta uba ya shige dayan dakin ya kyale ta.
Yana shiga wayan shi na kara ya dauka Yusuf ne yake son fada mashi ya gama tsara masu tafiyan da zasuyi kaduna.
Yace sai dai abinda zamu saya wa yaran nake son mu dauko khadija ta zaba muna abinda ya dace dasu tunda mu ba zaben kayan yara muka iya ba.
Yusuf ya ambaci sunan shi a kasalance Yusuf din ya amsa mai yace don Allah ka rabani da wanan yarinyar dake batun tarwatsa min gida da rayuwa na.
Cikin mamaki Yusuf din yace tayi ma wani abune kuma ban sani ba yace may ne ma batai min ba yanzun haka in ka saurara zaka iya jiyo hargowan Nafisa akan khadija.
Da sauri Yusuf din yace dashi kai haba sun hadu ne komai ko ta samu labarin khadija din ne yace basu hadu ba sai dai yau kaddara ya hadasu a wayana.
Nan ya koro mai abinda ya faru yau din dariya sosai Yusuf ya kwashe dashi lokaci guda yace kai khadija akwai jan magana da rashin tsoro.
Yace ni yau taja min masifa da fushin Nafisa a gidan nan ban son wanan bakin kishin na Nafisa wallahi idan ya tashi bataji bata gani imagine wai har ni Nafisa ke ma zargin zina yau.
Intrested ashe yau tasan zaka iya kara aure ko wani lokaci ke nan wow i am impress da jin wanan labarin Allah yasa haka yasa ta fara gyara halin ta.
Rikici kake son jawo min Yusuf da ka hada ni wanan aljanan yarinyar mai shegen rigima wai dole sai itace zatai min wanan aikin ne ?
Kana son mu canza wata ce ya tambaya shi a cikin gatse yace No da sauri yace ta faye matsala ne wallahi.
Yace da matsalan nata za a gyara komai kai dai ka kara hakuri don Allah yace wallahi yarinyar ta fara shiga raina amma kuma ta faye matsala ne ai.
Yanzu yaya zan iya shawo kan Nafisa a gidan nan gaba daya ta birkice min yau kan kishin wace ma bata sani ba har da duka na fa takeyi.
Duka kuma subbahanallahi kai kuma sai kai tsaye tana dukan ka ko mai yace to may zan mata Yusuf kit Yusuf din ya kashe waya alaman yaji haushin maganan abokin nashi.
Dariya ya soma yi bayan ya kashe ma Samad waya yace komai na zuwa yadda nake so da alama samad ya fara son khadija.
Wayana ya kira bayan mun gaisa yake tambayana ashe yau mutumin yazo gurin ki shi kadai nace eh dan matsalan yazo min wai bashi da lafiya.
Sai bayan na taimaka mai da magani yaji sauki ya soma karanta min haukan shi wai na fita mai a motar shi tunbai balbalani ba.
Dariya yayi yace may ya hada ku har haka nace bakin rigima na yasani daukar mai wayan matarshi da take neman shi ganin kamar barci yake wayan nata ruri nikuma sai na dauka.
Dariya yayi sosai a lokacin yace aiko nasan yau suna can suna tafka fitina a tsakanin su kin ja mashi aiki yau
Nace shi ta sha matsoracin namiji kawai wanan ma ko ga maza yan uwan shi nasan matsoracine wallahi dariya Yusuf yayi sosai.
Yace to yanzu na kiraki ne don Allah gobe indan kina free zaki taimaka muna da sayen kayan yaran samad don Friday zamu shiga kaduna insha Allahu.
Nace idan dashi ne gaskiya ba zan tafi ba yace saboda may khadija kefa kika kawo wanan idea din zaki ce kuma bazaki tafi ba.
Ki daure ki karasa ladan ki don Allah ai ba don shi zakiyi ba yaran fa kika dauki alkawarin taimakawa saboda Allah shiru nayi yace may kikace nace a hankali naji sai dai idan ya wuce gobe ba zan samu fita ba don ina da exam talata kuma zan wuce gida.
Yace nagode khadija Allah ya biyaki da alherin sa yadda kike muna Allah ne kadai zai saka miki sai mun hadu goben zamuyi magana Allah ya kai mu nace dashi.
Na kwanta cike da tunane a raina wai dama da gaske akwai mazan da suke irin wanan rayuwan a gidajen su don dai ni nasan mahaifin mu zaki ne a gidan shi akan iyalin shi.
Wai duk gidajen masu kudi haka yake ne rayuwan su sai mata ke juya su yadda suka ga dama idan ka gansu awaje sai kai masu kallon isa da izza amma a gidajen su sai ka raina su.
Yaya matashi kamar Samad zai zauna mace tana juya shi haka yadda take so wai kuma yana sunan miji a gidan shi gashi da ilimi daya dace yayi amfani dashi ako ina ya kama amma mace ta na juya shi son ranta.
Kwafa nayi nace wallahi gobe zasu ga tsiya don sayayya zanyi masu kamar na hauka inta gani ta haukace da tushe.
Washe gari nace ma maryam ta shirya zamu fita da su yaya Samad zasu zo mu muyi wa iyalin shi sayayya tace tau da murnan ta.
Mun shirya tsab don Yusuf ya bugo min waya suna kan hanya zuwa wani dan abu ne ya tsayar dasu yanzu.
Sun iso wayan Yusuf ya shigo min gasu a kofan mu nace gamu tafe yace keda wa khadija nace da kawata maryam zata tayani zaben kayan ne sai kun fito yace min.
Mun fito daga gidan kwanan namu na dalibai muka hango su can nesa kadan inda suka aje motar su muka karaso wurin .
Motar Yusuf ya fito ya bude muna muka shiga ya rufe sai da muka zauna muka fara gaida su wanda nidai kusan Yusuf kawai na gayar maryam ne tace da Samad yaya jikin shi yace cikin daga hannu da sauki.
Sai looacin ciwon kan da yazo dashi jiya ya fado mashi a rai don fitinan da suka kwana sunayi da Nafisa yasa ya manta da komai nashi.
Kawar ki bata magana ne Yusuf ya kawar dashirun da motar yayi a lokacin maryam ne ta bashi amsa da fadin ai itace dai magana ya zama aiki a gare ta nikan ko aku ya ganeni ya kauce min wurin zuba.
Ashe kuna da aiki shi yasa abin yazo maku daidai naji mamakin da kika iya zama da wanan mai zubin yan ruwan dariya ta danyi tana cewa ashe kaima kyaunta na ruda ka haka.
Haka take ruda maza a cikin makarantar dama wajen makarantar amma kunsan may wai duk wanan bata ga may mata ba har yanzu ga kyau yana tafiya a banza a gurin maza.
Tsuki yaja tare da juyowa ya dan watsa mata harara lokacin da take fadin ni wallahi ina son ganin lucky man din zai iya sace zuciyar wanan yar kwalisan yarinyar.
Zaki ko sha zaman jira don maza basu son zuben mace irin wanan da ko ina tabi surar ta na rawa sun fi son mace mai natsuwa da kamala.
Yusuf yace har kin sa yau na fahinci wani abu da kika kawo wanan maganan haka nayi real sign ba karamin kyau ki ga khadija ba da har na kasa fahintar abinda yasa abokina yake yawan rudewa idan ya hadu da khadija ashe kyawon tane yake yawan tsorata shi yana mata kallo mai kama da tsoro but still yanzu da yai maganan nan sai na gane kyauta ne yake yawan ruda shi.
Da na dan shiga rudanin wanan abin amma yanzu maganan nan da kikayi yasani a hanya watau a takaice aboki na yana rudewa idan yaga khadija sai take mashi zubin yan ruwa idan ya kalle ta.
Tayi saurin fadin ya gano sirin da Allah ya boye ne anan ai khadija matar manya ce wallahi duk namijin da yai saa ta kalleshi da manyan idanun nan nata yakan shiga rudu ne ya rasa inda yake ina ga shiya take tsoron fita wallahi.
Don Allah malam idan kun gama kaja mota kakai mu inda zamu ko ka mayar damu inda ka dauko mu zaifi ya fada batare da ya juyo gare shi ba
Yi hakkuri malam abinda na gani na fada yasin khadija ta hadu ba karya a gurin nan kai mai dani inda ka dauko ni ya fada a dake.
Nidai nayi kamar badani suke yi ba kaina yana duke ina danna wayana dake hannu na muna charting da zarah.
Yusuf yace karkai fushi dani abokina gaskiya muka fada anan take a deep breath and confess khadija ta fi matan da kake gani haduwa.
Bude baki yayi ya zaro ido yana kallon yusuf da mamaki kalaman shi dayaji na bazata yasan Yusuf ne kadai duk duniya yake iya fahintar shi lokaci daya.
Yusuf ya sake kallo shi ya dan lagabe kai tare da girgiza mashi kai yace dont give me that look just say yes to your mind she is realy beautiful as you see.
Take ya daure fuskan shi tamau tankar bai taba dariya ba yace Yusuf kayi kuskuren furtan hakan a gare ni don kafi kowa sanin banda lokacin yin hakan .
Nace kunyi babban kuskure Yusuf da kuke son kamanta da wanan mutum matsoraci ko kuna zaton sakewan da nayi daku kun dauke shi da wani manufane ?
Ba so ko wani abu makamancin haka cikin zuciyana don ban taba daukan haka ba a tsakanina dakai sai mutunci da niyar taimakon ka a zuciyata don rayuwan ka na bukatan taimako da agaji ga wanda yasan shi.
Tsakanina daku kuma sai dangantarkar irin na zumunci na an fito wuri daya da biye min da kukeyi da kyautatawa .
Da ka sani da baka dauki haka ba da zafi don zuciyar ka ta baka ba daidai ba me yasa zakayi zaton soyayye zai yuyu a tsakanin mu don kana kyakyawa mai kudi maiji da ilimi da wayewa ko may ?
To ni duk wanan nasaban naka baya burge ni don ni ina fatan samun miji ne wanda yasan kanshi yake iya mulkata ba in mulkeshi ba ko wata tana mulkanshi.
Barin fada maka ban taba jin son ka wallahi a raina don halinka bai mun ba bai kuma taba burgeni ba tausayi ne da fatan alheri ka shirya da iyayyen ka takowani hali .
Don halinka da dabiar ka yanayin rayuwan da ka shiga da komai naka yana bukatan gyara a yanzu.
Ya isa yace da karfi ya fada cikin kuna rai, yayin da maryam tunda na fara magana take rufe min baki waina bar maganan .
Idon shi yayi mai jawur hankalin shi yana neman barin jikin shi zuciyar shi yana son tarwatse mai yace ba laifin ki ba ne.
Yaja wani irin huci ya furzar a bakin shi yace Yusuf ka juya mu sauke su inda ka dauko su don Allah.
Bana son inkara ganin fuskan yarinyar nan na tsane ta wallahi bana son kara haduwa da ita a rayuwa na .
Shiko Yusuf a ranshi ya gigice da fadan mu sosai yana rayawa yaushe ne zai samu cin ma manufar shi a kan mu yaushe zasu bar wanan halin may yasa Samad ke biye mata suna haka kamar wasu yara kanana.
Ya zama mai dole ya shiri mu tun yanzu tun kan mu rabu a hakan ba wani ci gaba gashi ya fara ganin hasken alamarin tun ba a je ko ina ba.
Ya zama dole ya gyara wanan abin tun anan don ba zai yarda abokin nashi yaci gaba da zama haka ba yanzu in ya bari muka watse a hakan abin bayi ba wallahi.
Naji Yusuf din yace Khadija ba nufin abokina ke nan ba baki fahince shi bane tun farko kin san tun jiya fa yana da haushin ki a ranshi don haka don Allah bashi hakkuri ya huce dake haka please.
Yadan juyo yana kashe min ido sai na gane manufarshi da sauri sai da na hade wani bakin ciki na iya furta to kayi hakkuri don Allah ban fahince ka bane na fada a sanyaye.
Da kyau Khadija matar na tuba ko bata laifi komai rintsi ya juya gurin shi yace kayi tsamanin jin hakan daga bakin ta yanzu a yadda tahau din nan.
Wani iri yaji yace a ranshi may yasa na kasa fahintar wanan yarinyar ne wai me yasa na fadi wanan maganganun masu zafi gareta yanzu bayan nasan gaskiya Yusuf suka fada.
Halinta daban ne da na sauran matan dake bina suna ribibin in so su kai tsaye zata iya fada ma gaskiya batare da tsoron komai ba kuma ya amfane ka.
A sanyaye yace Yusuf ban san may yasa take son bata min rai ko da yaushe muka hadu ba zan bata dama taci gaba da min yadda take so ko yaushe.
Motar ta tsaya a bakin wani plaza babba ba wanda yayi magana Yusuf ne yace bissimila mun iso mu shiga mu fito tukun.
Fita mukayi a motan har lokacin jikina a sanyaye nake jin shi don abinda ya faru a motan Yusuf ne yazo daidai inda nake yace khadija na gode da kika fahince ni ba komai nace dashi cikin yake.
Muna shiga shi yana bayan mu yana tako a cikin izza da kamala maryam tazo daidai kunne na tace dan dakata mai ku jera mana.
Hara na aika mata nace sai dai ya mutu idan sai na jera dashi din ya dai ci albarkacin Yusuf da kuma na iyayye wallahi.
Ban garen kayan yara muka nufa inda maryam ta fara duba kayan ina tayata har lokacin ban sake ba nan muka shiga jidan ma yaran kayan sawa da sauran abubwan yara.
Mu koma bangaren takalma da dasu sauran abin bukatan yara harda su tawul da sabule da su kulan zuwa school muka hado dashi a hankali na taka wurin kayan mata na zaba ma anty fati kusan kala goma masu kyau da tsada.
Su dai ido kawai suka saka min har lokacin da muka gama Yusuf yace mu zabi abinda muke so ni wani jakka da takalma kawai na dauka maryam kuma ta dauki wani dogon riga da jakka.
Munje gun biya muka da ja baya naga ya ciro katin shi na bakin ya basu suka debe kudin su suka miko mai mun shiga motar mun zauna.
Yace kina ganin mun sai komai da zasu buta nace insha Allahu har maman su ma da sauri ya juyo yadan kalle ni kamzaiyi magana sai kuma ya fasa yusuf yaja motan muka tafi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Hutun sati uku kacal muka samu wanan karshen zangon don haka naji dadi sosai da bai kasance dogon hutu bane don zan samu zama a minna tare da iyayyena in yi hutu.
Wanda rabo da in samu kasancewa dasu haka a wadace har na manta yanzun haka na fito daga zana jerabawan karshe na wanan zangon da mukayi da yazo min da rikicin haduwa da Abdulsamad da abokin shi Yusuf.
Ba ranan zan tafi ba sai washe gari don haka maryam ta tsaya jirana don taso muje gidan yayar ta na nuna mata ban son zuwa can din.
Komai na gama shiryawa a dakin sai kayan da zan saka ne da katifa ban samu daga wa sama ba don kwantawa da zanyi na yau kawai da safe in dage shi sama in tafi gida.
Bayan mun rabu dasu yusuf ya kirani yana tanbaya na ya muka isa hostel din mu tare da kara yi min godiya .
Bayan mun kashe wayan gidan Abdulsamad suka nufa sun kusa shiga gidan ne Abdulsamad din yace dashi idan sun tafi kada a sauke kaya da aka sayo a gidan shi abar kayan acikin mota kawai idan sun isa Yusuf yagane manufan shi na fadin haka.
Sai dai bai ma abokin nashi magana ba gamay da abinda ya fahinta na son kada a sauke kayan dayace kada ayi har lokacin gidan ba dadi tsakanin su da Nafisa.
Wanka ya fito yana goge ruwa akanshi ta shigo dakin har lokacin tana nan cikin fushinta da shi zuwa tayi tambayan shi kudin da tayi requesting wana zata yi tafiya zuwa gida.
Tace Samad kwanaki na ta matsowa har yanzu bakai magana kan abinda na bukaci ka bani ba wanda zan je gida dashi indan zan tafi sai in wuce dashi.
Yadda take magana bai sa ya daga kai ya kalle ta ba Samad dakai fa nake magana ya dan wuce ta zuwa bakin gado ya zauna .
Ta juyo gareshi tace magana fa nakeyi maka kana ji kuma ta fadi a hasale sai lokacin ya dago yace kada ki kara yi min maganan nan.
Don bashi ke gaba na ba gobe kaduna zan tafi in daba iyayye da iyali na wani irin gumzi tayi tayo kan shi tana fadin wallahi baka isa ba.
Ba kuma inda zaka kaje na fada ma don baka fada min zancen tafiya ka ba don haka ban shirya ma tafiyan ka yanzu.
Murmushi yayi yace kice ma mai shirya min tafiyan don kece zaki sallamay ke nan ko ?
May kake nufi da wanan maganan haka ban ci na sani bane idan za kai tafiya yanzu koma ko da da kake fada min ni nake sa ka fada min .
Yace shine kuskuren da na aikata a baya yanzun kuma a shirye nake da na gyara komai da ya faru ido ta zuba mai cikin firgici take.
Ganin zata damay shi yasa ya fice ya bar mata dakin don da dakin yaso ya gyara kafin ya kwanta don ya kwana biyu ba samu tsayawa ya gyara ba.
Don yanzu gyaran dakin kwanan nashi ya dawo kan shi saboda indan yan uwan nata sun mashi gyara sai abubuwan da dama suyi ta bacewa a dakin.
Wanan yasa ya daina bari su shiga mai daki suyi mashi gyara sai shi ya ke gyaran dakin nashi da kanshi ya don yafi mai sauki idan bai gyara ba ita bata da lokacin gyaran .
Haka kuma zata shigo ta kwanta a cikin dakin ba kunya ba tsoron Allah haka dai ake rayuwan a dunkule ba wani jin dadin irin na aure tsakanin mata da miji.
Laptop din shi ya dauko ya na dubawa sai dai tunane ya hana shi yin wani aiki a ciki bakomai yake tunane ba sai irin maganan da nake fada mai, mai kama da shagube yana jin haushi na ashe gaskiya nake fada mashi.
Yaushe rabon shi da yaran shi suzo kusa dashi su zauna a matsayin shi na mahaifin su suji dadi babu.
Ya tanbatar da ya tafka babban kuskure da Allah zai iya kama shi da laifin da ba zai iya amsawa ba gobe kiyama.
Khadija khadija ya furta a hankali kin taimake kin ceci rayuwana ta yadda ban taba zato ba wanan wace irin yarinya ce mai hikimà da basira.
Ya dade a wurin zaune har ya kai kwance sai da wayan shi yayi ringing ya daga wani yaron shi na wurin aiki ke gaya mai an samu wasu filaye ns gwaunati a gwagwalada da wasu mutane ke son ci.
Yace da yaron nashi ya bari sai next week za a duba case din idan Allah ya kaimu sun gama waya kiran Yusuf ya sake shigo mai inda yake fada mai gashi a kofan gidan shi sin dawo da motaci an gama duba su .
Yace gaya nan fito mikewa yayi ya zura santala santalan kafan shi cikin wasu budaddun takalma ya sauko zuwa kasa inda ya samu falon cike da yan uwan Nafisa kamar suna shawara.
Ganin yadda ya fito yasa ta dago kai tana kallon shi ya fito ya samu Yusuf din zaune a saman dan wani dakali yana jiran fitowan shi.
Ya fito ya fara mai baiyanin komai basuyi aune ba sai ganin Nafisa sukayi a gaban su tana huci ba bata lokaci ta shiga dura ma Yusuf din zagi tana ai banta shi.
Bai tanka ta ba sai faman kururuwa take masu a kai tana kiran da munafuki dan bakin ciki ko bai so sai ya gansu da Samad agidan shi.
Dama tasan duk wani munafuncin da ga wurin shi yake fitowa daga shi har samad din sai ta dauki mataki a kansu.
Amma dai karki manta bakece Allah ba ko don haka babu wani abin da zaki iya muna sai Allah don in da sabo ya saba da wanan halin na Nafisa.
Sau da yawa idan sun kwaso rikici da mijin ta a kanshi take saukewa don tana ganin shine mai zuga shi sai taga ta kamo shi da kyau dan lokaci kadan kuma sai abin ya juye mata.
Wanda take ganin Yusuf din ne ke mata zagon kasa a hakan sai dai bai nasaran rabata da Yusuf din da yake son yi ko yaushe.
Da kyat yan uwanta suka samu takoma ciki bayan sun kare masu kallon banza suka shige da ita cikin gida tana ta haure hauren rashin mutunci.
Washe gari tun da safe ya shirya Yusuf yazo zasu tafi kamar yadda ya saba motoci uku zasuyi tafiyan da shi sai dai wanan karon tafiyan ya canza masu sallo.
Na farko su kadai ne ba tare da buzuwa ba na biyu kuma tare da a abin arzikin da bai saba tafiya dashi ba zasu dunfari gidan.
Ana kara gyara kaya kamar daga sama sai ganin ta sukayi a wurin motacin tana ganin kayan ta shiga tonawa har ta gano abinda ke cikin buhuhunan da akayi siling din su din.
Ranan sun ga masifa haka sukaja mota suka tafi ransu bace da halin da Nafisa ta nuna masu din sun isa a cikin lokaci gari bai je gidan ba sai da ya karasa gidan shi ya huta don sun iso kan shi yana mashi ciwo sosai saboda hayaniyar da baiso.
Tunda Yusuf ya sauke shi yanufo gidan nasu da abinda suka zo inda sai gani motane keyi anata shiga da kaya a cikin gidan ana jibgeasu a kofan hajiya mama kamar yadda ya umurce shi da yi.
Sun kasa boye mamakin su anty amarya ce ta fara tambaya anya wanan abin da Nafisa ko aka zo wanan karon dariya Yusuf yayi yace bada ita bace anty muka dai muka zo.
Mommu tace abin kan da mamaki gaskiya Allah yasa babangida ya canza daga wanan karon dariya Yusuf yayi yace insha Allahu mommy kudai taya mu da addua.
Ya shiga dakin hajiya mama don ya gai da ita ya samay ta da yan matan ta suna mamakin wanan sayyayan da suka gani haka wai daga gun Abdulsamad ya fito haka ?
Ya shiga dakin sai da ya zube kasa ya fara gaida ita sai faman murmushi take yi har lokacin ta kasa boye mamakin ta bayan sun gama gaisawa dakin take tambayan shi wanan sauyin yanan Abdul din data gani.
Yace hajiya adai taya mu da addua kusan kece sillar canzawan nan nashi lokacin fada maki komai baiyi ba amma nan gaba insha Allahu zan sanar dake komai so nake komai ya tafi haka yadda muke so dashi .
Don yanzu insha Allahu akwai canji sosai wallahi nan dai suka dan taba hira yace Abdulsamad na tafe zamuyi bayananin komai idan ya shigo.
Duk da zaman lafiyan da akeyi gidan bai hana a kebe gefe ba ana gulman wanan sabon yanayin da aka hango a gare shi.
Sai dai kowa ya matsu yaga abinda ke cikin buhuhunan wanda ba wanda ya iya gane komau ye a cikin su su indan gaiyan aikin nasu ya shigo.
Saida suka sauko sallah jumma a ya shiga gidan iyayyen nashi a falon Alhajin su ya fara shiga ya gaida shi da mashi yaya jiki ranan yaga sauyi sosai na sakin fuska a wurin mahaifin nashi wanda ya dade bai gani ba.
Bayan sun gama da mahaifin nashi ne ya shiga ciki ya fara gaida ummi sai mommy sai anty amarya ya wuce dakin hajiya mama wanda dama kullun itace karshen shiga da yafito kuma sai ya bar gidan.
Sun gaisa da ita acikin sakin fuska ya dubi Affan dake zaune gefenta yana cin abinci ya kira yaron saboda rashin sabon da basuyi ba dashi ya dago ya kalle shi kawai ya gaida shi.
Sai baiji dadin yadda yaron yayi mashi ba shiru ya dan biyo dakin take tambayan shi iyali ya amsa da duk sina lafiya hajiya tace dole ita da yan uwanta zamu tambaye ka don sune yanzu iyalin naka.
Babangida yanzu kana ganin abinda kakeyi kana aikata daidai a rayuwanka mutum ya watsar da iyalin shi ya rugumi wasu bare can.
Shiru yayi ya dukar da kanshi tace kaima kanka fada kada ka mutu a cikin wanan halin kasan Allah na zai barka ba Yusuf ne yace ayi hakkuri hajiya komai zai zo daidai in Allah ya yarda adai tayamu da addua.
Nan ya fara mata bayanin kayan da suka zo dashi inda ta fahinci komai yace saura kayan abinci muyi magana ko za a kawo zuwa yamma sai a raba yadda ya kamata.
Yayi mamakin yadda yaji mahaifiyar tashi tana kwararo mashi addua yau da saka mashi albarka wanda ya dade baiji ba daga gare ta duk zuwan da yake yi da fada sukan kare ya fita rai a bace.
Yau sai gashi sanadin yarinyar da yake gani mai matsala a gare shi yaja mai samun addua irin haka a gurin mahaifan shi bai fita gidan ba sai da yayi masu alheri yakuma mata alkawari zai je zaria yayi masu taaziyan rashin da akayi can.
Taji dadin jin hakan sosai na ya fito ya barsu a cikin farin ciki ya koma gidan shi don yana bukatan hutu a lokacin bayan fitar shine hajiya ta kira su mommy tana masu bayani aka shiga bude kayan da ta nuna masu din.
Kowa yayi mamakin ganin hakan don basu zaci haka ba yanzu a gare shi sai addua suke mashi da fatan gamawa lafiya kowa aka cire mai nasa cikin farin ciki da jin dadi.
Tunda ya koma wake kwance a dakin shi na gidan ba abinda yake tunane sai irin yadda na fada mai magana mai amfani acikin gatse kuma yayi mai tasiri.
Yani yace a ranshi lalai ya zama dole in san yadda zan gyara alamarina da yarinyar nan don ita din ba abin yar wa bace .
Cikin dan lokacin kadan tayi min sanadin dawo min da farin ciki tsakani na da iyayyen har da yan uwa wanda wanan tunanen bai taba zuwa min ba ko wani ya tsayar dani ya fada min gaskiya yadda take fada min kai tsaye.
Tayi namijin kokari wurin ganin ta tsaya ta fada min maganna irin haka kai tsaye bataji shakka ko nauyin fada min yadda kowa ke shayi na ba.
Wayan shi aka kira ya daga Faiza ce take mai godiyan abinda aka kawo masu yace babu komai ta kashe kuma Lawisa yar wurin ummi ma ta kirashi tana mashi godiya haka suka dinga kiran shi sai da yagaji ya kashe wayan shi ranan.
Wani irin farin ciki yake jin kanshi ciki mara misaltuwa da wanan kiran da yan uwan shi suke mai a lokacin don ba zai ce ga ranan da suka kirashi karshe ba.
Ya zama dole gare shi ya san yadda ya gyara mu,amulan shi da duk wani dan uwa nashi da ya watsar da farko.
Sai yaji yana sha, awan ya kira layin khadija a lokacin yayi mata godiya haka yasa ya jawo wayan shi ya kira layin ta.
Ina fitowa cikin makaranta na samu guri na zauna ina jiran maryam tafito mu wuce cikin gidajen mu don an kara muna kwana daya yanzu.
Kiran shine ya shigo min wanda tun bayan rabuwar mu ranan ban kara ji daga gare ba sai yanzun da ya kirani din na tuna dashi.
A hasale na dauki wayan ba tare da nayi magana ba don na gane shine jin shiru ya danyi yawa banyan na dauki wayan sai nace
A hasale nake fadin lafiya ka kirani ko ka kirane ka fada min ka tsane ni din da kake fada min ko yaushe ?.
Murmushi naji yayi kasa kasa sai ya sake kiran suna full yace khadija a zuciye nace ina jinka ai yace ba wanan kiran nayi maki ba yanzu.
Nace may ye ka kira malam ni kada ka bata min lokaci haushi ne ya ishe shi a lokacin yana rayawa a ranshi yaya zai yi dani ne wai ?
Cikin sanyi murya yace min thanks khadija na gode kwarai da taimakon ki gare ni sai dai don Allah, , , ,
Dama abinda yasa ka kirani ke nan don ka samu wani sabon yaudara ka zageni kuma dashi na fahince ka don haka banda lokacin ka ni yanzu.
Na fadi a cikin tsigar tsokana tare da saurin kashe wayan sai dai a zahiri jikina yayi sanyi da yadda naju yana maganan cikin wani yanayi.
Shiko ina kashe wayan yabi wayan da kallo kamar nice wayar ya sauke wani irin ajiyan zuciya yana fadi a fili shi kadai a daki.
Wanan yarinyar ni yaya zanyi da ita ne wai ta fahince ni yanzu ya girgiza kai yace kina da matsala khadija yarinya haka bata da kwaciyar hankalin fahinta.
Why why khadija baki so na da kwanciyan hankali a tare dani yanzu ne mikewa yayi daga kwancen da yake ya nufi fridge ya dauko goran ruwa mai sanyi a ciki ya kwankwada tare da wurgi da goran ya fito falon shi.
Mutane ya samu sunzo gaida shi inda ya bisu da alheri sai yamma lis ya samu suka rage nan ya nufi bathroom din shi don ya dan watsa ma jikin shi ruwa ko zai ji sanyi.
Dan ruwan dumi ya hada saboda yanayin garin na kaduna ya shige jacuzzi ya dan dauki lokaci yana tunane kafin ya fito ya sa kaya a jikin shi ranan a maslcin uguwan su yayi sallah magariba tare da jamma, an unguwa da mahaifin shi aciki.
Ba abinda yake tunane sai yadda zai samu mu shirya a tsakanin mu gashi dan lokaci kadan yarinyar ta shiga zuciyana ta samu wuri a ciki.
Tunanin yadda zai shawo kaina amma ya kasa samun mafita har wanan lokacin shigowan suraj soja wurin shi yasa ya matan halin da yake ciki don sun dauki lokaci dashi suna fira kafin Yusuf ya shigo mai da abincin da mommy ta girka masu.
A tare da Suraj da Yusuf din sukaci abincin suna hira a tsakanin su bayan fitan Suraj ne suka samu kebewa da Yusuf wanda tun bayan zuwan su basu samu zama a tare ba.
Nan yake kara mai godiyan kokarin da yake mashi inda yake sanar dashi ya kira ni don yai min godiya amma naki fahintar shi Yusuf din yace ya sake kirana zan fahince a hankali.
Ba laifi yace dashi sun dan dauki lokaci sukayi sallama akan da safe zai shigo su tafi zaria idan sun dawo yana son kuma ya dan je wurare masu muhinmanci a kaduna daya dade bai tafi ba.
Yusuf na fita ya kira waya maryam ta dauka ta miko min bayan ta dana recieve na dauka da sallama na kara a kunne na.
Bayan mun gaisa ne yake rokona da in karba wayan abokin shi inji may zai fada min dariya nayi tare da fadin abokin nan naka ne ai sai a solo baida mutunci.
Yace kada kice haka Khadija baki fahince shi bane amma abokina mutumin kirki ne wallahi ki bashi dama ku fahinci juna yanzu zai bugo waya godiya yake son yi maki akan taimakon da kikai mashi na bashi shara kuma yabi yaji dadin shawaran ki shine zai maki godiya akai.
Munyi sallama dashi ranan maryam tazo dakina wai a nan zata kwana saboda exam din da zatayi washegari yana da zafi ita kuma tana son tayi karatu a daren ranan.
Muna tsaka ga karatu wayana yayi kara na daga tare da karawa a kunne na muryan shi naji yana tambayana har yanzu baki barci bane.
Karatu mukeyi na bashi amsa yace OK dazun na kiraki in maki godiya kika kashe waya nace ina busy ne a lokacin.
Khadija ya kira sunana amsawa nayi ciki ciki yace please ki bani dama in maki godiya akan abinda kikai min shiru nayi na kasa magana.
Khadija kina jina nace ina jin ka mana sai naji tayi wani kasalalen murmushi yace in tambaye ke zaki ban amsa tsakani da Allah ?
Nace sosai makuwa idan har na sani may zai sa in boye maka tunda ba rike min baki zakayi ba.
Ajiyan zuciya naji ya sauke sai can yace may yasa kike son yawan bata min kina son ganin hasalana ni koda ban tashi hasala ba ?
Kin tsane ni kin ki jini baki kaunar ki ganin a cikin farin ciki why khadija why kika zabi wanan rayuwan a tsakanin mu.
Shiru nayi na kasa magana nauyin shi da kunyanshine suka kamani a lokaci daya na rasa may zance dashi don yadda yake magana bazakace shi din bane mai izza da jiji da kai.
Nasan kin san bawai son soyayya ne a tsakanin mu ba amma kuma kika zabi yin haka a gare ni ki fada min may ke sakina tsana na haka da yawa.
Dan murmushi nayi tare da fadin yaya Abdulsamad ke nan ni nasan babu dingo soyayya ma a tsakani mu tun farko sanan kuma ni ko in so ka ko da so ka ba abinda zai ragaka dashi duk dayane a wurin ka.
Ni dama ba kai na tsana halin ka na tsana da matar ka da bata san mutucin yan uwanka ba har hali ku ya juye iri daya da ita.
A yau in rayuka zai sauya kasan mutucin kan ka dana yan uwanka ka farga ka dawo yadda mahaifan ka suke son ganin ka da yan uwanka ka san darajan su da mutuncin su fiye da kowa.
Amma ni may zai sa na tsane ka kana a matsayin yayana aiko don mama zan so ka zanyi muamula dakai kamar kowa.
Don dama ba kinka nayi bani halin ka dai na tsana bani ba kowa ma zai so ya kulla halaka dakai ta yadda baka zata ba.
Murmushin da naji yayi yasani shiru yace khadija idan nace maki ashiri nake da in caza yanzun zaki yarda koma in ce dake din na canza a sanadiya ki.
Jin shi kawai nakeyi ta yaya ni zan iya canza mutum kamar Abdulsamad a lokaci daya haka.
Muryan shi naji yana fadin kina mamaki abinda na fada ne yanzu yace yes ke khadija kin tunatar dani abinda na manta acikin abinda nake dauka shirmay kukeyi ke da Yusuf a lokacin.
Nace ba abinda mukayi da har zai kawo sauyi gare ka haka da wuri sai dai idan dama Allah ya kaddara tamu din abin zai fito ma.
Kuma ina mai farin ciki da jin haka idan ya kasance gaskiya ne maganar ka da sai nafi kowa farin cikin haka a duniya.
Yace to ki fara farin ciki daga yau don ko kin sa iyayyena sun min abinda suka dade basu min ba a yau don haka khadija ban san ta yaya zan gode maki ba da tunatar dani da ki kayi ga abinda na manta hakki na ne yinsa a baya.
Koda da wasa ko gatse kika fada min wanan magana to ki sani your words inspired me har nakai ga samun kalmar albarka a bakin iyayyena yau abinda na dade baji ba a gun su.
Yau kin dawo min da farin cikin dana rasa da dadewa a tare dani kalman ki na ranan gare ni sun sa na dawo da natsuwana.
Ya kuma fara dawo min da respect da power na ga idon mutane dana rasa a baya wa yanda ya kamata ace komai wuya komai dadi ina tare dasu.
Ba zan iya kwantata maki dadin da naji ba yadda na kasance da yan uwana da abokai kai har ma da makwabta na ayau suna murna da zuwa gare su.
Don haka yazama dole in gode maki please khadija kada kiki fada min gaskiya a duk lokacin da kika ga na kauce ma hanya.
Murmushi nayi nace naji dadi kuma na tayaka murnan dawowa farin cikin ka gare ka don ko yau ranan kace ranan farin cikin ka.
Ka kuma gode ma Allah da bai sa ranan ya kasance ranan nadamar ka bace ya fargar dakai da wuri haka.
Allah ya kars shirya zukatan mu ni zan kashe karatu nakeyi ka tsayar dani don gobe zamu gama exam jibi gida zamu.
Da sauri yace jibi wata rana nace talata inda Allah ya kaimu da safe zan tafi gida don yin hutu a can.
Yace No kada ki tafi don Allah ranan ki jira in dawo akwai abinda nake son in shirya akan tafiyan ki nace Allah sarki dama ka hutar da kan ka don ni a shirye nake yanzun haka.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
A zoto na shika dai ne a cikin motar sai da na isa kusa ne naga sabanin haka ashe tare suke da dan baiwa yana zaune kamar kullun ya aza Laptop a cinyar shi yana dubawa.
A sanyaye nake nace dasu sannu ku da zuwa yaya hanya yaya mutanen gida kun barsu lafiya ?
Yusuf yace ke ce African ta gidi khadija tambaya haka a jere lokaci guda wani zamu fara amsa maki daga cikin wanda kika jero muna a lokaci daya ?
Nace amsa daya ya wadata gareni wanda nake fatan alheri a cikin shi yace to duka amsan ki alheri ne don duk Alhamdullahi gaba daya kowa na lafiya kuma hanya lafiya.
Murmushi nayi sai yace baki gaisa da oga na ba kuma aboki na dan satan kallon shi nayi nace ai bugu daya nayi maku gaba daya nashi gaisuwan daban ne kuma ?
Yace oga ne fa khadija kema kin sani ai dole gaisuwan manya ya zama daban da na saura nace a wurin ka yake daban don kace shi din ogan ka ne amma ni a wuri na duk daya kuke gare ni.
Eh to kya iya fadin haka yanzu amma dai nasan nan gaba bazaki fadi hakan ba dariya nayi nace saboda may kana ganin zanyi aiki a karkashin shi ne ko may , ?
In wanan kake tunane may zai kai lawya aiki a FCDI kuma sai in dai bukatan haka yataso mu a bukace mu a wurin muyi aikin mu mu bar wurin.
A a a ashe da babban lauya muke bamu sani ba haka nace cikin murmushi lawyer to be insha Allah ba ya juya gare shi yace kai kaji ashe da Barister muke bamu sani ba shike nan yanzu muyi abin mu ba kwabo muna da mai kare mu.
Nace wa ni ai nice ma zan tsaya sai na kama masu cinye ma gwaunati kudin filayen ta in daure mutum inga tsiyan kwashe kudi ana tura ma yan Niger suna cinyewa dama yan Nigeria kuke ba sai in maku sausaci a kai.
Sai lokacin ya dan sake murmushi yace ashe har kin fara hada evendece a kaina ban sani ba nace tun yaushe na fara hadawa zan tura babban kotun mu.
Dariya sukayi sosai gaba dayan su yace dama karatun da kike yi ke nan ashe nace kwarai don kama manyan bariyin gwaunati ba.
Yace ashe aiki ya ganki magana yake ba tare da ya dago kai ya kalle ni ba sai dakilan laptop da yake yi hankali kwance da gani abin ya zama mai jiki hakan.
Yusuf yace wai kin san ban taba sanin abinda kike karantawa bs ke nan sai yanzu na dan natsu nace shi nake karantawa ai Allah ya bada saa yace nace amin nagode.
Still bai dago kai ba yace wace zata kama ka kakewa addua haka kuma yace ai addua ya zama dole muyi mata shi fadi take yi kawai mutum ya taba kama kanshi da laifi ne.
To wai ni fa kun barni a cikin duhu yakamata ace yanzu ina gida kun tsayar dani a nan aikin oga ne haka khadija bai son ki bar garin nan yanzu ne yasa ya tsayar dake.
Kallon shi nayi sai faman aikin shi yake yi hankali a kwance bai dago ya kalle mu ba nace ni ai ba yar Niger bane da yake tarawa a gidan shi kamar almajirai.
Dama titi yake bi yana ba mabukata alheri da zai fi samun lada ga Allah da wanan ciyar da mayaudaran dayake yi zai fi mai Alheri sosai.
Rufe Laptop yayi tare da fadin wai ke maye matsalan ki da yan Niger ne cikin rashin sani nayi subul da baka nace kishi mana lokaci daya suka ce kishi nace wallahi.
Murmushi naga yayi yana lumshe ido Yusuf ko sai kallo na yake yana dariya shi ya bude idon shi yace kishi yana jijiga kai nace na kasata ba .
Sun zo suna kwashe muna dukiya suna raya kasan su da sunan aure nan ko barayi ne na zaune Yusuf yace a a kada ki gyara zancen kuma mana khadija yar mama.
Nace a in ba kishin kasata ba kishin may zanyi kuma Yusuf yace gashi a gaban ki kishin dai kike yi amma kada ki gyara kice kuma wai kasan ki.
Ikon Allah akan may zanyi kishin shi shi mijina ne ko wani nawa ba hadin kifi da kaska ai Yusuf yace waye kifin waye kasa yanzu.
Yace itace kaskan mana nine kifin ba ita ta lake min ba kana gani kuwa ido na waro waje nace ni din yace Yes kamar zanyi magana sai kuma na kalle su tare da fadin sai anjiman ku.
Ina juyawa da sauri Yusuf yake kirana ban tsaya ba ya fito daga motan ya sha gabana shiko yana ciki sai murmushi yake ba abinda ke mai yawo a rai sai kallaman kishin da nace.
Ya samu na tsaya yace ke ko daga wasa zaki mai da abin wani magana nace ina nuna shi bakiji may ya fada min bane yanzu wai ina like mai.
Yace ai wasa ne ko shima yasan baki like mai shiyasa ya juye maganan yace ke ce mai like mai yanzun bamu muka zo wuri ki ba wake nan kaskan a cikin mu ?
Bude motar yayi ya fito yana mika tare da nufo inda muke tsaye yana fadin wai may kaskan nan take fadi ne haka ka tsaya wani bata magana can.
Yusuf yace kin gani ba har ya kai ga fitowa a mota don ki yace ai ita ma ta fito don ni ko, kallon shi nayi na kauda kai na gefe daya.
Ya karasa takowa zuwa inda nake yace wai yaushe ne zaki tafi in samu in huta da wanan matsalar taki.
Nace nice yar matsalar yace gashi ko kina muns ko yanzu kai na girgiza kawai nace ba komai baka da laifi fito war maryam ya tsayar damu daga maganan .
Ta fito tana gaishe tare da masu yaya hanya da mutanen gida yusuf yace suna gaida ku tace kuna nan da miss barister ne yace wallahi kuwa kauna a kwai rigima ai.
Tace da kyat na shawo kan ta ta tsaya da yanzu tana gida baku samay ta ba Yusuf yace kin kyauta shi dai tunda ta fito bai mata magana ba ko gaisuwan da tayi bai karba ta ba sai ma daure fuska da ya kara yi yanzu.
Yaushe ne zata wuce Yusuf ya tambayi maryam tace bataki ko yanzu wanan ta bar gari ba ta isa da dare da sauri shi yayi magana da fadin No bako a cikin daren nan ba kan gaskiya.
Nace may ye a hanya da zaka ce ba da daren nan ba zan isa ko lafiya yace No sai gobe za a zo a kai ki har gida.
Nace a a kada ku wahal da kan ku motar kasuwa
nake shiga yanzun ma shi zan bi in Allah ya yarda bani kadai ba kowa dake wurin yayi mamakin maganan shi da yace.
Ba zan yardan ba ki bi motar haya ke kadai idan wani abu yaje ya samay ki fa a hanya ki sani a wani hali don haka ki shirya gobe zan turo malam sani ya kaiki gida da safe.
Ido gaba dayan mu muka tsura mashi da yake maganan kamar wani uba da yar shi ko miji da matar shi yadda ya hakikance yana fada a hasale dani.
Zan yi magana Yusuf yace ya gama yanke hukunci akai Allah ya kai mu gobe din ai yau da gobe duk na Allah ne ko amma ki bi motar haya wani abu yaje ya samar mashi ke a hanya kuma ?
Maryam ne tayi dariya nikan hararan shi nayi mai dani gida yace a dake Yusuf yace to bissimillah muje in sauke ka ko ya juya ya fara tafiya ba tare da yayi magana ba kuma.
Sai Yusuf ne ya tsaya yana ce muna yar mama ni zan tafi ban sani ba ko zamu sake haduwa ga wanan ayi ma kanne tsara ba dashi ya mika ma maryam sai kuma ya sake ciro wasu yana miko min wai na karba.
Kai na girgiza mai nace daka barshi don ni ina da kudin mota a hannu na tsaraba kuma ai kowa yasan makaran ta naje basu expecting din tsaraba a wuri na.
Yace daga wanan time din sai ki fara masu tsaraba baki san tsaraba ko ga babba yana da muhinmanci ba ne mutuka kauna na.
Dole ya mika min na karba tare da mashi godiya har dan Baiwa ya fara mashi horn a mota yace Allah sada mu da alherin sa nace amin yaya Yusuf ya juya ya tafi sai da suka shige muka koma ciki.
Maryam bata shigo daki ba don haka ni kadai na shiga na adana kudin tare da cire rigar da nasaka a jikina.
Can ta shigo ta hada muna abinda zamu ci ina kwance a wurin tunane ya addabe ni a raina har ta gama tace inzo muci don na idar da sallah a lokaci.
Sai da muka zauna cin abincin ne muka fara hira da ita take tuna min maganan shi da yayi dazun tare da fadin guy din ya hadu wallahi
Daure fuska nayi nace a naki ganin kike ganin haka amma ni mai zaisa in sawa raina abinda nasan ba mai yuyuwa bane gare ni ai ko a mafalki wallahi.
Ko dai baki san ko shi waye bane yasa kike wanan magana haka shima dai Yusuf ai yanayi ne don wasa kawai amma ba gaskiya bane so kima daina wanan zancen don Allah.
Wayana dake gefe ne yayi kara ban gani don wayan a silent take lokacin sai maryam ne ta gani take ce kamar kiran ki ake a waya fa sai nayi saurin juya don in duba.
Tashi nayi na dauko wayan mai kiranane yaban mamaki tunda basu dade da barin wuri na ba, daukan wayan nayi na kara a kunne na da sallama yace fito gani waje.
Da mamaki nabi wayan da kallo muryan shi naji yana fadin kin ji abinda nace nace eh maryam na kalla da ta tsareni da idanuwan ta nace a sanyaya wai shine a waje .
Ta kwashe da wanin irin dariya bance da ita kala ba komai ba na zura rigana na fita zuwa jin may ya kawo shi kuma.
Ina fita na hango motan shi dan nisa kadan damu na karasa wurin na samu ya fito da kafa daya a waje yana duba abu a cikin motar na iso wurin.
Ina wuni ya dan juyo ya kalle ni yace zagaya ki shiga dan jin nayi bai zagaya ba kamar yadda ya umurce ni dayi ya sake dagowa bayan ya rufe cabinet din motar yana fadin baki ba ne dole na zagaya kamar yadda ya umurce ni din dayi.
Bayan na shiga naga ya tayar da motar ya bar gurin down hostel din ya halba motan muka hau expresse ba wanda yayi magana a motan sai dai gaba na yana dan fadi don ban san ina muka nufa dashi ba.
Mun dan yi nisa da gurin ya juyo ya kalle ni yana fadin maman ki ita kadai ne a gurin mahaifin ki ?
Mamakin tambayan nashi nayi sai ban iya bashi amsa ba na kawar da kaina gefe yace ina magana kin kyale ni nace akan may zakai mun wanan tambayan haka.
Yace don na isa na tambaya yasa na tambaye ki OK idan kana son sani sai kaje ka gani da idon ka ai.
Kan nen ki nawane dariya tambayan ya bani sosai nace yau ni naga ikon Allah to kannen na biyar ne na bashi amsa tare da kawar da kaina.
Ok kawai yace mukaci gaba da tafiya sai wani katon Plaza muka tsaya ya juyo yana fadin bissimillah fito mu shiga yace.
Ban ki ba na fito muka shiga shagon sai faman gaida shi masu shagon keyi layin kayan sawa muka nufa yana gaba ina bayan shi.
Abin ya ban mamaki yadda naga yana jidan kaya a wurin ya ban mamaki ya koma layin kayan yara sai lokacin ya juyo ya tambaye ni shekarun su nawa ne kallon shi nayi nace a kwai sha uku da sha daya sai takwas da shidda mutum biyu.
Maza da mata ne ya kara tambaya nace maza uku mata biyu sai yaran yaya na biyu yan she kara takwas da shidda maza.
Bayan mun gama wurin takalma muka nufa muka zaba sai layin zanuwa nan ya zaba da dama ya zaba sai ya duba kudi ya gani yake daukan mafi tsada a wurin.
Ya sa yaron shagon ya tura yakai yace a samu trolley masu kyau a saka mai kayan a ciki muka bar shagon hanyar down hostel muka nufa sai lokacin hankalina ya kwanta.
Bayan ya tsaya da motar nayi kokarin budewa naji ta a rufe gam na juyo na dan kalle shi naga shima ni yake kallo a lokacin sai na kawar da kaina gefe daga kallon shi.
Ina son in maki godiya amma kin kasa tsaya ki bani daman yin hakan gare ki nace godiya akan may fa ?
Au baki ma san abinda kikayi ba ke nan nace ban sani ba sai ka fada min iska ya dan furzu daga bakin shi yace OK you can go zamuyi waya idan kin isa ki gaida gida na gode kawai nace na fita.
Banji yace dauki kayan ko wani abu ba nikan na shige abina ina fadin dan rainin wayo kawai dama sayayya zan rakashi shine yake min tambayan bazan a hanya.
Har yasa gaba na faduwa ina zan kai wanan uban kayan danaga ya jida a shagon sai yanzu hankalina ya kwanta.
Koda takwas na safe yayi mun gama shirya komai muna zaman jiran su sai na tafi maryam tace zata wuce itama takwas da wani abu ya bugo min yana fafin in fito da kayana ga mota a waje ana jirana.
Fitowa nayi da kayan maryam ce mai karasa min su a wurin motar har aka gama na rufo kofana na saka key din a jakka ta mukai sallama tace za a zo yanzu a dauke ta ta buga waya gida itama.
Driver ya bude min baya na shiga muka dauki hanyan minna shigan wuri zan ma minna wanan karon ba yadda na saba ba da dare nake shiga garin.
Tunda muka kama hanya barci ya dauke don sanyin motar da lafiyar ta sai faman gudu driver ke shararawa dani ina barci na hankali kwance.
Barci nayi sosai driver naji ya tsaya a wani gari na bude ido fita naga yayi zuwa gun masu sai da manja da doya a hanya ya saya aka loda mashi a motar muka kama hanya kuma.
Tun ina duban waya sai na koma barci abina muryan driver ne ya tayar dani yana fadin hajiya wani unguwa zamu je na bude ido ina kallo har mun isa deport din mai zamu shiga cancaga .
Nace a cikin gari kwagila road, zaka kaini yace ban san wurin ba don ni bakon garin ne nace OK mushiga sai in nuna maka.
Miko min envelop yayi yace oga yace idan mun iso in baki wanan sako wai sai kin shiga gida ki bude nace OK
Mun wuto ina mashi kwatance har kofan gidan mu motar ya tsaya duk da rana ne kowa na zirga zirgan gaban shi nai hana masu zama layin namu zama suna ganin motar ya tsaya kofan mu suka sako ido caa suga waye a motar yazo gidan mu.
Driver ya fito ya bude min motar na fito can naji wani classmates dina na primary yana fadin yau Khadija ce a garin namu.
Murmushi nayi mai nace Faisal mun samay ku lafiya ya karaso muna gaisawa dashi na shiga yace bari ya taimaka min da saka kaya a gida.
Da sallama na shiga inda kanne na dake daki suka fito da gudu taro na suna ihu na rungumay su tsayawa nayi ina kallon kayan da su Fesal ke shigowa dashi gidan namu.
Na kasa furta komai mama ma kallon kayan take da mamaki yaran suka fita sai gasu suna shigowa da ba adadi nace wai duk mu muka zo da wanan kayan haka wai ?
Mama tace waya zo dashi in ba ke ba bagashi kin ga ana shigo dasu ba tare da kayan ki ko kina nufin baki san da su bane wai ?
Wallahi mama ban sani ba sai yanzu nima nake ganin su anan kamar kowa yadda ya gansu mama ta katse nu da cewa motar wa kika shigo ne naji yara na fadin kin zo a mota mai kyau.
Shiru nayi na dukar da kaina ba tare da magana ba har suka gama shigo da kayan mama tace ku dauki ruwa kusa a plate kukai ma mai motar kafin ya tafi.
Yaran suka ruga da gudu suka dauki ruwan leda suka sa a plate suka fita dashi waje kamar yadda mama tace dasu ta wuce tabar ni tsaye a gurin.
Dakina na nufa tare da dan hand bag dina dake rike a hannu na rai na babu dadi ko kadan a tare dani ina fadin yaya wanan mutumin zai min haka ya hadani fada da iyayyena su fara zargina.
Anty khadija wai yace a fada maki zai wuce nace ya kice Allah ya kaishi lafiya nace a hasale yaron ya fita da gudu daga dakin zuwa fada mashi.
Daddy ya shigo gida yana fadin ance baby na ta dawo sai kuma yaja ya tsaya yana kallon kayan da mamaki dake zube a tsakar gida.
Mama tace kai nake jira dama kazo ka gani ko zata fada ma inda kaya ya fito haka don wai ita ma bata sani ba tace kuma su sukazo da kayan.
A sanyayye na dago labule dakin na fito ina fadin daddy sannu da dawo wa mun samay ku lafiya ?
Lafiya baby na sai dai wanan kayan kuma fa ina suka fito haka nace wallahi daddy ban san da su ba sai da muka iso na gansu.
Kamar yaya bakin san dasu ba bake kika zo dasu ba sai nayi kasa da kaina ban yi magana ba kuma kayan yake bi da kallo tiryan tiryan yace ikon Allah.
Shiga ciki ki huta zamuyi magana anji yanzu zan tafi inyi sallah ne ya wuce gurin da buta yake yana dauka ni kuma na sake labule na koma ciki jiki a sanyayye.
Na fada saman gadon dakin duk da kuran da yake ciki don ba gyara ake ba a kai akai tunda ba kowa a cikin sa ina zaune kamal kanina ya dawo shiya fara shigo min da kaya yana min sannu da zuwa.
A dadafe na amsa mai ina kallon akwatinan daya shigo min dasu akwatunan da muka sayo a daren jiya ne dashi inba idona ke min gizo ba.
Watau kayan de na yan gidan mu ne kenan ba wasu ya saya wa ba mikewa nayi don in yo alwala ina shiga banda ki sai na samu ai period dina yazo min ba daman inyi sallah ke nan haka na fito jiki a sabule na aje butan.
Sai mama ta aiko da abinci a kawo min ban kali abincin ba nace kaunata ta aje min a nan kawai ina jiran dawowan daddy daga wurin sallah.
Envelop din da driver yaban na tuna dashi na dauko a cikin jakata na bude a hankali kudine a ciki sabbi ful din su anyi rubutu kamar haka a wrafer farko daddy sai na biyun mama.
Na ukun ne bai rubuta komai ba na shiga uku nace tare da yin nadama da haduwa da shi karo na farko a rayuwana don ban san yadda daddy da mama zasu fahince ni ba.
Nayi dana sanin tsaya jiran shi da yace inyi har na tsaya din sam ban kawo komai a raina ba irin haka don ban taba zaton hakan ba dayayi min.
Muryan daddy daya shigo naji ana gaida shi yasa ni kaduwa bai min magana ba har yaci abincin shi ya fita haka na tashi na gyara dakin tsab na fita da na wankewa na wanke a ranan.
Na dawo na sa kamshi a dakin tare da gyara komai a yadda nake bukatan shi a dakin na koma na zauna wayan maryam ne ya shigo tana tambayana yaya muka isa ?
Nace wai kin san abinda mutumin nan yayi mun kuwa maryam nan dai na koro mata labarin abinda ya faru bayan isowar mu gida da driver.
Tace ikon Allah sakayyan da yai maki ke nan ashe kai lallai mutumin nan yaci sunan sa dan Baiwa ne shi din.
Nace ke maryam har kin samu bakin yabashi ko may may kike son in fada ma iyayyena yanzu don Allah wa zance yake gare ni da yai min wanan kyauta haka.
Tace ki fada masu gaskiya taimakon shi kikayi ya saka maki da alheri haka nace ban sin su san ko shi waye tundai Ya Amina .
Dariya tayi tace komai dadewa ai zata sani ne nace amma fa ba yanzu ba koda zata sani din don ban son ta fasara ni da wata manufa.
Har dai dare banji daddy yayi min magana ba haka yasa na dan sake jiki naji shigowan daddy gidan sai na sha jini jikina a daki ban fito yadda na saba muyi hira ba dashi.
Ina nan kwance wayana yayi kara na dauka kamar yadda na rubuta a sunan shi dan Baiwa shi ya baiyana a wayan.
Kamar ba zan dauka ba dai na daga maimakon inyi magana sai na kama kuka nace may yasa zakai min haka don Allah ?
May kake son in fada ma iyayyena yanzu a kan kayan nan yace daddy na gida nace yana nan yace dama shina ke son magana dashi na kira ki yanzu.
Da sauri nace may zaka fada ma daddy din yace gaisawa nake son muyi dasu in masu bayanin kayan ba shike nan ba.
Yasir na kira nace ya kaiwa daddy waya ana magana dashi ban san yadda sukayi ba a wayan har mama naji suna gaisawa da ita.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Washe gari muka shirya zuwa beji duba wani kakan mu dake zaune acan kanin mahaifin maman mu ni da ya Amina da yaran su.
Bayan Nkwa bamu iya wani gaisuwan kirki ba sai habalu da sauran kananin kalma irin na gwarawa da muka rike a bakin mu.
Tsohon yaji dadin ganin mu yana ta murna da zuwan mu gidan duba su anan muka wuni tare da su sai yamma muke son mu dawo mu biya maikunkele gidan iyayyen mama din.
Tsohon bagwaren yana waje zaune da bakon shi muka fito zamu wuce muna masu sallama bakon nashi ne yayi yare sai naga tsoho yayi dariya tare da fadin yaki nan amarya na.
Nazo na duka a gaban shi yace bako na ne ke son ganin ki sai na gaida dattijo ya mika min hannu alaman in bashi nawa hannun.
Ban ki ba nayi kamar yadda yace min sai da ya kalli tafin hannu na da kyau yayi murmushi yace Allahu akabar akwai tarin alheri ga wanan hannun naki sosai zan ba kaka ku wani abu ya baki gobe ba mai wuya bane abin inda zaku tsaya na awa daya zan iya hada maki ko anan ma.
Don tsari juyawa nayi na kalli ya Amina tace ai zamu iya tsayawa mu karba nan saman tabarman muka zauna ya bude jakkar shi ya ciro wani dan farin abu a wani kwanko yayi ta abinda zaiyi a abin sai ya miko min hannu na mika mashi nawa.
Ya fara murza min abin a tsakiyar tafin hannu na har saida abin ya bace bat a hannu na ya dan dade rike da hannu na yana min tofi har kaina sai daya dafa yayi min yadda yayi a hannun ya sake ni dama tsamin jikin shi duk ya isheni sosai.
Ya Amina ma tace aiwa yaranta da ita ba irin wanda yayi min yayi mata ba zamu tafi na bude jakka na fido dubu daya na bashi ya girgiza kai.
Yace idan ina da dari biyu in bashi kawai yaci goro dashi na duba naga wani sabon dari biyo na dauko na bashi nayi mai godiya muka tafi.
Muna cikin mota ya Amina tace na rasa may sa tun kina karama idan mun fita ke kawai mutane ke taimakawa wanan karo na biyu ke nan da haka ya faru dake.
Nace su suka san abinda idon su ke gani a kaina wanda mu bamu gani hakan dariya tayi tace kila ya hango maki buzuwan ku ne .
Kai ya Amina may yasa kuke fadar haka ne karfa maganan nan yakai kunnen su mommy da yan gidan su fa.
Tace indan ya kama suji ai ji zasuyi khadija lokacin jin su ne baiyi ba kawai amma duk wanda yaji mamaki zai yi wallahi.
Sai dare muka isa gida don mun bata lokaci a maikunkele wurin yan uwa da abokan aarziki ko da muka dawo wanka kawai nayi na samu wuri na kwanta abina.
Da safe muka tashi da labarin haihuwan antyn mu Anty Hauwa dake aure a pilamigo easther wanka mukayi muka nufi gidan ta acan muka wuni sai four muka baro gidan ta.
Koda muka dawo gida mama tana dora girkin dare sakwara zatai muna da miyan egushi tubewa nayi na fara taya mama aikin dakan sakwara don doyan ya dahu ko.
Ya Amina data fito dakin ta tsaya tana kallon yadda nake dakan sakwaran ta kwashe da dariya tace ashe kin iya idan nace muyi sai kice bakya son ci.
Sallaman da muka jiyo a kofan shigowa gidan mu ya hana ni bata amsa naci gaba da dakan sakwarana.
Anty Amina ce ta dan leka raga mai sallaman sukai kicibis da Yusuf a tsaye yana gyara rigar shi da ya dan takure ga zaman mota.
Kamar daga sama ta san shi a gidan su mommy shine dai bai santa ba tace cikin mamaki Yusuf kune tafe haka da yamman nan ?
Yayi mamakin sanin shi da tayi haka shi bai santa ba sai dai ya gane muna da kama da ita sosai sai dai tsayin da nafita da kuma hasken fata don ni daddy na fadin gidan mu na debo sosai ina da zubin fulanin su na ka,aje ne.
Ta juya tana fadin barin sanar da Khadija gata can yau sakwara take daka muna a gidan yayi dariya ta wuce ciki ina ganin ta shigo tana dariya ina rike da tabarya mama na duke tana saka wanda na daka a leda tace khadija ga ki da baki fa a kofan gida.
Da sauri nace da ita su waye ya Amina tace wa kike tsamani zai zo maki yanzu banda su Yusuf da abokin shi nace kai haba dai ya Amina may zai kawo su nan in ba gulma ba.
Tace to gulman ko ya kawo su gasu can a waje dai nace wai da gaske tace ina wasan haka dake ne dama tabarya na aje ina fadin yau na shiga uku.
May suka zo yi yanzu kuma don Allah tace kyaji idan kin fita ai ni wallahi sai naci masu mutunci don may kuma zasu biyo ni har gida haka ?
Harara mama ta watsa min tace idan zaki natsu ki natsu kije ki gan su falo ya Amina ta shiga ta fara gyara wurin inda zasu zauna ko kafin in fita na samay su da daddy suna gaisawa a waje na juyo na dawo ciki abina.
Har ciki daddy ya shigo dasu ina labe a dakin mu ina kallon su sai da suka shiga sun dade ciki da daddy da ya Amina kafin ta fito ta kwala min kira ban fito ba ta samay ni a dakin tana dariya.
Ya Amina may wanan mutumin ke nufi da nine wai for god sake may ya kawo su har gidan mu ne don bata min suna.
Kallona tayi da mamaki tace zuwa gidan ku shine barnan suna khadija ai gara da suka zo zai fi hankali mama ya kwanta.
Ni kan na shige su wallahi tace don Allah ki natsu kije ku gaisa sunce hanya ne ya biyo dasu nan suka ratso su gan mu.
Ina shiga na samu har da abinci aka aje masuz sai hira Yusuf keyi da daddyn mu shiko sarkin miskilanci ido kawai ya zuba ma kofan shigowa falo.
Da sallama nashiga tare da samun wuri gefe na zube gwaiwa na a kasa ina gaida su Yusuf ne ya amsa min shiko ido kawai ya zuba min kamar yadda na samay shi zaune.
Daddy ya fita falon yana cewa dasu yana zuwa ya fita daga falon bayan fitan daddy ban daga a yadda nake na dago ina kallon su nace may ya kawo ku may kuka zo yi gidan mu ?
Baiyi magana ba sai bude kula abincin yayi yana kallon sakwaran tare da fadin ke kika yi wanan abincin wai ?
Yaya akayi suka san haka nake tambaya kaina a zuciyana Yusuf ma budan abincin yake yana faadin yar mama ashe kin iya girki ne haka ?
Yayana may kuka zo yi nan yace gashi kinga munayi kawai dai mun yi marmarin cin girkin gidan ku ne mukazo muci dan harara na aika masu.
Abdulsamad din ne yace kina ganin zaki iya kashe min waya don kada na kiraki da sauri nace ni ba kashe ma waya nayi ba.
May yasa baki kuna wayan naki ya tambaya cikin kura min idanuwan shi dake ban tsoro yanzu nace wayar ce bata da lafiya.
Baiyi magana ba ya fara cin abincin ba ko kunya hankali a kwace nace baku da kunya ne zaku ci a binci a gidan mu ku wai wasu irin mutane wai ?
Ruwan abincin gidan ku zaki muna ya fada nace ni naci na gidan ku ne to yace wayasan iyaka wallahi ban taba shan ko ruwan gidan ku ba ni.
Yusuf yace saboda may yar mama yana kai lomar sakwara a bakin shi kunya su nake ji ban iya shan ko ruwa a gidan don nauyi.
Ashe ko kin cuci kan ki don ni dai a sani na gidan mu bako bai shiga ba a tare shi da abin sha ko na ci ba daddy ya kwala min kira daga cikin gida na mike na fita da sauri ya daga kai ya bini baya na da kallo.
Saurin kawar da kanshi yayi yana cin abincin da yaji dasin dan danon shi har cikin ranshi ina fita naga baba da leda ya sawo drinks.
Yace in kai wa baki a falo a tire na saka nakai na dire masu a gaban su nace gashi kun sa baba kashin kudi bai shirya ba.
Murmushi magana na yadan yi sun ci abincin sosai suka wanke hannu na fita da kayan bayan sun gama ne suka ce inyi masu iso su gaida mama zasu tafi.
Fita nayi na kira ya Amina ina fada masu abinda suka ce man ita ta fada ma mama zasu shigo su gaida da ta nan mama ta gyagyara suka a kofan daki aka shimfida masu tabarma suka zauna.
Bayan fitar sune na samay su a waje har sun shiga mota ina isowa Yusuf ya miko min waya kallon wayan nayi ina tambayan shi ta may yace ogana yace a baki tunda naki ta lalace kiyi maneji da wanan kafin ki dawo Abuja a sai maki wani.
Amma don Allah kada ki kara kashe muna waya mu kira bamu samay ki ba ran mu baya dadi rashin jin ki da bama yi a koda yaushe.
Kai na girgiza tare da fadin kubar wayan ku ni wayata lafiya take kashewa nayi kawai don, , ,
Ban karasa ba naji yace don kada kiji muryan mu ko may khadija nace kawai abubuwa ne sukai min yawa a nan bata waya nakeyi ba.
Yaushe zaki dawo school don hutu ya kara nake gani nace sai anyi sunar yayan mu data haihu zan dawo uffer week may zaki zauna yi har uffer week Abdulsamad ya tambaya.
Ba a gida nake ba tare da iyayyena na bashi amsa da hakan yace ranan tuesday zan turo a dauke ki yana fadin haka ya rufo kofan motar Yusuf yayi min sallama tare da kara mika min wayan suka tafi.
Azato sun tafi ne sai ga yara suna shigo da drinks da wasu abubuwa a kwali wai i ji su ina daki ina kallon wayan daya ba babban wayace mai tsada fara kwal da ita.
Ya Amina ne ta shigo dakin tana kallo na tare da fadin wai shi baya gajiya da wanan daiwaniyar da yake haka ne kuma kin ce ba soyayya kuke dashi ba.
Wayan da ya bani ne na miko mata ta karba tana fadin ta maye wanan kuma nace shiya bani do kawai nace tawa ta samu matsala ne yasa basu samu na .
Abin nayi ne ashe yanzu a ka fara wasan da ba ansan maci tuwo ba sai miya ta kare nace ba wani wasan da aka fara indai nice da na koma zan kakabe shi in huta da zancen su gaba daya.
Tace ai wanan da alama kin samu kaska baya kakabuwa wasan dadi don ko ya fiki dabara yanzu gashi ya gama daure ki a gurin daddy da mama ko.
No way to exscape daga tarkon shi a kwai game da na sani kan nan gaba din ba karamin aiki kika banbaro muna ba yarinya.
Kai ke ya Amina ke kekara ma abin wuta wallahi ni may zanyi da mijin da wata ke juyawa a gidan shi kina so in shiga nima in koma yar bi ce kamar fati ?
Ke zaki tsayane ki zauna kamar ita a wirin shi ta kai zaune tana fadin da farko ina tsoron abinda ke shirin faruwa tsakanin ku da shi.
Amma yanzu zuwa na gida da daddy ya wayar min dakai sai hankali na ya kwanta da zance nake ganin kece haske da zai yaye duhun da Abdulsamad din ya shiga.
Ya Amina ki bar wanan magana kimun fatan alheri a rayuwana ba irin wanan fatan ba na shiga wurin da fitina ta nuna kan ta a fili.
Khadija kin taba ji ko ganin Abdulsamad ya taba bata lokacin shi ga wata mace irin haka amma sai gashi a kanki abubuwa na ta shirin faruwa a tsakanin ku.
Na tabbatar da su hajiya mama zasuyi fari ciki da jin wanan labarin don wata kila adduan su ne ya fada kan ki.
Shiru nayi ina sauraren ta tace abu daya zuwa biyu ne na farko gaba dayan mu sai mu dage da addua gaba dayan mu na biyu kuma kiyi kokari ki cusa mashi so da kaunar ki ta yadda buzuwa ba zata iya mashi gibi ba.
Har muka gama magana ta fita ban iya cewa komai ba ta barni ina cike da tunane a raina na yadda abubuwa ke zo min a haka.
Sai dare sosai suka shiga Abuja inda Yusuf ya aje shi gida ya nufi nashi gidan da motar shi da ya bari gidan don tafiya da ba shiri sukayi.
Ko da yashigo gidan shiru yaji kamar yau mutanen gidan nashi basu ciki bai tsaya falon ba ya haura sama inda dakunan kwanan su yake.
Ga kaya nan ko ina a warwatse ko ina agidan anyi amfani dasu an kasa kawar dasu don tsabagen kiuya da lalaci har ya kai kofan dakin ya tura a hankali ya shiga.
Baiyi mamakin ganin ta a yanayin da ya samay ta ba don duk kwanankin nan a yamutse take a gidan ba wani gyara ko kwaliya da take samun yi .
Tana zaune saman gado gashin kanta a wawatse ba gyara ta dago ido ta kalle shi tare da kallon agogon bangon dake dakin tace Samad ina kafito a wanan lokacin.
Aikena kikayi da kike tambayana ya bata amsa tare da wuce wa wurin wardrobe din shi yana rage kayan jikin shi.
Samad neman mata kafara ko mai yace idan na nemay su ba namiji nake ba wallahi baka isa ba ta fadi da karfi ya juyo gare ta yace ban isa ba fa ki ka ce Nafisa.
Tace baka isa ba wallahi may na rage ka dashi a wanda ban baka da har zaka lakanci neman mata a yanzu daga sama.
Ya ciro wani dogon jallabiya baka yana fadin waya san iyaka Nafisa baki san komai ba banda son kan ki da kashin kudi abaki kuma baki godiya.
Kudi dole ne ka bani don kasan sune buri na kuma akwaisu bathroom ya shiga ya barta ta ta fadin bakaken maganganu gare shi har ya fito bata fasa magana ba.
Gadon ya duba yace duba don Allah wai a inda mutum zai kwanta ke nan ya fara kakabe shimfidar da wani dan karamin towel daya fito dashi daga ban dakin.
Yace mace sai tarin kazanta na fada maki bani son wanan kazantar taki amma ke abin sai gaba yake yi gare ki.
Ai kasan a haka nake kuma ka aure ni na dauka idan kin shigo cikin daula zaki canza ne ashe ni ban san abin a jinin ki yake ba.
Kazantar ne a jina na yake Samad yace in ba ajiin ki yake ba za a ce duk yawan ku baku iya gyaran wuri tace samad wa kake so in sa aiki a cikin gidan nan.
Kafa san daga kanne na sai yayyena anan sai kuma kawu naina da gwago na yace may yasa kika boye min hakan da farko kin fada min yan aiki ne kika samo min kuma biyan su nake duk wata.
Sai yanzu zaki ce min wai yan uwan ki ne na jini baki iya saka su aiki a gidan nan kin zo gidan nan kin samu masu aiki kika ce baki yarda dasu ba.
Na baki go ahead da zaki kawo wanda kika yarda su suyi mana aiki ashe ke yaudarana kikayi ki kwaso yan uwanki kika cika min gida dasu.
Samad ta fada da karfi kawo yan uwana danayi a gidan shi ne kake kira da yaudara yace yaudara ne mana mutum da gidan shi ba dama ya shigo ya huta a ciki yaji dadin ranshi.
Samad yau ni kake fada ma haka don ka gani da ciki kake kokarin ka wulakantani yanzu ko may babu zancen wullakanci sai maganar gaskiya.
Haukace mai tayi ranan tana fadin bai isa ya rabata da yan uwanta ba don tare ya gansu ya kuma yarda ya aureta a hakan.
Haka ya kwana da tarin bakin ciki babu kunya washe gari kuma sai gata ta neman sulhu dashi don dai kawai ya biya mata bukatan ta don bata iya hakkuri dashi duk yadda ranta ya baci dashi ga wasu kudi da take son karba a wurin shi masu yawa don ai mata aiki a kan shi.
Bata samu ko daya ba ranan don asubanci yayi ya fita wirin aiki da wuri koda yaje gurin aikin bai iya aiwatar da komai ba.
Yusuf ya shigo ya samay shi a haka yake tambayan shi wai may ke faruwa dashi ne bai tsaya boye mashi ba ya sanar dashi halin da yake ciki da nafisa a gidan shi.
Da yan uwanta da suka cika maigida da sunan yan aiki ta kwaso yana biyan su a wata ashe ba haka abin yake ba.
Kai inji Yusuf lamarin Nafisa akwai daure kai wallahi Abdul yace nima bashi ba kazantar nan ke damuna Yusuf.
Ka san dai halina da kyakyami wallahi komai na gidan nan yanzu kazantar shi nake ji in ba ruwan gora ba ban iya cin komai a gida na .
Yusuf yaya zanyi da wanan masifa dana dauko ma kaina nasan ina son nafisa sosai why da ba zata gyara halin ta ba may ye ban ma Nafisa a rayuwan ta.
Kamar karta samu cikin nan yanzu abin ya karkare jagule mata mace ba wanka ba saka sutura a jiki idan anyi magana sai tace wai lalurar cikine haka take cikin ta.
Au dama ta taba ciki ke nan naga auren budurwa mukai mata wani kallo ya jefe shi dashi yace Nenan yar waye idan bata taba haihuwa ba nima daga bayan nan na fahinci yar tace ashe.
Yanzun haka zan kare ga yawon restaurant ina cin abinci a garin nan kamar wani mara galihu dani.
Kai innalillahi abin nakune akwai daure kai wallahi saukin abin khadija zata dawo next week zaka dan samu sauki a awurin ta.
Saukin may zan samu a gurin ta ya tambayi Yusuf a yanayin rashin fahintar maganan shi Yusuf yace koba komai tunda ta iya girki naga ai zata dan dinga maka idan tana da time.
No ban san in jefa rayuwan yarinyar ga halaka ko kadan nafi son ayi komai a kaidance yace kana nufin auren ta zakayi.
Shiru yayi ya dafe kanshi bai sake magana ba ya fahinci bai son maganan don haka ya kyale shi tare da canza topic.
Yusuf na fita ya jawo wayan shi ya kira layina muna gida ya Hauwa mai jego ya kira wayana ina wanke kayan miya a kitchen aka kawo min wayan.
Sai da ya kusa katsewa na dauka tare da sallama yace ina kika shiga kika bar waya na ruri haka nace ina kitchen ina girki wa ya hauwa da ta haihu.
Kuna gidan ta ke nan ya tambaya nace eh may kike girka mata nace miyar shuwaka zanyi mata da tuwon shikafa.
Ke wa ya koya maki girki haka ne wai nace girkin ma har sai an koya ma mutum yin shi idai kana mace ai zaka iya girki ko wani iri dole.
Aranshi yace ga macen da ta san kanta ba sai kuma yace ke wace irin yarinyace da baki iya kiran mutane kiji ko sun sauka lafiya ?
Na aiku tafiyan dare ne ko ni na saka ku yin tafiyan da kuyi din yace OK haka zaki ce ma nace haka din ne ma ai.
Sai naji ya kashe wayan dariya nayi nace zaka kaji ai ka daina in yar da magoro in huta da kuda har dare muna gidan sai tara muka dawo gida a gajiye .
Ban kara bi ta kanshi ba har akai bukin suna aka watse lafiya drinks din da suka kawo muna yayi muna rana do shi mukai amfani dashi wurin taron sunan.
Mun fara shiri don tare da yaAmina zamuyi tafiyan kamar yadda na fada mata yace zai turo mota hakan ne ya faru sai ga mota zuwa sha biyun rana ya tsaya a kofan gidan mu.
Nan muka fito mukayi haraman tafiya nasha nashi ha a wurin mama da daddy kafin mu wuce muka dauki hanyar Abuja tare da ita don zata kwana a wurin mu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
0 comments:
Post a Comment