✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
Suna shiga Part ɗin su Habiban babu kowa a parlour'n, sai tace mata, "she just seat there and called her mother." koda ta je tana Toilet tana wanka shiyasa ta dawo tana mata murmushi tace, "Come, let's go to my room."
Tashi MEEMAN tayi ta bi bayan ta suka shiga ɗakin Habiban
Nuna mata kan gadon ta tayi tace mata, "set". Sannan ta fice ta ɗauko mata Fresh Yo me sanyi ta haɗo da Cup, zuba mata tayi ta miƙa mata tace, "take drink".
Murmushi MEEMAN tayi mata ta sanya hannu ta amsa tana me furta, "shukran". Kafin ta sanya a baki ta ɗan kurɓa kaɗan
Habibah cike da fara'a tace, "You can also teach me Arabic because I really like it."
"Ok insha Allah If you want I will teach you".
"Thanks. But I want you to tell me about your country. In the past we wanted to come but Baba refused to bring us."
Murmushi kaɗai MEEMAN tayi bata ce komi ba
Habiban na shirin magana sai ga Inna ta tura ƙofan ta shigo, kallon su tayi fuska a ɗaure tace, "uban me wannan yarinyan ta zo min a nan? Ke kika kawo ta ko Habibah ban miki kashedi ki fita harkan ta ba?"
Tura baki Habiban tayi tace, "kai Inna Wai me tayi muku ne da kuka tsane ta? Ni dai ina son ta tunda ƴar uwata ce kuma idan aka tsaga jini na dole sai an ga nata a ciki.."
"Uban ki tayi mana, ki je ki tambayi uban ki sai ya faɗa miki abinda tayi, tun wuri ki sallame ta ta bar min gida tun kafin in saɓa miki wlh, kuma ki zo ki tattara kayan ki ki wuce gidan Amina tunda ke ba kya jin magana, gwara ki je can ki zauna da ita ki riƙa mata aiki. Ki zo ki wuce kar ki sake kuma in dawo in tarar da ita wlh na gaya miki". Bata jira cewar ta ba ta ficewar ta
Gaba ɗaya zuciyar Habiba babu daɗi don har ƙwalla ne suka taru mata a idanu, dole ta mayar da su ta saka wa fuskar ta murmushi saboda kallon da MEEMAN take mata tace, "Don't worry. Inna is talking about the job she did for me."
Gyaɗa mata kai kawai tayi ba tare da tace uffan ba.
Shiru ne ya ratsa saboda Habibah ta kasa yadda zata yi ta sanar mata, "Let them go". Tun da ita ta kawo ta kuma yanzu idan tace mata, "su tafi." Zata iya gane Innar ta ce ta kore ta
Ita kanta MEEMAN duk da bata yarda da abun da Habiban ta sanar mata ba domin a jikin ta ta ji cewa faɗan da Innar ta yiwa Habibah a kanta ne. Shiyasa ta tashi tana kallon ta tace, "I'm leaving because I have a job. "
"Ok, let's go with you." Habiban tafaɗa tana mata murmushi
Fita suka yi ta kaita har bakin ƙofan su Murjana, bata shiga ba tayi mata sallama ta koma
Ita kuma MEEMAN ta buɗe ta shiga
Umma da Murjana ce a Parlour'n while Umma tana sanar mata da abun da ya faru ɗazu. Shiyasa yanzu da ganin MEEMAN sai Murjana tace mata, "Zulaiha, come here, Ummah she's calling you. "
Tsaya wa tayi tana kallon su, sai kuma ta taka ta isa wurin su ta tsaya ƙiƙam a kansu tana kallon su
Murjana tace, "Umma says she will not guarantee that you will stay in this house. You have to go out to work. It is not possible for you to sit on the room of a girl who is being cooked in your mouth and eat and then go back to bed, you have to do the housework since my mother gave it to you."
"Work?" According to MEEMAN full of surprise on her face
"Yes working or you Don't do it?"
"Na'am I can't". Tayi maganar tana juya wa ta wuce ɗaki. Tana jin Murjanan na zagin ta but bata ko juya ba har ta shige
Umma tace, "wai me tace ne?"
"Cewa tayi wai baza ta iya ba, ki ji fa Umma?"
Ƙwafa Umman tayi tace, "bar Ni da ita bari Abban naku ya dawo ai ya kusa zuwa. Je ki kira min Sajjad a ɗaki".
Tashi tayi ta wuce ɗakin Sajjad ɗin, koda ta je ta ganshi a kwance a saman gado yana ta sharan barci. Hannu ta sanya ta soma tashin shi tana kiran sunan shi
Daƙyar ya buɗe ido ya zuba mata yana kallon ta
"Umma na kiran ka".
Shiru yayi kawai yana kallon ta
Ita kuma ta juya ta fice abin ta, ta koma wajen Umma tana sake zuga ta a kan MEEMAN
A lokacin da Sajjad ya fito shima Abban ya dawo
Sannu da zuwa suka yi masa
Ya amsa yana zama cike da gajiya
Umma ta tashi ta kawo masa ruwa kana ta zauna tana kallon sa tace, "dama yanzu jiran ka nake yi Abban Sajjad, a kan wannan yarinyan da ka kawo ta ka ajiye min babu aikin fari bare na baƙi haka zata zauna min a gida wato? Kuma ɗazu na ce tayi min aiki ƙiri-ƙiri Sajjad yace baza ta yi ba, to Ni ban gane abin da ake nufi da ita ba domin wlh baza ta zauna min a sashi ba ta aikin komi ba sai dai ta ci ta sha abun da ta iya kenan, idan haka ne sai dai ta koma sashin Zubairu gaskiya".
Sajjad da ya buɗe baki ya soma magana Abba ya katse shi da cewa, "kayi shiru Sajjad ban son jin bakin ka. Ke kuma Jamila meye ne na son takura mata don Allah? Mene ne a kan aiki ca nake yi na ce zan kawo miki me aiki but kika ƙi? To ki barta kawai ta zauna tunda ko kin saka ta na tabbata bata iya ba, ba na son ki takura mata don Allah saboda zaki iya rusa mana shirin mu".
"Abba wai meye shirin naku?" Cewar Sajjad
"Ka bari zuwa anjima zan sanar maka, sannan zancen auren ku mun tsayar da shi nan da wata ɗaya me zuwa domin so muke yi ayi-ayi".
Umma zata yi magana ya katse ta da cewa, "Please Jamila ba na son musu kiyi abin da nace miki kawai, taso mu je ɗaki akwai maganar da zan faɗa miki". Ya ƙare maganar da tashi tsaye
Haka ta tashi itama ta bi bayan sa kamar zata fashe
Suna shige wa ɗaki Murjana ta bi Sajjad ɗin da kallo dake ta faman farin ciki sai tace, "wai Yaya don Allah me ka gani a wurin yarinyan nan da zaka aure ta? In fact ma su Abba fa so suke yi su amshi kaf dukiyar ta su kora ta ta bar gidan nan".
Fara'an fuskar sa ne ta gushe yana kallon ta yace, "whattt Are You saying? Ban fahimta ba?"
Sai a lokacin ma ta gane katoɓaran da tayi sai tayi saurin cewa, "suna so ne su amshi dukiyar ta su mallaki komi nata ya dawo hannun su shiyasa ka ga sun bar ta ta zauna, amma na san tunda ka kawo zancen auren ta sabida kai ne fa kawai zasu iya barin ta a gidan nan, kuma na san Abban zai buƙaci ka taimaka musu idan ta zama matar ka tunda ta ƙi yarda da su".
Shiru Sajjad ɗin yayi be ce komi ba illa tunani da ya faɗa, sai da Murjanan tayi masa magana kafin ya ɗago ya kalle ta yace, "to Ni ina ruwa na idan har zan aure ta? Su dukiyar ta suke so Ni kuma ita nake so, in dai zasu bar Ni in aure ta wannan me sauƙi ne ai, bari in je wurin Abban." ya tashi ya wuce ɗakin Abban da ya ga sun shiga
Itama Murjanan bin Bayan sa tayi da sauri.
********** *****
MEEMA da ta shiga ɗakin; computern ta ta ɗauko dana Abee ɗin ta ta ci gaba da aiki, sai dai gaba ɗaya fuskar ta babu wani walwala aikin kawai take yi but tana tuna abubuwan da Murjana ta gama sanar mata. Tana ganin zaman ta a gidan ya kusa zuwa ƙarshe idan har zasu takura mata... Shigowar Murjana ya dawo da ita cikin hayyacin ta, da sauri ta rufe computern ganin ta a gaban ta tana kallon cikin computern
Wayance wa Murjanan tayi tana sakin guntun murmushi da cewa, "Please barrow me your phone because I don't have a card in my own, I want to make a phone call with my friend's".
Mamaki ne ya hana MEEMAN motsi illa kallon ta da take yi. Bata ce komi ba dai ta ɗauki wayan ta miƙa mata
Sai da tace, "You did not remove the code."
Sannan ne ta tuna ta cire mata ta miƙa mata
Murjana ta so ta ga yanda take cirewan ne, but yanayin yanda take sauri wajen danna code ɗin yasa bata fahimci komi ba, dole ta amshi wayan don kar ta gane wani abu, ta samu wuri a gefen gadon ta zauna sannan ta saka Numban Abba ta kira sa. Yana peaking tace dashi, "hello Murjana ce". Shiru tayi tana sauraron sa sai kuma tace, "eh na amsa wayan amma ban ga yadda ta cire ba"... "Ok to". Daga nan sai ta katse wayan ta goge Numban ta miƙa mata tana sakin guntun murmushi da cewa, "thanks".
Gyaɗa mata kai kawai tayi ta amshi wayan ta ajiye, sai dai ta kasa ci gaba da abun da take yi domin har yanzu mamakin ta take yi. Ganin ta ƙi tashi a wurin sai ma kwanciya da tayi shiyasa ta kashe computern tare da miƙe wa ta kai ta ajiye a cikin Trolly ɗin ta, sai ta koma can gefen gadon ta soma dealing Numban Ishaq, sai dai har yanzu ba ya shiga that's why ta mayar da akalan kiran ga Esha. Gyara zaman ta tayi jin ta ɗauka ta sauya harshe zuwa larabci suka soma waya, sun jima suna waya duk a kan Ishaq ne da yanda za'a yi Eshan ta je gidan su ta duba mata shi, sai ta samo mata Numban shi
Murjana na zaune tana jin ta sai dai ba ta fahimtan komi shiyasa ta tashi ta fice
Fitan ta yasa MEEMAN ta tsakaita wayan tare da yin ma Esha sallama sannan ta ajiye wayan. Shiru tayi tana me faɗa wa tunani, a haka har aka kira sallah ta tashi tayi ta koma ta sake kwanciya, ko fita ta ci abinci ta ƙi yi
Sai ga Murjanan ta zo kiran ta, "su ci abinci".
She looks at her in amazement, sai dai bata ce komi ba and she got up and followed her
Suna zaune duk kan su a saman dainning
Da sauri Sajjad ya tashi ya ja mata kujeran kusa da shi yana mata murmushi da cewa, "have a seat Baby".
Ko kallon sa bata yi ba ta samu wuri ta zauna
"Daughter, don't go into the room. You sit here with your siblings, stay in them and talk to them ok?" Inji Abba yana kallon ta da murmushi
Jinjina kanta tayi kawai ba tare da tace uffan ba
Sajjad da ya ɗauki Plate zai yi serving ɗin ta yace, "What will you eat if I pour it on you?"
"Nothing".
Abba said, "you mean you don't eat anything?"
"I'll have some tea."
"Tea is not food Daughter. Carry and eat ok?"
Still kanta ta jinjina masa
Sai yace, "Sajjad serve her".
"Ok Abba". Shi ya zuba mata jollof rice ɗin tare da veggies ya tura mata a gaban ta
Bata ce komi ba ta ɗauki spoon ta soma ci kaɗan-kaɗan don ko kwatan cokalin ba ta iya cuko sa
Shiru wurin ya ɗauka kowa sai cin abincin sa yake yi, while Sajjad gaba ɗaya hankalin sa na kan MEEMA, sosai yanda take cin abincin nata ya ɗauki hankalin sa har yana manta wa da shima abincin yake ci
Sai da Murjana ta bugi cokalin sa sannan ya dawo hayyacin sa, "kai yaya ka mayar da hankali a kan abincin ka ba guduwa zata yi ba kuna tare".
Hararan ta yayi yana langaɓe kai ya kalli Umma yace, "Umma ki ce mata ta fita harka ta yarinyan nan".
Taɓe baki ita kuma tayi bata ce komi ba illa abincin ta da take kaiwa baki fuska babu walwala
Murjana tace, "Yaya ya kamata ka kaimu shopping da ita hakan zai saka mu sake shiga jikin ta, ko ya Abba?"
"Yes haka ne Murjana," sai ya kalli MEEMAN yace, "Daughter, are you going shopping with your siblings and seeing the city."
MEEMA da ta ɗago kai tana kallon sa kasa cewa komi tayi. Sai da ya sake maimaita mata sannan tace, "ok". Ta mayar da hankalin ta kan abincin da take ta faman cakala. Ita ta soma tashi ta wuce ɗaki
Hakan yasa da sauri Murjana ta tashi ta bi bayan ta. Tana shiga ɗakin ta ganta a zaune sai tace, "get ready to go don't Bro Sajjad hear us silently".
Bata ce komi ba ta miƙe ta shiga Toilet ɗin, wanka tayi bayan ta fito sai Murjana ta shiga
MEEMA tayi shirin ta kamar ko yaushe yanda ta saba, bayan ta saka riga da wando sai ta ɗauki Abaya baƙa me kamar alkyabba ta sanya, ta yane kanta da farin gyale me Stones wanda ya ƙara fito da cuty face ɗin ta sosai ta ƙara yin fayau kasancewar babu abinda ta sanya, babu wani annuri a face ɗin ta haka suka fice a ɗakin ita da Murjana
Sajjad dake jiran su a Parlour tun fitowar su ya kasa ɗauke ido a kan MEEMA, gaskiya Allah yayi diri a nan wurin, yana rasa nutsuwar sa a duk sanda yayi tozali da ita ji yake yi kamar ya je ya haɗiye ta tsaban shauƙin da yake ji a kanta, har yana jin kamar bazai iya jure har nan da one month be mallake ta ba, be san ya zai yi da tarin buƙatuwar ta a zuciyar sa ba. Daƙyar ya iya control kansa suka fice a gidan bayan sun yiwa su Abba Good bye
Da suka fita MEEMA baya tayi ninyan shige wa sai Sajjad ɗin yace, "ta dawo gaba".
Tsaya wa tayi tana kallon sa while tana sake haɗe kyakykyawar fuskar ta
Shi kuma murmushi yayi mata yana sake roƙon ta a kan, "She Return the front seat".
Kasancewar Murjana tuni ta shige baya shiyasa ta buɗe gidan gaba ta shiga
A haka ya ja motan suka fice a gidan
Duk inda suka bi idanun MEEMA na kai, sai kallon yanayin garin take yi duk da ba wai farin ciki take ji a zuciyar ta ba
Hakan da Sajjad ɗin ya gani ne yasa yake mata bayanin duk inda suka wuce
Sai dai bata kula sa ba har suka kai wani ƙaton shop Mall suka fito. Tana biye da su duk inda suka sanya ƙafa har suka shiga ciki. Sai dai duk yanda suka yi da ita, "ta dauki abun da take so." but ta ƙi ɗauka
Dole Sajjad da kansa ya dinga jidan mata abubuwan duk da ya ga yayi masa
Itama ta fannin Murjana duk abinda ta ɗauka tana daukar mata, domin tana ganin ta hakan ne zata sake shiga jikin ta sosai idan ta bata kayan a matsayin gift ɗin ta.
Har suka gama suka fito suka wuce wajen shan Ice cream, nan ma MEEMA ta ƙi taɓa duk abin da suka bata, ce musu tayi, "she does not want to drink anything." Dole suka kyale ta sabida banza tayi da su daga baya
Murjana tace, "gaskiya Yaya kana da jan aiki a gaban ka wajen yarinyan nan, Allah ba na tunanin zata so ka ko kaɗan, kana gani fa abun da take yi ko magana wannan bata taɓa yin maka ba".
Sajjad da kamar zai yi kuka yace, "Murjana nima ban san meyasa take min haka ba? Kina ganin akwai makusa a jiki na da har zata ƙi so na?"
Murmushin ƙeta tayi kafin tace, "babu Yaya sai dai kawai ina tunanin har yanzu bata saba da mu bane, tabbas akwai abun da ke ranta da har ta ƙi sakin jikin ta da mu, amma ina ga duk sanda ka aure ta sai yanda ka juya ta Yaya, nayi maka alƙawari sai ka juya ta kamar waina domin sai ta koma a tafin hannun ka, kawai ka bari lokaci yayi Yaya kai da kanka zaka sauke mata duk wani abun da ke kanta".
Dariya yayi yana ɗan shafa tulin gashin kansa, sai ya kalli MEEMAN da hankalin ta ke kan waya amma tana sauraron abun da suke faɗi, sai dai kasancewar ba ta gane abun da suke cewa shiyasa bata san da ita suke yi ba. "Ƙanwata nima wannan lokacin nake jira, abu ɗaya ne yake hana Ni aikata abin da ke raina a halin yanzu a kanta, sabida kawai ina son mallakan ta that's why komi nake yi a sannu, ai kamar yau ne wata ɗayan zai cika." Sai ya ci je leɓe yana faɗin, "zata san waye Sajjad Aliyu Ahmad Riskuwa".
Dariya Murjanan ta sheƙe da shi tana ɗago Glass cup ɗin hannun ta dake cike da Ice cream ta miƙa masa suka haɗa Cup ɗin sannan suka ci gaba da sha suna ci gaba da hiran su. Daga ƙarshe gida suka wuce bayan sun gama zagaye-zagayen su.
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏼
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NO_18*
Tun daga ranan MEEMA ta soma ganin canji a gidan, sosai Murjana ta shiga jikin ta duk inda ta sanya ƙafa tana biye da ita, tun ba ta sakar mata fuska har dai itama ta saki jiki da ita sosai tunda har ɗaukar ta take yi su fita wajen friends ɗin ta tare, ko kuma wajen dangin su suyi ta yawo hakan yasa MEEMAN ta sake sakin jiki da ita har suka shaƙu sosai
Gefe ɗaya kuma ana ta shirye-shiryen auren ta ita da Sajjad but babu wanda ya sanar mata sai da ana jibi biki Habiba ta dawo gidan saboda bikin, da ɗokin ta ta je wurin MEEMAN tana tsokanar ta da, "Amarya Amarya."
A nan ne abun ya bata mamaki take tambayar ta, "Who is the Bride?"
"Oh you mean you don't know who bride is? I know everything wlh, I just wish you the best of luck you are lucky you got Bro Sajjad, I congratulate you because you are compatible with each other".
MEEMA fa kanta ya ƙulle cike da rashin fahimta tace, "I do not understand you. Please explain to me?"
In Surprised Habiba said, "You mean you don't know this week you're going to get married? Are you kidding me?"
Quickly MEEMA stood up looking at Habiba but she couldn't say anything
While Habiba itama miƙe wa tsaye tayi ta kamo hannun ta ta mayar da ita tana cewa, "What's going on? What's wrong with you?"
Idanuwan ta ciko wa suka yi da hawaye still tana kallon Habiban tace, "I don't know what you mean. You said I was going to get married but who am I going to get married without my knowledge?"
"You and Sajjad, I think you are in love, and any service you see in this house is for your marriage."
"I don't know about it. I don't love Sajjad. In fact I hate him in my heart. I don't love him! How can I trust him to marry me? Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Ta ƙare maganar tana tashi tsaye da sauri duk ta gama rikice wa. Sai kuma ta juyo a firgice tana kallon Habiban da cewa, "I will not marry him. I hate him! I have to leave this house today. I will not stay." Ta wuce wajen kayan ta cikin ruɗe wa har hawaye sun soma zubo mata
Da sauri Habiba ta je ta riƙo ta ta dawo da ita bakin gadon suka zauna, "Calm down Zulaiha, I understand your situation but there is no way you can leave this house now, be patient please stay".
"Do you want me to marry him? Do you want me to marry someone I don't like?"
Jinjina mata kai tayi tana kallon ta and she Said, "yeah but..."
"Noo! it is not possible. I have someone I love, and Sajjad is not one of the few men I can marry. How can they marry me without my knowledge? It is not possible until I leave this house." Sai ta saki kuka tana kifa fuskar ta a tafukan hannayen ta
Sosai Habibah ta rikice ganin yanda MEEMAN ke kuka sosai. Duk rarrashin da tayi mata taƙi yin shiru. Buga ƙofan da ake yi yasa Habiban ta sake rikice wa tana kallon MEEMA a firgice tace, "Please Zulaiha be quiet, I will help you to leave this house but be quiet so no one understands".
Kallon ta MEEMAN take yi da idanun ta da suka kaɗa suka yi jazur sai tsiyayar da hawaye take yi
Hannu ta saka ta share mata hawayen tana cewa, "Don't let anyone understand what's going on. Please pretend there's nothing ok?"
Gyaɗa mata kai tayi itama tana sanya hannun wajen share face ɗin nata tare da gyara wa
Ita kuma Habiba zuwa tayi ta buɗe ƙofan. Murjana ta gani a tsaye sai tayi saurin sakin murmushi da cewa, "har kin dawo?"
"Yes na dawo, wai me kuke yi ina ta buga ƙofa kun yi banza da Ni?" Tayi maganar tana ƙoƙarin shige wa
Jirga mata tayi a hanyar tana me rufo ƙofan da cewa, "babu komi muna hira ne da Zulaiha, dama yanzu nima nake son in tafi".
Murjanan da ta shiga ɗakin suna haɗa idanu da MEEMA ta nufe ta da mamaki tana cewa, "Sister, what's wrong with you? I look at you with tears in your eyes".
Shiru MEEMA tayi tana kallon ta sai kuma ta mayar da idanun ta ga Habiba, zata buɗe baki tayi magana kenan
Sai Habiban tayi saurin zama kusa da ita tana cewa, "wani abu ne ya faɗa mata a idon shiyasa kika ga sun yi ja, yanzu na gama cire mata har kuka tayi min kamar wata Baby". Ta ƙare maganar tana dariya
Itama Murjanan dariya ta saki tana cewa, "I'm sorry sister".
MEEMAN murmushi kaɗai tayi mata ba tare da tace uffan ba don bata san me Habiban ta faɗa mata ba
"Ok yanzu ki tashi mu je Part ɗin ku akwai kayan da na kai can zamu haɗa a can, kin san su Khalid zasu zo min bikin nan, akwai tanadin da nayi musu but ba na son su Umma su gani don ba wanda zan ba shi".
Dariya Habibah tayi tace, "to mu je". Har ta tashi sai kuma ta kalli MEEMAN tace, "will you follow us?"
Murjana tayi saurin cewa, "No, leave her let's go. We'll be back soon."
Har suka fita MEEMA bata ce da su komi ba. Shiru tayi tana lumshe idanun ta tears welled up in her eyes
Habiba ce ta dawo ɗakin da sauri tana ce mata, "sorry i'll help you later, but please don't go and stay till i come back ok?"
Gyaɗa mata kai tayi tana me aza kanta saman pilow ta mayar da idanun ta ta rufe ruff
Ita kuma Habiban ta fita ta barta a ɗakin.
Zuwa magriba sai ga ta ta dawo, bata bari kowa ya ga shigowar ta ba har Murjana don a lokacin tana ɗakin Umma, ta shiga da sauri tace ma MEEMAN, "She picked up her Trolley and left". Ita ta taimaka mata da ƙaramin jakar suka fice har wajen gidan. Kasancewar an shiga sallah shiyasa babu wanda ya gansu. Rungume ta tayi tana hawaye tare da kallon ta tace, "Where are you going from now? I don't want you to go because I will miss you!"
With tears in her eyes, she said, "I miss you too! but I have no choice but to go back to Riyadh Saudi Arabia."
"No, please, I beg you not to go back and live alone like everyone else. If they refuse to hold you honestly they want to marry you. I know your mother will hold you in both hands. Please go back it will be better for you. If you live alone you will not be happy. Stay here in Nigeria or one day we will see each other please." Habiba ta ƙare maganar hawaye sosai a wannan lokacin suna fitar mata a idanu
MEEMA kasa magana tayi kasancewar itama shashsheƙan kukan da take yi ya ci ƙarfin ta. Tana shirin zame hannayen ta ba tare da tace da ita uffan ba
Sai Habiban ta sake rungume ta kafin ta sake ta tana share hawayen fuskar ta da bayan hannun ta, ta ɗaga mata hannu tana cewa, "Please stay here in Nigeria, hurry up and leave here to let Abba come out to see you". Daga haka ta juya ta shige gida da sauri
Itama MEEMAN jan Trolley ɗin ta tayi tana rataye da ƙaramin a hammatar ta taci gaba da tafiya. Har sai da ta fita titi kafin ta tsaya tana faman waige-waige. Bata sha wahala ba ta samu keke napep tace, "he peak her with hotel". Kasancewar ta ga dare yayi baza ta iya zuwa wani wuri da daren nan ba. Kai tsaye ana kaita hotel ɗin ta kama ɗaki ta shiga. Zuwa washe gari zata wuce Kaduna tuna wa da tayi akwai mahaifiyar Ummee ɗin ta da ƙanin ta, ko a wajen su zata iya zama ba sai a wajen Ummeen ta ba, duk da bata so yanke wannan shawaran ba amma tuna wasiyyar mahaifin ta da kuma maganar Habiba yasa taga ya dace ta koma wajen su, bata da kowa a can Riyadh baza ta iya rayuwa ita kaɗai ba.
Da safe bayan ta gama shirya wa ta fito ta sami me napep ya kaita tasha inda zata samu motan Kaduna. Wannan karon ma drop ta ɗauka suka wuce Kaduna, wajen goshin magriba suka isa.
A cikin G.R.A Ummeen ta take zaune ita da Mahaifiyar ta da ƙanin ta, shi yanzu ƙanin nata ya koma Abuja da zama da shi da Matar sa da ɗan su guda ɗaya, wajen shekaru shidda kenan da aka tura sa yaƙi ya tafi ya bar matar tasa a can Abujan kasancewar tana aiki shiyasa bata dawo nan Kaduna ba, sannan kuma ɗan su na school wannan dalilin ne ya zaunar da su can, sai dai jefi-jefi tana zuwa Kadunan ta gaishe su. Yanzu haka mahaifiyar Ummee me suna Hajiya Halima suna kiran ta da Hajiya, tana cikin halin rashin lafiya na hawan jini wanda yasa har ta rasa ƙafafuwan ta tana zaune a wheelchair ne. Mahaifin su Ummeen shi ya daɗe da rasuwa, su biyu Hajiya ta haifa daga ita sai ƙanin ta Captain Hashim. Kuma mahaifin su dai-dai gwargwado ya bar musu dukiya me ɗumbin yawa, don gidan su babban gida ne me hawa biyu. Part ɗin Hashim da matar sa daban duk a ciki idan ya zo hutu suna sauka a nan, sannan sai na Hajiya sai kuma inda Ummee ke zaune a halin yanzu, tana aiki ne a wani Company tun dawowar ta daga Riyadh.
Kwatancen da MEEMA ta yiwa Me motan be sha wahala ba wajen tambayar mutanen garin, tunda sun rigada sun shiga G.R.A ɗin, duk da MEEMA bata taɓa zuwa ba amma ta riƙe sunan gidan su Ummeen nata sosai tunda ba wani ɓoyayye bane, har Numban gidan sai da Abee ya sanar mata da zai rasu hakan yasa nan da nan suka gano gidan.
Bayan ta sauka ta sallami me motan ta ɗauki kayan ta ta taka a hankali zuwa bakin Gate ɗin. Ta jima a wurin tana ta kallon ƙofar gidan ta kasa buga wa, lokaci ɗaya idanun ta suka cika da hawaye yayinda zaciyar ta ta soma zugi tsaban ƙuncin da ya ziyarce ta a halin Yanzu ɗin. Ba komi ya haifar mata da hakan ba sai tuna wa da tayi a yau zata haɗu da mahaifiyar ta wacce ta guje su a cikin rayuwar su gaba ɗaya, kuma bata taɓa tunanin ta neme su ba har ga shi Abee ɗin ta ya bar duniya da baƙin cikin ta, ta kasa gane wani irin abu ne Abee ya aikata mata da har ta zaɓi tayi masa wannan mummunan hukuncin? Baƙin ciki da ƙuncin da take ji a wannan lokacin tamkar yanzu ne Ummeen ta tafi ta bar su, sanadin ta sun rasa farin cikin su wanda hakan yasa ta rasa mafi soyuwa a rayuwar ta wato Abee ɗin ta. Sai kawai ta fashe da kuka sosai har bata iya ganin komi tsaban yanda hawayen suke kwaranya a face ɗin ta. Hannu ta sanya ta dinga share wa yayinda wani tuƙuƙin baƙin ciki ke kai komo a maƙogwaron ta. Ta kasa ɗaga ƙafafu ta isa bakin Gate ɗin bare ta buga. Tana nan tsaye wadda ta fi mintuna talatin a wurin har an kira sallan magriba ana shirin shiga
A lokacin ne aka buɗe Gate ɗin gidan wanda me gadi ne da shi da masu hidiman gidan su biyu suka fito zasu wuce masallaci. Da kallo suka bi ta ganin ta da suka yi a wannan yanayin kuma a jikin gidan su. Sai dai babu wanda ya samu halin yin magana illa idanu da suke bin ta da shi kamar wacce basu taɓa ganin halitta makamanciyar nata ba, gaba ɗaya a cikin zuciyoyin su mamakin ganin Balarabiya a bakin ƙofar gidan suke yi. A haka har suka wuce ta suna waigen ta
While MEEMA tunda tayi musu kallo ɗaya taci gaba da share hawayen ta kafin ta ja ƙafafu a hankali ta isa ƙaramin ƙofan ta tura ta shige. Kallon gidan take faman yi tana tafiya a hankali har ta isa ƙofar da zata shiga gidan, a nan ma ta ɓata lokaci kafin ta sanya hannun ta dake faman rawa ta soma Nocking. Kasancewar a hankali take Nocking ɗin shiyasa sai da ta ɗau lokaci tana yi kafin a zo a buɗe mata
Wata mata ce me jiki don a ƙalla zata kai shekaru arba'in, wanda daga gani ƴar aikin gidan ce. Tunda ta ɗaura ido a kan MEEMAN ta tsaya kallon ta, sai da ta gama ƙare mata kallon kafin tace, "baiwar Allah daga ina?"
Ita MEEMA yanda bakin ta yayi mata nauyi shiyasa ta kasa yin magana illa zuba mata idon itama da tayi tana bin ta da kallo. Koda tayi mata maganar bata fahimci abun da tace ba amma hakan yasa ta buɗe baki a hankali tace, "May I come in?"
Jin tayi turanci kuma bata gane ba kasancewar yanda take furta words ɗin sai Matar ta sake cewa, "to Ni gaskiya ba na jin ki ina zuwa". Sai ta juya ciki tana ce ma Hajiya dake zaune a kan wheelchair ɗin ta, "wata budurwa ce ta zo Hajiya, amma gaskiya ba na jin yaren nata, turanci ne ko wani yaren ne oho don maganar nata wani iri wlh, Idan kika ganta kamar ba ƴar nan bace, sanye da kayan Larabawa ta zo".
Hajiya dariya tayi da cewa, "Kai Zabba'u kin cika Zabbo ta, wlh kin ci sunan ki. Idan ban dake memakon ki zauna kina min kwatancen ta ai gwara ki ce mata ta shigo kin bar ta a waje kuma".
"To kuma fa haka ne Hajiya, to amma kin san yanda duniya babu gaskiya shiyasa gwara in soma sanar muku don wlh ban yarda da ita ba Ni daga kallon ta, sak bata yi kama da ƴar nan ba, yaren nata ma fa ban fahimci me tace ba don ba turanci bane ai da zan gane ko ya ya ne tunda ina jin kaɗan-kaɗan."
"Ki dai zauna kiyi ta rattaba zance da Allah kin bar baiwar Allah a waje". Hajiya tafaɗa tana jan guntun tsaki
Hakan yasa Zabba'un ta wuce da sauri bayan ta ce, "to kiyi haƙuri Hajiya kar ranki ya ɓaci, bari in CE ta shigo to". Tana zuwa bakin ƙofan tace da MEEMA, "shigo baiwar Allah".
MEEMA da bata fahimci me tace ba ko motsi bata yi ba sai kallon ta da take yi
Sai Zabba'un ta sake maimaita mata da gwarancin turancin ta tana sanar mata, "ta shigo ciki".
A hankali ta taka ta shiga ciki idanun ta suna faɗa wa kan Hajiya wanda itama ta kafe ƙofar da kallo
Da sauri ta furta, "Zulaiha ke ce?"
Har gaban ta ta tako ta tsaya ba tare da ta furta komi ba illa son hana fitowar hawayen ta da suke maƙale a kwarmin idanun ta
"Ya ki Jika ta, taho.. taho wuri na". Hajiya ta furta cike da rawan baki tsaban murnar ganin MEEMAN
Yanda take ya fico ta da hannun ta ne yasa ta isa gare ta a hankali tana duƙa wa a gaban ta
Hannayen ta ta kama cike da farin ciki kamar zata yi kuka tace, "Will I ever see you again? How did you get here? Who brought you? Where is your father?"
Bata iya amsa mata ko kalma ɗaya ba duk da a ranta ta ɗan ji sanyi da yanayin karɓar da tayi mata, sannan kuma farin cikin da ta ga ya bayyana a fuskar ta yasa ta gane tana murna da zuwan ta. Shiyasa ta matsa sosai ta rungume ta hawayen idanun ta suna sauka kamar an kunna su
Sosai itama Hajiyan ta sake ƙanƙame ta a lokacin tana kuka da sambatu
Ita dai Zabba'u baki ta kama kawai tana kallon su. A lokaci ɗaya kuma sai ƙwaƙwalwan ta ta bata ƙila yarinyan Ummee ce, domin ta san da cewar tana da ɗiya kasancewar wani lokacin tana yawan jin suna ambatar ta, sai dai a zahiri bata taɓa ganin ta koda a hoto ne duk da ta daɗe a gidan tun kafin Ummee ta dawo Nigeria, shiyasa tayi tunanin ita ce ɗiyar Ummee duk da ba wai kama suke yi ba, amma Idan ka kalle ta tabbas zaka gane jinin ta ne.
Sun jima a haka kafin Hajiyan ta sake ɗago ta tana me riƙe mata hannu da cewa, "Zulaiha, will we see you again? Your mother do not came to check on you, and I was sick and had legs, and your uncle was not in the country to go and check on you and your father, I hope he feels better?"
Fashe wa tayi da kuka tana girgiza mata kai tace, "My father is dead. He is dead.. He is dead." Yanda kukan ya ci ƙarfin ta ta kasa ƙarisa zancen nata dole tayi shiru tana sake rungume ta a wannan lokacin tana kuka sosai
Salati kawai Hajiya take yi tana bubbuga bayan ta. Sun jima a haka kafin ta ɗago ta taci gaba da rarrashin ta, sannan ta kalli Zabba'u da har yanzu tana wurin tana ta kallon su, tace da ita, "ki kawo mata ruwa ta sha sannan ki kira min Zulaiha a ɗaki".
"To Hajiya". Ta amsa ta tana wuce wa wurin Fridge ɗin da sauri
Ita kuma Hajiya hannu ta sanya tana share mata hawayen fuskar ta tana ci gaba da rarrashin ta, sannan ta ɗago ta ta zaunar da ita kan sofa dake jingine da wheelchair ɗin ta. Da Zabba'u ta kawo ruwan ita da kanta ta amsa ta bata ta sha tana sake shafa mata fuska cike da rarrashi
Zabba'u da ta wuce kiran Ummee bata kai ga hawa benen ba ita Ummeen ta fito daga saman zata sauko, kyawu da zubi da tsari gami da haɗuwa da tsaban iya kwalliya shi zaka soma gani a tattare da ita, a kallon farko baza ka taɓa ce mata ta haura shekaru arba'in ba, but tsaban kyawun jikin ta da ɗaukan wanka irin nata sai kayi tunanin ƴar shakara talatin ne, sam bata da jikin manyanta. Tana sanye da lesi me uban tsada da tsantsan kyawu, gaba ɗaya hannayen ta da wuyan ta duk ta zuba sarƙa da awarwaron Gwal sai walwali suke yi, fuskar nan nata ya ɗau Powder duk da ba kwalliya ne a fuskar ba, yanda take tafiya zaka tabbatar da babban mace ce me aji sosai. Tun daga saman benen idanun ta suka sauka a kan MEEMA, sai dai bata gasgata itan bace kasancewar ba ta ganin fuskar ta sosai. Hakan yasa ta ɗan ƙara sauri wajen sauko wa tana son ƙaryata idanun ta. Sai dai bata gama ƙarisowa ba suka haɗa ido da MEEMAN wanda a lokaci ɗaya ta tsaya cak daga inda take tsaye.
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏻
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NO_19*
Wasu sabbin hawaye ne suka wanke mata fuska saboda arba da tayi da fuskar mahaifiyar ta a yau, kimanin shekaru biyar da watanni kenan rabon da ta sake tozali da ita. yanda idanuwan ta suke mata zafi ne yasa ta mayar da idanun nata ta rufe ruf tana sauke numfashi daƙyar
While itama Ummee tuni hawayen ne suka cika mata idanu, sai dai ta kasa samun ƙwarin gwiwan da zata iya tunkaran MEEMAN a halin yanzu, gaba ɗaya ta kasa motsa wa a inda take
Inda Hajiya tace da ita, "ki ƙariso mana kin tsaya a wurin, ko zuwan nata ma baki yi murna da shi bane?"
Girgiza kanta ta soma yi still hawaye na zuba a face ɗin ta, sai a lokacin ta samu damar taka wa ta iso gaban MEEMAN zata sanya hannu ta taɓa ta tare da furta, "My daughter..."
Saurin janye jikin ta tayi tana tashi da sauri, ido cikin ido take kallon ta cike da wani irin yanayi da fushi a tattare da ita tace, "Don't touch me again! I am not your daughter because I will never be your daughter." Sai ta juya ga Hajiya cike da rawan murya a wannan lokacin tace, "She is not my mother. If she touches me again I will leave this house. I will enter the world wherever I am and, I will not stay here."
Gaba ɗayan su shiru suka yi suna sauraron kukan ta da a yanzu take yi da ƙarfi wanda ke fita da ɓacin rai da tuƙuƙin baƙin cikin da ya kasance da ita tsawon shekaru
Hajiya ce tayi ƙarfin halin kiran sunan Zabba'u tana bata umarnin, "ta kai MEEMAN ɗakin kusa da nata".
Hakan yasa ta iso da sauri ta ja Trolley ɗin bayan ta ɗauki ƙaramin
Hajiya ta yiwa MEEMAN bayanin, "she follow her."
Bata ce komi ba ta bi bayan Zabba'un har ɗakin da zata kaita, a downstairs ne ɗakin bayan ka wuce dogon corridor zaka hangi ɗakuna guda biyar a jere, ɗaya daga ciki ta shigar da MEEMAN. Dayake ɗakin babu datti tunda a koda yaushe ana gyara wa, tana ajiye mata jakan ta ta fito ta bar ta.
********
"To kin gani abun da nake gudan miki kenan tuntuni Zulaiha, son zuciya da ruɗin ƙawaye yasa kin aikata mummunan aikin da zai ja miki dana-sani a rayuwa, yanzu ke baki ji kunya ba da kiran ta da kika yi a matsayin ɗiyar ki? Kin san kina son ta meyasa kika yanke wannan hukuncin? Dama na sha sanar miki akwai ranan da zaki yi nadama, tunda kika tafi kika bar su baki sake waiwayan su ba, sannan ni ba ƙafa ba bare in je in ga lafiyan su, wanda kuma zai je ɗin yanzu kusan shekaru shida kenan basu dawo ba, bamu da tabbacin yana raye a halin yanzu ko ba ya raye, wata huɗu kenan da wayan Hashim ba ta shiga, ba don haka ba da shi ne zai riƙa zuwa yana duba mana a halin da suke ciki. Ni na tabbata Faruk ya tafi da baƙin cikin ki a zuciya domin kin cutar da shi sosai, ya koma ga Allah ya bar ki a duniyar da kike ganin ya fi miki shi, mutum me ƙaunar ki amma kika kasa zama ki tallafi rayuwar sa da ɗiyar sa, wannan wani irin zuciya ce da ke Zulaiha? Anya kina da ɓurɓushin imani?"
"Wlh Hajiya nayi matuƙar nadaman abin da na aikata, na san zuciya ta bata yi min adalci ba da har na yanke hukuncin barin su, amma wlh ina matuƙar nadama da abun da nayi musamman ma a yau..." Kukan da ya ci ƙarfin ta yasa a dole tayi shiru
Hajiya tace, "hmm kaɗan ma kika gani, yanzu ga shi kin koya wa ɗiyar ki tsanar ki a zuciya, ba na tunanin a yanzu kina da wani sauran mutunci a idanun ta, wacce ta tafi ta bar ƴar ta tsawon lokaci babu waiwaya ai ba na tunanin akwai wani sauran soyayya, gwara ma ki tashi min a nan tun kafin raina ya ɓaci, kuma ban amince ki takura mata ba domin muddin ta bar gidan nan a sanadin ki wlh sai nayi mummunan saɓa miki Zulaiha". Daga haka Hajiyan ta kwaɗa wa Zabba'u kira. Tana zuwa tace mata, "ta mayar da ita ɗaki."
Haka ta ja ta suka wuce ɗakin Hajiyar suka bar Ummee a wurin tana ta faman share hawaye. Zuciyar ta sosai take mata tuƙuƙi da baƙin ciki sabida fama abun da ke cikin ta. Ta jima a wurin ta rasa me ke mata daɗi, daga ƙarshe ta tashi ta wuce ɗakin da aka sauke MEEMAN
Tunda ta shiga ɗakin MEEMA ta sauke ido a kanta sai tayi saurin kawar da su tana sake haɗe rai sosai
Ita kuma a hankali ta taka izuwa bakin gadon da take zaune, kasa zama tayi illa tsaya wa da tayi tana kallon ta yayinda idanuwan ta har yanzu suna da danshin hawaye. A hankali ta soma magana a cikin harshen turanci. "I know I was wrong with you and your father, and I do not know how to apologize to you. I was a mother who loved herself more than anyone else. I followed the deceptions and advice of my friends. I made a big mistake that I now know..." sai tayi shiru sabida kukan da ya taho mata sosai a yanzu ɗin. Daƙyar ta iya buɗe baki da zummar taci gaba
Sai MEEMAN ta dakatar da ita wajen ɗaga mata hannu da cewa, "enough..! I do not want to hear your words in my ears, you are a tyrant in my place, you do not love me and you do not love my Abee, if you had faith you would never do that to us, how can I call you mother? Do you think that is appropriate? Tell me, do you think that is appropriate?" Ta ƙare zancen da wani irin ihu tana kuka sosai. Sai kuma ta haɗe hannayen ta wuri ɗaya tana haɗa su da fuskar ta tace, "please leave this place before my heart beats, I do not love you and I don't want to see you around me!"
"Daughter..."
"Please out". Tafaɗa cikin tsawa yayinda take kallon ta a wannan lokacin ido cikin ido hawaye na zuban mata
Shiru Ummeen tayi ta kasa motsa wa, sai kuma a hankali ta juya ta fice har tana sake waigo ta
Ita kuwa tuni ta kifa kanta a saman gadon ta soma rusa kuka sosai, ji take yi kamar ta haɗiye zuciya ta mutu tsaban baƙin ciki, why Ummee zata yi mata haka? Anya ita uwa ce a gare ta da har ta zaɓi rabuwa da su? Ba ta tunanin akwai wata uwa makamanciyar nata uwar, shin wani hujja ne da take da shi da har zata tsallake tabar su alhalin suna matuƙar buƙatar ta? Tana ga rashin lafiyan Abee ɗin ta ba hujja bace da zata aikata musu haka, abun da take gani kawai Ummeen ta bata da imani, rashin imanin ta ne yasa ta aikata musu wannan abun, to, don me itama zata ɗauke ta a matsayin uwa? No hakan bazai taɓa yiwuwa ba domin tun sanda ta tsallake ta bar su itama ta cire ta daga zuciyar ta, a yanzu ita ba mahaifiyar ta bace, bata da kowa a yanzu sai ita kaɗai, a ko yaushe kuma hakan zata riƙa ɗauka... ta jima a nan zaune tana ta sharɓan kuka wanda har kanta ya soma mata zugin ciwo kafin ta shafa wa kanta lafiya ta haƙura, kiran sallan da ta ji ana yi shi ya ankarar da ita bata yi sallolin dake kanta ba, don haka ta tashi ta shiga Toilet ta ɗauro alwala ta ciri hijabin ta ta soma rama sallolin ta
Tana cikin yi ne Zabba'u ta shigo ɗakin, ganin tana sallah sai ta juya, babu jima wa kuma sai ta dawo da ƙaton faranti a hannun ta ta ajiye mata ta fice
Ita kuma ta jima tana sallan, sai da ta haɗa da shafa'i da wutri sannan ta sallame sallan, ta zauna yin addu'o'i na tsawon lokaci kafin ta shafa, yunwan dake addabar ta shi ya sanya ta jawo farantin ta zuba abincin dake cikin coolar a cikin ƙaramin Plate, haka tayi ta tusa abincin a baki ba don yana mata daɗi ba, duk tsawon lokacin da ta ɗauka tana cin abincin ko rabin Plate ɗin bata yi ba ta ture ta tashi tsaye. Wanka ta shiga tayi kafin ta sanya kayan barcin ta tabi lafiyar gado. A lokacin wajen ƙarfe 11:30pm. Na dare ne, sosai tunani suka bijiro mata a zuciya wadda yasa ta kasa barcin sai daƙyar ya sure ta daga baya. Tunda ta tashi da asuba tayi sallah ta sake komawa kasancewar akwai barcin sosai a idanun ta, bata farka ba har sai sha biyu saura domin Hajiya ta hana a taso ta har sai idan ita ce ta tashi, ta san tabbas akwai gajiya a tattare da ita. Koda ta tashi sai da tayi wanka ta shirya a cikin riga da skert na wani jan yadi me flowers da aka yi da kalan maroon color. Rigan tana da igiya ta baya wanda ta ɗaure shi, sai kuma gaban rigan a buɗe yake sai dai an saka raga-raga kalan maroon, shi kuma skert ɗin ya buɗe sosai tun daga saman ƙugun ta har ƙasa, sun mata cif sun fito mata da kyakykyawar surar jikin ta da Allah ya bata, while ta tufke gashin ta a ƙeya ta sanya ɗan kwalin kayan tayi Rolling da shi wanda ya saukar mata iya kafaɗun ta, exactly ta fito a tsantsan Balarabiyar ta. Koda ta gama shirya wa bata fita ba sai tayi zaman ta a kan gado, wayan ta dake kashe tun daren jiya ta ɗauka ta kunna, da saƙonni ta soma cin karo wanda ta fahimci Sajjad ne ya turo mata, domin kasancewar shi ya bata Simcard ɗin that's why ya mallaki Numban, a ko yaushe yana kiran ta but tunda ta san shi ne bata sake ɗauka ba, yanzu ɗin ma bata duba ko ɗaya ba illa zare layin da tayi ta karya shi biyu ta jefar. Miƙe wa tayi ta bar wayan a wurin ta zira room slippers ɗin ta da ta ciro su daga Trolley ɗinta ta fita. Ta cikin corridorn da ta san an biyo da ita ta nan ta fita sai ga ta a tsararren parlour'n gidan
A lokacin Hajiya na zaune a Kan wheel chair ɗin ta tana karanta littafin Hisnul Muslim sanye da eyeglasses. Ganin ta yasa ta tsayar da karatun nata tana me yalwata fuskarta da murmushi tare da yiwa MEEMAN alamu da hannun ta alamun ta ƙariso gare ta
A hankali ta taka izuwa wurin ta yayinda ta ɗan saki fuskarta kaɗan. Hannun Hajiyan da ta miƙa mata ta kama tare da ɗan ranƙwafa wa kaɗan ta sumbaci hannun cikin sassanyan muryan ta da a yanzu be fita ko kaɗan ta gaishe ta
Sai da ta riƙo mata kafaɗun ta ta zaunar da ita a saman kujera kafin ta amsa ta cikin tsantsan fara'an da dole zaka gane tana a cikin farin ciki sosai, kana ta tambaye ta yanda ta kwana?
A taƙaice ta bata amsa tana kallon ta
Murya Hajiyan ta ɗaga ta kirayi Zabba'u
Babu jima wa kuwa sai ga ta ta bayyana a gaban Hajiyan, cikin washe baki ta kalli MEEMAN tace, "Barka da safiya ƴar nan".
Kasancewar da hausa tayi bata amsa ta ba
Sai Hajiya tace, "ki riƙa mata magana da turanci ne saboda ba ta jin Hausa. Tukunna ki je ki haɗo mata Breakfast ɗin ta ki kawo mata nan sai ku gaisa daga baya".
"To Hajiya". Ta amsa cikin sauri tana juya wa
Ita kuma Hajiya ta kalli MEEMAN tace, "Now she'll bring you your Breakfast. Hope you stay home?"
Guntun murmushi ta saki tana jinjina mata kai
"Calm down, ok? Whatever you are want ask me directly, insha'Allah you will never touch Zulaiha. I am always with you."
Still kanta ta sake ɗaga mata a lokacin idanun ta suna me ciko wa da hawaye
Murmushi Hajiyan tayi mata, kana kuma ta mayar da kallon ta kan Zabba'u da ta kawo Breakfast ɗin a saman faranti. Still she keeps her eyes on MEEMA asking her, "what she wants?"
"Tea alone is enough". Tafaɗa a hankali cikin muryan ta da har yanzu be washe ba sakamakon kukan da ta sha jiya
Saka Zabba'u tayi ta haɗa mata tea ɗin. Bayan ta gama ta amsa da kanta ta miƙa mata
Ita kuma Zabba'un zama tayi kana ta kalli MEEMAN da har ta soma kai Cup tea ɗin bakin ta, cikin turancin ta na ƴan koyo tace, "Good morning and hope you are fine? Hope you enjoyed the stay?"
Kasancewar har yanzu Cup ɗin na bakin ta, kallon Zabba'un kawai take yi tare da gyaɗa mata kai kawai ta ci gaba da shan tea ɗin
Sai ita Zabba'un ta kalli Hajiya tana muskuta zaman ta tace, "Hajiya wai yanzu ita ɗin dai yarinyan Hajiya Zulaiha ce kenan?"
"Ƙwarai kuwa. Baki ga sun yi kama bane?"
"Eh na gani wlh, ai ban yi tunanin ta kai girman haka ba, Masha Allah gaskiya tana da kyau matuƙa tamkar dai ƴar can ƙasan wlh". Ta ƙare maganar tana washe baki
Ita dai Hajiya bata ce komi ba illa ɗaukan Hisnul Muslim ɗin dake jikin ta taci gaba da karanta wa
"Hajiya nace ba. Amma tana da aure ko?"
Ɗago wa Hajiyan tayi tana kallon ta da cewa, "ke dai Zabba'u kina da son tsegumi wlh, idan tana da aure ai zaki sani tunda tare muke da ke tsawon shekaru a gidan nan, a baya nasha sanar miki labarin su tun Zulaiha na can, sannan kuma koda ta dawo baki taɓa jin mun ce miki tayi aure ba".
"Haka ne Hajiya. To kiyi haƙuri".
"Idan ban yi haƙuri da ke ba ya zan yi ne Zabba'u? ki tashi dai yanzu ki je ki ɗaura mana sanwan abinci kina gani rana tayi amma kin zauna tsegumi".
Tana washe baki tace, "Hajiya ai na ɗaura miyan har ya kusa soyuwa zan sauke, dama farar shinkafar kaɗai ya rage in girka".
Bata ce mata komi ba ta juya ga kallon MEEMA da har yanzu tana kafe da Cup tea ɗin a bakin ta. Tace da ita, "What do you want to eat?"
Sai a lokacin ta cire Cup ɗin a lokacin ta shanye tass duk da kuwa zafin shi, domin ita ta fi son ta ji tea da zafi-zafin sa, kuma ta shanye sa a hakan ya fi mata a ko yaushe. Ce mata tayi, "She doesn't need anything, that's enough."
"No, Zulaiha, tell me something to be cook for you, because you will not sit still and eat nothing but tea."
She Said, "I will eat whatever is prepared."
"To maza tashi ki girka ki kawo mata". Inji Hajiyar tana kallon Zabba'un
"An gama Hajiya." Ita kuma tafaɗa tana tashi ta wuce
Hajia Looking her said, "I am still not tired of being sorry with you for not coming to see you. Please be patient. Your uncle is not in the country that's why he did not come to you, but forgive us."
Hannu MEEMAN ta sanya ta riƙo nata, fuskar ta a sake sosai a yanzu ɗin tace, "Don't worry my grandmother because you are not criminal. Ummee is a criminal and I am the only one who is angry with her. "
Hajiya tace, "But do not be angry with her because she is your mother, bind yourself to hide what you feel about her in your heart, don't forget she's a mother to you, no matter what she does to you, you should not hate her."
Girgiza kanta MEEMA ta soma yi hawayen idanun ta da suka taru suka soma zubo wa, cikin amon muryan ta me kama da ɓacin rai tace, "No, I will never forgive her for taking me not her daughter, I will never see her as my mother, I have long removed her as my mother. Please grandma I don't like talking about her".
"Well. Since you said I will never speak to you again." Ta ƙare maganar da shafa mata kai tana mata murmushi.
Lokacin ne Ummee ta sauko daga sama a cikin shigan ta kamar yanda ta saba, yau ma tayi kwalliya da baƙin less me kyan gaske, duk ta saka sarƙa da awarwaro a hannayen ta, duk da a yanzu ɗin damuwa ce cinkushe a fuskar ta, ga shi idanuwan ta sun yi ja sun kumbura sosai. Koda ta iso gaishe da Hajiya tayi tana samun wuri ta zauna a kan sofan da ke kallon wanda MEEMA ke zaune
Hajiya amsa mata tayi tana kallon ta da cewa, "wai yau baza ki je aiki bane sai yanzu kika fito?"
"Eh Hajiya yau bazan iya fita ba".
"To me ya sami idanun ki suka yi ja haka? Kar dai ace tunanin MEEMA kike yi?"
MEEMA da kanta ke sunkuye tun zuwan Ummeen sai ta ɗago kai ta kalli Hajiyan jin ta kira sunan ta, duk da bata fahimci me suke cewa ba ta gane da ita ake yi
Ita kuma Hajiya murmushi tayi mata tana dafa hannun ta, sai kuma ta mayar da kallon ta ga Ummee da ta ƙura wa MEEMAN ido, tace da ita, "tun wuri ki dena saka wa kanki damuwa tunda komi da ke faruwa ke kika jawa kanki, son zuciyar ki yasa kika aikata hakan, kin baro Ƴar ki da mijin ki kin taho nan, to, meye na saka wa rai damuwa? Abinda kike so fa kika aikata, kuma duk rarrashi da ban bakin da nayi miki domin ki koma amma kika ƙi bin shawara ta".
"Hajiya ba haka bane wlh nayi nadama tun ba yanzu ba, abun da na aikata yana damu na a zuciya na rasa yanda zan yi in koma, ban san ya Faruk zai kalle Ni ba shiyasa na kasa koma wa, baƙin ciki na yanzu ya koma ga mahaliccin mu ban nemi afuwar sa ba Hajiya, ya zan yi da raina?". Ta ƙare maganar cikin muryan kuka
Tsam MEEMA ta tashi zata wuce ɗaki
Hakan yasa Hajiya ta dakatar da ita tana tambayar ta, "where to go?".
"There is something I have to do.". Daga haka ta wuce ba tare da ta jira cewar ta ba
"Yanzu ya ya zan yi Hajiya ɗiya ta ta dawo tana ƙauna ta? Bazan iya jure halin da take ciki ba, Ina son ganin farin ciki a fuskar ta, ina son ta ɗauke Ni a matsayin mahaifiyar ta me ƙaunar ta. Nayi kuskure sosai ban san ya zan yi in dawo da farin cikin da ta rasa ba, na san MEEMA ta kasance a cikin baƙin ciki na tsawon lokaci, nayi ƙoƙarin neman ta a waya a baya but wayoyin su duk ba sa shiga."
"To ai haƙuri zaki yi tunda ke kika jawa kanki, a sannu wata rana zata gane idan kika fahimtar da ita, Ni dai ban ce ki riƙa damun ta ba na gaya miki domin idan har ta bar gidan nan sai dai ke ma ki bi ta."
Shiru kawai Ummee tayi yayinda hawaye ke zuba a saman fuskar ta, hannu ta sanya tana share wa zuciyar ta na mata zafi da raɗaɗi
"Ki je ki karya ga Breakfast ɗin ki can a dainning Zabba'u ta shirya miki". Hajiyan tafaɗa tana kallon ta
Bata ce komi ba ta tashi ta wuce kan dainning ɗin.
******
Shigan MEEMA ɗakin kwanciya tayi a saman gadon tana hawaye, danne kanta tayi a ƙasan pilow ta saki kuka me tsuma rai, ta jima tana kukan kafin ta tsagaita tana tashi zaune ta sanya hannayen ta tana share hawayen. Sai ta miƙe ta nufi jakar ta ta ciro computern ta ta soma aiki a ciki
Bata jima da fara wa ba Zabba'u ta shigo ɗakin da sallama
A ciki-ciki ta amsa mata bayan ta ɗago ta kalle ta sau ɗaya ta mayar da kanta
Cikin washe baki Zabba'u tace,
"good job. Hajiya says let me call you cooking is complete."
Gyaɗa kanta tayi ba tare da ta furta komi ba ta mayar da hankalin ta ga computern
Ita kuma Zabba'u ta fice
Kamar mintuna goma kafin ta rufe ta tashi ta fita.
*WhatsApp only*
07065334256
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NO_20*
Tafiyan MEEMA ya ja tashin hankali matsananciya a wajen su Uncle Ali. Musamman ma Sajjad domin hauka tuburan ya nuna musu a kan, "sai sun nemo mishi ita duk inda ta shiga." Kuka sosai yake yi duk ya hargitsa musu gida, su kansu sun kasa zama suyi tunanin mafita illa rarrashin sa da suke yi a kan, "ya kwantar da hankalin sa zasu nemo ta duk inda ta shiga."
Mutanen da suka soma taruwa sai dai suka tafi a washe garin ranan tunda an nemi Amarya an rasa. Wasu har tsegumi suke yi da dalilin tafiyan nata
Su kuma tun suna ɗaukan abin da Sajjad yake yi a matsayin na ɗan lokaci dole zai haƙura; sai kawai zazzaɓi ya kama sa, sosai yake jin jiki wanda a koda yaushe sai dai yayi ta musu sambatu, "shi fa a nemo masa Zulaiha, bazai iya rayuwa babu ita ba." Hakan yasa suka wuce da shi asibiti tunda abun nasa sai gaba yake yi.
Uncle Ali da Uncle Zubairu sun rasa inda za su fara zuwa su neme ta, hankalin su a matuƙar tashe yake sabida rashin amsar komi daga wurin ta, tabbas suna tunanin ta gane auren da zasu yi mata ne ta gudu, kuma ko kusa basu yi tunanin zata iya zuwa wajen Ummeen ta ba kasancewar ita Ummee ta bar su tun ba yanzu ba, ba sa tunanin cikin sauƙi zata je can. Shiyasa suka yanke shawarar zuwa Riyadh ɗin su duba ta
Umma duk ta tashi hankalin ta itama sai kuka take yi, a yanda ta ga Sajjad ya ƙi haƙura da zancen MEEMAN yasa itama take kuka da faɗin, "a nemo ta duk inda ta shiga don ɗan ta bazai mutu a kanta ba, a nemo ta a ɗaura mishi aure da ita idan har ɗan ta zai samu lafiya."
Uncle Zubairu shi ya je har Riyadh ɗin amma masu aikin gidan suka ce, "bata zo ba". Kwanan sa biyu a can yana zaman jiran ko zata zo amma babu ita babu alamar ta, dole ya dawo gida ya sanar wa da Uncle Ali. Hankalin su ya sake tashi sosai, sai dai babu yanda suka iya dole suka mayar da hankali wajen samun lafiyan Sajjad tunda har yanzu ya ƙi dangana shi a dole sai an nemo ta. Har ya samu sauƙi sun koma gida ya tayar da hankalin sa, "shi da kansa zai je neman ta a Riyadh ɗin." Ba don sun so ba suka bar sa ya soma shirye-shiryen tafiya. A ransa ya ƙudura aniyar, "muddin be ganta ba bazai dawo gidan ba, dole tare za su dawo, a ko ina take a faɗin duniyar nan sai ya nemo ta, ba shi da matar aure sama da ita, yana matuƙar ƙaunar ta bazai taɓa barin ta ba".
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
Zaman da MEEMA tayi a gidan ta samu kwanciyar hankali sosai, duk abin da take so Hajiya tana mata, tare suke zama suyi ta hira har da Zabba'u don yanzu ta saba da ita kasancewar ta akwai surutu da shiga abun da babu ruwan ta, yanda take shige wa MEEMAN ne dole ta saki jiki da ita, sai dai matsalan ko kaɗan ta ƙi bai wa Ummee dama wajen ganin ta wanke kanta daga laifukan da tayi mata, ko magana ba ta mata koda suna zaune wuri ɗaya, tun Ummee na damuwa sosai a yanzu har ta saba da halin MEEMAN, itama a hankali yanzu take ɗan shiga sha'anin ta duk da ba kula ta take yi ba, amma wani abun sai ta riƙa mata ko don ta faranta mata, musamman girkin da ta san tana matuƙar so irin ciman Larabawa, haka zata zaƙe tayi mata but ko kula wa ba tayi, Hajiya ke sanya ta taci wani lokacin shiyasa take ɗan ci idan ta ga dama.
Yau ma suna zaune da Hajiyan, Zabba'u na gefe tana musu surutu Hajiya na amsa ta, ita kuma MEEMAN tana zaune tana kallon su wani lokacin idan suka sako ta a zancen su tana tsulma musu baki
Dayake Ummee na wajen aikinta bata dawo ba
Duban Zabba'u Hajiya tayi da cewa, "yauwa Zabba'u kira min drever zan aike sa, zai siyo wa MEEMA layin waya ne ta ce min tana buƙata."
"To Hajiya bari in je." Tayi maganar tana tashi da sauri ta fita
MEEMA da ke kallon su sai tace, "grandma I also want to learn Hausa because I want to know what you are saying".
Dariya Hajiya tayi da cewa, "Are you tired of hearing us talk? Don't you understand?"
Ita kuma sai tayi murmushi tana jinjina mata kai, sai kuma ta ƙara da cewa, "yet I want to be able to."
"Ai kuwa zaki koya, da sannu ai zaki saba dama".
"You say what?"
Hajiya smiled and said, "I said you will learn slowly."
MEEMA smiled at her looking at her
"But I think your stay there makes you very anxious. what i was thinking why not get a job you going out, It will help you a lot and you will forget about any worries."
"Na'am grandma. I need a job, I want to start working." She spoke excitedly
Hajiya itama murmushi tayi da cewa, "If that makes you happy, you will be offered a job".
Zabba'u da Ummee ne suka shigo a tare
Hajiya ta amsa musu sallaman tana kallon su
"Sannu da gida Hajiya." Inji Ummeen tana zama a kan sofa
"Yauwa an dawo?"
"Eh."
Zabba'u da itama ta zauna take faɗin, "Hajiya wai ya fita zuwa shago yanzu zai dawo, na bar wa me gadi sallahu idan ya dawo ya faɗa masa kina neman sa."
"Tom shikenan." Cewar Hajiyan kafin ta mayar da kallon ta kan Ummee dake yunƙurin tashi tace, "zauna zamu yi magana".
Koma wa tayi ta zauna tana kallon ta
"MEEMA tace tana son Fara aiki kinga ke ya kamata ki nema mata abun da ya kamata tayi".
"To Hajiya sai in nema mata a wurin aikin mu hakan zai fi mu riƙa zuwa tare." Inji Ummeen tana kallon MEEMA da murmushi
Hajiyan kallon MEEMA tayi tana sanar mata da abun da Ummee tace
Fuskar ta babu walwala ta dubi Hajiyan tace, "Laá. I do not like."
They were silent
Sai kuma Hajiyan tace, "But you said you needed it, or did you break it?"
Kafin tayi magana sai Ummee tace, "a'a Hajiya ina ga ba ta son yi a inda nake yi ne, kuma dama mass.com ta karanta Ni ce dai nake son tayi aiki a companin da nake aiki hakan zai sa ko yaushe muna tare, amma tunda ba ta so sai in Yi ma Idris magana ya samo mata a wajen aikin su na gidan t.v hakan zai fi."
Hannun MEEMAN Hajiya ta riƙe tana kallon ta tace, "well. Now you're going to get a job somewhere, did you?"
Kanta kawai ta ɗaga har yanzu kyakykyawar fuskar ta a turɓune
Ita kuma Ummee tashi tayi ta haura sama
While su kuma suka ci gaba da taɓa hira ban da MEEMA da ke latse-latse a cikin wayan ta
Nocking ɗin da aka yi ne yasa suka yi shiru suna ba da iznin shigo wa
Drever ne ya shigo da sallama a bakin sa, ya isa wajen su ya durƙusa yana cewa, "Hajiya gani an ce kina nema na".
"Eh Salihi. Layin waya zaka siyo wa Jika ta."
"To Hajiya".
"Yauwa Zabba'u ɗauko mishi 2k a ɗaki na ya je da shi."
Amsa mata tayi tana tashi ta wuce
Drever'n yace, "amma Hajiya wani iri ne zan siyo?"
Kallon MEEMA tayi da cewa, "What brand do you want with the Simcard?"
Sai a lokacin ta ɗago da idanun ta daga duba wayan da take yi, "MTN." Ta furta a taƙaice
"To kaji. Mtn take so ka siyo mata."
"To Hajiya."
Koda Zabba'u ta kawo kuɗin ta miƙa masa ya fice. Ita kuma tace, "Hajiya bari in shiga kichen in ɗaura mana abinci. Ko zaki taya Ni ne MEEMA?" Ta ƙare maganar da kallon ta tana washe baki
Jin ta kira sunan ta yasa MEEMAN ta kalle ta ba tare da ta furta komi ba
Hajiya tace, "kin yi mata Hausa taya zata san me kika faɗa mata?"
"Oh wlh manta wa nake yi Hajiya." Sai ta maimaita mata da turancin
Girgiza kanta MEEMA tayi tace, "laá I can't."
"But you should always learn that it will benefit you even at your husband's house."
Murmushi kaɗai MEEMA tayi bata ce komi ba ta mayar da hankalin ta kan wayan ta
Ita kuma Zabba'un sai da ta gama zuba surutun ta da Hajiya duk dai a kan MEEMAN kafin ta wuce kichen ɗin
Hajiya ta kaɗa kai da cewa, "Zabba'u baki da dama ke dai, a nan kika fi auki wajen surutu, ayi mutum kullum ba ya gajiya kin girma baki san kin girma ba."
Ɗago kai MEEMA tayi ta kalle ta tace, "grandma you do it for me?"
Tace, "No, I'm not doing it. I'm doing Zabba'u. She's worried about you coming. She's going to teach you how to cook."
"I can't grandma." She spoke in a calm voice
"Then if you want she can teach you, because you should learn. If you get married who will go and teach you?"
Shiru MEEMA tayi and she drops head down
"If you have time, she will teach you ok?"
Gyaɗa kanta tayi kawai. Sai kuma ta miƙe tana kallon Hajiyan da cewa, "I'll go into the room and lie down."
Hajiya amsa mata tayi ita kuma ta wuce zuwa ɗaki.
Tafiyan ta babu jima wa wani saurayi wanda bazai fi sa'ar MEEMAN ba ya shigo da sallama ciki
Hajiya ta amsa mishi tana masa lale da faɗin, "idon ka kenan Idrisu?"
Dariya yake yi ya ƙariso ya zauna yana cewa, "Allah ya bar mu da Hajiyar mu. Kin ci zamanin ki kina cin tamu, tsohuwa me ran ƙarfe an buga an bar ki, na same ki lafiya?."
"Ai bazan amsa ba tunda sai yanzu ka san da Ni, gaba ɗaya ka manta da Ni sai yau zan ga ƙafafuwan ka a gida na."
"Woo! Hajiya kina da ƙorafi ne na rantse da Allah, ban da abun ki duka-duka yaushe ne na ɗauke ƙafafu na a gidan nan? Kin san kuma aiki na ne ba ya bari na in shigo amma da sai kin gaji da gani na." Yafaɗa still yana dariya
Hajiya tace, "babu wani nan, da ace ban san daɗin bakin ka bane."
"Tukunna dai Hajiya inyaso daga baya sai mu ci gaba da taƙaddamar tamu, ina Aunty ita take nema na?."
"To ka ji batu ashe sai da aka neme ka ka shigo?"
Dariya yayi da cewa, "Hajiya tawa ke dai so kike yi ki laƙaba min laifi, kowa ya san ina mugun ƙaunar ki, ko su Umma sun san cewa ina na fito wurin ki ne, ina zan tafi wurin ki ne, amma kike faɗan haka; idan wani ya ji ai sai yayi mana dariya Allah kuwa."
"Ni zan fara yin dariyan kuwa. Dama ai ba yau kuka saba ba, sunan dai kuna miji da mata ne." Cewar Zabba'u da fitowar ta kenan daga kichen ta tsinkayi maganar nasa
"To kin gani ko Hajiya ta? Ai dama nace miki akwai ƴan saka eyes wlh, kin ga ɗaya ta ɓullo. Bamu san kuma nawa za su ƙaru ba a nan gaba."
Dariya suke yi su duka
While Zabba'u tana faɗin, "ai yau har gidan su Umman taku sai na je kai gulman ku."
"Kin gani ko Hajiya? To ki faɗa mata ba faɗa muka yi ba."
"Ƙyale ta Idrisu na, duk wanda yace zai gan mu a rana ai zai ruɓe ne, Ni da miji na ai ba ma ɓaci. Yanzu dai kira Zulaihan a waya tana sama ne."
Wayan sa ya ɗauka yana latsa wa yana ci gaba da bai wa Zabba'u amsa wacce ta sako shi a gaba sai ba'a take mishi. Bayan ta ɗau wayan ne ya sanar mata, "ya zo."
Ba'a jima ba kuwa sai ga ta ta sauko. Ta zauna a kan sofan tana amsa gaisuwar sa, kana ta ƙara da faɗin, "Idris aiki zaka samo wa yarinya ta MEEMA a wajen aikin ku, Ina fata za'a samu?"
"Eh Aunty za'a iya samu insha Allahu, idan ma hakan ya gagara zan yi ƙoƙari ko a ina ne in samo mata, amma Aunty Kar dai ace yarinyan ki ta Riyadh ita ce ta zo?"
"Eh ita ce." Ta ba shi amsa tana murmushi
"Wow! Gaskiya zan so in ganta, kin san na daɗe da jin labarin ta wajen Hajiya sai dai baki taɓa zuwa da ita nan ba."
"To ai yanzu sai ka gaji da ganin ta kuwa Mijin, tunda muna nan da ita ta dawo gaba ɗaya." Cewar Hajiya tana dariya
"Allah Hajiya ta?"
"Ƙwarai kuwa Mijin. Yanzun nan ma ta tashi ta shiga ɗaki."
"To in dai haka ne insha Allahu I will try my best to get her a job. But I need her documents so I can go with them."
Ummee da sauri ta kalli Zabba'u tace, "ki kira ta sai ki faɗa mata ta kawo takardun nata."
Tashi Zabba'un tayi ta wuce ɗakin MEEMA. Bata jima ba ta dawo ta sanar musu, "ga ta nan zuwa".
Ba'a jima ba MEEMA ta fito riƙe da documents ɗin a hannun ta ta taka a hankali zuwa wurin su
Hajiya na murmusa wa tace, "to ka ganta nan Idris, Jika ta kenan."
Idris da ke faman kallon MEEMAN miƙe wa tsaye yayi fuskar sa yalwace da fara'a yace, "gaskiya tana da kyau Hajiya, Allah ya baki jika kyakykyawa. Anya Hajiya ba daga can ƙasar kika sanyo ta da naki ba?" Sai kuma ya kama haɓa yana sake ƙare wa MEEMAN kallo da cewa, "Hajiya Ni fa ban yarda ba, kwata-kwata ban ga tayi kama da ke bane ai."
Dariya suke yi duk kan su sabida abin da ya faɗa
While Hajiya tace, "ai yaro duk kyawun nan da ka gani kaɗan ne da wanda nayi a zamanin da nayi ƴan matanci na, wannan ai bata kai Ni kyau ba."
"Nima haka na gani ki bar sa kawai Hajiya don ya ga kin taƙwarƙwashe ne shiyasa yake faɗan haka." Inji Zabba'u tana dariya
They all laughed. while MEEMA na tsaye tana kallon su bata ce uffan ba tunda ba jin su take yi ba
Idris yace, "ƴar uwan tawa ba ta magana ne Hajiya naga tayi shiru ko fara'a ba ta yi?"
Zabba'u tayi tsagal ɗin cewa, "ba ta jin ka ne shiyasa, baka yi mata da Yaren da zata gane bane."
"Kina nufin larabci?" Yafaɗa yana ƙwalalo ido. "To ai Ni ban iya ba."
Ummee tace, "kayi mata da turanci."
Murmushi yayi ya kalli MEEMAN da cewa, "sorry sister. My name is Idris. Our house is looking at this house, we are staying outside Hajiya, I am happy to meet you."
Guntun murmushi tayi masa da cewa, "me too."
"Ok Bring the documents." Yafaɗa yana miƙa mata hannu
Handing him the fetus without saying anything again she turned and walked away
Hajiya tace, "to sai ka ƙoƙarta Idrisu na."
"Kar ki damu Hajiya ta baki da matsala. Ni zan tafi don akwai inda Abba ya aike Ni dama. Zuwa gobe ko jibi zaku ji me ke akwai in Allah ya yarda."
Daga nan sallama suka yi ya fice ya bar su. Su kuma suka ci gaba da ɗan taɓa hira, inda Zabba'u ta wuce kichen domin ci gaba da aikin ta.
Ba'a rufa kwana biyu ba Idris ya dawo gidan ya shaida musu, "an dace da samun aikin MEEMA".
Zuwa Monday suka soma fita aikin tunda a wurin aikin su ta samu, tare suke fita da Idris kasancewar sa me son Wasa da barkwanci a cikin ƙanƙanin lokaci suka soma saba wa, idan ya shirya sai ya zo gidan su tafi tare
Tunda ta fara fita aikin ta sake sakin jiki sosai, abubuwan da ta gani a wurin aikin nasu da kuma yanda ake gudanar da al'amura gunun sha'awa a wurin ta. Musamman yanda mutane suke son mu'amala da ita domin sosai tayi farin jini a wurin jama'a, kowa MEEMA kowa MEEMA sai hakan yake sanya ta farin ciki da nishaɗi, duk da ba kowa take kula wa ba iyakan gaisuwa sai kuma abun da ya kaita tunda ko yaushe suna tare da Idris, ga kuma cousin ɗin shi Laɗifa komi tare suke yi, ita take jan MEEMA a jiki tana koya mata wasu abubuwan musamman idan bata fahimta ba kasancewar yanayin mu'amalar mu ta nan bata san da su ba, ga kuma rashin iya Hausa da har yanzu ko Eh ta gaza fahimta.
Musamman Ummee ta siyo mata mota sabuwa fil domin ta riƙa zirga-zirga da ita na yau da kullum zuwa wajen aiki, amma ta ƙi amsa
Hajiya da kanta ta kira ta, ta miƙa mata keey ɗin motan daƙyar ta amsa. Sai dai bata taɓa hawa ba kullum Idris take bi tunda sun zama tamkar friends ne a cikin ɗan ƙanƙanin lokacin da be gaza wata ɗaya da haɗuwar su ba. Wani lokacin ma har gidan su take shiga wajen Umman sa, kasancewar gidan akwai yara shiyasa zaman gidan yake mata daɗi, kowa so yake yi ya ja ta a jiki saboda farin jinin ta. Shiyasa a ɗan ƙanƙanin lokaci ta saki jikin ta ta soma saba wa da sabon rayuwar ta, a hankali ta soma manta duk wani rayuwar ƙunci da tayi na tsawon shekaru, duk da har yanzu ta kasa manta wa da Abee ɗin ta duk idan ta tuna sa tana zubar da hawaye sosai, sai ta riƙa jin tsanar Ummeen ta yana sake zama sabo a zuciyar ta, tana jin tamkar baza ta taɓa yafe mata ba. Ita ce silan komai.
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏼
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*FAƊAKARWA*
```Manzon Allah yayi mana bayani cewa, "Bambancin da yake tsakanin mumini da kafiri shi ne rashin yin Sallah." Busaida ya ruwaito wani hadisin mai kama da wannan inda ya ce, "na ji Manzon Allah yana cewa," "haƙƙin da ya bambanta mu da su shi ne salla. Duk wanda yayi watsi da ita ya zama kafiri."
Shi kuwa Abdullahi Ibnu Umar ya ce ne wata rana Annabi yayi magana a kan Sallah yace, "Ga wanda yake tsayar da sallah, takan zame masa haske, shaida da kuma tsira a ranar lahira. Wanda ba ya tsayar da ita kuwa, gare shi babu haske, babu shaida, babu tsira, kuma a ranar lahira za a haɗa shi da Ƙaruna da Fir'auna da Ubayyu ibnu Khalaf."
Da hadisai da ayoyin Alkur'ani duka suna nuna irin munin zunubin da yake rataya da ƙin yin salla, suna kuma nuna matsayin mai yin hakan duniya da lahira. Dokar musulunci dai tana yin gargaɗi ne ga mabiya addinin cewa su riƙe shi da gaskiya ta yin Sallah, babban jigon Islama kuma aikin addini mafi girman daraja. Ashe ba abin mamaki ne ba mu ji cewa duk wanda ya guje mata ya kafirta, ya kauce ma hanya miƙaƙƙiya. Alƙur'ani kam na kiran irin wannan mutum mai zunubi wanda aka tanadar wa wutar jahannama, mai ƙona komai, mai cinye Mutane da tsananin zafin ta. Kyakykyawan sakamako ga wanda ya bijire. Ubangiji ba ya zaluntar kowa. Allah yasa mu dace yasa mu gama da duniya lafiya.```
*NO_21*
Yau ma kamar kullum MEEMA tayi shirin ta kamar yanda ta saba, Abaya ta saka blue color da aka yane shi da kwalliyan Stones daga saman wuya har ƙasa, sai faffaɗan hannu me kamar alkyabba shima an sanya Stones da kuma bakin lessi, tayi Rolling da jan veil sai ta saka cover shoes Shima ja, haka zalika agogon hannun ta. Iyakan Powder da lipstick ta saka sai ta zizara kojol a idanun ta, I can't describe to you how beautiful she is, but her beauty is even more beautiful. Fita tayi Parlour inda Idris ke zaune da Hajiya suna hira yana jiran fitowar ta
"You look so cute Zulaiha." Cewar Hajiya kenan sanda ta ƙyalla ido ta ganta
Ita kuma murmushi tayi ta isa wurin ta tayi mata peak a goshi tare da faɗin, "thank you Grandma."
Idris da ya miƙe tsaye a yanzu ɗin yace, "to Hajiyata mu zamu wuce sai mun dawo."
"To Allah ya bada Sa'a Allah ya tsare." Tafaɗa tana murmushi
Daga nan sallama suka yi mata suka fice. Sanda suka isa bakin motan Idris ɗin da kanshi ya buɗe wa MEEMA ƙofa yana solute ɗin ta
Kyakkyawar murmushinta ta sakar mishi tana ƙarisawa ta shiga ciki
Ya rufe shima ya zaga ya shiga ya ja motan zuwa wajen aikin su. A cikin motan sai janta da hira yake yi duk da kasancewar ba amsa mishi take yi ba sai dai tayi masa murmushi kawai, a haka har suka kai suka fito
A nan suka haɗu da Laɗifa itama zuwan ta kenan, ta isa wurin su cikin farin ciki suka rungume juna da MEEMA
Idris da ke kulle mota yace, "to saura Ni baza ayi hugg ɗina bane?"
Hararan sa Laɗifa tayi tana cewa, "haka kawai ƙato da kai ba miji na ba, na ƙi ɗin." Sai kuma ta kalli MEEMA tace, "let's go." Ta riƙo hannun ta suka shige ciki suka bar Idris na kwaɗa mata kira. But ta ƙi tsaya wa suka shige ciki. Dayake Office ɗin su ɗaya ne can suka shiga suka zauna suna ɗan taɓa hira
Sai ga Idris ɗin ya shigo yana cewa, "wato ke ina kiran ki kika yi banza da Ni Ko? Kin ganki; ki fa mayar da hankali a kan aikin da oga ya sanya ki don na kula tunda na kawo miki Abokiyar hira kike wasa yanzu."
"A'a yaya kai ne dai kake ganin haka but ina aiki na yanda ya kamata wlh."
"Ok on that talk of ours we are going to meet the Senator tomorrow, he has given us an appointment tomorrow, but I have a place to go tomorrow, there is work for me to go to Zaria, now you and MEEMA will visit his house tomorrow, I hope you can?"
"Don't worry Bro, we'll go together."
"Ok let me go I have a job, kiyi sauri da Allah ki gama wancan aikin ki zo mu fara ɗaura videon Nan." Yafaɗa Yana kallon Laɗifan
"Ok." Tace da shi tana janyo computern ta gaban ta
Shi kuma ya fice ya bar su.
There they were at work and MEEMA raised her head looking at Ladifa and said, "Where are we going tomorrow I don't understand?"
Laɗifa tace, "There is someone who is seeking the Senate seat in this city, we have been wanting to interview him on this television station for a long time, but we have not had the opportunity yet until this time, he is a great man because everyone wants to meet him. But now we have a way to go tomorrow. We going to interview him."
"Ok God Lead us." Cewar MEEMAN tana mayar da hankalin ta kan abin da take yi.
By 02:00pm. Suka je suka yi sallah, Idris ya ɗauke su zuwa wani restaurant da babu nisa da wurin suka ci abinci, sai hira suke yi gunun sha'awa suna dariya har suka dawo. Zuwa ƙarfe 03:00pm. Suka tashi, Laɗifa ta sauke MEEMA a gida tunda Idris Yana da aiki ba yanzu zai koma gida ba. Sallama suka yi Bayan ta sauke ta taja motan ta ta tafi
Ita kuma MEEMA tayi Nocking aka buɗe mata ta shiga ciki, lokacin da ta isa parlour babu kowa sai Zabba'u wacce ta buɗe mata ƙofa tana mata sannu da aiki
"Where is Grandma?" Ta tambaye ta tana kallon ta
"She is in her room praying."
"Ok." Tace tana wuce wa. Sai da ta shiga ɗaki ta watsa ruwa a jikin ta ta sanya wata ƙaramar riga na shan iska wacce tsawon ta be wuci iya ƙasan gwiwan ta ba, kalan ta kalan ruwan Powder ne, sannan ta fito ta wuce ɗakin Hajiya. Sai dai a lokacin babu ita a ciki shiyasa ta fito Parlour ta tarar da ita tana karatun Hisnul Muslim. Wajen ta ta nufa tayi hugging din ta tana sakar mata kiss a bayan hannun ta tare da faɗin, "Weldon Grandma."
Murmushi tayi mata tana shafa kanta da cewa, "it works hope you enjoy the project?"
"Alhamdulillah." Tafaɗa itama tana mayar mata murmushin
"Ok go eat and come back for a chat."
Amsa mata tayi tana miƙe wa ta nufi kichen. Tana shiga ta ga Zabba'u a bakin madafa tana juya miya, ta isa wurin ta tana murmushi tace, "you are always cooking, you are not tired?"
Dariya Zabba'u tayi tace, "How can I get tired of cooking after a woman is known for cooking? You too should come in and teach you because cooking is for women. What are you looking for?"
Taɓe baki tayi tana sake duban kichen ɗin tace, "nothing. I came to see what you are doing."
Murmushi Zabba'un tayi tana ci gaba da juya miyan. Sai kuma tace, "your food is on the dainning table go and get it."
Kanta ta gyaɗa tana juya wa bata ce komi ba ta fice. Sai da ta ɗibi abincin sannan ta koma kusa da Hajiya ta zauna tana ci tana kallon ta
While ita kuma tana ta karatun ta
Bayan ta gama ta ɗauki Plate ɗin zuwa kichen
Lokacin Ummee itama ta dawo gidan, gaisa wa da Hajiya tayi ta haye sama.
The following day.
Har gida Laɗifa ta zo ta ɗauke ta suka wuce G.R.A where they will go to the Senator's house to find out about him being that the election is near, they want to post his interview on their television channel
Koda suka isa bakin Gate ɗin gidan an hana su shiga
Laɗifa ce ta fito a motan ta isa wajen Gate man ɗin tace, "Malam don Allah ka faɗa masa ƴan jarida ne daga Light T.v suke son hira da shi ya san da zuwan mu Please."
"Ok sai ku jira in sanar a ciki idan ya san da zuwan naku."
"Ok thanks." Tafaɗa tana kallon shi
While shi kuma ya shige ciki
Shiru-shiru kusan mintuna goma babu me gadi. Laɗifa da ke waje har yanzu sai kai komo take yi tana faman jan tsaki
Sai daga baya sai ga shi ya fito yace mata, "su shigo."
Hakan yasa ta koma wajen motan ta sanar wa MEEMA da ke zaune a ciki tana latsa wayan ta. Fitowa tayi da Laptop a hannun ta suka jera zuwa cikin gidan
Babban gida ne me Part-part da yawa. A can daga nesa akwai wani babban gini don shi kaɗai ne upstairs a gidan. Duk inda ka gifta masu aiki ne suke yawo suna ta faman aikin su, tsarin ginin sosai zai tafi da kai saboda tsantsan haɗuwar shi, daga gani ka san mamallakin gidan me kuɗi ne sosai. Sai da suka zagaya round about da ke tsakiyar gidan kafin suka isa wannan dogon ginin. Dayake suna biye da wani house men ne yana musu jogara zuwa wajen ogan nasu
Kafin su kai ga isa ginin ne sai ga wata tsaleleliyar budurwa wacce a ƙalla baza ta fi 24years ba, ta ɗau wanka a cikin ƙananan kaya tamkar baza ta taka ƙasa ba, tana tafe tana amsa call ta fito a ɗaya daga cikin sashin gidan. Tana matsowa wajen su ne while su ma hakan. Sai da suka yo gab da juna sannan ta ɗaga kai ta kalle su. Kallon kallo suka yi gaba ɗayan su yayinda ta ƙi ɗauke nata idanun a kan MEEMA wacce ita tuni ta ɗauke nata tun kallon da tayi mata daga nesa. Har sun gota ta kuma sai ta kira House Men ɗin tana yafico shi da hannu
Hakan yasa ya dakata daga yin musu jagoran da yake yi ya nufe ta da sauri ya duƙa a gaban ta
Magana take mishi tana nuna su MEEMA da yatsa
Shi kuma yana bata amsar tambayar ta. Sai kuma ya tashi a bisa umarnin ta ya nufi su MEEMA ya sanar musu, "kuyi haƙuri Ƙanwar Yallaɓoi tace baza ku samu ganin shi ba."
"To saboda mene?" Inji Laɗifa cike da haushi
"Haka tace in sanar muku."
Kallon inda budurwan ke tsaye tayi. Tana nan har yanzu da waya a kunnen ta idanun ta na kallon wani wurin. Hakan yasa Laɗifa ta kalle shi tace, "kai mu je ka kai mu."
"To." Yafaɗa da sauri yana yin gaba
MEEMA da bata san ma me suke faɗa ba ganin Laɗifa tayi gaba yasa itama ta bi bayan ta tana jan gajeren tsaki, kasancewar akwai rana sosai duk tafiyan nan da suka yi daga bakin Gate zuwa nan duk ta gama takura, har wani gumi ne yake tsatstsafo mata sabida yanayin shigan kayan ta
Budurwan da itama ta biyo bayan su cikin ɗaga murya tace, "Hi.. Hi.."
Dole suka ja suka tsaya gaba ɗayan su jin muryan ta a sama wanda yake nuni dasu take yi
"Me nace maka? Ina zaka kai su bayan nace maka baza su samu ganin shi ba?" Tayi maganar a ɗaurewar fuska tana kallon House Men ɗin
Kafin yayi magana sai Laɗifa ta riga shi da faɗin, "kiyi hakuri ba wajen ki muka zo ba, shi wanda muka zo wajen shi shi ne yace a shigo damu don haka baza mu koma ba." Sai ta ja hannun MEEMA suka yi ciki ba tare da ta sake bi ta kan ɗan rakiyan ba
Ita kuma ƙwafa tayi tana bin su da kallo har suka ƙule mata, sannan ta ja dogon tsaki ta wuce zuwa wajen motan ta ta shiga tabar gidan.
A dogon ginin Laɗifa ta ja tunga ta tsaya domin a ranta tana da tabbacin nan ne ya kamata su shiga. Sai ta soma Nocking ƙofan
MEEMA da ke kallon ta tace, "but who is that? What is she asking us?"
"Forgot her. I think she's also a housewife, or his younger sister oho."Cewar Laɗifa still tana ci gaba da Nocking ɗin
Babu jima wa aka buɗe musu. House maid ne ya buɗe yana kallon su da tambayar, "wanda suke nema?"
Laɗifa tayi mashi bayanin abin da suka zo yi
Yace, "ok ku shigo". Ya shigar da su har cikin ƙaton parlour'n ya basu wurin zama. Sannan ya kawo musu drinks sai ya wuce kiran musu me gidan. Be jima ba ya dawo yace musu, "su biyo shi."
Kallon MEEMA Laɗifa tayi tace mata, "let's go."
Tashi tayi ta bi bayan ta suka shiga wani ƙayataccen parlour'n sai dai shi be kai wancan girma ba, amma ya fi haɗuwa sosai da sosai
Wata matashiyar yarinya wacce a shekaru baza ta fi 8yers ba ke zaune a parlour'n tana buga Game a t.v, Remote ɗin na hannun ta tana sarrafa wa. Daga ita sai siririn wando da vest a jikinta, ganin su yasa ta tsayar da abun da take yi tana faman kallon su
Shi kuma house maid ɗin yace musu, "su zauna."
Zama suka yi while Laɗifa sai baza idanu take yi a parlour'n kasancewar yayi mugun tafiya da ita, babu shakka kuɗi na inda suke, baza ka taɓa cewa a duniya kake ba idan ka ji ka a cikin parlour'n nan saboda tsantsan tsaruwar shi. Sosai haɗuwar sa ya tafi da ruhin Laɗifa kasancewar bata taɓa tozali da irin tsararren gidan nan ba
While MEEMA kuwa kasancewar ta taso a wanda ya fi shi sau miliyan shiyasa bata tsaya kallo ba domin babu abinda ya birge ta sai wani hoto da ta ƙyalla ido ta hanga. Hakan yasa ta sake ɗago kai ta sauke a kan yarinyan da ke zaune tana bin su da kallo sannan ta sake mayar wa a kan hoton. Yarinyar ce a cikin hoton ita da wata wacce bata kai ta Shekaru ba, sun rungume mutumin da ke a cikin hoton duk kan su suna dariya, tsananin kaman da suke yi da shi dole ka gane mahaifin su ne, babban Mutum ne domin ya sha manyan kaya me ruwan madara, riga da wando da malin-malin ɗin shi, a ƙalla bazai wuce shekaru 37years ba, amma tsaban kwarjinin shi da tsantsan kyawun shi dole sai ya cika maka ido. Shiru tayi tana kallon fuskar mutumin tana son zurfafa tunanin ta, sai muryan yarinyar ya dawo da ita a cikin hayyacin ta. Hakan yasa ta mayar da kallon ta wajen ta
Faɗa yarinyar take yiwa hause Maid ɗin a kan shigowar su MEEMA cikin parlour'n
Shi kuma yake sanar mata, "Mahaifin ta ne yace a kawo su wurin."
Sai ta ja dogon tsaki tana ɗaukan Remote ɗin taci gaba da Game ɗin ta bata sake magana ba bare tabi ta kansu
While me aikin tuni ya fice
Su kuma suka zauna jigum babu wanda ya sake bi ta kansu. Har MEEMA ta gaji ta juyo da kallon ta ga Laɗifa tana cewa, "I'm so tired I'm leaving."
Hannu Laɗifa ta saka ta riƙe nata tana marairaice fuska da cewa, "Please let us wait a little longer, since we have come so far we will sit and wait."
Bata ce komi ba ta ɗauke kai ta mayar ga T.vn da yarinyar take yin Game. Sai kawai ta shagaltu da kallon Game ɗin domin tunawa tayi da itama sanda take gida, a lokacin da Abee ɗin ta yake lafiya, tare suke buga Game ɗin suna farin ciki da nishaɗi, kasancewar ta me matuƙar son game shiyasa ba sa rabo da buga wa tare, kala-kala take da su domin har ɗakin Games ne da ita... Hawaye ta ji sun cika mata idanu ta kai hannu ta share waɗanda suka silalo mata a kunci tana ɗan jan majina kaɗan.
_Barka da wannan rana me albarka. Ina ma ɗaukacin masoya na murna da zagayowar wannan rana ta juma'a. Allah ya sada mu da albarkatun ta yasa mu dace duniya da lahira. Ayi weekends lafiya._
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏼
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```(WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NO_22*
Yanda aka shanya su a wurin ne yasa ran MEEMA ya ɓaci ta miƙe tana kallon Laɗifa fuska babu walwala tace, "Please get up and go. I'm very tired."
Bata kai ga yin magana ba sai wata yarinyar ta fito a guje tana kiran sunan, "Aunty Hafsah.. Aunty Hafsah." Tafaɗa kan kujeran da ƴar uwan ta ke zaune
"What's wrong?" Ta tambaye ta tana ajiye Remote ɗin hannun ta
Ita yarinyar tuni ta mayar da kallon ta kan su MEEMA tana kallon su. Sai kuma ta nuna su da yatsa tana cewa, "Aunty waɗannan fa su wane ne?"
"Oho ki tambaye su ga su nan."
"Baby come I want to ask you." Cewar Laɗifa tana ma ƙaramar murmushi
Hakan yasa ta taso izuwa wurin ta
Sai ta riƙe mata hannu still tana mata murmushi tace, "what's your name?"
"My name is Yusra."
"Ok Yusra ko zaki kira mana mahaifin ki?"
Gyaɗa mata kai tayi kana ta juya da gudu ta hau upstairs
Tafiyan ta yasa Laɗifa ta kalli MEEMA tace, "Sister, sit down. Now she will be called for us, Let's wait a little longer."
Ɗauke kai tayi bata ce komi ba kuma ta ƙi zama
Babu jima wa sai ga Yusran sun fito ita da mahaifin nata. Daga shi sai jallabiya fara sol da waya a kunnen sa yana amsa call
Har suka sauko ƙasa Laɗifa idanun ta na kanshi, sosai take tasbihi da tsantsan kyawun da Allah ya yi masa
While MEEMA itama tunda ta kalle su sau ɗaya sai ta sami wuri ta zauna
Har ya iso wajen hankalin sa be kai ga su Laɗifa ba, sai da ya zauna a ɗaya daga cikin manya-manyan kujerun parlour'n sannan ya sauke fararen idanun sa a kan su
Hafsah da Yusra tuni sun haye kan shi
While shi kuma yana ci gaba da wayan shi, sai dai tunda ya ɗaura idanun sa a kan MEEMA ya ƙi ɗauke wa. Hannun sa ɗaya na a saman giran sa yana murza wa hakan yasa baza ka gane ita yake kallo ba
Ita kuma a jikin ta taji ana kallon ta shiyasa ta sake ɗaga kai a karo na biyu ta kai duban ta gare shi. Hakan yasa idanuwan su suka shige cikin na juna. Ko soconni bata ɗauka ba ta cire nata idanun tana jin gaban ta na faɗuwa matsananciya, tabbas tana ji kamar ta san wannan fuskar, a jikin ta tana jin kamar ta taɓa ganin sa
Shima haka a wajen sa. Shiyasa ya kasa cire idon sa a kanta yana son tuna inda ya san fuskar ta. Be ɗauke idanun nasa ba har sanda ya tuno ta kuwa. Ya tuna sanda ya je Umrah ya hayo jirgi daga Riyadh, ita ce wacce suka zauna a jirgi tare zuwa Abuja. A lokacin ya dawo da dare babu wanda ya sani shiyasa ya wuce gidan Abokin shi Hashim a barikin sojoji ya kwana. Tabbas ita ce. Hakan yasa ya lumshe idanuwan sa yana me sake buɗe wa a kanta, sallama yayi da wanda suke wayan ya mayar da kallon shi sosai a kan su har Laɗifa yace, "ku ne kuke nema na?"
"Eh ranka ya daɗe!" Inji Laɗifa cike da murmushi a fuskar ta
"Ok sorry I settled you, there's something I'm doing what's important in it."
Hakan yasa MEEMA ta sake ɗago kai ta kalle shi jin abun da yace, sai suka sake haɗa ido tayi saurin ɗauke kanta
Shima haka janye nashi idon yayi yana kallon yaran nashi da cewa, "ku ɗan bamu wuri zamu yi magana My Babies."
"Ok Daddy." Suka faɗa a tare suna tashi da gudu suka yi cikin gidan
"Ina sauraron ku. I give you ten minutes to do what brought you here."
"Ok Sir." Laɗifa ta faɗa da sauri tana amsar Laptop ɗin hannun MEEMA ta buɗe
Ita kuma ido kawai ta zuba mata bata ce komi ba.
Nan ta soma mishi tambayoyi tun daga full name ɗin shi zuwa shigan shi siyasa
A taƙaice dai ba wani amsa mata sosai yake yi ba, wasu ataƙaice yake bata amsa. Daga ƙarshe duba agogon sa yayi yace, "lokaci ya cika. Ina da abun yi." Sai ya tashi ya wuce be jira cewar su ba
Dole su ma suka tashi suka fice a gidan. Sanda suka hau mota Laɗifa take cewa, "I don't think we will ever see him wlh, he is very well connected and it is beautiful, but I honestly didn't like the way he answered our questions."
MEEMA da ta kwantar da kanta a jikin kujeran idanun ta a rufe, tana jin ta but ko magana ta gaza yi sabida ɗan tunanin da ya hau mata kai, so take yi ta tuna inda ta san fuskar nan domin ya tsaya mata a rai. Sai da Laɗifa ta taɓa ta sannan ta ɗago kanta tana kallon ta
"I mean you're silent what do you do?"
"Nothing."
"Ok call Bro Idris and let him know we're done." Laɗifa tafaɗa tana ci gaba da tuƙin
MEEMA bata ce komi ba ta ɗauki waya ta soma neman layin Idris. Sai dai a kashe aka ce
Laɗifa tace, "maybe it is still not in Zaria. We'll try again later."
Da haka suka ƙarisa wajen aikin su.
Zuwa ƙarfe uku Laɗifa tayi dropping ɗin ta a gida. Lokacin da ta shiga Parlour Hajiya da Zabba'u suna zaune sun yi baja-baja da kaya
"These are your belongings, come and see if they do it for you." Cewar Hajiya bayan MEEMAN ta zauna
Kallon kayan take yi bata ko motsa ba
Zabba'u da ke washe baki tace, "These items are all Hajiya's choice for you. In fact, Hausa clothes will look good on you. God willing, they will please you."
MEEMA kallon Hajiya tayi tace, "Thanks grandma, I am very happy."
"Ok come and see. Look at everything that is not yours and you will be changed."
Kanta ta gyaɗa kafin ta tashi ta iso gaban kayan ta durƙusa tana duba wa
While Zabba'u tana taya ta ɗauko wa
Atamfofi ne da lessi sai materials kala-kala. Sai takalma har da gyale
Ɗago kai MEEMAN tayi tana kallon Hajiyan a marairaice tace, "But how can I use them? I can't."
Dariya suka yi mata
Hajiya tace, "You will learn, no matter what you say you can't. Since you came back to our country you have to learn all our culture."
Murmushi kaɗai tayi tana ci gaba da ɗaga kayan, wasu kuma sai ta kara a jikin ta kafin take ajiye wa
Hajiya tace, "You go with Zabba'u to take your sewing, then choose the style you want. Go eat and rest later and take it to your sewing shop."
"Ok." MEEMA tafaɗa tana tashi ta wuce ɗaki
Yayinda Zabba'u kuma ta haɗa kan kayan ta mayar a cikin leda.
Koda MEEMA ta shiga ɗaki wanka tayi ta saka riga da wando masu taushi ta fito Parlour. Abinci ta sawo ta zauna a gefen Hajiya tana ci tana sauraron hiran nasu. Sai da ta gama ta wuce ɗaki ta ɗaura after dress baƙi a saman kayan ta tayi Rolling da ɗan kwalin shi kafin ta fito suka fita. Drever ya ɗauke su suna shirin fita itama Ummee ta dawo gidan.
Koda ta shiga parlour'n ta tarar da Hajiya. Sannu da gida tayi mata kafin ta tambaye ta, "ina su MEEMA zasu je ta gan su a mota?"
"Kaya ne na ɗaukar mata wajen Dillaliya, ɗazu nace ta kawo min shi ne zasu kai ɗinki."
Gyaɗa kanta tayi, sai kuma tace, "amma Hajiya da kin bari na siyan mata da kai na kar ɗawainiyar yayi miki yawa."
Hajiya tace, "yanzu ma ban hana ki siyan mata naki ba, Ni nayi ra'ayi baza ki hana Ni abun da nayi ninya ba."
"To Hajiya ai ba na faɗa bane abun." Ummee tafaɗa tana murmushi
Shiru Hajiya tayi mata tana mayar da idanun ta kan t.v dake faman aiki shi kaɗai
Ita kuma Ummeen sai ta wuce sama inda ɗakin ta yake. Sai da tayi wanka ta sauya kaya kafin ta fito ta zuba abinci ta dawo Parlour. Tana cikin ci ne sai kuma ta kalli Hajiya da cewa, "Hajiya baki yiwa MEEMA magana a kan ƙadaran mahaifin ta ba, ya kamata a san abun yi sabida be kamata a bar su a can ƙasar babu me kula da komi ba, sannan akwai magada a ciki kamata yayi a sauke mishi nauyi tun yanzu."
Hajiya da ta dawo da kallon ta kan Ummeen tace, "nayi tunanin hakan, sai dai be kamata mu tayar da maganar yanzu ba, mu bari zuwa nan gaba bayan ta sake sakin jiki sosai damu, har yanzu ina ganin damuwa sosai a tattare da MEEMA, har yanzu ba wai ta manta mutuwar mahaifin ta bane, shiyasa duk wani abun da zai saka ta farin ciki nake iyakan ƙoƙari na wajen naga nayi mata. Tunda ke kin gaza a matsayin mahaifiyar ta ki bar ni Ni inyi mata, Ni kaɗai take kallo take jin daɗi a yanzu."
Cike da sanyin jiki Ummee tace, "Amma Hajiya mene ne na gori kuma?"
"A'a ba maganar gori bane gaskiya na faɗa. Yarinyar nan tana cikin damuwa tsantsa, ko fuskar ta kika kalla bata cika yin fara'a ba, wani abun ma tana yi ne kawai domin mu, don haka ba na son ma a cika mata maganar da zai riƙa tuna mata da mahaifin ta."
"To shikenan." Cewar Ummeen tana ajiye Plate ɗin abincin. Sai kuma ta ɗauka ta kai kichen ta haura sama.
Ba su wani jima ba su MEEMA suka dawo gidan.
Da dare suna cin abinci a dainning Idris ya shigo gidan. Kai tsaye wajen su ya nufa yana jan kujera ya zauna yace, "nima yau da Ni za'a ci abincin duk da na cika ciki na daga gida."
Hajiya tace, "dama wa ya isa yace ban da kai za'a ci Mijin?"
"A'a gaskiya ban girka da kai ba, ka tashi ka bamu wuri." Inji Zabba'u cike da barkwanci
"Wai kin ji Hajiya in tashi?"
"A'a zauna ka zuba abun da ranka yayi maka, idan ba ka kawo wa taya za su samu su ci?"
"Yauwa Hajjaju na Ni kaɗai, an dai Gwale wasu." Yafaɗa yana dariya
Su ma dariyan suke taya shi ban da MEEMA da ido ta zuba musu tunda ba ta fahimta
Gaishe da su yayi kafin ya mayar da hankalin sa kan MEEMA yana tsokanar ta
Ita dai murmushi kaɗai take mishi har suka gama cin abincin suka koma Parlour
A nan ya ɓata lokaci kafin yayi musu sallama ya tafi. Dama ya zo wajen MEEMA amsar Laptop ne kasancewar ita ta taho da shi lokacin da suka tashi daga aiki tunda nashi ne.
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
Horn tayi har kusan biyar kafin me gadi ya buɗe mata ƙofa. Ta shige da motan ta zuwa wajen parcking. Fitowa tayi ta nufi Part ɗin su da ke a cikin gidan
Tana shiga parlour'n Momy da Abdul dake magana suka tsayar da maganar suna kallon ta
Ita kuma kai tsaye kan kujera ta nufa ta zauna tana ajiye numfashi
"Har kin dawo?" Cewar Momyn still tana kallon ta
"Eh." Ta bata amsa a taƙaice. Sai kuma tace, "Momy da zan fita naga wasu ƴan jarida sun shigo nan gidan."
"Nan gidan kuma?" Tafaɗa Momy mamaki cike a fuskar ta
Shima Abdul ya ƙara da cewa, "kina nufin ƴan jarida suka shigo gidan nan? To waye ya gayyato su?"
Tsaki ta ja da cewa, "waye kuwa ban da Yaya Umar. Wajen shi suka ce sun zo."
Momy tace, "Mata ne ko maza?"
"Mata ne su biyu suka zo, Ni ban ma ga sun yi kama da ƴan jarida ba gaskiya."
Momy tace, "ba na tunanin Umar Faruk zai gayyato su nan gidan duk da dai ban sani ba, amma kin san zaɓe ya kusa nan da kwana huɗu dole dama zasu takura masa, but mun yi maganar da shi kuma na san bazai ƙetare magana ta ba, babu wani amfanin yin hira da ƴan jarida bare har su tako wannan gidan."
"Gaskiya ne Momy, Ni ina ga wankin hula yana so ya kai mu ga dare." Abdul yafaɗa fuskar sa babu walwala ko ɗigo. "Momy i hate this Guy wlh! na gaji na gaji da ganin shi kiyi wani abu don Allah, Nima fa Ina so na fara watayawa a ƙasar, don Allah jibe yanda ya jajibo wani siyasa saboda iyayi don ya ga uban shi yayi, so nake yi Ni in gan Ni a matsayin sa Momy amma ba shi ba, Ni ya kamata nayi suna ba shi ba Momy. Sannan a kan wannan siyasan kowa zai san waye shi and kowa zai san arziƙi mu muke ci a gidan nan. Wannan ai tonon asiri ne."
Ajiyan zuciya Momy ta sauke tana kallon shi tace, "kayi haƙuri Abdul da sannu burin mu zai cika, da sannu komi zai kasance namu, Ni fata na ba na so muyi wani abun da zai ja hankalin police a gidan nan, ka san yanda muka kashe Nusaiba a gidan nan, mun bata guba ta ci daƙyar muka samu muka tsallake zargin ta, ba don mun biya ASP kuɗi me yawa ba ba na tunanin zai goge hujjojin da ya samu a kan gaskiyar guban da aka bata, so dole sai da dabara burin mu zai cika a kan Umar Faruk, muna da sauran lokaci da zamu aiwatar da shirin mu, yau saura kwana huɗu ayi zaɓe, kafin lokacin dole zamu cika burin mu a kan shi, sai dai wani ba shi ba."
Duk kan su murmushi ne ya suɓuce a fuskar su
Yayinda Luwaira wacce fuskar ta babu walwala ta buɗe baki da ninyan yin magana sai suka ji Nocking a bakin ƙofa
Shiru duk suka yi ko wanne yana kallon ƙofan. Sai da aka sake Nocking ɗin ne kafin a tare Momy da Abdul suka amsa, "yes. Waye ya shigo."
Hafsah da Yusra ne suka fara shigo wa kafin shi ya biyo bayan su. Kamar yanda ya saba yayi shigan shi na manyan kaya, farar shadda wacce sai maiƙo take yi tsaban sabunta da ɗaukan guga, tamkar wani ango sabida kyawun da yayi, gaba ɗaya turaren sa ya cika parlour'n da ƙamshi. Da gudu yaran suka isa wurin Momy suna rungume ta. Yayinda shi kuma ya taho a cikin ƙasaitan sa ya sami wuri a kan kujera ya zauna
Momy sai rungume yaran take yi tana musu maraba da zuwa fuska a washe
While Abdul yace, "to ku taho nan mana yara na, Momy kaɗai kuka sani ne?"
Da gudu suka dawo jikin shi suna kiran sunan shi da, "Uncle Abdul."
Ya rungume su yana cewa, "yauwa babies ɗina."
Umar Faruk da ke murmushi sabida yanda suke nuna wa yaran shi ƙauna sai ya mayar da idon shi kan Momy yace, "dama zan fita ne ina da meeting sai zuwa dare zan dawo, kuma ba na so su zauna su kaɗai, idan na dawo komin dare zan zo in ɗauke su."
Momy cike da fara'a tace, "ok babu damuwa my son. Ka kula da hanya ka san zaɓe ya kusa, kar ka soma ka fita kai kaɗai ka je da masu tsaron ka Please my son. Allah ya kiyaye ya dawo min da kai gida lafiya, Allah ya bada sa'ar abun da aka je nema kaji ko?"
Cike da jin daɗi wanda ya nuna a fuskar shi yace, "Amin Momy. Sai na dawo." Ya ƙare maganar da tashi tsaye. Idanun sa a kan Luwaira yace, "Luwaira babu addu'a kamar muna faɗa?"
Murmushi tayi tace, "haba yaya ko zan yi faɗa da kowa ai bazan yi da kai ba. Ina jiran Momy ta gama nata ne Nima inyi maka nawa special."
Murmushi yayi da cewa, "no ba na tunanin naki ne special ke dai kar ki ɓige da daɗin baki. Na Momy na ne special. Yanzu dai yi min naki in tafi."
Daga Momy har ita dariya suka yi
Momy tace, "yauwa ɗan albarka ashe dai ka gano ta."
Murmushi yayi kaɗai
Luwaira tace, "to Yaya Allah ya tsare ya kare hanya."
"Amin my dear sister. Ban manta da maganar ki ba idan na dawo zamu tattauna ko zuwa gobe."
Washe baki tayi tace, "to Yaya."
Daga nan fita yayi bayan ya sake yiwa yaran shi Ba-bye.
Yana fita Momy ta kira Talatu me aikin ta tace, "kwashe su ki wuce da su ɗakin ki ku zauna tare."
"To Hajiya." Tafaɗa tana jan hannun yaran
Sai Hafsah ta ɓata fuska tace, "Ni bazan je ba wajen Uncle Abdul zan zauna, ai yace zai kai mu shan Ice cream."
"No Hafsa ki je wajen ta ai ba yanzu zan fita ba, yanzu akwai abin da zan yi zuwa anjima sai mu je ko?" Yafaɗa hakan da murmushi a fuskar sa yana riƙe da kumatun ta da hannayen sa biyu
Murmushi tayi masa sannan ta bi bayan Talatun da ke riƙe da Yusra suka wuce
Tafiyan su Luwaira ta ja dogon tsaki tace, "wlh Momy na tsani yaran nan sosai kamar yanda na tsani uwar su. Ni ban ga amfanin su ba, kamata yayi su ma a aika su inda uwar su ta tafi."
"To abin hauka ne ashe? Ki bar maganar yaran nan ƙananan alhaki, idan mun gama da uban su zamu dawo kan su. Shirin mu kawai na plan A. Yanzu zamu mayar da hankali, idan haƙan mu be cidda ruwa ba zamu sauya wani shawaran. Abdul kai yanzu ya kamata ka samo mana waɗanda zasu yi aikin nan, in two days komi zai kammala ba na son a wuce wannan ranan."
"An gama Momy. Bari in je akwai inda zan je yanzu. Idan na dawo zamu yi magana."
"To."
Daga haka ya tashi ya fice
Luwaira kuma ta dawo kusa da Momyn tana ɓata fuska da cewa. "Ni Momy meyasa baza ku amince da nawa plan ɗin bane? Gaskiya ba na jin zan haƙura da shi cikin sauƙi haka. Ku taimaka min Momy."
"Ban san shirmen banza ke Luwaira. Wai meyasa kike haka ne sai mun kai magana ki dawo damu baya? Gwara ma idan zaki cire wannan shirmen naki a zuciya ki cire shi tun wuri, baza ki taɓa auren Umar Faruk ba, ke ma kin san da haka kar ki sake zuwar min da wannan maganar. Dalla tashi ki ban wuri."
Zumɓura baki tayi tana ƙunƙunai kafin ta tashi ta wuce
Ita kuma ta ja dogon tsaki tana bin ta da mugun kallo. "Idan ba iskanci irin naki ba ko mu mun amince shi zai amince ne? Ba na tunanin zai taɓa auren ki tunda yana kallon ki a matsayin ƙanwar shi ce. Kina so ki mayar da mu baya naga alama zamu dena saka ki a aikin mu, duk wannan abin da nake yi ina yi ne duk don ku amma ke ta banzan shirmen ki kike yi, to sai dai ki mutu kuwa don baza ki taɓa auren shi ba." Haka Momyn ta ci gaba da faɗa ita kaɗai duk da ita Luwaira tuni ta wuce ɗaki abun ta.
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
0 comments:
Post a Comment