Ni kuwa da na kasance mai hali irin na Mahaifinmu wato son more rayuwa sai tamu tazo d'aya, yana matuk'ar sona, duk abinda nake so shi ake mani, ina taka duk wanda naso, kuma yarinya sai idan batayi mani ba amma sai nayi kok'arin lasar zumarta, wasu basa tab'a sanin nine na aikata hakan agaresu, domin wani lokacin yarana nake sawa su sato mani yarinya kuma sai sun gusar mata da hankali kafin su kawota.
Har na gama abinda zanyi da ita su maida ta bata tab'a sanin abinda ya faru, hakan yasa nakeyin komai hankali kwance, yayin da wasu matan sune suke kawo kansu gare ni.
Tun ranar dana fara ganin Halima na kwad'aitu da ita, duk da itace mafi k'arancin shekaru da nasan na tab'a hayk'emawa, naso na cireta araina saboda ganin k'arancin shekarunta amma hakan beyuwu ba, nafi wata ina fama da kwad'ayinta, nayi yaki sosai da zuciyata amma shed'an yariga ya kwad'aita mani ita, a hankali na fara mata magana sai dai bata tsayawa kula ni, kasancewar ta hanyar gidan mu take wucewa zuwa makaranta yasa duk lokacin da zata wuce ni kuma nake fitowa domin na ganta.
Ganin na rasa hanyar da zanbi yasa kawai nayi amfani da abinda nakema sauran matan, Halima itace mace ta farko dana tab'a kaita cikin gidan mu da sunan fyad'e, domin duk abuna banayi agida, sai dai idan sauran 'Yan matana ne su wannan ina kawosu har d'akina, sai gashi na kasa hak'ura akai mani Halima inda nake kai sauran matan.
Wata rana da yamma ina zaune na gama had'a komai ina jiran wucewarta, tun ina jiranta har na fara fidda rai saboda aranar ta makara, har na tashi zan koma gida na yanke shawarar zansa a sato mani ita sai kawai na ganta zata wuce, farin ciki nayi, kasancewar unguwar mu bata da hayaniya yasa nayi saurin shan gabanta.
A tsorace tayi baya tana neman hanyar guduwa amma nayi saurin saka mata kyallen hannuna, dama na aiki mai gadin gidan mu, saurin d'aukarta nayi muka shige ciki.
Ajiyar zuciya ya saki hawaye suna zubo masa, kallon Halima yayi yana fad'in ban tab'a aikata fyad'en da nakasa samun natsuwar zuciya ba sai akanta, sam bana baccin kirki.
Bayan da komai ya faru sai gashi ta farka, nayi mamakin farkawarta domin maganin yana da k'arfi, amma sai ta farka kuma ta sheda ni, ganin haka yasa na tsoratar da ita, tashi tayi ta bar gidan, sai da nabi bayanta naga tayi hanyar gidansu, agaban idona ta zube hakan ya tabbatar mani maganin bai saketa ba, komawa nayi gida har lokacin maigadi bai dawo ba.
Bayan nashiga d'aki jinin da nagani ya tashi hankali na, saurin shiga wanka nayi amma jikina yana rawa, kasa daurewa nayi na kira d'aya daga cikin yarana nace yayi sauri yaje yaga halin da take ciki kuma ya gano mani asibitin da za'a kaita.
Ina tsaye a harabar gidan mu sai ga Dady, ganin da yayi mani cikin tashin hankali yasa ya tambaye ni, bana masa k'arya hakan yasa na fad'a masa komai, nan take yace kada na damu na bari muji asibitin da za'a kaita.
Muna nan Gayen ya kirani ya sheda mani yaga Mahaifinta ya samo mota sun nufi asibitin Dr. Kaseem, mamaki ne ya kamani nasan talakawa ne amma suka nufi asibitin kud'i, Dady yace kila baya son ya kaita babban asibiti atsaya b'ata masu lokaci wajen kiran 'yan sanda shiyasa ya kaita can.
Nan take Dady yakira Dr. Kaseem ya fad'a masa halin da ake ciki, kuma yace kada a karb'i kud'in su. A lokacin ya fita amma yace zaiyi sauri ya koma asibitin kuma zai rufe komai.
Wannan dalilin ne yasa Dr. Kaseem ya kori sister Asabe ya duba Halima kuma ya rubuta bayanin k'arya, domin yace har d'inki yayi mata.
Bayan kwana biyu da faruwar haka sai muka samu labarin an kaini kotu, hankalina yayi matuk'ar tashi, kuka nasa Dady yace kada na damu babu abinda zai faru, nan take yakira Dr. Sa'eed ya fad'a masa abinda yake so, babu b'ata lokaci ya shirya sakamakon k'arya akan rashin lafiyata, har gida ya kawo ma Dady suka tattauna yanda komai zai kasance, haka ya cika masa jaka da kud'i ya tafi.
Wallahi tun daga lokacin da haka ta faru ban sake samun natsuwa ba, hakan yasa a yanzu naga ya dace na fad'i gaskiya, kuma zan amshi ko wane hukunci aka yanke mun.
Shiru kotun tayi ana sauraren kukan Sameer. Dadynsa kuwa zama yayi jiki a sanyaye yana goge zufa, gashi d'an siyasa yana tsoron hakan ya tab'a masa mutuncinsa.
Jiki a sanyaye Alkali ya gama rubutu, gaba d'aya kunyar kallon Mahaifin Sameer yakeyi, babu yanda ya iya, Allah ma yaso Sameer ne ya tona komai yasan bazasu zargeshi ba.
Bayan ya kammala rubutu ya d'ago yana kallon Sameer...... Bisa hujjojin da aka gabatar ma wannan kotu da kuma samun babbar sheda daga bakin wanda ya aikata laifi cewar ya amince shine ya aikata wannan laifi, wannan kotu mai adalci ta yanke ma Sameer hukuncin daurin wata biyar agidan yari ko kuma tarar naira dubu d'ari biyar, sannan zai biya Halima tarar naira million talatin domin keta mata haddi da yayi, haka kuma zai cigaba da kula da lafiyarta har ta samu sauki, sannan idan rabo yashiga tsakanin su zai kula da ita har ta haihu da bayan ta haihu har zuwa lokacin da zata yaye abinda ta haifa ta bashi abunshi, idan kuma zata rik'e masa to shine yake da alhakin kula dasu.
Dr. Kaseem da Dr. Sa'eed zasu biya tarar dubu hamsin-hamsin bisa kamasu da akayi da kawo ma kotu shedar k'arya, idan aka sake kamasu da makamancin irin wannan laifin kotu zata soke lasisin su.
Kallon mutane yayi yana fad'in ina fatan wannan hukunci zai zama izna ga sauran mutane. Saurin tashi Brr. Bajinta yayi yana fad'in ina neman alfarmar wannan kotu data k'ara ma Sameer tarar da zai biya Halima saboda ya keta mata haddi, ya rabata da abinda yafi komai muhimmanci agareta. Nagode ya mai shari'a.
Jin jina kai Alkali yayi yana fad'in bisa duba da k'orafin lauya mai kare Halima wannan kotu ta amshi rokon ka, dan haka Sameer zai biya Halima tarar naira million hamsin, kuma dole ne ya biyasu akan lokaci... Kotttt.!!!!!
Gaba d'aya kowa ya tashi ana jinjina ma Alkali bisa hukuncin adalcin da ya yanke, haka kowa yarik'a masa jinjinar ban girma, wannan adalci da kowa yake samu yasa suke k'ara son Alkalin su.
Hannu Brr. Bajinta ya bama Ra'eez yana fad'in a wannan shari'ar dai na kada ka, amma duk da haka kayi kok'ari, nan gaba sai kayi kok'arin kada ni.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in na tayaka murna, amma nan gaba ka rik'a kok'arin tsayawa akan aikin ka kadena kok'arin juya akalar kariyar ka zuwa ga wani daban, sannan karika aikata abinda ya dace ba sai an fad'a maka ba.
Cira idanu ya fara yana yaken dole dan ya tuna d'azu da Ra'eez ya duko yana fad'a masa yayi sauri yatashi ya nemi a k'ara ma Halima kud'i hakan zaisa ya wanke kansa wajen mutane, hannunsa ya cire yana fad'in haka ne, kuma nagode.
Jabeer ne yaja Ra'eez suka bar wajen. Kusa da Sameer suka je wanda yake rungume jikin Mahaifiyarsa dan Dadynsa ana gamawa ya sulale ya bar wajen.
Dafa Sameer Ra'eez yayi yana fad'in kayi abun kirki, kuma har abada baza kayi danasanin abinda kayi ba, kaci sa'a ba kotun musulunci bace da sai kasha bulala, amma yanzu kana da damar biyan dubu d'ari biyar idan baka son zaman gidan yari.
Da sauri Mamansa tace kud'in zamu biya, mungode sosai lauya, idan bazaka damu ba ina son ganin ka idan kana da lokaci. Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in ayanzu Alhaji ya d'auki zafi, amma zanzo idan na samu lokaci.
Haka suka fito ita da Sameer suka wuce gida 'yan jarida sai d'aukarsu hoto sukeyi. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in wannan itace shari'ar ban dariya.
Jabeer yace wallahi yanda kasan a film, ban tab'a ganin irin wannan shari'ar ba, daga kai har Brr. Bajinta kun bani dariya. Ra'eez yace ai shiyasa na barshi ya fara, da yake be iya wasan ba ai kaga kowa ya ganoshi.
Jabeer yace amma nayi mamakin yanda Sameer yayi saurin amsa laifinsa. Ra'eez yace kila hakan yafi masa sauki. Kallonsa Jabeer yayi yana fad'in ban yarda da kai ba, anya babu sa hannunka? Dariya Ra'eez yasa yana fad'in muje ofis.
Iyayen Halima basu tsaya jiran Ra'eez ba dan ya fad'a masu ana gamawa su wuce gida baya son agansu atare. Duk da sunji haushin Brr. Bajinta amma abinda yayi daga k'arshe yasa sukaji dad'i, hakan yasa sukaje sukayi masa godiya.
Murmushi yayi yace haba babu komai, ai dama nace maku mune zamuyi nasara. Malan Haruna yace nawa ne kud'in ka? Brr. Bajinta yace haba kyauta nayi maku. Sosai sukayi masa godiya suka wuce cike da farin ciki.
Zagaye kawai Alhaji Barau yake a ofis d'insa, ya rasa taya zai kalli abinda Ra'eez yayi masa, ya akayi ya canza komai beyi amfani da abinda suka bashi ba? Dole ya turkeshi sai ya fad'a masa abinda yake nufi. Waya ya d'auko yana niyar kiransa.
K'ofa aka bud'e hakan yasa ya aje wayar. Alhaji Marusa ne yashigo fuskarsa d'auke da murmushi. Bayan ya zauna Alhaji Barau ya mik'a masa hannu suka gaisa dan shima haushinsa yakeji akan abinda yayi masu.
Daurewa yayi dan baya so ya gano ya san komai. Alhaji Marusa yace Babban Alkali da girman kujerar ka. Alhaji Barau yace zaka fara ko.
Dariya Alhaji Marusa yasa yana fad'in alokacin da nace kada ka bama Ra'eez shari'ar me kace? Na fad'a maku nifa jikina be yarda dashi ba, yaron da yazo a ranar farko ya cinye babbar shari'ar da aka sha wahala akanta taya kake tunanin zai amshi tayin rashin gaskiya? Tun farko na fad'a maku amma bakuji ba, sai kace wai zasu iya d'aukarshi, to ko sun d'aukeshi ba sai yana da hujjar nunawa ba, haba Alhaji Barau ya kake so kabar tsohuwar basirar ka ta gushe ne.
Ajiyar zuciya Alhaji Barau ya saki yana fad'in kai dai ka bari kawai Alhaji Marusa, kwanan nan na rasa abinda yake damuna, ganin yana neman yarinyar wajena yasa nayi tunanin zaiyi duk abinda na sashi sai gashi ya watsa mani k'asa a ido, wallahi yanzu daka shigo kiranshi nayi niyar yi naji dalilin da yasa zaiyi mani haka.
Dariya Alhaji Marusa yasa yana fad'in shiyasa nace basirar ka ta tsufa, taya kana Alkali zaka kira lauyenka ka titse shi akan shari'ar da yayi bayan kasan gaskiya ce, ai Brr. Bajinta ne kawai ze maka haka ka titse shi a zauna lafiya.
Abinda nake so da kai ka nuna baka damu ba, kuma kayi masa jinjinar ban girma ka gode masa akan abinda yayi, kuma ka fad'a masa baka san haka abun yake ba amma kace ka gode da yaje ya sake bincike, ina tabbatar maka idan ka fad'a masa haka zai yarda da kai, gashi ka yanke hukunci yanda ya kamata, domin ko wannan kud'i da za'a bata zai inganta mata rayuwar ta, kaga zaka fita daga zarginsa.
Jinjina kai Alhaji Barau yayi yana fad'in nagode da zuwanka Alhaji Marusa da na kwafsa, damuwa ce tamun yawa hakan yasa na kusa rasa dabarata, amma zanyi yanda kace.
Tashi Alhaji Marusa yayi yana fad'in zanje na rarrashi Alhaji, ya godema Allah da ba kisa yaron yayi ba, gashima har ka bada zab'i biyu, kuma nasan bazasu barshi ya shiga gidan yari ba.
Alhaji Barau yace ka gaishe shi kuma ka bashi hak'uri nagode. Alhaji Marusa yace zaiji.
***
Ina jinka Ra'eez, Jabeer ya fad'a yana sunno kanshi a fuskar Ra'eez. Dariya yayi ya tureshi yana fad'in kaga Malan kada ka dameni, taya zaka zo a wajen aiki ka ishe ni na baka labari idan wani yaji fa, kawai ka bari idan muka fita na fad'a maka.
Jabeer yace ai gashi can ana kiran sallah muje muyi idan muka fito sai ka bani. Ra'eez yace muna fitowa na tashi dan wallahi na gaji, kasan dama idan nayi shari'a bana son nayi zaman aiki. Jabeer yace aiko sai dai mutafi tare dan bazanji dad'in zama wajen nan baka nan ba.
Ra'eez yace idan kuma na bar kotun fa? Da sauri Jabeer ya kalleshi yana fad'in ban gane ba? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in ina nufin idan aka mana canjin wajen aiki. Jabeer yace insha Allahu hakan bazata faru ba. Ra'eez yace Allah yasa.
***
Bayan sun gama sallah yashiga domin ya fad'ama Alhaji Barau zai wuce gida.
Cike da jin nauyi Alhaji Barau ya kalleshi yana fad'in Ra'eez na rasa bakin da zan maka godiya, hakika zuwanka wannan kotun alkhairi ne a wajena, so biyu kana ceto ni daga yanke hukuncin danasani, bazan iya biyanka da komai ba wallahi, nagode sosai, sam banyi tunanin haka abun yake ba, shiyasa wanda nasa yaje yayi mani binciken yana kawowa ban tsaya dubawa ba na baka saboda nasan na yarda da kai, ashe abubuwan da suke ciki ba gaskiya bane, nagode sosai da ka sake bincike, duk da kayi kok'ari baka fito fili ka nuna kasan gaskiya ba, amma kayi aikin da yakamata ace Brr. Bajinta ne yayi, tabbas nasan wannan shari'ar ta yau ta juya ma mutane kai, domin ku duka lauyoyin an rasa gane a wane b'angare kuke, gaskiya nagode sosai, shima Brr. Bajinta ya taimaka daya gyara kuskuren da ya kusayi.
Murmushi Ra'eez yayi yace ai bakomai duk taimakon kaine, nima nasan bazaka bani abinda za'ayi rashin gaskiya aciki ba, hakan yasa dana duba shedar nasan baka duba ba, shiyasa banyi maka magana ba naje na sake sabon bincike.
Alhaji Barau yace naji dad'i sosai tunda kasa bamuji kunya ba. Ra'eez yace ina son zanje gida kaina yamun nauyi ne. Murmushi Alhaji Barau yayi yace haba bakomai kaje kawai nima yau da wuri zan tashi nagaji.
Tashi yayi yana masa sallama, da sauri Alhaji Barau yace zaka lek'a wajen mutuniyar ko? Murmushi ne ya kwace ma Ra'eez babu shiri, duk'ar da kai yayi alamun kunya yayi waje da sauri.
Dariya Alhaji Barau yasa yana fad'in Allah nagode maka daka zab'a mani suriki nagari, gaskiya Raheena tayi dace, Allah nagode maka da banyi saurin sata ta fiddo da miji ba ashe yana zuwa.
Da k'yar Jabeer ya bar Ra'eez dan yace sai ya tsaya ya bashi labarin yanda akayi, shi kuma Ra'eez yace ya gaji sai dai suyi waya anjima. Babu yanda ya iya dole ya kyaleshi ya tafi.
Bayan sunyi sallama da Jabeer yana kok'arin shiga mota yaji anyi masa sallama. Juyowa yayi tare da amsawa. Murmushi ya saki ganin kamar yasan fuskar wanda yake tsaye.
Hannu ya mik'a masa yana fad'in barka da kok'ari Brr. Ra'eez ina tayaka murna akan wannan nasara da kayi a wannan shari'a.
Hannu Ra'eez ya bashi yana fad'in nagode, amma kamar nasan fuskar nan? Murmushi yayi yana fad'in *Rafeek Labaran Zaki*, Ma'aikacin gidan redion *Liberty*.
Jinjina kai Ra'eez yayi yana murmushi yace yanzu kam na tuna, nagode Rafeek amma ai ba nine nayi nasara ba.
Murmushi Rafeek yayi yana fad'in wanda ka kare dai ya faad'i amma ai kaine hasken shari'ar, gaskiya kayi matuk'ar burge ni, na saurari shari'ar ka ta farko a wannan kotun, duk da alokacin ana gamawa na tafi saboda saurin da nakeyi, naso mu had'u amma wani aiki yasha kaina ga tafiye-tafiye, sai a wannan karon naji labarin wannan shari'ar shine nazo domin naji yanda zata kasance, sai gashi nazo nasha mamaki, gaskiya kai d'in na daban ne.
Ra'eez yace nagode. Rafeek yace gaskiya ina so mu kulla abota idan bazaka damu ba, yanzu naga kana sauri amma zan amshi lambarka duk lokacin da kake da lokaci zan iya kawo maka ziyara.
Kallonshi Ra'eez yayi, yasan dai ya girme mashi sosai, sai yaji kunya da yace zasu kulla abota. Kamar Rafeek yasan abinda yake tunani yayi saurin fad'in nayi maka tsufa ko? Dariya Ra'eez yasa yana girgiza kai.
Rafeek yace ita abota ai ba'a duba girma, idan na yarda da hankalin mutum ina abota dashi koda na haifeshi bare kuma nasan ban haife ka ba, dan haka kada ka damu kawai naji ka kwanta mani ne.
Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in nagode Yayana, kada ka hanani kiranka da haka domin nima naji inaso na kiraka da hakan domin ina buk'atar hakan.
Murmushi Rafeek yayi yana fad'in nima ina buk'atar samun K'ani domin na rasa nawa shekaru da yawa, amma tunda na samu wani nafi kowa farin ciki.
Wayarsa ya mik'a mashi, amsa yayi yasa masa lambarsa ya kirashi yana fad'in ga tawa nan, sai munyi waya nagode. Ra'eez yace nima nagode.
Mota yashiga yana kok'arin kunnawa wayarsa tayi k'ara, yana dubawa yaga lamba ce, yana d'auka yaji muryar Sameer da alamun kuka.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in lafiya Sameer? Cikin sanyin murya Sameer yace ina so mu had'u ne ko zaka mun kwatancen gidan ka? Ra'eez yace kada ka damu bara nazo Mamanka ma tace tana son gani na.
Sameer yace nagode sai kazo. Kashe wayar yayi yana murmushi, yaso yaje gida ya huta anjima yaje wajen Ummunsa amma dole yaje yaji dalilin kiran.....
Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
3⃣0⃣
Cikin kuka Sameer ya rungume Ra'eez yana fad'in nagode sosai Ra'eez da abinda kamun, wallahi yanzu ina jin sanyi araina, gashi dai na girma amma na kasa gane hakan, abinda nake so yanzu naje na nemi yafiyar Halimatu, da zata amince dani wallahi zan aureta ma.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in bakomai kadena kuka, tunda dai har kayi nadama Allah zai yafe maka, sai dai kaje ka nemi yafiyar Halima, idan da hali zaka iya tuna sauran matan da ka lalata ma rayuwa suma kaje ka basu hak'uri sannan kayi masu alkhairi hakan zaisa ka sake samun nutsuwar zuciya sosai.
Zama Sameer yayi yana fad'in zanje, wallahi zanje Ra'eez, duk da nasan ba lallai bane na iya samun wasu amma duk matan da nayi harka dasu nasan su, nagode Allah da basu da yawa kuma zanje na nemi yafiyarsu, amma ni ina son kashige mun gaba muje gidan su Halima.
Ra'eez yace kada kadamu zan zo muje, amma shawarar da zan baka ka ajiye kudirin ka na son aurenta a gefe, ina mai tabbatar maka Halima bazata amince da kai ba, duk da hakan taimako ne agareta amma baza ta amince ba, gara ka bata hak'uri idan akwai taimakon da zaka sake mata kayi mata kaje ka cigaba da istigfari ka samu wata mata can daban ka aura hakan zai fi maka kwanciyar hankali.
Jinjina kai Sameer yayi yana fad'in shikenan, dama tausayinta ne yasa nace zan aureta badan soyayya ba, saboda dama sha'awarta kawai nakeyi amma zanyi yanda kace.
Ra'eez yace kaga tunda baka sonta gara ka hakura, domin shi aure soyayya ce jigonshi, Allah ya k'ara tsare gaba.
Sameer yace amin, amma dan Allah a ina ka samu hoto na? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in tunda komai yawuce ai shikenan ba sai kaji ba.
Sameer yace shikenan, ai nasan sirrin ku ne na lauyoyi na barshi. Maman Sameer ce tashigo bakinta d'auke da sallama.
Bayan sun gaisa ta kalli Ra'eez tana fad'in nagode sosai, dama godiya nake so nayi maka domin ka taimake mu, sam banyi danasanin fad'uwar mu ba, domin gata kayima Sameer, gara mutum yaji kunyar duniya akan ta lahira, gashi ta silarka Sameer ya natsu, shima Alhaji da yayi fushi na sameshi nayi masa bayani kuma ya fahimce ni yace ayi maka godiya yana jin kunyar ka ba zai iya fitowa ba.
Ra'eez yace haba babu komai Allah ya tsare gaba. Sukace amin. Kallon Sameer tayi tana fad'in Alhaji ya tura maka duka kud'in da za'a kai kotu, sai ka shirya gobe kaje Ra'eez yayi maka jagora ka kai kud'in a aika ma su Halimar.
Sameer yace nagode Mamy, kuma Ra'eez yace zai rakani wajen Halimatu na bata hak'uri. Mamy tace angode sosai Ra'eez.
Tashi Ra'eez yayi yana fad'in nizan tafi, Sameer sai munyi waya kila ko zuwa goben ne sai muje can. Tashi Sameer yayi yana fad'in nagode sosai.
Mamy tace ka gaida gida dan Allah karik'a zagayowa muna gaisawa. Ra'eez yace insha Allahu. Sallama yayi mata suka fita shida Sameer.
Sai da ya shiga mota kafin Sameer ya rufe masa k'ofar yana masa godiya. Sai da ya b'acema ganinsa kafin ya koma gida cike da farin ciki.
*** ***
Sai yamma sosai ya isa asibiti, bayan sun gama shiriritar su da Ummunsa ya wuce ofis d'in likita dan Dr. Saddek ma yazo yana jiranshi.
Bayan sun gama gaisawa Dr. Saddek yace gaskiya Ra'eez jikin Ummunka yayi sauki sosai, domin a hoton da mukayi mata akwai cigaba sosai, matuk'ar zata cigaba da tunawa da abubuwan da suka faru abaya to zata dawo hankalinta, shiyasa yanzu an canza mata magani kuma akwai cigaba.
Ra'eez yace nagode sosai likita Allah ya saka da alkhairi, bansan da abinda zan saka maku ba. Dr. Sadeek yace haba ai babu komai, Allah dai ya bata lafiya. Ra'eez yace amin. Sallama yayi masu yawuce gidan su Rumaisa.
Tun a hanya Jabeer ya kirashi akan zaije gidansa sai Ra'eez yace ya sameshi gidan su Rumaisa. Dariya Jabeer yasa ya fara zolayarsa, be kulashi ba ya kashe wayar yana dariya.
Yana zaune bayan sun gama gaisawa da Mama tana masa murnar nasarar da yayi Jabeer ya kirashi. Tashi yayi yaje ya shigo dashi.
Bayan sun gaisa da Mama tasa Rumaisa ta kawo masu abinci. Ra'eez yace Mama ki barshi an kusa kiran sallah idan mukayi sai muci. Mama tace ai shikenan.
Jabeer yace Rumaisa bazaki fito mu gaisa ba? Murmushi Mama tayi tace ai tana jinka. Ra'eez yace ya akayi yau bata je islamiya ba ma? Mama tace kanta ne yake ciwo harta shirya zataje naga yanda jijiyoyin kanta suka tashi shiyasa nace tasha magani ta kwanta sai Abdallah ne kawai yaje nasan shima yanzu yana hanya.
Cike da damuwa Ra'eez ya kalli d'akin Rumaisa, badan yana kunyar Mama ba sai yaje ya ganta. Jabeer yace Allah ya bata lafiya ciwon kai beda dad'i. Mama tace amin.
Mama tace ya shari'ar taku ta kasance kuma? Zunguro Ra'eez Jabeer yayi yana fad'in ana magana fa. Harara ya buga mashi yana kallon Mama.
Murmushi tayi tana fad'in kaje ka duba jikin Rumaisar kafi jin dad'in bamu labarin. Rufe fuska Ra'eez yayi yana fad'in kai Mama! Dariya tasa Jabeer yace Mama ashe dai kin harboshi? Murmushi Mama tayi tana fad'in bara nashiga ciki na kira maka ita.
Da sauri Ra'eez yace dan Allah Mama ki zauna dama labarin nazo baki. Dariya Jabeer yasa yana fad'in haka ne Mama kizauna nima labarin zai bani sai ja mani aji yake.
Zama tayi tana fad'in ina jinka...... Labarin yanda shari'ar ta kasance ya bata har da zuwanshi gidansu Sameer.
Jabeer yace saura bayani akan hoton Sameer da yanda ya amsa laifinsa. Ra'eez yace wallahi idan maye ne kai ka kama mutum sai ka cinyeshi duka.
Jabeer yace naji kawai ka fad'a mana. Dariya Ra'eez yayi yana fad'in d'azu ma sai da Sameer ya tambayeni amma naki fad'a masa.
A cikin week end da na fad'a maka zan had'a komai, duk iya bincike na na rasa yanda zan samo shedar da zata nuna Sameer ne ya aikata laifin, Baba na kira nake tambayarsa basu da wani abu da zai nuna Sameer ne ya aikata laifin.
Sai yake fad'a mani alokacin daya d'aukota zasuje asibiti yana kok'arin gyara mata hijabinta yaji wani abu a akanta, yana dubawa yaga zobe shine ya cireshi ya aje, gashi nan ma zaije ya kaima Brr. Bajinta dan yana tunanin na Sameer ne.
Cikin sauri nace masa ya dakata zanje na amsa dan nasan ko ya bama Brr. Bajinta bazaiyi amfani dashi ba, bayan na amso nazo ina tunanin yanda zanyi dashi.
Komawa nayi unguwar su Sameer cikin sa'a na samo lambar wayarsa. Bayan na ajeta sai na shiga Whatsapp ina dubawa ko zan ganshi, cikin sa'a sai gashi, ina dubawa naga babu hoto a Dp d'inshi, har zan fita sai kuma na hau status ina cikin dubawa kawai naga ya d'ora wasu hotunanshi, yan dubawa sai naga hannunsa sanye da irin zoben da aka bani, saurin d'aukar hoton nayi.
Ban b'ata lokaci ba naje aka wanke mani hoton, sosai naji dad'in wannan hujja, ana gobe za'a shiga kotu nayi wani tunani, sai kawai na daure na kira Sameer, har ya kwanta bacci amma ina fad'a masa nine yayi saurin tashi.
Nan nake tambayarsa ya tabbata be bar wata sheda da zata tonashi ba? Sai yace mani yana da wata azurfa kuma tun bayan da abun ya faru be ganta ba, yasan kuma baya rabuwa da ita.
Anan na fad'a masa zanyi kok'arin nemota abinda nake so dashi ya fad'a mani gaskiya. Sai yace mun be aikata komai ba. Sai nace masa amma yace mun bayan abun ya faru bega zobensa ba.
Ganin na ganoshi babu b'ata lokaci ya tabbatar mani shine ya aikata laifin amma na rufa masa asiri, nan nayi masa nasiha na kuma ce masa ga zoben a hannuna, idan har ya iya fad'in gaskiya a kotu zan taimaka masa, kuma na tabbatar masa baza'a d'aureshi ba dole zab'i biyu za'a bashi nasan kuma Iyayensa bazasu bari a d'aureshi ba.
Anan ya amince zeyi abinda nace, amma nace masa kada ya fad'i gaskiya har sai na nuna zoben sannan. Kaji yanda mukayi dashi.
Jinjina Jabeer yayi masa yana fad'in gaskiya kai d'an baiwa ne Ra'eez, Allah kad'ai yasan irin baiwar da yayi maka amma ka gode masa.
Mama tace gaskiya kayi kok'ari, kaga ka fita daga zargin kowa, Allah dai ya k'ara tsare ka kuma ya baka sa'a akan shari'ar da za.... Saurin tashi Ra'eez yayi dan yasan abinda Mama zata fad'a shi kuma baya son Jabeer yasan komai yanzu.
Kallonshi tayi suna had'a ido yayi mata alama, nan take ta gane abinda yake nufi. Murmushi tayi tana fad'in duk son ganin Rumaisar ne baza'a tsaya na k'arasa addu'ar ba.
Jabeer yace idan ba ya ganta ba hankalinsa ba zai kwanta ba, ni Allah ma yasa ka bamu labarin dai-dai. Duka Ra'eez ya kai mashi da sauri ya mik'e yana dariya.
Tashi Mama tayi tana fad'in ai bakayi kokowa kana yaro ba gara kayi k'ari. Turo baki Ra'eez yayi yana hararar Jabeer da yake masa dariya.
Bayan Mama ta tashi ta turo Rumaisa. Fitowa tayi sanye da hijabi dan kanta yayi sauki. Zama tayi tana gaishe su kanta ak'asa. Saurin matsawa Ra'eez yayi yana fad'in Pretty na ya kan naki? Murmushi tayi tana fad'in ya warke ai.
Ra'eez yace bana son wasa da lafiyar ki kizo muje asibiti. Jabeer yace kaji mani mutumi, tace ta warke zaka jajibo mata wani asibiti.
Ra'eez yace malan ba ruwanka, kai da ko tsuntsu baka kiwo taya zakasan yanda ake kula da mutum ma, dan Allah idan ana maganar Iyali kadena tsoma baki.
Baki Jabeer ya rik'e yana kallon Ra'eez. Gwalo yayi masa ya zauna gaban Rumaisa ya juya ma Jabeer baya yana dariya k'asa-k'asa.
Tashi Jabeer yayi yana zungurinshi da k'afa yana fad'in ni zan wuce bazan iya tsayawa kallon kayan haushi ba. Dariya Ra'eez yasa yana fad'in kaje kayi fira da Baba Madu yanzu zan fito muje masallaci.
Wucewa Jabeer yayi yana murmushi, sai da ya kai k'ofa sannan yace daga masallaci wajen Raheenar ka zamuce ko dan nasan shine dalilin da yasa kace nazo nasan baka iya zuwa kai kad'ai.
A zabure Ra'eez yayi kanshi jin Bom d'in da yake had'a masa. Da gudu Jabeer yayi waje yana dariya. Kwafa Ra'eez yayi ya dawo wajen Rumaisa kada ta yarda da abinda yace.
**** ****
Kai amma Alhaji ka tsallake rijiya da baya, gaskiya Ra'eez d'an albarka ne, shiyasa nace maka gara azo ayi maganar auren su da Raheena tun kafin wata ta kwace matashi.
Gyara zama Alhaji Barau yayi yana fad'in abinda nake tunani kenan, jira nake yazo nasa Raheena tayi masa magana na fad'a masa ya turo iyayenshi ayi magana dan bana son aja bikin tunda mu duka kowa yana da halinsa.
Momy tace yauwa Alhaji dan Allah kada yawuce wata d'aya, kaga sai ka bani kud'i muje Dubai nida Raheena mu zab'o kayan da take so, idan so samune a cikin sati mai zuwa muje.
Alhaji yace haka ne, bakomai ku fara shiri zansa a nema maku Visa zuwa asabar sai ku tafi, dama bani da matsala akan kud'i dan akwai su a account kawai tura maki zanyi.
Murmushi Momy tayi tana fad'in dole ayi bikin da zai girgiza mutane, naji dad'i da muka tara yanda kowa zaizo ya dangwali arziki.
Alhaji yace ai da wuri zan bugo kati saboda kowa ya samu dan wannan babban biki ne. Momy tace Allah ya k'ara girma. Yace amin.
**** ****
Washe gari tunda wuri Ra'eez yaje wajen aiki, yana zuwa kai tsaye d'akin ajiyar tsofaffin kundi ya nufa yana addu'ar Allah yasa mai kula da wajen yazo.
Cikin sa'a ya sameshi, da sauri ya k'arasa ya fara gaishe shi kasancewar babban mutum ne. Murmushi mutumin yayi yana fad'in Malan Ra'eez ya gajiyar shari'ar jiya kuma? Ra'eez yace lafiya lau gajiya tawuce *Kawu Datti*.
Murmushi yayi cikin jin dad'in abinda Ra'eez ya kirashi dashi. Kallonshi Ra'eez yayi yana fad'in dama Kawu Datti akwai wata alfarma da nake son na nema awajenka idan babu damuwa.
Kawu Datti yace haba bakomai fad'i koma menene kaji Ra'eez. Cike da fatan nasara Ra'eez yace dama akwai wani kundi da nake son dubawa ne domin jiya Iyalan mutumin suka sameni ganin mun kammala wannan shari'ar suka kawo mani wata magana data girgiza ni, duk da nasan abun akwai wuya amma sun roke ni na tausaya masu kuma na masu alk'awarin zanzo na duba kundin ko bazan iya yin komai akai ba, shine nake son ka taimaka na duba kuma inason abun ya zama sirri dan Allah.
Murmushi Kawu Datti yayi yana fad'in kada kaji komai Ra'eez, kasa aranka tamkar da kurma kayi magana, domin bazan iya fidda sirrin makiyina ba bare kuma kai, wallahi Ra'eez tun shari'ar da kayi akan 'Yar uwata nake jinka araina, nasan baka san Amina 'yar uwata bace, idan baka manta ba shari'ar ka ta farko wata Amina daka tsaya mawa, to ita d'in tamkar 'Ya take awajena, kuma mijinta shine silar zamana anan gashi har yanzu ina cin gajiyar aikin, dan haka ka d'auke ni tamkar d'an uwanka bazan tab'a cin amanar ka ba.
Jinjina kai Ra'eez yayi cike da farin ciki yace nagode Kawu Datti, shari'ar anyita ne shekarar 2008, kila kana nan lokacin da akayi ta ma.
Jinjina kai Kawu Datti yayi yana fad'in tabbas ina nan, domin na fara aiki anan a shekarar 2005, duk wata shari'a da akayi a bayan wannan shekara babu wadda ban sani ba sai dai na manta, matuk'ar na zauna na saurareta kuwa to nasanta, kuma duk wasu kundi suna cikin d'akin nan nida abokin aikina muke kula dasu dan yau ma na amshe shi aiki.
Ra'eez yace amma naji dad'i nasan kila kasan shari'ar, dama ina so na samu wanda yasan shari'ar saboda ban tsaya na fahimci abinda suke nufi ba, sunce nayi kok'ari na duba kundin zan fahimci komai.
Kawu Datti yace akan me akayi shari'ar? Ra'eez yace akan tsohon shugaban Kwastam Alhaji Hamza Maiwada wadda aka mik'a direbansa Malan Sani gidan yari akan laifin shine ya kashe shi kuma yayi yunkurin yima matar Alhajin fyad'e silar haka ta samu tab'in hankali.
Girgiza kai Kawu Datti yayi yana fad'in kace azzalumar shari'a, ai bazan tab'a mantawa da wannan shari'ar ba, domin tunda na fara aiki ban tab'a cin karo da shari'ar da na zubar ma kwalla kamar k'aramin yaro ba irin wannan, kai Ra'eez wata shari'ar sai a lahira, amma Allah bazai bar azzalumai ba, domin wallahi tun a lokacin kawai naji ban yarda da shari'ar ba, dan dai an gabatar da shedu masu kyau, amma tabbas nasan akwai munakisa a shari'ar.
Kwalla ne ya ciko ma Ra'eez yayi saurin kauda kai yana kok'arin maidasu. Kawu Datti yace kayi hak'uri yanzu mutane sun fara zuwa, bana son kowa yasan abinda zakayi, domin naji ajikina zaka taimake su, ka bani lambarka zanyi kok'arin nemo maka kundin na kawo maka shi a b'oye ba tare da kowa ya sani ba, idan yaso sai ka kwafeshi ka maido amayar gudun matsala.
Murmushin jin dad'i Ra'eez yayi yana masa godiya. Lambarsa ya bashi shima ya bashi kafin yayi masa sallama ya tafi, sosai yaji dad'i da Allah yasa Kawu Datti ya iske dan yafi Malan Salisu fuskar kamala.
Wajen k'arfe da'ya Sameer yazo ofis d'in su Ra'eez, waya yayi masa ya fita suka had'u, shine yayi masa jagora ya gama cike komai na shedar biyan kud'in tarar da kotu tayi masa, bayan sun gama yace ma Ra'eez maganar zuwa gidan su Halima.
Kallon agogo Ra'eez yayi yana fad'in yanzu lokacin cin abinci ne, ina ganin muyi amfani da wannan damar muje mu dawo. Murmushi Sameer yayi yace nagode Ra'eez, Allah yasa Halima ta yafe mani. Ra'eez yace amin. Jabeer yayima magana yazo suka wuce.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
3⃣1⃣
Jinjina kai Baba Haruna yayi yana goge idonshi yayin da Sameer yake tsugunne akusa dashi shima kukan yake da alamu neman gafara yakeyi.
Kallonshi Baba Haruna yayi yana fad'in shikenan Sameer, k'addara ta riga fata, haka Allah ya tsaro ma Halimatu dole sai ta faru kuma, tabbas nasan da ace alokacin da abun ya faru nazo gidan ku na sanar maku bazaku saurare ni ba, da ace kamar yanda kazo ka rok'i yafiya irin hakan ne zai kasance alokacin da zanje gidan ku da farko wallahi bazan tab'a fitar da maganar duniya ta sani ba, amma sanin halin masu kud'i yasa dole sai da kowa yaji wannan maganar, a hakan ma badan wannan bawan Allah Ra'eez ya tsaya mana ba da shikenan ahaka zamu shigar da k'ara amma a tozar tamu kuma a sake b'atama Halima suna, amma duk da haka mungode ma Allah, bakomai, Allah ma muna masa laifi murokesa yafiya kuma ya gafarta mana, ni kama na yafe maka, bara na kira Mahaifiyarta da ita kuyi magana.
Bayan sunzo Sameer ya d'ora guiwarsa k'asa ya had'e hannuwansa biyu yana rokon su yafiya. Cikin kuka Maman Halima tace ta yafe masa. Kallon Halima yayi yana sake rok'onta.
Jinjina kai tayi tana share hawayen idonta tace na yafe maka, koba komai ta silata Allah ya ganar da kai gaskiya, kuma bazan bijirema Allah ba naki yafe maka ba, ina fatan kamar yanda ka cutar dani kuma ka rokeni yafiya na yafe maka Allah ya d'aukaka rayuwata, yasa ko nan gaba kada na wulak'anta daga ni har zuri'ata.
Gaba d'aya suka amsa da amin. Ra'eez yace gaskiya Halima kinyi matuk'ar burge ni, domin kalamanki masu tsada ne sai mai zurfin ilimi ne zai iya amfani dasu, gasu sun fito daga bakin mai k'ananun shekaru, ubangiji Allah ya amsa addu'ar ki amin.
Jabeer yace Allah ya k'ara tsare gaba, ga wannan check d'in kud'in ki ne da kotu tace abaki, Baba idan kana da asusu a banki sai muje a ciresu asaka aciki domin zasuyi mata amfani wajen karatun ta.
Baba yace gaskiya banda wani asusu a banki, amma inaso aje a bud'e da sunan Halima sai azuba su ciki, hakika badan hakkinta bane babu abinda zaisa na amshi kud'in nan, amma sune zasu taimaka ma rayuwarta wajen inganta, domin burin ta ne karatu musamman a fannin lafiya.
Kallonshi Sameer yayi yana fad'in ta kammala makaranta ne Baba? Kai ya d'aga masa yana fad'in sakamakonta ma yayi kyau.
Jinjina kai yayi yana fad'in zaka iya barinta taje waje tayi karatun fanin lafiya kamar a Madina? Shiru Baba yayi yana tunani. Ra'eez yace Baba ka barta ta tafi, domin Madina k'asa ce mai kyau, kuma zatayi karatu hankalinta a kwance, sannan zata koyo abubuwa da yawa na addini, a ganina Halima tana da natsuwar da zatayi karatu a waje.
Kai Baba ya jinjina ya kalli Halima yana fad'in zaki iya Halimatu? Saurin d'aga kai tayi tana sakin murmushi. Baba yace shikenan na amince, nasan wad'an nan kud'in zasu isheta ta kammala karatun ta.
Sameer yace Baba zan bayar da naira million biyar nasan zasu isheta ta kammala karatunta, sannan nine zan sama mata makarantar, wannan itace babbar kyautar da zan bata bisa yafiyarta agare ni, fatana Allah yasa kada mu samu rabo a tsakanin mu.
Baba yace nagode sosai, kuma insha Allahu babu rabon da za'a samu, domin tun a asibiti wannan malamar ta kawo mana wani magani tace abata tasha insha Allahu ciki bazai shiga jikinta ba.
Sameer yace amma naji dad'i sosai, kuma zanje nayima sister Asabe kyauta domin ta taka rawar gani akan wannan matsala, Allah ya k'ara tsare gaba. Gaba d'aya suka amsa da amin.
Ra'eez yace gobe idan Allah ya kaimu ko daga ofis ne zan zo na d'auki Halima muje a bud'e mata asusu a banki. Sameer yace muje na rubuta mata kud'in sai a had'a dasu.
Godiya sukayi masu kafin suka masu sallama suka tafi.
Bayan sun koma Sameer yace nagode sosai Ra'eez, Allah ya baka abinda kake nema duniya da lahira, ka bani account d'inka ina so nayi maka alheri.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in ka barshi, badan kud'i nayi maka ba, ko a iya abinda kamun ka biyani. Sameer yace nagode sosai, Jabeer nagode Allah ya huta gajiya.
Jabeer yace amin Allah ya k'ara tsare gaba, sai a daure a nemo mata kafin muma muzo mu wuce ka. Dariya suka sa gaba d'aya. Sameer yace insha Allahu zanyi kok'arin haka nima nasan na kusa tsufa damma bani da jikin kiba dan nayi arba'in idan ban wuce ba.
Ra'eez yace to Allah ya kawo ta gari. Murmushi Sameer yayi kwalla ta cika idonshi yana fad'in bazan ce maka komai ba domin kace Allah, amma bana tunanin zan samu mace tagari tunda ban kasance nagari ba.
Ra'eez yace kada kayi saurin yanke hukunci domin Allah baya duba da haka, abinda yake so ka tsarkake zuciyarka. Sameer yace insha Allahu nagode.
Suna shirin sallama wata mota ta tsaya a kusa dasu, kid'an da yake tashi ne a ciki yasa hankalin su ya koma kanta.
Wani gaye ne ya fito sanye da k'ananun kaya masu matuk'ar tsada a jikinsa fuskarsa sanye da wani bakin glass mai tsadar gaske. Rufe motar yayi yana taunar cingam.
Saurin cire glass d'in yayi yana fad'in Yaya Sameer, saurin k'arasowa yayi yana shafa kai. Murmushi Sameer yayi yana fad'in Fawwaz dama ka dawo k'asar nan? Risnawa yayi yana gaishe shi.
Hannu Sameer ya mik'a mashi suka gaisa, juyawa yayi yabama su Ra'eez hannu. Sameer yace lallai Fawwaz ka zama babban yaro da yawa ga abokin ka can hada yara biyu.
Fawwaz yace ai bansan meya shiga kan Adnan ba Yaya, ko kai bakayi aure ba sai shi, lokacin muna secondary kamar wayayye amma muna rabuwa shikenan yanemi zama ustaz, bansani ba ko jami'ar da yayi a Nija ne ya sashi komawa haka, shiyasa naji dad'i lokacin da Dad yace waje zai kaini karatu, koda na gama kawai nayi zama na acan sai wancan watan ne na dawo shima Mom ce ta matsa na dawo ta gaji.
Sameer yace ai gashi ya zama Baba ya bar ka, ina d'ayan abokin naku? Fawwaz yace Allah sarki Sufwan, har ka tuna mani dashi, ina can Adnan yake fad'a mani mutuwar sa domin kowa yasan mu three stars ne a Kings college amma mutuwa ta rabamu dashi daga zazzab'i na kwana biyu, gaskiya naji mutuwarsa sosai.
Sameer yace Allah yajik'ansa, lafiya kazo kotu? Fawwaz yace Dad ne ya aiko ni wajen Abba Barau. Kai Sameer ya jinjina yana fad'in ai kotun taku ce.
Murmushi Fawwaz yayi yace kai Yaya. Sameer yace emana, ai na d'auka kaima zaka biyo Dadyn ka ko lauya ka karanta ai yayi. Fawwaz yace Yaya wannan karatun ba irin namu bane.
Sameer yace to Allah ya taimaka, ka gaishe da mutanan gidan. Fawwaz yace zasuji agaishe da Adnan amma zanje naga Yaranshi. Sameer yace zasuji.
Sallama yayi masu ya wuce yana tafiyar 'yan gayu. Murmushi Sameer yayi yana girgiza kai. Jabeer yace dama wannan shine Fawwaz d'an tsohon Alkalin kotun nan? Sameer yace shine fa, kai duniya babu gaskiya, idan kana da iko da kud'i baka da matsala.
Ra'eez yace ai shiyasa mutane suke son kud'i. Sameer yace yaron nan fa alokacin suna makaranta har kisan kai ya tab'ayi amma da yake Mahaifinsa babba ne ko maganar ba'a tada ba, agaban su Adnan yayi kisan sai dai kasancewar su aminan juna ne yasa suka rufa masa asiri, kuma Mahaifinsa ya basu kud'i masu yawa shikenan sukayi shiru alokacin Adnan yana Niga, uhm shikenan maganar ta mutu, yaron ma da sukace ya gansu shima babu labarinsa sai gawarsa aka tsinta, silar haka aka tura Fawwaz waje karatu.
Shiru Ra'eez yayi yana tunani, da sauri ya kalli Sameer yana fad'in a wace shekara akayi abun? Sameer yace lokacin dai suna aji shidda dan har sun fara jarabawar fita, ina ganin kamar 2008 ne, E a lokacin Adnan ya kammala makarantarsa.
Jikin Ra'eez ne yayi sanyi, tabbas wannan labarin yana da had'aka da yaron da Kawu ya bashi labari, amma zaibi komai a hankali zai had'a kan zaren da sannu.
Sameer yace bara na wuce na tsaya ina cinye maku lokaci. Jabeer yace shikenan mungode sai munyi waya. Hannu ya basu yawuce.
Dafa Ra'eez Jabeer yayi yana fad'in lafiya kuwa Ra'eez? Ajiyar zuciya Ra'eez yayi yana fad'in me ka gani? Jabeer yace tun lokacin da naji an fad'i mutuwar wannan yaron ka tambayi shekarar da akayi abun naga kamar ka canza.
Murmushi Ra'eez yayi yace kawai abun ne ya bani tsoro, dalilin tambayar shekarar ina so nasan shekarunsu har suka iya aikata haka.
Jabeer yace to yaran masu kud'i meye basa aikatawa, kai dai kawai ayi sha'ani. Ra'eez yace Allah ya kyauta. Wayarsa ce tayi k'ara, yana dubawa yaga ansa Journalist, murmushi yayi dan ya gane Rafeek ne.
Bayan sun gaisa Rafeek yace ko anjima bayan isha'i kana da lokaci na kawo maka ziyara? Ra'eez yace ina nan kuwa, zan turo maka da kwatencen. Rafeek yace to nagode.
Kallonshi Jabeer yayi yana fad'in kai da wa? Ra'eez yace wani d'an jarida ne yake son mu had'u bayan isha'i. Jabeer yace sarakan tambaya, sai ka kula kada su saka fad'ar wani abun kasan su da wayon tsiya ga dabara.
Ra'eez yace ai tsakanin su da 'Yan sanda da kuma mu ana fafatawa, domin kowa yana da ilimin fasaha da 'yan dabaru, dan haka kada ka damu zan iya bi dashi. Jabeer yace ai nasanka.
****
Bayan sun tashi daga aiki sukayi sallama da Jabeer kowa ya shiga motarsa ya tafi. Har Ra'eez ya d'auki hanya wayarsa tayi k'ara, yana dubawa yaga Kawu Datti, saurin tsayawa yayi ya kashe wayar sannan ya kirashi.
Cike da farin ciki yace gani nan waje Kawu bara na matso. To shikenan bara na jiraka anan sai ka zo. Kashe wayar yayi cike da farin ciki.
Kwankwasa k'ofar da akayi yasa yayi saurin bud'ewa. Shigowa Kawu Datti yayi ya zauna ya rufe k'ofar. Kallon Ra'eez yayi kafin ya d'age rigarsa ya zaro kundu ya mik'a ma Ra'eez yana fad'in ban tsaya dubawa ba kawai na d'auko maka shi kaje ka duba amma ka maidoshi da wuri, Allah yasa kana da abun photo copy dan bana son kaje wani waje ayi maka idan baka dashi gara ka kwafeshi kawai.
Ra'eez yace nagode Kawu Datti, kuma babu wanda zai san dashi ina da komai a gidana zanyi na maido maka shi gobe. Kawu Datti yace ina maka fatan nasara.
Kud'i Ra'eez ya ciro ya mika masa yana fad'in amin. Girgiza kai Kawu Datti yayi yana fad'in idan na amsa tamkar cin hanci ka bani.
Ra'eez yace wallahi Kawu ba cin hanci bane, ai tsakanin mu babu wannan, ka d'auke ni tamkar d'anka dan Allah Kawu.
Murmushi yayi ya amsa yana fad'in nagode sosai. Ra'eez yace nima nagode. Sallama yayi masa ya fice daga motar ya koma ofis. Hamdala Ra'eez yayi yawuce gida cike da murna.
****
Sai da suga gama firar soyayya da Rumaisar sa kafin yayi masu sallama dan yasan Rafeek ya kusa zuwa. Har bakin mota ta rakashi sai shagwab'a take masa bata so ya tafi. Ra'eez yace kiyi hak'uri ai kullum muna tare, kicigaba damun addu'a domin nakusa fara bincike, dan haka dole ki aramun lokacinki.
Rumaisa tace bakomai in dai lokaci nane na baka domin naka ne, kuma ina maka fatan nasara, addu'a kuma kullum ina maka. Murmushi yayi yace nagode Pretty na. Sallama sukayi yawuce.
A hanya Raheena ta kirasa, kin d'auka yayi dan baya son damu yasan kuma daya d'auka zata tsaidashi da surutu. Ganin ta cigaba da kira yasa ya d'auka, ko magana batayi ba yace mata yana hanya ta bari wajen 11 zasuyi waya. Kashe wayar yayi yana tsaki ya k'ara gudun motar.
***
Lemu da ruwa ya aje masa yana fad'in sannu da zuwa Yaya. Murmushi Rafeek yayi yana fad'in yauwa sannu Ra'eez, yau dai bani da aikin dare nace zan zo mu gaisa sosai.
Ra'eez yace ai naji dad'i sosai, naso na fara kai maka ziyara gashi har ka rigani. Rafeek yace ai bakomai, na fad'a maka babu babba a abota.
Jinjina kai Ra'eez yayi ya mik'a masa ruwan daya zuba yana fad'in gidan gauro ne babu abinci. Dariya Rafeek yayi yace haba ai babu komai, wata rana idan kayi auren zan zo naci.
Kallon Ra'eez yayi yana fad'in gaskiya ka burge ni a shari'ar da kukayi jiya, kuma nayi mamaki da kayi masu haka, sai nake tambayar kaina dama kasan gaskiya ne yasa kace kaine zaka tsaya masu? Girgiza kai Ra'eez yayi yana fad'in Mahaifin yarinyar da ya fad'a mani abinda ya faru yasa nace zan taimaka masu, duk da alokacin na riga na amshi tayin su Sameer.
Rafeek yace ai ka kyauta sosai Allah ya biyaka, shima Mahaifin Halima ya burge ni, duk da yana talaka amma ya iya neman hakkinsa, wallahi ina son naga an zalunci mutum ya tsaya akan neman hakkinsa.
Ra'eez yace nima ina son irin mutane masu dakakkiyar zuciya haka, shiyasa nace zan taimaka masu sosai.
Rafeek yace shiyasa a shekarun baya da aka kashe K'ani na naso mushigar da k'ara amma Baffa yace baya so dole muka hakura, duk da alokacin ina makaranta amma naso ashigar da k'ara.
Ra'eez yace Allah sarki, ashe kaima an kashe maka wani, to Allah yaji k'ansa. Rafeek yace amin, har yanzu inajin d'acin mutuwar Naseer, yaro yana shirin kammala secondary d'insa amma aka samu wasu suka kashe shi, kamar marar gata haka aka wurgar da gawarsa.
Ra'eez yace wayyo Allah ya saka masa, yana gab da fara sabuwar rayuwa suka katse mashi ita, domin duk wanda ya gama secondary alokacin yake fara shirya burinsa.
Rafeek yace wallahi kuwa, a Kings college yake har sun fara jarabawa aka kashe shi, a shekarar su biyu aka kashe a makarantar kuma duk ajinsu d'aya.
Saurin kallonshi Ra'eez yayi yana fad'in a wace shekara ne Yaya? Kallonshi Rafeek yayi yace shekarar 2008 ne, ai bazan iya mantawa da wannan shekara ba, alokacin ina jami'a.
Shiru Ra'eez yayi jikinsa yana tsuma, runtse ido yayi yana tasbihi ga Allah, tabbas Allah ya fara haska masa akan shari'ar da zai gabatar, domin ayau ya fara had'uwa da abubuwan da sukayi had'aka da rayuwar Abbunsa, tabbas yana buk'atar natsuwa yayi dogon nazari, dole yaje kano yayi shawara da Abbah akan Rafeek, domin yaji ajikinsa shid'in zai taimaka masa da wani abu, yana jin zai iya bari yasan wayeshi da kudirinsa, amma idan Abbah be amince ba shikenan zaiyi yakin shi kad'ai.
Dafashi Rafeek yayi yana fad'in Ra'eez lafiya kuwa? Ajiyar zuciya ya saki yana fad'in Yaya abun ne akwai tausayi, wallahi bana so naji an kashe mutum, kawai ina hango yanda mutum zaiji alokacin da ake kashe shi, Allah yajikansu da rahma.
Rafeek yace amin. Amma Ra'eez ba anan garin kake ba ko? Ra'eez yace a Kano nake aiki ne ya maido ni nan. Jinjina kai yayi yana shirin jefo masa wata tambayar wayarsa tayi k'ara, yana dubawa yaga Baffansa ne.
Bayan ya gama wayar ya kalli Ra'eez yana fad'in Baffa ya katse mana fira, wai yana nemana yanzu. Ra'eez yace kai amma banji dad'i ba muna ta firar mu. Rafeek yace bakomai idan nasamu lokaci zan dawo dan bana so mu had'u a ofis d'in ku ko namu dan kowa yasan su waye mu, da an gammu tare kowa zai fara tunanin wani abu, dan haka idan ka samu lokaci idan zaka kawo mani ziyara a gidana zakaje.
Ra'eez yace insha Allahu nagode sosai. Tashi yayi yana fad'in nima nagode. Har bakin mota ya rakashi, sai da ya tafi sannan ya rufe gidan, kundin da Kawu Datti ya bashi ya d'auka ya nufi d'akin kayan aikinsa domin ya fara gamawa da su.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:40 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
3⃣2⃣
A wannan dare Ra'eez kashe wayarshi yayi dan baya son damu, sai da ya gama copying komai kafin ya maida komai yanda yake yasa a leda dan kada ya manta, d'akinshi ya koma ya fara duba takardun.
A hankali ya gama karanta komai, ya mai-maita yafi so ukku, hawaye ne kawai suke zuba a idonshi, yana kallon abun kamar yana wajen yake faruwa, jiyake ina ma shine lauyen da yayi shari'ar a wancan lokacin, domin ga hujjoji nan da yawa daya kamata akare Kawu dasu amma ba'ayi amfani dasu ba, tabbas yasan lauyen daya kare Kawu sarewa yayi alokacin shiyasa be kula da hujjojin ba.
Jin kansa yana ciwo yasa ya tattara komai ya tura k'asan gado dan yasan anan ne kawai zasu b'oyu, duk da shi kad'ai ne agidan dole ya fara b'oye duk wata sheda tashi saboda ayanzu zai fara fuskantar kalubale saboda da manyan mutane zai gwabza, zesa rayuwarsa cikin had'ari, idan yana da tsawon rayuwa shikenan, idan kuma akan kwato ma Mahaifinsa hakkinsa zai rasa ransa a shirye yake daya bada ranshi.
Bayan ya adana komai ya kwanta yana tunanin ta yanda komai zai kasance da haka har bacci yayi gaba dashi.
**** ****
Washe gari tunda wuri ya isa ofis, sai da ya bama Kawu Datti kundin yayi ta masa godiya, sosai Kawu Datti yaji dad'i, hankali kwance yaje ya maida inda ya d'auko su.
Bayan ya rage aikin da yake gabanshi ya samu ya fita dan yaje ya d'auko Halima su gama komai da wuri. Babu b'ata lokaci suka kammala komai cikin lokaci.
Sai da ya maidata gida sannan ya koma ofis. Yana shiga yayi turus yana kallonta zaune a saman kujera Jabeer ya kawo mata lemu tana sha.
Saurin tashi tayi tana sakin murmushi, matsowa tayi tana fad'in D. sannu da dawowa wallahi na kasa hakurin rashinka shiyasa nazo, tun d'azu ma naso nazo Momy tace na bari sai anjima.
Murmushi Ra'eez yayi ya ratse ta yawuce ciki. Zama tayi tana fad'in na manta ina kwana? Ra'eez yace lafiya lau, daga shigowata ba gaisuwa kin rufeni da surutu.
Hannu tasa abaki tana fad'in wallahi mantawa nayi kewarka ce tamun yawa shiyasa duk na rud'e. Ra'eez yace ai na fad'a maki ina da aiyuka agabana.
Raheena tace duk da haka D ko waya ne sai ka kirani, bakasan yanda nake shiga damuwa ba idan banjika ba, dama kai ba kirana kake ba ni kuma na kira kace kana aiki.
Ra'eez yace daga yau kada ki sake zuwa wajen aiki na, duk macen da take iya bin namiji to bata da daraja a idon kowa, kuma ni bazan iya auren macen da take bina ba, domin zan rik'a ganin kowama haka kike masa.
Saurin tashi tayi tana fad'in Allah ban tab'a bin kowa gidanshi ba, kaima dan ina sonka shiyasa na biyoka amma kayi hakuri bazan sake ba. Kai ya d'aga ya jawo wasu takardu yana fad'in hakan zaifi maki.
Jabeer ne yashigo hannunsa d'auke da leda da alamu wani abu ne a ciki. Tsaye yayi yana kallon Ra'eez. Jaka Raheena ta d'auka tana fad'in Jabeer zan wuce.
Saurin kallonta yayi yana fad'in ban gane ba, keda kikace mun wuni kikazo mana taya zaki tafi kuma? Murmushi tayi tana kallon Ra'eez tace dama Momy ce tace nazo zata aike ni.
Kallon Ra'eez Jabeer yayi yana murmushi. Kauda kai yayi yacigaba da aikinsa. Jabeer yace shikenan ga wannan sai ki tafi dashi.
Amsa tayi tana godiya. Jabeer yace ki gaishe da Momy sai mun leko, Yallab'ai sai kaje ka rakata ai. Harara Ra'eez ya aika masa.
Raheena tace haba Jabeer ya kake son bama D wahala bayan yanzu ya dawo, ka barshi ya huta, kallon Ra'eez tayi tana fad'in D kayi aiki lafiya amma kada ka matsa ma kanka dan Allah.
Murmushi yayi yana kallonta, sai kuma ta bashi tausayi ganin yadda tayi kok'arin kareshi a wajen Jabeer, tabbas yasan zuwa yanzu Raheena ta canza sosai.
Tasowa yayi yana fad'in nagode Raheena da ziyara ki gaishe da Momy idan na samu lokaci zan zo nima. Murmushi ta saki tana jin wani dad'i.
Iyaka bakin k'ofa ya tsaya dan baya son kowa ya ganshi da ita. Sai da ta tafi kana yashigo ciki. Dariya Jabeer yasa yana fad'in Allah ya shiryeka abokina.
Tsaki Ra'eez yayi ya zauna yana fad'in zaka fara ko? Jabeer yace kai d'in ne sai a hankali wallahi kana wahalar da Raheena sosai.
Ra'eez yace ai sai ka rama mata. Jabeer yace ni na isa, kawai tausayinta nakeyi, saboda kai duk ta canza, kalli yanayin shigarta komai ya canza, wallahi tausayi take bani, irin su Raheena zasu iya yin komai akan abinda suke so, kuma ko aurensu kayi baka tab'a samun matsala dasu.
Tab'e baki Ra'eez yayi yana fad'in kaga malan ina da aiki gara kaje kayi hidimar gabanka. Rik'e baki Jabeer yayi yana fad'in lallai kam, ya Allah ka nuna mani ranar da Ra'eez ze fad'a son Raheena.
Tofar ta miyau Ra'eez yayi yana fad'in har abada wallahi, nan take idanuwansa suka canza kala yana b'ata fuska. Shiru Jabeer yayi cikin mutuwar jiki yake kallon Ra'eez.
Kasa rubuta komai yayi haka ya rufe takardun da k'arfi yayi saurin barin ofis d'in yana jin wani b'acin rai. Sosai jikin Jabeer yayi sanyi akan abinda ya faru, bai tab'a ganin Ra'eez a irin wannan yanayin ba,daga wannan maganar har zai iya fushi haka, ya d'auka yana son Raheena amma yau ya tabbatar da zahiri, sai dai dole akwai dalili. Ajiyar zuciya ya saki tare da barin ofis d'in.
***
Bayan an tashi ya fito ya hangi Jabeer a jikin motarsa yana kok'arin shiga, da sauri ya k'arasa wajensa. Dafashi yayi yana fad'in yau guduwa zakayi babu sallama.
Murmushi Jabeer yayi yana fad'in haba Ra'eez, meyasa har yanzu baka d'auke ni kamar yanda na d'auke ka ba? Kasan kuwa yanda na d'auke ka? Wallahi kamar d'an uwana da muka fito ciki d'aya haka nake jinka, amma na lura akwai abubuwan da kake b'oye mani naka, ban gama tabbatarwa ba amma ka sani duk ranar dana tabbatar da hakan aranar zan san matsayina awajenka, domin ni ban b'oye maka komai nawa ba, tun ranar had'uwar mu na sanar da kai komai nawa, amma babu komai bance dole sai ka sanar dani labarin ka ba.
Ajiyar zuciya Ra'eez ya saki idanuwansa suka ciko da kwalla, tabbas ya aminta da Jabeer, amma alk'awarin Abbah ne bazai fad'ama kowa labarinsa ba yanzu.
Jin motsin Jabeer yashiga mota yasashi saurin shiga yana goge idonshi. Da kallon mamaki Jabeer ya bishi. Hannunsa Ra'eez ya kamo yana fad'in kayi hakuri Jabeer, zanje kano cikin satin nan nayi maka alk'awarin zan sanar da kai labarina idan na dawo.
Murmushi Jabeer yayi ya rik'o hannunsa yana fad'in kada kadamu abokina, bana son kana zubar da kwalla, na dad'e da sanin kana da ciwo aranka sai dai bansan komeye ba, amma nasha ganin ka cikin damuwa wani lokacin, dan haka kayi hak'uri da abinda nace maka bazan sake tada maka maganar ba.
Murmushi yayi yana fad'in nagode da ka fahimce ni. Jabeer yace bakomai zo mu tafi. Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in ka gaishe da Mamy. Jabeer yace zataji agaida Rumaisa.
**** ***
A ranar alhamis ya lek'a gidan su Raheena saboda damunshi da tayi yazo siyi sallama zasuji Dubai ranar asabar.
Bayan sun gaisa da Momy Raheena ta shige kicin domin d'auko masa kayan motsa baki. Kallonshi Momy tayi tana fad'in yau dai Raheena hankali zai kwanta kazo, kullum cikin damuwana take kaki zuwa, nace mata ai aikin ku haka yake, shine yau tace zaka zo kuyi sallama.
Kai a duk'e Ra'eez yace wallahi kuwa. Momy tace ai gara muje a fara rago siyayyar kayan d'aki dan Alhaji yace baya son bikin yawuce wata guda, shine zamuje Dubai jibi musiyo kayan d'aki, naji tace kaima zaka je kano ko? Kai Ra'eez ya d'aga yana mamakin wannan lamari.
Momy tace idan kaje ka gaishe su, ai gara kaje a kammala komai, muma kwana biyu zamuyo kada suzo bamu dawo ba. K'ara duk'ar da kai Ra'eez yayi yana sakin murmushi.
Tashi Momy tayi tana fad'in Raheena kuje falon baki nan kada ayita gitta maku. Raheena tace to Momy. Kallon Ra'eez tayi tana fad'in D muje can.
Kallonta yayi yana sakin murmushi mai kama da dariya yace ai wucewa zanyi akwai abinda zanyi. Zama tayi tana fad'in kai D zamuyi sallama bazaka tsaya muyi fira ba kuma.
Hannu ya mik'a mata alamun ta zuba mashi ruwa. Saurin zuba masa tayi ta mik'a masa tana fad'in yi hakuri ina wuni. Lafiya lau sarkin mantuwa, ya amsa. Murmushi tayi tana rufe fuska.
Tashi yayi yana fad'in Allah ya kiyaye hanya zance ko? Murmushi tayi tace nagode kaima ka dawo lafiya, me kake so nasiyo maka? Ra'eez yace dama tambaya akeyi? Girgiza kai tayi tana fad'in shikenan zan kawo maka zab'ina.
Kai ya jinjina yana fad'in ki gaida Momy zan wuce. Biyoshi tayi tana fad'in wallahi kamar kada ka tafi. Ra'eez yace dole ko na tafi. Har bakin mota ta rakasa, sai da ya tafi kana ta wuce gida.
Daga wajenta wajen Kawu ya wuce, sun dad'e suna tattaunawa kuma ya sanar masa duk kok'arin da yakeyi kana ya fad'a masa zaije kano gobe. Kawu yace agaishe mani da Alhajin kuma insha Allahu zan cigaba da addu'a Allah yashige mana gaba. Ra'eez yace amin, zasuji.
Sai da ya fara biyawa wajen Ummunsa kafin yawuce gidansu Rumaisa, daga can bayan ya gama yawuce gida dan yagaji sosai.
*** ***
Washe gari be tsaya aka tashi dashi wajen aiki ba, bayan yayi ma Alhaji Barau sallama Jabeer ya kaishi filin jirgi dan ta jirgi zai bi. Sun dad'e suna fira kafin lokacin tafiyarsu yayi, haka sukayi sallama ya tafi.
***
Jinjina kai kawai Abbah Mansur yake yana kallon takardar da Ra'eez ya kawo mashi hawaye suna fita a idonshi. 'Dago kai yayi yana kallon Ra'eez wanda shima kukan yakeyi bayan ya gama fad'a masa abinda ya faru da kuma wanda ya gani awajen Rafeek da Sameer wanda suka fad'a masa.
Hannu Abbah yasa ya goge idonshi yana fad'in tabbas a wannan karon Ra'eez kaine zakayi nasara a kotu, hakika Malan Datti yana da matuk'ar mutunci, sannan na amince maka daka fad'ama Jabeer da Rafeek sirrinka, domin inaji ajikina sune bangon da zaka jingina dasu, sune tsaninka wanda zaka taka zuwa matakin da nakeso kaje, domin na fahimci Jabeer aboki ne nagari, dan haka ka sanar dashi komai saboda duk lokacin daya fahimta da kanshi abotar ku zata iya samun matsala.
Ra'eez yace shikenan Abbah zan fad'a masu, dama umarninka nazo nema dan bana so nayi abinda ya kaucema umarnin ka. Murmushi Abbah yayi yana fad'in na sani Ra'eez, nasan bazaka tab'a tsallake umarni na ba, Allah yayi maka albarka.
Ra'eez yace amin Abbah. Murmushi yayi yana fad'in zuwa gobe sai ka lek'a wajen Labiba ku gaisa dama tana korafin rashin zuwanka. Ra'eez yace tunda nazo dole naje mu wuni muyi fira.
Abbah yace maganar motar fa? Sosa kai Ra'eez yayi yana fad'in Abbah kaga gobe zanje gidan Mamyn Sultan bansan lokacin da zan dawo ba, kuma jibi da wuri nake son tafiya inaga abar motar zan dawo ko nan da wata d'aya sai na kaita gyara.
Abbah yace da alamu nakusa sayar da motar nan. Zaro ido Ra'eez yayi yana fad'in kai Abbah, shikenan ko ina can sai ka bama mai gyaranka sai ya duba mani ita kaga ina dawowa sai na tafi da abuna.
Murmushi Abbah yayi yana fad'in shikenan zan bashi ya duba maka ita amma yanzu yayi tafiya ni kuma nafi aminta dashi idan ya dawo zan kirashi yazo ya tafi da ita, amma ka sani bazaka je Lagos da ita ba, ko an gyara ta anan za'a barta domin ana kammala wannan shari'ar Kano zaku dawo gaba d'aya sai kacigaba da aikin ka anan.
Ra'eez yace haka ne Abbah, nima bani da buk'atar zama a Lagos, muna kammala shari'ar har gidan zan sayar domin nasan Ummu bazata iya komawa gidan nan ba. Abbah yace to Allah yashige mana gaba. Ra'eez yace amin.
**** ***
Yaji dad'in zuwanshi Kano har yaji kamar kada ya tafi, haka Abbah ya kaishi ya hau jirgi ya tafi cike da kewar juna.
Tun kafin ya taso ya sanar ma Jabeer, aikuwa suna sauka ya iskeshi yana jiranshi. Rungume juna sukayi kafin suka shiga mota suka tafi.
Jabeer yace wallahi abokina ka canza kwana biyu. Ra'eez yace ba dole ba ina can ana shagwab'ani. Dariya Jabeer yayi yana fad'in naga alama ai.
Waya Ra'eez ya ciro ya kira Rafeek. Bayan sun gaisa Ra'eez yace Yaya ko kana wani abu zuwa dare? E dama inaso kazo gida akwai maganar da zamuyi ne. Toshikenan sai kazo nagode.
Jabeer yace ina ka samu Yaya kuma? Murmushi Ra'eez yayi yace wannan d'an jaridar da nake fad'a maka ne. Jabeer yace lallai kayi Yaya kuwa. Ra'eez yace idan yazo zan fad'a maku wata magana, dan haka yau muna tare. Jinjina kai Jabeer yayi yace Allah ya kaimu.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:40 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
3⃣3⃣
Lokacin da Ra'eez ya kammala basu labarinshi babu abinda akeji sai sautin kuka, gaba d'ayansu an rasa mai lallashin wani. A hankali Ra'eez ya zame ya kwanta yana jin wani iri a zuciyarsa, kasancewar shine aka bama labarin da farko shiyasa beji abinda yakeji yanzu ba, dan ayanzu da yake bada labarin abinda ya faru da kanshi sai yakejin wani irin d'aci a ranshi.
Sun dad'e a haka kafin Rafeek ya kamo hannun Ra'eez yana fad'in tabbas Yaron da Abbunka ya rage ma hanya Naseer ne k'anina, domin a ranar shima aka tsinci gawarsa, duk da bani da masaniyar haka amma zuciyata ta bani hakan, domin kace Kawunka ya fad'a maka yaron da suka d'auko yace abokinsa ne yaron da suke magana alokacin an kashe a kings college, tabbas ina zargin mutane iri d'aya ne suka aikata kisan Abbunka da Naseer, banbancin shi Abbunka bayan an kashe shi anyi amfani da allura, amma da wuya idan allurar aka fara masa, domin ance akwai sahun hannu na shaka, haka shima Naseer shakeshi akayi har ya rasu.
Ajiyar zuciya yayi yana fad'in dole akwai abinda Naseer ya sani agame da mutuwar abokinsu wanda Sameer yace Fawwaz ne ya kashe shi, tabbas wannan yaron da Adanan k'anin Sameer yace ya gansu shima ankashe shi Naseer ne, amma zamu zauna mu zana yanda komai yakasance, dole akwai abinda yake faruwa,
Abbunka - Naseer
⬇
*Fawwaz, - tsohon Alkali mahaifin Fawwaz,- Alhaji Barau,- Alhaji Marusa, - Mr. Kallah*.
Wad'annan mutanan suna da alak'a da mutuwar Abbunka, idan ko haka ne Alhaji Barau shine abokin tsohon Alkali a wancan lokacin, kunga Fawwaz yaron Alkali yayi kisa dole su san yanda suka shafe maganar, domin wannan dalilin ne yasa aka tura Fawwaz waje karatu.
Saurin gyara zama Jabeer yayi yana fad'in, amma ya akayi Naseer yaje wajen aikin Abbun Ra'eez? Domin a cikin labarin Kawu yace sunzo fitowa suka had'u dashi hakan yasa suka taimaka masa, bayan kuma kace aranar yace ma Hajiyar ku zaije wajen abokinsa Mannir, kuma kace ba wajen unguwarsu bane, to meya kaishi wajen aikinsu Abbunka?
Rafeek yace yes! Wannan maganar taka tana kan hanya, a yanzu muna cikin damuwa dan haka mu bari bayan kwana biyu muzo anan domin mu bama kanmu tambaya kuma mu nemo amsa, kafin nan dole sai Sameer yashigo, domin ya had'amu da K'aninsa, sai dai bazamu fad'a masu case d'in Abbunka ba, iya abinda ya shafesu kawai zamu sani, case d'in Abbunka ya tsaya iya mu har zuwa lokacin da komai zai kammala, sannan bayan mun fara wannan aikin dole muna buk'atar ganin Uncle d'in ka Jabeer, domin shine lauyen daya tsaya ma Kawu a wancan lokacin, kaga yanzu yana abuja babbar kotu komai zai zo mana da sauki.
Jabeer yace babu damuwa, naji Dady yana maganar zasuyi wani taro k'arshen satin nan na family ne kuma maza kad'ai ne zasu zauna, nasan dole Uncle zaizo dan irin wannan taron baya wuceshi, abinda nake gani mu bari yazo zanyi masa maganar, idan yana buk'atar ganin ku sai muje gaba d'aya.
Rafeek yace yauwa komai ma zaizo da sauki, insha Allahu wannan shari'ar da zafi zamu d'auketa, a wannan karon zasu gane kuskurensu, domin zasu had'u da 'yan zamani, kamar yanda sukayi amfani da basira haka zamuyi muma, kuma a hankali zan nemo duk mutanan da suka bada gudummuwa wajen aikata laifi, zan amshi sunayen likitocin da suka kula da gawar Abbu, hatta da wanda ya duba Ummunka inaso na ganshi, sai kuma 'yan sandan da suka kula da case d'in dan nasan yanzu duk sun zama manya, amma komin girman mutum bazai ja da shari'a ba, insha Allahu zamu gudanar da komai, Ra'eez kasa aranka tare zamuyi wannan yaki, kuma insha Allahu zamuyi nasara, sai Kawu ya fito kuma sai an d'aure duk wani mai hannu a cikin wannan laifin.
Jinjina kai Ra'eez yayi yana hawaye dan ya kasa magana saboda wani sanyi da yakeji. Kamoshi Jabeer yayi sai yaji jikinsa yayi zafi ga rawar sanyi da yakeyi. Saurin kallon Rafeek yayi yana fad'in Yaya Ra'eez fa beda lafiya.
Tasowa Rafeek yayi yana fad'in damuwace ta haifar masa da hakan, ai yana ma kok'ari, akwai ciwo arayuwarshi amma haka yake daurewa domin ya sa burin d'aukar fansa aranshi, dole muje asibiti a aunashi saboda asan irin maganin da za'a bashi dan damuwa tayi masa yawa.
Jabeer yace Ra'eez tashi muje asibiti. Girgiza kai yayi yana hawaye. Rafeek yace wallahi sai munje, matuk'ar kana son kammala wannan shari'ar to ka bari a duba lafiyar ka, sannan kasa jarumta aranka kamar yanda Kawu yayi, idan ba haka ba ciwo zai kwantar da kai.
Jinjina kai yayi yana kok'arin tashi, kamoshi Jabeer yayi tare da gyara masa rigarsa suka fita waje, rufe gidan sukayi suka wuce asibiti.
***
Cire glass likitan yayi yana fad'in Rafeek ya akayi Brr, yake barin damuwa aranshi har haka? Jininsa fa ya hau ga zuciyarsa tana samun damuwa saboda yana yauwan tunani, gaskiya dole akula dashi idan ba haka ba zai iya kamuwa da ciwon zuciya.
Jinjina kai Rafeek yayi yana fad'in insha Allahu za'a kiyaye likita, kasan yanayin aikinsu, ga rashin hutu gashi dole sai mutum yana zurfafa tunani, amma duk da haka za'a kula insha Allah.
Likita yace dama kana da alak'a da hazikin lauyan nan? Murmushi Rafeek yayi yana fad'in cousin d'ina ne a Kano suke da zama. Likita yace lallai kunyi dace da samun hazikin lauya, dan haka ku kula dashi kada al'umma ta rasa mutum mai gaskiya.
Murmushi Rafeek yayi yana fad'in zamu kula insha Allah. Likita yace ba sai mun kwantar dashi ba zaku iya maidashi gida tunda nasan zaku kula dashi acan. Rafeek yace likita inaso ka bashi gado ko na kwana biyu ne, domin Ra'eez yana da buk'atar hutu sosai, idan ya koma gida bazai iya hak'ura beje aiki ba, koda munce kada yaje acan wajen aikin bazasu gane beda lafiya ba, amma idan suka san yana kwance a asibiti dole zasu d'aga masa k'afa.
Jinjina kai likita yayi yana fad'in shikenan bara a bashi VIP room domin babban mutum ne. Dariya Rafeek yayi yana fad'in lallai kanaji da Ra'eez, ko dai ya tab'a tsaya maka ne? Murmushi likita yayi yana fad'in ko d'aya, ban tab'a zuwa kallon shari'arsa ba ma, kawai dai yanayin aikinsa ne yake burgeni, domin an bani labarin shari'arsa ta farko, sannan an bani labarin wadda yayi wancan satin, tun daga lokacin kawai nake sonshi.
Rafeek yace to mungode, akwai magungunan da za'a siyo ne? Likita yace yanzu kam tunda a nan za'a barshi zamuyi masa komai, kuma nine zan biya domin gwarzo na ne.
Tashi Rafeek yayi yana fad'in nagode abokina. Likita yace haba bakomai, muje akaishi d'akin saboda akwai allurar da zan saka masa a ruwa wadda zata sashi bacci mai k'arfi.
***
Sai da aka gama masa komai kana Rafeek yace ma Jabeer yaje gida ya fad'ama su Momynsa tunda yace anan zai kwana, amma kada ya fad'a ma Maman Rumaisa tunda dare yayi abarsu zuwa gobe.
Jabeer yace ai ba sai naje ba sai nayi masu waya kawai. Rafeek yace baza'ayi haka ba, kwanciya asibiti tana buk'atar shiri, kaje ka fad'a masu nasan kaima bazaka rasa abinda zaka d'auko ba. Jabeer yace shikenan bara naje ai kana nan ko? Rafeek yace ina nan har sai ka dawo zan tafi.
***
Bayan mintuna Jabeer ya dawo. Haka Rafeek yayi mashi sallama yace zuwa safe zaizo ya kawo masu kayan kari. Godiya Jabeer yayi masa, har bakin mota ya rakashi sannan ya dawo.
*** ***
Washe gari wajen k'arfe bakwai da rabi Rafeek ya iso asibiti ya kawo masu kayan kari, alokacin Ra'eez ya fito daga wanka yana zaune ya idar da sallah, dan Jabeer be tashe shi da asuba ba ganin yanda baccinsa yayi nauyi.
Tashi yayi jiki a sanyaye dan har lokacin baya jin kwarin jikinsa, zama yayi yana gaishe da Rafeek. Matsowa yayi yana fad'in Ra'eez ya jikin? Ra'eez yace da sauki nagode Yaya.
Zama yayi yana fad'in kadena gode mani domin duk abinda zanyi maka dan Allah ne nayi, dan haka bana son godiyar ka, kallon Jabeer yayi yana fad'in kaci abinci kaje gida ka shirya sai ka sanar ma su Mama bayan ka shiryo ka taho da ita sai ta zauna dashi kafin mu taso.
Tashi Jabeer yayi yana fad'in ka had'a masa abincin idan naje gida zanci ni. Rafeek yace shikenan amma ka biya ka fad'a masu kaga kafin ka shiryo itama ta gama shiryawa. Jabeer yace to. Sallama yayi masu yana fad'in Ra'eez sai na dawo.
****
Cike da damuwa Mama ta kalli Jabeer tana fad'in shiyasa nace ya dawo nan da zama yana ganin mu bazai rik'a damuwa ba, amma ya je ya zauna acan dole yarika damuwa, a d'akin Abbunsa fa yake kwana a saman gadonshi, taya bazai d'aura aure da damuwa ba, amma ka barni dashi dole ya dawo nan duk da yafi sabawa da can amma bazan bari wani abu ya sameshi ba.
Jabeer yace haka ne Mama, nima tunda wannan abun ya faru nake wani tunani, amma mujira asallamosa sai musan abunyi. Mama tace shikenan kaje ka shiryo zan k'arasa aiki kafin ka dawo, abinci ma Rumaisa zata tsaya tayi idan ta gama sai ta same ni can ai tasan asibitin.
Jabeer yace shikenan sai na dawo. Kallon k'ofar d'akin Rumaisa yayi yana murmushi dan tunda ya shigo ya fara magana ya ganta tsaye tana hawaye. Suna had'a ido tayi saurin sakin labulen. Murmushi yayi yana ma Mama sallama ya fice.
**
Ko da sukaje alokacin Ra'eez ya koma bacci anyi masa allura bayan yaci abinci yasha magani. A tare da Rafeek suka fito zasu wuce aiki, Mama sai godiya take masu. Bayan sun tafi ta zauna cike da tausayin Ra'eez.
***
K'arfe 12:00 Rumaisa ta iso asibitin, waya tayima Mama ta fito suka shiga ciki, a bakin k'ofar shiga suka had'u da likita tare da Alhaji Barau da Brr. Bajinta.
A jingine da filo suka iskeshi yana shan lemun da Mama ta bashi kafin ta fita. Da sallama suka shiga. Kallonsu yayi da idanuwanshi da suka fad'a a dare guda.
Murmushi yayi yana masu sannu da zuwa. Shigowa sukayi Alhaji Barau yana fad'in kaga ikon Allah ko Brr. Bajinta, jiya fa mukayi waya yace mun ya dawo lafiya ashe a asibiti ma zai kwana.
Brr. Bajinta yace aishi ciwo beda lokaci, idan mutuwa ce ma haka zamu jita daga sama. Hannu ya mik'ama Ra'eez yana fad'in sannu ya k'arfin jikin? Ra'eez yace da sauki.
Gaishe da Alhaji Barau yayi. Alhaji Barau yace lafiya lau ya jikin? Ra'eez yace da sauki sosai. Su Mama suna gefe tashiga gaishe su. Kallonta Alhaji Barau yayi yana fad'in lafiya lau ya mai jiki? Mama tace da sauki.
Tashi sukayi Alhaji Barau ya aje kud'i masu yawa a gefen Ra'eez yana fad'in ban siyo komai ba ga wannan an saya masa lemu Allah ya k'ara lafiya, zuwa anjima da dare zamuzo tare da Hajiya, amma nasan Raheena tanaji zata taho nan.
Godiya Ra'eez yayi mashi fuskarsa a d'aure. Brr. Bajinta yace to Allah ya k'ara lafiya. Sallama sukayi ma su Mama suka fice. Tsaki Ra'eez yayi yana jin wani bakin ciki, hannu yasa ya ture kud'in daya aje suka fad'i k'asa.
Matsowa Mama tayi tana fad'in munafikin Allah, da yardar Allah k'arshensa bazeyi kyau ba, zezo ya kawo ma mutane kud'in haram.
A hankali Ra'eez yace Mama d'auke su nadena ganin su, ki ajesu idan kika fita ki badasu sadaka. Mama tace sai dai sadakar, amma wallahi ko da yunwa nake kwana bazan iya cin kwandalar munafuki ba.
Kwashe su tayi ta nemi bak'ar leda tasa sannan tasasu ajaka. Matsowa Rumaisa tayi idanuwanta cike da kwalla, tsaye tayi a gefen gadon tana wasa da yatsunta.
Tashi Mama tayi tana fad'in bara naje waje kila na samu mabarata. Har ta fita Rumaisa bata d'ago kai ba sai hawayen da suke sakko mata.
Tsura mata ido Ra'eez yayi shima idanuwanshi cike da kwalla, a hankali yasa hannu ya jawota ta fad'o jikinshi, kamar jira take ta kifa kanta tare da sakin kuka.
Lumshe ido yayi hawaye masu zafi suka sakko mashi, tabbas daga jiya zuwa yau yana jin wani irin ciwo a rayuwarshi, amma dole yasa jarumta aranshi matuk'ar yana so yabar asibitin nan gobe.
Sun dad'e a haka yana bubbuga mata baya, a hankali tayi shiru tana ajiyar zuciya. Duko da kanshi yayi yana fad'in Pretty kinaso ciwo na ya tashi ne, kinsan dai kukan ki yana d'aga mani hankali sosai, gashi jinina ya hau idan kina kuka zai k'ara hawa.
Saurin tashi zaune tayi tana goge idonta. Murmushi yayi yana fad'in ashe dai ba'aso na mutu? Turo baki tayi tana fad'in dan Allah Yaya na kadena maganar mutuwa.
Waro ido yayi yana fad'in yau kuma na koma Yaya? Kai ta girgiza tana murmushi. Ra'eez yace to afad'amun sunan. Murmushi tayi tace kai Annur! Dariya yasa yana fad'in yanzu naji.
Tashi tayi ta zuba masa abinci, gyara masa filo tayi ya gyara zamansa kafin ta mik'a masa filet d'in. Ido ya tsura mata be amsa ba, jin shiru yasa ta kalleshi. Turo baki yayi yana mak'ale hannu a baya.
Murmushi tayi ta zauna gefen gadon ta fara bashi abaki. Haka yarik'a amsa idan yaci d'aya sai yace dole sai taci dan yasan bataci komai ba saboda rashin lafiyarsa. Haka suka cinye hada k'ari, abincin da sukaci sunyi mamaki dan basu san sunci ba.
Wajen k'arfe 3:00 Jabeer ya iso, a d'akin waje ya iske Mama tana jan carbi Abdallah yana gefenta wanda Rumaisa taje ta d'aukosa a makaranta.
Duk'awa yayi suka gaisa yayi mata ya mai jiki. Mama tace yaji sauki sosai suna ciki kashiga. Tashi yayi yana fad'in Allah ya k'ara sauki.
Yana tura k'ofar Rumaisa tana kok'arin bama Ra'eez aiba a baki. Cak ta tsaya tare da duk'ar da kai tana murmushi. Da sallama yashigo yana murmushi.
Harara Ra'eez ya aika masa yana gyara zamanshi. Zama Jabeer yayi yana fad'in ae dole a tura Mama waje ashe ana nan ana.... Da sauri Rumaisa tayi waje cike da kunya.
Dukan wasa Ra'eez ya kaima Jabeer yana fad'in wannan ai wulakanci ne mutum yana jin dad'i da iyalinsa azo a takura masa.
Jabeer yace lallai kam Yaro ka samu, banda wukalanci a asibiti zaku zo kuna soyayya saboda rashin kunya kayi wani kwance ana baka abinci abaki.
Ra'eez yace wani ma ya samu hakan, kaga malan bana son sa ido. Dariya Jabeer yayi ya bashi hannu suka gaisa yana tambayarsa jiki.
Ra'eez yace da sauki sosai, ai Pretty tana zuwa naji na warke gabad'aya. Jabeer yace da alama yau ita zamu bari ta kwana kaga kafin gobe sai ka koma dai-dai.
Dariya Ra'eez yasa yana fad'in wallahi baka da kirki, mutumin ka fa yazo shida d'an kazaginsa. Jabeer yace ina zuwa na fad'a mashi shine yace dole yazo ya dubaka.
Ra'eez zeyi magana aka turo k'ofa, Raheena ce tashigo bakinta d'auke da sallama. Jabeer ne ya amsa yana mata sannu da zuwa. Wani b'acin rai ne ya ziyarci Ra'eez, shikenan zatasa Pretty cikin damuwa.
Cikin sauri ta k'ara so idanuwanta suna kawo ruwa, gefen gadon tazo zama da sauri Ra'eez yasa k'afarsa a wajen yana mata nuni da kujera. Jiki a sanyaye taja kujera ta zauna ta fara gaishe su.
Tashi Jabeer yayi yana fad'in matso da kujerar jikin gadon keda kika zo jinya. Murmushi tayi ta matso tana tambayar Ra'eez jiki. Zamewa yayi ya kwanta yana amsawa.
Kallonshi tayi tana fad'in sannu Dear, wallahi bakaji yanda hankalina ya tashi da Dady ya fad'a mun ba, tare muke da Momy tana wajen wasu anan da alamu 'yan uwanka ne shine ta tsaya suna gaisawa.
Kai Ra'eez ya jinjina yana fad'in nagode. Momy ce tashigo bakinta d'auke da sallama. Jabeer ne ya amsa mata yana mata sannu. Bayan ta zauna suka gaisheta tayima Ra'eez sannu.
Kallon Raheena tayi tana fad'in to ke haka ake zuwa jinyar bazaki zuba abinci ki bashi ba? Murmushi Raheena tayi tana fad'in Momy yanzu zan zuba mashi ai.
Momy tace yauwa, matsa ki zauna gefen gadon ki bashi ba sai ya wahalar da hannunsa ba. Saurin juyawa Jabeer yayi ya fita saboda dariyar da ta taho mashi. Da sauri Ra'eez yace akoshe nake yanzu naci abinci.
Raheena zatayi magana sai ga Rumaisa ta shigo da sauri, tunda taga Raheena hankalinta ya kasa kwanciya musamman da Momy ta fad'a masu daga inda suke.
Ganin Raheena akusa da gadon Ra'eez yasa tayi saurin k'arasawa, bata san lokacin data zauna gefen gadon ta kamo hannun Ra'eez tana fad'in Annur baka buk'atar komai ko? Runtse ido Ra'eez yayi ganin Rumaisa zata rusa masa shiri.
A firgice Raheena ta kalli Rumaisa jin abinda tace. Ganin Ra'eez ya runtse ido yasa Rumaisa tayi saurin sakin hannunsa tana fad'in Yaya dama fa Mama tace nazo na tambayeka idan akwai abinda kake buk'ata tunda taga surikarta tazo jinya.
Murmushi ne ya sauka a fuskar Raheena da Momy wad'an da sukayi zuru suna jiran k'arin bayani. Da sauri Ra'eez ya bud'e idonshi jin abinda Rumaisa tace, a cikin idanuwanta ya sauke nashi, sai dai ganin yanda idanuwanta suka canza yasashi gano tsananin kishi a ciki.
Da sauri Raheena tace lallai wannan k'anwar tamu tana ji da Yayanta, kada ki damu ina nan zan bashi duk abinda yake buk'ata, idan kina son zuwa gida ki huta zaki iya tafiya dan sai dare zan bar nan shima dan bazeyuwu na kwana anan ba da zan kwana dashi.
Momy tace sosai kuwa, tunda kinzo zasu iya tafiya su huta dan nasan tun safe suke nan. Kai Rumaisa ta jinjina dan bazata iya magana ba tayi saurin barin d'akin.
Runtse ido Ra'eez yayi cike da jin haushin Raheena da Momynta, yasan Rumaisa zata shiga damuwa, ko abinda tayi ganin ya rufe ido ne yasa ta fad'i haka kuma ya gano da biyu ta fad'a.
Tashi Momy tayi tana fad'in Ra'eez Allah ya k'ara sauki, zan tafi na barku kuyi firar ku, Raheena idan direba ya maidani zai maido maki motar sai ya koma gida saboda idan kin tashi komawa sai kiyi amfani da ita.
A hankali Ra'eez yace nagode. Raheena tace Momy sai na dawo. Momy tace ki kula dashi sosai fa. Raheena tace to Momy.
Sallama tayi masu Mama ta wuce. Jabeer da yake kok'arin shiga yaji abinda ya faru dan tunda yaga Rumaisa ta fito idanuwanta jawur yasan akwai abinda ta gani.
Yana shiga Ra'eez yayi saurin tashi yana fad'in Jabeer kayana akwai matsala fa, kaje ka gyara komai bana so asamu matsala suyi kura. Murmushi Jabeer yayi yana fad'in da alamu ajiyar tayi kura sosai, bara naje na kakkab'e kada k'ura tayi mata illa.
Kwanciya Ra'eez yayi yana fad'in kayi sauri dan Allah. Raheena tace Dear meyasa zaka aje kaya baka rufe ba ai dole k'ura ta b'ata su, Allah yasa ba fararen kaya bane nasan dole a sake wanke su🤣.
Kasa rik'e dariya Jabeer yayi da sauri ya fita yana fad'in farare ne tass sosai Raheena yanzu zanje na gyara komai. Raheena tace sai ka dawo. Murmushi kawai Ra'eez yayi yana lumshe ido jin abinda Jabeer ya fad'a.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:40 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
3⃣4⃣
Saurin b'oye fuska Rumaisa tayi tana kok'arin goge hawayen da suke fuskarta jin labarin da Jabeer ya bata. Murmushi Jabeer yayi yana fad'in a mana afuwa matar lauya, laifin mu ne da bamu fad'a maki shirin mu ba, amma yanzu ina fatan kin fahimci labarin dana baki, sam Ra'eez baya son Raheena, yana so shima ya rama abinda akayi ma Abbunsa ne.
Jinjina kai Rumaisa tayi tana fad'in Allah ya so ban kwafsa ba, ai da farko kansu ya d'aure da na kirashi Annur, amma jin na ambaceta amatsayin surikar Mama sai hankalinsu ya kwanta, nima haka kawai naji na fad'i surikar Mama dan naga yanayin fuskar Yaya kamar beji dad'in abinda nayi ba.
Jabeer yace ai kin kyauta, ina fatan kuma zaki taya Ra'eez yakin da yake gabansa, ki d'auka Raheena namiji ce kawai, kuma kirik'a kokarin kaucema had'uwar ku waje d'aya hakan zesa zuciyarki ta natsu.
Rumaisa tace wallahi bakomai, ni mai iya sadaukar da farin cikina ne matuk'ar Yaya zai cika burinsa, yau ko cewa akayi saiya aureta zan iya amincewa idan har hakan zaisa ya cika burinsa.
Jabeer yace hakan ma bazata faru ba, domin yanzu ne zamu fara aiwatar da komai, kinga ana kammala shari'ar sai musha biki. Murmushi tayi ta rufe fuska.
Jabeer yace muje na ajeku gida tunda nazo. Rumaisa tace bara nayima Mama magana. Jabeer yace shikenan.
Tare da Mama suka shiga d'akin, mamaki Rumaisa tayi ganin Ra'eez a kwance ya rufe ido kamar me bacci ga Raheena a kusa dashi sai kallonshi takeyi. Saurin amsa sallamarsu Raheena tayi tana matsawa hada duk'ar da kai.
Bud'e ido Ra'eez yayi jin muryar Mama. Gyara kwanciyarshi yayi yana fad'in sannu Mama. Murmushi tayi tana fad'in kai ne da sannu, ya jikin naka? Da sauki Ra'eez ya amsa.
Kallon Rumaisa yayi suna had'a ido ya kashe mata ido d'aya, murmushi tayi itama ta rama. Mama tace zamu koma sai gobe idan Allah ya kaimu tunda ga Jabeer nan yazo.
Ra'eez yace kai Mama, ku bari zuwa dare bana son ku tafi. Da sauri Raheena tace haba ka barsu suje su huta ai akwai gajiya, tunda gashi nazo zan zauna da kai har wajen tara sai na tafi.
Murmushi Mama tayi tana fad'in sannu da kokari angode. Turo baki Ra'eez yayi yana fad'in to Rumaisa ta zauna sai ya kaiki ke da Abdallah anjima zai maidata.
Mama zatayi magana Raheena tace gaskiya baza'a wahalar mun da K'anwa ba, da ganinta ta gaji taya zaka ce ta zauna bayan ko ta zauna sai dai ta koma wancan falon tunda bazata iya zama anan ba dan a takure take.
Murmushi Rumaisa tayi tana fad'in maganar ki gaskiya babbar Yaya, nima bazan zauna ba kada na shiga hakkin ki. Raheena tace to ka gani, Mama kawai kuje ku huta zan kula dashi.
'Daure fuska Ra'eez yayi ya koma ya kwanta, jiyake kamar ya kwad'a mata mari saboda haushi, shi sam beso zuwanta ba yaso ace Pretty d'insa ce akusa dashi yau su sha soyayya amma wannan anacin tazo ta zauna.
Muryar Mama yaji tana fad'in to sai da safe kaci abinci sosai kafin kasha magani. Kai ya d'aga yana hararar Rumaisa. Dariya tayi ta wuce tana fad'in Yayana Allah ya baka lafiya kaji.
Suna fita Raheena ta matso tana fad'in D ashe ba bacci kake ba kawai ka rufe ido ka barni shiru,. Kauda kai yayi bece komai ba. Hannunshi ta kamo tana fad'in idan ina tare da kai tamkar ahalinka ne a kusa da kai, domin zan d'auke maka abinda bazasu iya d'auke maka ba ma.
Saurin zare hannunshi yayi yana mata wani kallo. Baki ta rik'e tana fad'in yi hak'uri wallahi mantawa nayi, zamana akusa da kai sai nake ganin kamar agidan mu muke shiyasa na iya rik'e ka amma ba halina bane.
Zeyi magana Rafeek ya shigo. Murmushi ya saki yana fad'in Hajiya Raheena kece mai jinyar kenan? Murmushi ta saki tana gaishe shi, sosai taji dad'i, duk da bata sanshi ba amma tasan abokin Ra'eez ne, lallai Ra'eez yana sonta, gashi har abokanshi sun santa.
Zama Rafeek yayi yana fad'in Ra'eez ya jikin? Ra'eez yace da sauki Yaya ya aikin? Rafeek yace akwai wahala, sai yanzu fa na tashi, abinci kawai na biya naci agida.
Ra'eez yace sannu da aiki. Shigowar Jabeer yasa Ra'eez ya kalli Raheena yana fad'in ki tashi ki wuce gida magriba ta kusa. 'Bata fuska tayi tana fad'in ka barni sai zuwa anjima bazan iya barin ka a..... Kallon da yayi mata yasa tayi saurin tashi tana turo baki.
Murmushi Jabeer yayi yana fad'in wai a ina aka tab'a korar d'an jinya? Rafeek yace ai mace ce ga magriba ta kusa kaga babu dad'i ta zauna nan, da ace babu kowa dan ta zauna ba wani abu bane, amma bana son ina ganin mace a waje da dare domin ba mutuncinta bane.
Murmushi Raheena ta saki jin abinda Rafeek ya fad'a, sai yanzu ta gane Ra'eez baya son tayi dare a waje, sannan ga abokansa duk maza yana kishi ta zauna a cikinsu.
Jaka ta d'auka tana fad'in D kana da gaskiya, tunda akwai maza a d'akin be kamata na zauna acikinsu ba, wasu ma zasu iya zuwa kaga babu dad'i a kalle maka ni, shikenan zan tafi sai zuwa goben.
Dariya Jabeer yayi yana fad'in ai kinsan abokina akwai kishi. Harara kawai Ra'eez yake aiko masa, be kulashi ba yacigaba da fad'in nan gaba kila bazai barmu shiga gidansa ba.
Raheena tace ai jin dad'i ne ka samu mai kishinka. Jabeer yace sosai kuwa, ai Allah ya nuna ranar biki. Raheena tace amin.
Juyawa tayi tana fad'in D kaci abinci da yawa dan Allah. Rafeek yace zaici, ki gaida gida. Fita tayi tana murmushi.
Tsaki Ra'eez yaja yana fad'in wallahi Jabeer kashiga hankalin ka. Jabeer yace daga fad'in gaskiya. Ra'eez yace shikenan, insha Allahu kaine zaka aureta.
Dariya Jabeer yasa hada rike ciki yana fad'in amma baka ta kirki, yanzu ka rasa da wadda zaka had'ani sai Raheena, haba ai koda bani da budurwa bazan iya aurenta ba.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in me yasa kake shiga maganarta to? Jabeer yace kawai ina tausayinta ne, duk da bansan zafin so ba amma ina tausaya mata domin ta kamu da sonka, kuma ma ni bazan iya auren wacce take son wani ba, to na aureta nace na auri wa? Ka auri mace, Ra'eez ya fad'a.
Dariya Rafeek yayi yana fad'in wallahi idan mutum yana kusa da ku sai kusashi ciwon ciki saboda dariya, yanzu kai Jabeer ai taimakon ka Ra'eez yayi daya baka ita, domin naga ko 'yar tsana baka da ita.
Dariya Ra'eez yasa yana fad'in wallahi kuwa Yaya, kaganshi nan kullum yana gida, lokacin bacci haka yake kwanciya babu mai sashi farin ciki, dan na bashi Raheena ai banyi laifi ba.
Jabeer yace sai dai ka bani Rumai.... Kamar walkiya Ra'eez ya diro daga gado, dariya Jabeer yasa yayi bayan Rafeek. Nufoshi Ra'eez yayi sai ga likita ya turo k'ofa.
Dariya Rafeek yasa yana fad'in likita kaga marar lafiyar ka ko? Murmushi likita yayi yana fad'in da alama yau zan baku sallama. Zama Ra'eez yayi yana fad'in wallahi da yafi.
Dariya suka sa Jabeer yace aikuwa sai jibi. Rafeek yace tunda dai ya warke ai shikenan. Matsawa Likita yayi yana fad'in bara na duba na gani.
Har likita ya gama dubashi yana hararar Jabeer. Kallon Rafeek likita yayi yana fad'in gaskiya jikin lauya da sauki, ko yanzu zaku iya tafiya gida.
Rafeek yace nima naga alamun sauki gara asallameshi mu koma gida. Likita yace shikenan bara ayi sallah. Jabeer yace mungode.
Sai da sukayi sallah kafin suka had'a kaya suka wuce. Kai tsaye gidan Ra'eez suka wuce dan Rafeek yace Jabeer ya kwana acan zuwa gobe sai suje wajen Mama aji abinda ta yanke akan zaman Ra'eez.
**** ****
Washe gari tare da Jabeer suka nufi gidan su Rumaisa, Mama tayi mamakin ganin su dan sauri take ta had'a kayan abinci Rumaisa ta kai masu.
Bayan sun gaisa suka fad'a mata sallamar da akayi masu. Murmushi tayi tana fad'in to Allah ya k'ara sauki, kaga yanzu sai kuje a kwaso kayanshi ga d'aki can ya zauna aciki.
Jabeer yace Mama ina ganin abar Ra'eez a gidanshi zaifi, domin a ayanzu akwai shirin da zamu fara kuma yana buk'atar natsuwa, tun bayan da ya bani labarinshi na fara tunanin yanda zan taimakeshi, rashin lafiyarsa da sanin abinda yake damunshi yasa na yanke shawarar komawa kusa dashi kafin Allah ya bama Ummu lafiya, hakan yasa na samu Iyaye na nayi masu bayanin zan koma gidanshi mu zauna, kuma sun amince mun.
Jinjina kai Mama tayi tana fad'in gaskiya mungode, dama haka Allah yake, idan ka rasa wani jigo sai ya baka madadinsa, hakika kai aboki ne nagari, Allah ya saka maka da mafificin alkhairin sa.
Jabeer yace amin. Rungume Jabeer Ra'eez yayi yana hawaye. Murmushi Jabeer yayi yana fad'in meye na kuka kuma, yanzu ka zama d'an uwana.
Bayan sun karya Jabeer ya bar Ra'eez anan yawuce gidansu saboda zaije wajen aiki. Shimfid'a Mama tayi masa a falo ya kwanta dan bacci yake ji saboda maganin da yasha.
Sai da Rumaisa ta kammala aikinta kafin taje ta zauna a kusa dashi, duk da bacci yake amma haka ta zauna tana gadinshi.
Wayarsa ce tayi k'ara, tana dubawa taga ansa Raheena. Tsaki tayi ta maida wayar silent. Ganin an cigaba da kira yasa ta d'auka.
Cikin sauri tace bacci yakeyi. Raheena tace Rumaisa ce? Kai ta d'aga tana fad'in itace. Raheena tace dama naje asibiti akace an sallameshi shine nake son naji inda yake nazo.
Rumaisa tace ai bacci yakeyi ki bari zuwa anjima da rana sai amaki kwatance kizo. Ba haka Raheena taso ba amma haka ta daure tayi mata godiya tare da kashe wayar.
Murgud'a baki tayi tana fad'in jarababbiya kawai, hakanan kin takuwara ma mijina, wallahi badan shiri bane da na nuna maki iya karki dan bazan lamunci had'a Annur da kowa ba.
Haka tayi ta masifa tamkar agaban Raheena take. Ra'eez da tun farkon wayar ya tashi ido ya tsura mata sai murmushi yakeyi ganin yanda ta dage tana masifa ita kad'ai.
Kamar ance ta juyo, waro ido tayi ganin Ra'eez ya tashi yana kallonta, da sauri ta yunkura zata gudu yayi saurin jawota ta fad'o jikinshi. Tusa kanta tayi tana mashi shagwaba.
Dariya yayi ya tashi tare da cire hannunshi ajikinta yana fad'in babu inda zaki sai kin mai-maita abinda kika fad'a.
Rufe fuska tayi ta zame gefe tana fad'in nifa bance komai ba. Ra'eez yace shikenan, amma ki sani ina binki bashi. Saurin d'aga kai tayi tana fad'in naji.
Wayarsa ce tayi k'ara, yana dubawa yaga Raheena, kallon Rumaisa yayi yana kallon wayar. Tsam ta tashi tayi waje da sauri. Murmushi yayi kafin ya d'aga.
D ina kwana ya jikin? Lafiya lau, ya amsa cike da yanga kamar mace. Wayyo D d'azu na kira Rumaisa ta d'auka wai kana bacci, dama ina so nazo na dubaka tunda ance an sallameka.
Yatsina fuska yayi yana fad'in ki barshi bana son kina zuwa kunyar Mama nakeji. Murmushi tayi tana fad'in nikam bazanji dad'i ba idan banzo ba, kasan fa har yanzu gajiyar Dubai bata sakeni ba amma tunda naji baka lafiya naji bazan iya zama ba, muma ranar lahadi muka dawo cikin dare, naso na kira alokacin amma naga dare yayi, da safe kawai Dady ya fad'a mana kana asibiti nan take naji gajiyar ta tafi.
Murmushi yayi yana fad'in kun dawo lafiya ko? Raheena tace lafiya lau, kayan suna hanya sai zuwa jibi zasu iso, D bakaga zab'en da nayi mana ba, tsarabar ka tana nan idan kazo zan baka.
Girgiza kai yayi yana fad'in ki adana mun ita sai nan gaba zan amsa. Kai ta jinjina kamar yana ganinta tace angama Angona, fatana Allah ya baka lafiya.
Ra'eez yace ina so na kwanta. Murmushi tayi tana fad'in ka huta lafiya idan ka tashi ka kirani kada na kira kuma baka tashi ba na katse maka bacci.
Ra'eez yace angama. Kashe wayar yayi yana sakin murmushi. Hannu yasa yana shafa wuyansa, ta wani gefen yana tausayin Raheena, bayaso Allah ya kamashi da laifin yaudara, Raheena batayi masa komai ba, asalima lokacin da abun ya faru batasan komai ba, mahaifinta ne me laifin shi yakamata ya amshi hukunci ba ita ba, amma dole ya dakatar da komai koda hakan zai ruguza amintakar da Alhaji Barau yayi masa, domin ko yanzu suka b'ata bazai damu ba, domin lokacin fafatawa yayi.
Ajiyar zuciya ya saki yana tunanin hanyar da zaibi dan kada ya cutar da zuciyar Raheena, yasan koya rabu da ita yayi mata gata, domin ta silar shi ta canza rayuwar ta wacce duk wanda ya aureta zaiji dad'in hakan. Lumshe ido yayi yana tunani.
***
Har la'asar suna tare da Jabeer, tashi sukayi domin suje gidan su Jabeer daga can su wuce gida. A tare suka fito. Mama tace ina kuma zakuje? Jabeer yace ai gara mu fita hakan zeyi masa dad'i, zamuje gidan mu daga can mu wuce.
Mama tace to abincin daren fa? Ra'eez yace Mama kinsan bana cin abu mai nauyi da dare. Mama tace to Jabeer fa? Jabeer yace nima hakan take mama.
Murmushi tayi tana fad'in haka kawai kun maida kan ku turawa, ai shikenan sai Allah ya kaimu, amma kasha maganin ka. Ra'eez yace to Mama.
*** ***
Kamar ya saba da 'yan gidan su Jabeer haka sukayi ta fira, har isha'i suna tare, anan suke jin Kawun Jabeer zaizo gobe. Jabeer yace yauwa idan yazo zanyi masa maganar ka, kaga sai muzo musameshi muji yanda zaice. Ra'eez yace Allah ya kaimu.
Wayarsa ce tayi k'ara, yana dubawa yaga Yaya Rafeek, bayan sun gaisa yace yana jiransu a gidanshi tare suke da Adnan k'anin Sameer zasuyi magana akan mutuwar Naseer.
Ra'eez yace gamu nan zuwa. Tashi sukayi suna masu sallama suka nufi gida cike da farin ciki, koba komai zasu fara samun hujjar shiga kotu.
0 comments:
Post a Comment