"Habibty wannan wace irin tambaya ce haka kuma?"
"Kaima wannan wane irin sunane, ni dan Allah ka dinga faɗar sunana"
"to naji Wudas"
"Allah ka ƙara gayamin kaima sena samo wani sunan na sama ka mara daɗi"
Dariya yayi yace "ke baki san ina matuƙar jin nauyin faɗar sunan nan bane? Yanamin nauyi a bakina, bana iya faɗar sunanki fa"
Cikin Shagwaɓa tace "to meye abun wahala a Widad ɗin?"
"ƙaunar da nakewa me sunan ne yasa yake min nauyi"
"kaga ni duka ba wannan ba, ka bani amsar tambaya ta"
"meyasa kika tambayeni?"
Widad tace "na tambaye ka kuma kana tambayata"
"to ai tambayar ta kice tazo a wata iri, nama rasa me zance miki"
A waje daka ke koyarwa in sun tambayeka wace amsa kake basu? "
" ƙureni zakiyi kenan? "
" ba wani ƙurewa ka bani amsa kawai "
Yusuf yaja ajiyar zuciya yace "Aure ba farilla bane, amma yana da fa'ida tunda Allah ya halatta yinsa, idan kika duba akwai tarin hadisan manzon Allah salallahu alaihi wassalam da suke magana akan Aure, sannan akwai ayoyi a cikin Al'qur'ani da suke magana akan Aure, akwai wani Hadisin Annabi salallahu alaihi wassalam yace 'kuyi aure ku hayayyafa domin inyi alfahari daku ranar Alƙiyama, kinga anan yana daga amfanin Aure samun zuriya, yin aure ka haifi' ya'ya nagari babban Alkhairi ne shima duba ga hadisin manzon Allah salallahu alaihi wassalam da yace 'idan bawa ya rasu dukkanin ayyukansa suna tsayawa banda abubuwa guda huɗu, wanda ya mutu yana me imani da Allah, da sadaƙatul jariya sadaka me gudana, kamar gina rijiya makarantar islamiyya da sauransu, ko wanda ya sanar da wani ilimi wanda ko bayan ya mutu ske amfani da shi, da kuma ɗa nagari, kinga anan yana daga cikin amfanin Aure kayi shi ka samu ɗa nagari ka mutu ya dinga maka addu'a, duk ayyukan bawa suna tsayawa idan ya mutu, amma in kayi Aure Allah ya baka ɗa nagari, yana maka addu'a, kinga babbar ribace wannan, ko yayi wani aiki da ladan ze dinga iskeka. Akwai hadisin manzon Allah salallahu alaihi wassalam da yake cewa 'ya ku taron samari, wanda ya samu iko a cikinku to yayi Aure, idan kuma bashi da halin yin Aure to yayi Azumi, kinga Aure yana da amfani domin shi katanga ne daga aikata zina, yana sanya nutsuwa a zukatan wanda suka yi shi, akwai tarin hadisan manzon Allah salallahu alaihi da ayoyi da suka yi magana akan Aure, dan haka Aure yana da mahimmanci sosai your majesty"
Ajiyar zuciya Widad tayi tace "idan mutum be Aure ba ya aikata laifi?"
"A'a, kamar yadda na gayamiki Aure ba farilla bane, dan haka babu laifi ga wanda beyi ba muddin ze kiyaye iyakokin ubangiji ya tsare kansa daga aikata dukkan wani nau'i na Zina, sedai darajar wanda yake da Aure da wanda bashi da shi ba ɗaya bane, mussman mace duk abunda tayi na aiki kona ibada a cikin gidan Aurenta tana da lada, hakama namiji duba da gaba ɗaya shikansa Auren ibada ne, akwai wanda sam Aure be halatta suyi shiba, misali wanda bashi da abunda ze iya riƙe Auren, ko yake da wata nakasa da baze iya sauke haƙƙin iyalinsa na Aure ba wanda ze zamana da cutarwa a ciki"
Se kuma yai shiru, be kuma cewa komai ba, Widad ta sake gyara kwanciyarta a jikinsa tace "to amma a haka akewa mutum wani kallo dan mutum be Aure ba, yau anyi abunda ya ɓatamin rai, yau na fara ganin anawa mutum rashin mutunci akan ba shi da saurayi, baka ga Abunda aka yi wa Hindu ba, abun ya bani haushi sosai ya bani mamaki"
Yusuf yace "To ai cikar mutuncin mutum shine Aure Habibty, kece kike masa wani kallo na daban"
"to tunda dai Auren ba dole bane, ai bekamata a dinga takurawa mutum ba, yanzu by mistake idan tayi Auren wani abu daba a so ya faru still ita za'a ɗorawa laifi, gaba ɗaya yau wani iri ta wuni tayi kuka sosai"
"Kin damu da Hindu sosai Gimbiya"
Widad tace "Wallahi kuwa, ina sonta har raina tana da kirki"
Yusuf yace "Ashe kin san meye son, nine kawai bakya so"
"Nifa ban san irin son da kai kake faɗa ba, amma ina jin Hindu kamar 'yar uwata, inaji dama gidanmu ɗaya ace ina da sister nima, nifa da zasu yadda idan zamu koma gida in tafi da ita"
Yusuf yace "Ai kina dasu, gasu Amal nan da Ramlah suma sisters ɗinki ne, amma kike musu wulaƙanci"
Widad tace "Wallahi na tsanesu, tsana mafi tsanani da ban taɓa yiwa wata halitta ba, kuma ina nan idan na koma gida se sun bar mana gida, dan ba gidan ubansu bane"
"Subhanallah meyasa?"
"Bakomai" ta bashi amsa tare da gyara kwanciyar ta a jikinsa.
A hankali yace "bazaki gayamin ba?"
Shiru tayi masa taƙi magana, tana jin yadda yake ta jera numfashi, kamar wani mara gaskiya, zuciyarsa na harbawa da sauri da sauri, ga ruwan sama da yake ƙara zuba kamar da bakin ƙwarya.
A ɗan shagwaɓe Widad tace "Yoseef am scared, kuma sanyi nake ji"
Yusuf yace "calm down, muna tare ba abunda ze faru insha Allah, keep praying"
Ta jinjina masa kai, a hankali Yusuf ya shiga kiran sunanta, tana jinsa amma taƙi amsawa, sema wata kasala da take saukar mata.
Tana jin abunda Yusuf yake yi, amma ta kasa ko motsi, duk yadda Yusuf yaso tattara nutsuwarsa ya guje faruwar wani abu a tsakaninsa da Widad abu ya gagara.
Ba dan ruwan saman da'ake ta kwararawa ba kamar da bakin ƙwarya, da babu abunda ze hana mutanen ƙauyen da kewaye sanin abunda ya faru a tsakaninsu, saboda yadda Widad ta dinga kuka da neman temako, rakin tsiya da kuma Shagwaɓa.
Tun tana kukan har tayi shiru, muryarta ta dena fita sosai.
Seda Yusuf ya dawo hayyacinsa dafe kansa cike da dana sani, da tuhumar kansa akan wani ganganci ne ya ɗebe shi ya aikata hakan?
Widad se ajiyar zuciya take, tana kuka ƙasa ƙasa, gaba ɗaya Yusuf ya bata tsoro kuma ya bata mamaki.
Gaba ɗaya jikin Yusuf yayi sanyi ya kasa magana, ya rasa mema zece mata.
A hankali yaja rigarsa ya saka, ya miƙe ya ɗau bokiti da tukunya ya fita tsakar gida, a cikin wannan ruwan da ake ya tafi rumfar da'ake girki, ya dinga tona cikin murhun, ya tattara gawayi da ƙyar ya tashi garwashi, ya ɗora ruwa.
Haka ya zauna ya dinga fama, seda ruwan nan yayi zafi sosai ya haɗa mata, ya kai banɗaki ya ajiye.
Shi kansa jikinsa a matuƙar mace yake, ya koma ɗakin ya shiga ya tarar da ita a inda ya barta a kwance tana kuka, Ya durƙusa ya ɗagota ya samata hijjabi, a hankali yace "tashi muje ga ruwan wanka can na kai miki"
Bata kula shi ba ta miƙe tsaye, ta dafa bango sedai tana zuwa bakin ƙofa ta tsaya, saboda tsoro ga tsigar jikinta dake tashi, saboda wani irin sanyi da take ji, gashi gaba ɗaya tsakar gidan ya jagwale.
Kawai ji tayi yayi sama da ita, ya kaita banɗaki ya ajiye mata fitila, ya koma can tsallaken wajen rumfa ya tsaya.
Ta daɗe sannan ta buɗe ƙofar banɗakin, Yusuf yaje ya ɗauke ta ya maida ita ɗaki, shi be tsaya wani dafa ruwa ba, saboda garwashin duk ya mutu, a haka ya ɗebi ruwan da sanyi da komai yaje yayi wanka.
Ya dawo ya tarar da ita ta kwanta, ta duƙunƙune a cikin hijjabi, yasa bargo ya rufeta, shima ya kwanta kowa yayi shiru yana saƙe saƙe a cikin ransa.
Mussman Yusuf wanda dana sani da haushin kansa suka baibayeshi.
Wani private hospital aka kai Nurat, nan da nan suka karɓeta a emergency, likitoci suka shiga ƙoƙarin ceto ran Nurat, ta hanyar tsaida jinin dake ta zuba a goshinta.
Da ƙyar jinin nan ya tsaya, aka nan naɗe mata goshinta da bandeji, goshin ya kumbura suntum har gefen idonta saboda buguwar da tayi.
Mahaifiyar Nurat da mahaifinta suna reception, Mahaifiyar Nurat tana ta goge Hawaye, ta kasa zaune ta kasa tsaye.
Likita ne ya fito ya samesu a reception, suka yo kansa gaba ɗaya suna jero masa tambayoyi.
"ku kwantar da hankalinku, raunine kawai ta samu, Allah ya rufa asiri be shafi idonta ba, amma idan ta farfaɗo akwai gwaje gwajen da zamuyi muga inda yuwuwar ayi mata hoton Ƙwaƙwalwa, dan naga jini yana fita daga hancinta, karmu je ko akwai internal injury "
Mahaifiyar Nurat tace " Na shiga uku, hoton Ƙwaƙwalwa kuma likita? Ba dai haukacewa tayi ba? "
Tsaki Alhaji Musa yayi yace " kaga dan Allah ƙyaleta, na fahimce ka idan ta farfaɗo ɗin in akwai buƙatar hakan se ayi hoton, ni dai fatana Allah ya bata lafiya"
"dole kace a rabu dani mana, tunda ka kusa kashemin 'ya, kuma yanzu kana wani nuna kamar ka damu da ita"
"A nan ɗinma sekin nuna halinki ko?"
"ban sani ba, kuma wallahi duk abunda ya samu' yata kaine"
Likita yace "haba dan Allah yallaɓai, da girmanku da komai, hakan be dace ba ai, akwai marasa lafiya a kwance, kamata yayi kuyi ta lafiyar 'yarku ba faɗa ba"
Haka sukayi shiru likita ya wuce.
Wayar Alhaji Musa ce ta shiga ringing, ya ɗanyi gefe ya ɗakko wayar yasa a kunnensa yace "Hello ina ji"
"kana inane? Akwai magana fa"
"ina Asibiti, an kwantar da' yata"
"Subhanallah meye ya sameta?"
Alhaji Musa yace "eh Home Accident ne, ta faɗi ne ta bige but is not that complicated"
"Ok to shikenan, Allah ya ƙara afuwa, zamu shigo mu duba ta insha Allah"
Alhaji Musa yace "shikenan nagode sosai"
Wata Nurse ce tazo wucewa, Maman Nurat tace "Sister dan Allah ko zan iya shiga gurin Nurat?"
Nurse ɗin tace "eh zaku iya shiga ku ganta, bacci take"
Cikin rige rige suka nufi ɗakin da aka kwantar da Nurat.
Nurat tana kwance tana bacci, ga drip an sa mata suka ƙarasa gaban gadon Nurat, mahaifiyar ta ta zauna a gefen gadon ta kamo hannun Nurat, jikinta ya ɗau zafi sosai Amma baccinta take ta sha.
A hankali Nurat ta buɗe ido, ta kalli inda Mummynta take, a hankali ta kai hannu tta shaf goshinta inda aka nannaɗe da bandeji, ta kalli Mummynta tace "Mummy me aka samin a goshina?"
"bandeji ne, aka rufe miki ciwon ki"
"Mummy kaina ze tsage ciwo yake min"
"kiyi haƙuri, ze dena insha Allah"
Alhaji Musa ya ƙarasa gaban gadon yace "Babyna ya jikin naki?"
Kallo ɗaya tayi masa, ta ɗauke kanta tana kuka.
Alhaji Musa yace "Am sorry kinji Babyna, is just a little bit mistake, kema ki dinga jin magana ki dena taurin kai"
Ita dai ba tace komai ba, kuma taƙi kallonsa.
Widad se farkawa tayi ta nemi Yusuf ta rasa a ɗakin, tayi tunanin ko ya tsaya sallar Asuba ne yayi karatu, gaba ɗaya jikinta ciwo yake, ta lallaɓa taje tayi sallar Asuba.
Ta koma kan katifarta ta kwanta, kanta se ciwo yake da duk ilahirin jikinta ciwo yake mata, ba ƙaramin mamaki Yusuf ya bata ba jiya, bacci ne ya sake yin awon gaba da ita.
Har sha ɗaya na safe bata ga Yusuf ba ba taga alamarsa ba, ta tashi ta lallaɓa ta gyara ɗakinta, ta ɗau bokiti taje ta karɓi ruwa tayi wanka.
Ta koma ta ɗau kofi ta fita tana takawa a hankali, saboda yadda tsakar gidan ya jagwalgwale sakamakon mamakon ruwan saman da'akayi jiya da daddare, tsigar jikinta se tashi take saboda ƙyanƙyami, ga ƙarnin ruwa daya kwanta.
Ƙofar ɗakin gwaggo taje tayi sallama, Gwaggo ta amsa mata, ta nemi izini sannan ta shiga.
Gwaggo tace "Amarya, yanzu nake sa ran in aiki Hindu ince ta dubamin me, yau shiru ban ganki ba ko dan anyi ruwan sama ne"
Widad tace "bana jin daɗi ne, in akwai Abinci ki bani yunwa nake ji"
Da yake yau ba Gwaggo ce da girki ba, yanzu se ranar girkin Gwaggo ake basu Abinci, dan Widad bata cin Abincin kowa se nata, in dai ba ita tayi girki ba baza taci ba, sedai Yusuf ya girka mata wani abun.
Gwaggo tace "Amarya bani nayi girki ba yau, amma ina da garin kunu an karɓomin jiya daga gurin niƙa, bari in dama miki"
Widad tace "to"
Ta nemi guri ta zauna tana sake ƙarewa ɗakin Gwaggo kallo, wand ke matuƙar birgeta, sedai sam abunda ya faru tsakaninta da Yusuf jiua ya kasa barin zuciyar ta.
Hindu tayi Sallama da kaya a hannunta, Widad ta amsa.
Hindu tayi murmushi tace "Amarya dama kin tashi? Na zata har yanzu bacci kike ai"
Widad tayi murmushi tace "A'a yazan ta bacci har I yanzu, na tashi tun ɗazu ai"
"Amma ya naganki wani iri, ko baki da lafiya ne?"
Widad tace "A'a me kika gani?"
"gani nayi kinyi wani iri, idonki kamar kinyi kuka, kuma kamar me zazzaɓi"
Widad tace "lafiya ta ƙalau fa, yunwa kawai nake ji"
Hanne ta bankaɗo ɗakin ta shigo, babu ko sallama ta kalli Widad da Hindu taja wani uban tsaki, ta ƙarasa ciki basu kulata ba Hindu ta cigaba da jerawa Widad sannu.
Gwaggo ta kawowa Widad kunu, Widad tayi ta godiya ta tashi ta koma ɗakinta.
Dama ba'a batun sugar acikin kunun da suke sha ko kuma koko, a haka suke sha itama kuma ta saba a haka take sha.
Kunun nan da ta sha har la'asar, bata sake cin komai ba, se Dafaffiyar gyaɗar da Hindu ta bata.
Shikam Yusuf nauyin Widad ne ya hana shi dawowa, be san da wani ido ze kalleta ba, besan da wani kalaman ze amfani gurin kare kansa ba, tabbas yasan yayi aika aika a daren jiya, wadda shima be yi shirin afkuwar al'amarin ba, besan ta ina ze fara haɗa ido da ita ba, besan wani mataki zata ɗauka a kansa ba.
Haka nan ya tunkaro gidan yana tunanin, gabansa yana faɗuwa se Addu'a yake.
Yai sallama ya tsaya suka gaisa dasu Hari, yai sallama a ƙofar ɗakin Gwaggo ma suka gaisa, da yake yau tun Asuba be dawo ba.
Cike da fargaba ya nufi ɗakin su, yai sallama.
Tana daga kwance a inda take ta amsa masa a ciki ciki.
Ya shigo musu da 'yan kayan Abinci ya ajiye.
Jiki a sanyaye ya kalle ta yace "Yama ganki a kwance"?
Da harta buɗe baki za tayi masa tsiwa, kawai ta tuna abunda ya faru jiya da daddare a tsakaninsu, ba shiri ta tsuke bakinta kawai tasa kuka.
Dama Yusuf yasan a rina, ya ƙarasa inda take, yasa hannu ze kama hannayenta amma ta janye hannunta.
Yusuf ya ɗan ƙura mata ido, ji ba ƙwari ya fara magana yace "Widad ban san ta ina yakamata in fara ba, bani da kalaman da zanyi Amfani dasu wajen baki haƙuri, gaba ɗaya na rasa me yakamata inyi, ina me baki haƙuri sannan na shirya karɓar duk irin hukuncin da kika shirya Yimin" yai maganar fuskarsa na fallasar da tsantsar damuwa dake kwance a zuciyarsa.
Cikin kuka tace "shine ka tafi ka barni tun safe, bayan kasan...." ta ɗanyi shiru sannan ta ɗora "bayan kasan abunda kayi min, bani da lafiya tun Asuba baka sake dawowa ba, ga yunwa nake ji, Se gurin Gwaggo naje ta bani kokon tsamiya" ta ƙarasa maganar cikin kuka.
Seda Yusuf yaji kamar yayi dariya, amma ya dake yace "subhanallah, am very sorry, na manta ne kuma ina jin nauyinki sakamakon abunda ya faru jiya, dan Allah kiyi haƙuri, i don't even know how it happens"
Widad a ranta tace 'jimin ɗan rainin hankali, wai he don't even know how it happens, se kace yana maye yayi abunda yayi'
Haɗe rai ta sake yi ta cigaba da kukanta, tace "Kuma seka sake ni"
Yusuf yace "Naji amma ba yanzu ba se mun koma gida, for now am very sorry please, am not able to fulfill my promises to you, dan Allah kiyi hakuri Widad"
Banza tayi masa taƙi cewa komai, da haushinsa take ji kama sosai he takes away her pride, sannan yasa ƙafa yayi tafiyarsa tun safe ya barta, bata shirya faruwar haka ba sam a rayuwarta, babu Aure a gabanta, amma Yusuf ya ɓata mata komai yanzu.
Hannu ya kai ze taɓa ta, aikuwa ta zabura ta miƙe zaune da sauri tana faɗin "wayyo Allah Daddy"
Yusuf a rikice yace "yi haƙuri ba wani abun zan kuma yi miki ba"
"Kuma sena gayawa Daddy idan muka koma gida, idan kayi min hakane dan karka sakeni, let me tell you, we must go separated, you must divorce me na gaya maka"
Yusuf yace "Widad trust me, is not intentionally shiyasa nake iya ƙoƙarina akan in kiyaye, but am human being, am not super natural"
"you said i should trust you how? After you know this is arranged marriage, but you took away my pride, how can I trust you Bayan Kamin ƙarya a baya, bazan taɓa trusting ɗinka ba"
Gaba ɗaya Yusuf ya rikice, ya rasa abunda yake masa daɗi, ya dafe kai yana kallon yadda take kuka, tausayinsa ne ya kamata, tace "Nifa Yunwa nake ji, kokon tsamiya kawai na sha tun safe"
Yusuf yace "to, bari in ɗora mana girki"
Yai maganar tare da miƙewa, ya hau kokawar ɗora Abinci.
Yana cikin gaganiyar ɗora girki taga kamar yana ɗingishi ne, bata kula ba ta share shi.
Ya dawo ya ɗakko leda ya ɗakko mata pad guda goma sha biyu, da Maclean sabo da su man shafawa yace "Kinga na siyo miki pad ɗin, kuma naga Maclean ɗinmu ya kusa ƙarewa na ɗanyi mana siyayya"
Tasa hannu ta karɓa tace "Nagode sosai Allah yasaka da alkhairi" yaji daɗin godiyar da tayi masa tace "amma zan bawa Hindu, itama ta dinga amfani da pad instead of cloth"
Yusuf yace "duk yadda kika yi"
Ta tashi tayo alwala, ta dawo ɗaki Yusuf ya zauna ya tsince shinkafar hausa tsaf, ya fita yana wankewa, Hanne ma ganinsa tace "Laa dama ka iya aikin mata haka?"
Yusuf yai murmushi yace "eh na iya mana, gashi inayi"
"Kawo in wanke maka, kar ayi sallama a ga kana wanke shinkafa da kanka, bayan kana da Aure kuma akwai mata a gidan"
Yusuf yace "karki damu Hannatu, ai shinkafar kaɗance zan iya wankewa"
Hanne ta ƙaraso tana faɗin gaskiya a'a, nidai bani nan in wanke maka.
Widad ta gani tsaya a bakin ƙofar ɗakinta, tana watso mata wani mugun kallo, take Hanne ta tuno da shaƙar data sha, nan da nan cikinta ya kaɗa ta tsaya tayi sororo, Yusuf ya ɗaga kai ya waiga, yaga ashe Widad ta gani, bata ce musu komai ba ta shige ɗakin, tana jiran Yusuf ya shigo ta zazzage masa.
Ita mamaki ma take yi, yadda ta kasa zagewa ta ƙare masa saboda abunda ya shiga tsakaninsu, tunda ya shiga ɗakin take binsa da kallo.
Be ce mata uffan ba, ya zuba shinkafar
"Malam daga yanzu idan zakayi kule kulenka ka bari seka sakeni tukuna na gaya maka"
Kallonta Yusuf yayi yace "Dagaske har ranki so kike ki rabu dani?"
Kallonsa tayi tace "to da tare aka halicce mu? Ko kuma ka manta bisa yarjejeniya mukayi Aure ne haba? Nifa bani nace ka fara sona ba, dan baka gara tun wuri kasan abunyi"
Shiru yayi ya cigaba da tunani, har ya kammala girkin ya sauke, ya ɗora mai akan wuta ya soya, sedai bisa tsautsayi saboda tunani mai ya zubar masa a hannu.
Firgigit ya dawo hayyacinsa yace "Subhanallah"
Da sauri ta juyo taga abunda yake faruwa, ai nan da nan ta ƙarasa gabansa tana faɗin "Subhanallah, yoseef garin Yaya? Me kake tunani haka? Kalli yadda ka ƙone hannu, innalillahi"
Ta riƙe hannun nasa, ta sa rigarta tan goge masa inda man ya zuba a hannun sa, karaf idonta ya sauka akan ƙafar wandonsa, kamar jinine a jiki, ta kai hannu ta janye wandkn, rauni me yaji a gurin, kamar an saka ƙarfe anja gurin.
Ɗaga ido tayi ta kalle shi tace "Yoseef, meye wannan?"
"wannan karki damu, dama zanje cikin garine in siya miki pad ɗin nan, to kin san hanya bata da kyau, shine muka faɗi a babur, amma karki damu zan warke Insha Allah"
Kallonsa tayi, wani irin tausayins ya game zuciyar ta, hawaye sharkaf a fuskar ta tace
"This is serious, ya isa haka, yakamata mu koma gida kome ze faru ya gara faru, ba zamu cigaba da zama a nan lafiyarka na taɓuwa saboda ni ba"
Yusuf yayi murmushi cikin jarumta yace "wannan ai ba ciwo bane me girma, zan warke very soon insha Allah, ki kwantar da hankalinki"
Cikin kuka ta shiga girgiza kai tace 'No, Yoseef se mun bar garin nan haka, wahalar da kake sha saboda ni ta isa haka, is enough ba dangin iya ba na baba se wahala kake saboda ni? Idan har lafiyarka ta cigaba da taɓuwa bazan yafewa kaina ba, gida zamu koma ba zamu ci gaba da zama anan ba kome ze faru ya faru"
Tai maganar tana riƙe da ƙafar Yusuf tana kuka
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
58 _59
Ɗan ƙura mata ido Yusuf yayi yace "haba Widad, ya zaki ce mu koma gida a wannan yanayin? Komai ze iya faruwa fa"
"Koma meye yafarun, amma be kamata ratuwarka ta cigaba da cutuwa saboda ni ba, kalli ƙaddara daga wannan se wannan yakamata inyi maka adalci bekamata in nuna son kaina da yawa ba"
Yusuf ya shiga share mata hawaye yace "Karki sake cewa ba dangin iya babu na baba tsakanina dake, koba komai koda mun rabu kin taɓa zama wani ɓangare na tarihin rayuwata wanda baze taɓa gogewa ba, dan haka kome nayi a yanzu domin farincikin ki bakomai domin kuwa haƙƙina ne inyi miki, a gurin Allah babu wani abu like arranged marriage, duk abunda abunda ze sameni saboda kare rayuwarki baze dameni ba, saboda mahimmancin da kike dashi a gurina, kidena kuka zan warke insha Allah "
Girgiza kai ta shigayi, tana son yin magana amma ta kasa dan haka kawai ta faɗa jikinsa ta cigaba da kuka.
Yusuf a ransa yace 'alamu sun bayyana ƙarara Widad tana sona, sedai ita bata san hakan ba'
'Amma idan harka bari Widad ta fara sonka kayi mata adalci kuwa? Kayi mata ƙarya a karo na biyu, anya ƙaddarorin rayuwarku zasu haɗu a guri guda?' wata zuciyar ta shiga gargaɗinsa.
Jiki a sanyaye yake dukan bayanta cikin sigar rarrashi yace "ni ban gaji dake ba, kuma duk abunda yake faruwa dani baze taɓa sawa in juya miki baya ba, saboda Amana ce na karɓa a gurin mahaifinki, kuma Allah ya jarabci zuciyata da sonki, babu yadda zanyi ƙaddrata kenan"
A hankali ta tashi daga jikinsa, ta ɗan zuba masa ido, shi kuwa Yusuf me yake ji haka game da ita da baya iya ganin laifinta, kuma yake tarar dukkan ƙalubalen daze taso?.
A hankali tace "Muci Abinci, ina jim Yunwa"
Yusuf ya haɗa musu shinkafa da mai da gishiri, suka fara ci sedai Widad da ƙyar take cakalar Abincin, ƙarshe Yusuf ne ya bata Abincin.
"Kaje Asibiti kuwa da kaji ciwon?"
"Naje chemist, na sai magani ciwon bayamin zafi ai, bari nayi alwala inje waje inja salla"
"ba in da zaka, ka zauna ka huta"
Yusuf yace "Amma..
" ba wani amma, kawai kayi salla a gida, kar kaje ka fama raunin nan"
Da ƙyar ta yadda yaje yayi salla ya dawo, tazo ta zauna ta saka masa man zaitun a gurin, ta nayi tana jera masa sannu.
Da kanta ta gyara masa shimfiɗarsa, ya kwanta, tana sake kallon yadda ciwon ya ɗanyi zurfi.
"Allah ya baka lafiya kaji"
Tai maganar tana shafa sumar kansa, yai murmushi yace "Ameen ya Allah nagode sosai"
"meye wani ka gode?" kawai se ya shagala da kallonta, ta kalle shi tace "naga kana kallona, idan ka sake kayi abunda bana so koka tsokaneni ko, zaka ga yadda zanyi da kai"
"ya akayi kika san abin da zan miki?"
"Fuskarka kawai na kalla na gane hakan ' ta bashi amsa
Ya shammaceta ha janyota kan shimfiɗarsa, ya mirginata aikuwa ta ware baki zata kurma ihu, cikin hanzari ya toshe mata baki yace "sekin tara mana jama'a tukuna?"
"Ka cikani ko inyi ihu Allah"
"to me nayi miki da zakiyi ihu?"
"Ai dole ka tambayeni me kaimin, tunda jiya...
Sekuma tayi shiru," Mhmm ƙarasa mana"
"dan Allah ni ka ƙyaleni bacci fa nake ji"
Shiru yayi bece komai ba, ya cigaba da kwanciya a jikinta.
"Masoyiyya, meyasa da muna gida kika cemin ke Karuwa ce? Alhalin ba haka bane?"
Widad tace "eh ai ba ƙarya nayi ba"
"Meyasa kikeyin abunda bakya so ai miki ne?"
"meye maraba ta da karuwa a wannan lokacin? A shigar da nayi, da kuma inda naje harka ɓatami rai ranar, Daka san me najeyi da bakamin haka a wannan ranar ba"
"Nifa tun a wannan lokacin ina matuƙar kishinki ne, tun a lokacin nake sonki shiyasa nake nuna kishina a fili, Abubuwa da yawa suna ɗauremin kai a wancan lokacin ina buƙatar warawara daga gareki"
"Yoseef kenan, kaine mutum na farko da ya shigo rayuwata a hagunce kuma ya zama garkuwa a gareni, ya samu damar da da ɗunbin mutane basu samu ba, kayi nasarar canza wasu daga cikin tunanina, sedai har yanzu baka bani labarin sakamakon bincikenka da kayi ba akan maƙiyana"
Yusuf yai murmushi yace "Naƙi na gaya mikin, nima ban yadda dake ba"
Dariya Widad tayi, harda kai masa dukan wasa a ƙirjinsa tace "nice baka yadda dani ba? Ai nima daliline yasa hakan, koka manta niɗin mahaukaciya ce? Haukana ne yasa bana yadda da mutane, kai kuma kaga kana da hankali"
Yusuf yace "Nifa gaskiya inada question mark akan wannan ciwon naki, meya hana ciwon tashi anan?"
Kasancewar a duhu suke, yasa se shseshsheƙar kukan Widad yaji, cikin sauri yace "Am sorry, i don't mean to hurt you, ban san ze ɓata miki rai ba tambayar yi haƙuri" yai maganar da sigar rarrashi, yana shafa bayanta.
Yauma Allah ne ya kiyaye, dan tana jin Yusuf ya fara zarce ƙa'ida ta narka masa cizo, ba shiri ya cikata ta miƙe ta koma kan shimfiɗar ta, tayi shiruu kamar ruwa ya cinye ta.
Kwanan Nurat uku a Asibiti, anata zuwa duba ta, Allah ya temake ta da akayi hoton ƙwaƙwalwar, babu wata matsala a cikin kanta dan haka aka sallameta daga Asibitin.
Suleiman ne zaune a gaban wani mutum a office, da gani mutumin babbansa ne a gurin aiki, mutumin ya kalli suleiman yace "Nagaji da gafara sk ko ƙaho ban gani ba, har yanzu babu wani bayani akan Assignment ɗin nan da muka bayar"
Suleiman ya gyara zama yace "Yallaɓai ai akwai matsala ne"
"Matsala wace iri?"
"yallaɓai wanda muka bawa aikin, shine direban 'yar gidan Alhaji Nasir kuma tare aka sace su"
Ɗan waro ido mutumin yayi yace "ban fahimceka ba"
Suleiman ya gyara zama yace "ƙwarai yallaɓai, Yusuf jam'in mune, yaje da saunan aikin direba amma shine wanda muka tura muka saka aiki, kuma yanzu haka tare aka sace su ita dashi"
Jinjina kai mutumin yayi yace "Amma babu wani abu daya fara gabatarwa na sakamakon binciken da yayi?"
"gaskiya Yallaɓai babu, dan a satin da nayi masa magana ya cemin zezo office yayi bayani, a satin aka sace su"
Mutjmin yayi ajiyar zuciya yace "shikenan you can leave"
Suleiman ya tashi yayi saluting mutumin sannan ya fita.
Susu huɗune zaune a wani matsakaicin falon Hotel, Alhaji Bukar yace "wata maganar banza da naji, wai yaron nan da'aka sacesu tare shine jami'in tsaron da aka tura yayi wannan binciken"
Alhaji Musa yace "wane yaron?"
Bukar yace "direbanta mana"
Alhaji Musa yace "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, shikenan na kaɗe har ganyena inda wannan yaron da suke yawo tare ne"
Alhaji Haruna yace "kamar yaya ka kaɗe?"
"Ranar da Nurat take birthday sukazo, lokacin da nayi attempting a sacemin ita, shiya ritsa Nurat da bindiga ta gaya masa inda Yar Daula take"
Alhaji Munir yace "ji wata maganar banza, to me yasa tun a lokacin baka faɗa ba se yanzu"
"to ta yaya zan in sani, na tambayi Nurat tacemin itama bata san waye ba, se yanzu da akayi zancen nan sannan na gane"
Alhaji Haruna yace "gaskiya malam ka kwafsa mana, kayi mana gyɗa a gurin nan, maimakon tun a lokacin kasa ayi bincike a gano maka shi, aji dalilin da yasa ya hana a sace yarinyar, wataƙila ma da tun a lokacin munsan waye shi"
Alhaji Bukar yace "ku dakata, kuskure ne dai an riga anyi shi, sedai a kiyaye gaba kuma a sake shiri, babban abunda ya ɗagamin hankali shine, bai bada komai na shedar binciken da yake yi ba, babu wanda yasan meye sakamakon binciken nasa, amma tabbas tunda ya gano kayi yunƙurin saceta, nasan ze maida hankali da yin bincike akanka"
Zufa Alhaji Musa ya shiga sharewa yace "yanzu meye abunyi? Hankalina fa ya fara tashi, gashi babu wanda yasan inda suke"
Alhaji Munir yace "kaine a ruwa ai, tunda kikayi shirme da sakaci"
"Mune a ruwa dai, idan Asirina ya tonu ai naku ma gaba ɗaya ya tonu"
Alhaji Haruna yace "dan Allah kuyi shiru mu nemo mafita, aikin gama ya gama ba yanzu ya kamata a nemi mafita ba, abun da ya kamata mu yi yanzu shine neman mafita"
Alhaji Bukar yace "yanzu magana ta farko dai shine, mu matsa lamba musan inda Daula yake, ɓatan Daula ma fa wani babban giɓine kuma hatsari a garemu, ga 'yarsa itama bamu san a inda take ba yanzu, ga wannan yaron da wannan maganar ta taso yanzu"
Alhaji Munir yace "Sannan wanda ya sa aka saki Yaron gurin Halima shima ba ƙaramar barazana bane a gare mu, dan bamu san waye ba, kuma banu san manufarsa ba"
Alhaji Musa yace "Aini nafi kowa shiga matsala, a hanzarta a nemo mafita gaskiya"
Alhaji Bukar yace "ku kwantar da hankinku, zan san abunyi insha Allah, nasan yadda zanyi da al'amarin"
Alhaji Munir yace "Yallaɓai meye mafitar to?"
Bukar yace "when I come out with the final decision I will let you know, Musa ka kwanta da hankalinka, ba abunda ze faru zanwa tufkar hanci"
Alhaji Musa yace "to shikenan tunda kace haka yallaɓai"
"Mummy karɓi wayarki, tana ta ringing kin barta a falo"
Hajiya Halima tasa hannu ta karɓi wayar tace "Salamu Alaikum"
"Wa'alaikum Salam, Halima yakike ya yara?"
Haɗe rai tayi tace "Kai harkuna da bakin da zaka wani kirani kana ya Yara? Bayan rashin mutuncin da kukayi min akan belin Anwar?"
Alhaji Haruna yace "ke, ki bar wannan maganar akwai matsala ne fa"
"Matsala ta ƙaremu ku acan tsakaninku banda ni, karka sake sani a cikin matsalarku tunda kowa kansa ya sani"
"Aikuwa kece a wannan matsalar, dan wallahi kina ruwa"
"Kamar yaya?" tai maganar cike da mamaki.
"Yaron nan Yusuf yake ko Yunusa, ashe jam'in sirrine, shine wanda yake binciken"
Mummy tace "kai ɗan tsaya mana, Wai Yusuf direban Widad?"
"Oho nima ban sani ba, wanda dai aka sacesu tare, ashe shine yaron da yake binciken nan, muna ganin munyi dabara ashe da kanmu muka burmawa kanmu wuƙa, yaron nan shine yake gudanar da binciken"
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, na shiga uku Haruna dan Allah yaron nan dagaske ɗan sanda ne?"
"ƙwarai kuwa, ɗan sanda ne ma farin kaya, kuma shike gudanar da binciken nan"
"Shikenan, wallahi idan ya dawo garin nan tabbas na kaɗe, an karɓi bayanin binciken kuwa?"
"ba'a karɓa ba dan ba'a samu ba, amma Alhaji Bukar yace mu saurare shi, ze faɗa mana abunda za'ayi"
Hajiya Halima tace "ni dai dan girman Allah ku gaggauta samo mafita, wallahi akwai matsala" tai maganar tare da ajiye wayar tana faɗin na shiga uku.
Amal tace "Mummy meyafaru ne?"
Ramlah ma shigowa tayi tana faɗin "Mummy lafiya kuwa?"
"Yara akwai damuwa fa, wai ashe munafukin yaron nan ɗan sanda ne?"
Amal tace "wane yaron wai?"
"wannan shegen direban me siffar munafukai mana"
"Wai Yusuf?"
"Shi, wai ashe ɗan sanda ne"
Ramlah tace "ta yaya ya zama ɗan sanda? Mummy ke waye ya gaya miki?"
"Yanzu mukayi waya da Haruna yake gayamin"
Ramlah tace "No wonder, sam wannan beyi kalar wanda za'ace yana cikin wahala ba, ko kuma rashin ilimi, ashe munafukine shiyasa na tsane shi, shege Azzalumi"
Amal tace "shiyasa wani lokacin nake hanaki yi masa wasu abubuwan Mummy, ki saki baki kiyi ta sakin maganganu anyhow, gashi abunda ya faru ai"
Ramlah tace "dan Allah kiyiwa mutane shiru, yanzu mafita za'a nema ko surutan zaki cigaba dayi?"
Amal tace "ko anemi mafita ko kar anemi mafita aikin gama ai ya gama, sedai a kiyayi gaba"
Hajiya Halima tana jinsu tayi shiru, gaba ɗaya ta shiga tunani yadda take sakin magana yadda taga dama, ashe kallonsu kawai yake"
Ramlah tace "Yanzu Mummy meye abunyi ne?"
Mummy tace "Nima ban sani ba, amma Bukar yace mu saurare shi, ze samo mafita"
"to Ubangiji Allah yasa mafitar me ɓullewa ce, amma nikaina abun ya tsoratani"
Ramlah tace "ki kwantar da hankalinki Mummy, Insha Allah bakomai, dan ni kaina a tsure nake, kin san na taɓa zuwa nace ya samomin Password ɗin Widad, Amma tunda Alhaji Bukar yace akwai mafita, to tabbas akwaita, ki kwantar da hankalinki"
Mummy ta jinjina kai, Anwar ne yai sallama a ɗakin, ya kalli fuskokinsu yace "Ya dai na ganku kunyi jugum jugum, akwai matsala ne?"
Ramlah tace "babu wata matsala"
"Ya zakice babu matsala bayan fuskokinku sun nuna hakan?"
A fusace Mummy tace 'Kai fita ka barmin ɗaki, uban bin ƙwaƙwƙwafi, ance maka bakomai amma ka dage "
" Allah ya baki haƙuri " daga nan yai waje abunsa.
Da Asuba tayi Yusuf ya dawo daga gurin karatu, lokacin gari yayi haske ya ɗumama musu shinkafa sukaci da safe.
Ya miƙe ze fara shirin fita, ta kalle shi tace " naga kana shiri, ina zakane? "
" Yau ranar kasuwa fa, zanje nema"
Widad tace "ba inda zaka se ciwon nan ya warke"
"Meyasa?"
"Se kaje wani abun ya kuma faruwa? Ka bari ƙafar ta warke kana ɗingisawa da ƙyar kana maganar zaka fita"
Yusuf yace "Nifa lafiyata ƙalau, kawai dai..
" ba wani kawai, idan kace seka fita kana tafiya, nima zan ɗauki hijjabina in tafi "
" ki tafi kije ina? "
" duk inda Allah yayi "
Yusuf yace " to shikenan, naji na fasa fita"
Widad tace "karma ka fasa ɗin"
Ta ɗau bokiti tayi waje, suka gaisa da Gwaggo, Gwaggo tace "Amarya ɗan miƙomin robar can me ruwan ɗorawa"
Widad ta tsaya tana waige waige, tace "tana ina robar take?"
Gwaggo tace "gata can a bayanki"
Widad tace "to ai ban san meye ɗuruwar ba"
Gwaggo tayi murmushi tace "ruwan ɗorawa nace, gata can a gefen randa"
Widad ta ɗakko robar, tace "Gwaggo meye ruwan ɗaurawa"?
"Kalar robar ce ruwan ɗorawa"
Widad tace "Ok Yellow kenan zaki ce Gwaggo"
Gwaggo tace "Ahh mu nan haka muke cewa"
"Gwaggo dan Allah meye faskare?"
Hari tace "na shiga uku da wannan lamari, waike komai baki sani ba? Kwarankwatsa ko a birni an san waɗan nan abubuwan, amma kiyi ta rainawa mutane hankali"
Kamar basuji me tace ba, Gwaggo tace "Saran itace shine Faskare"
Widad tace "a dinga saran bishiya?"
"Eh a sassara bishiya, a farfasa yadda aza'a iyayin girki dashi"
Widad ta ɗanyi shiru, sannan ta jinjina kai, ta kuma cewa "Gwaggo wai meyasa naga ruwanku seya dinga yin kala, ni wanda Yoseef yake ɗebo mana yafi wannan kyau sosai"
Gwaggo tace "ban hana kiran sunansa kai tsaye ba"
Widad ta toshe baki tana dariya, tace "yi haƙuri na manta ne, wanda mijina yake ɗebowa"
Hari tace "hmmhmm wa yaga kwaɗo, ba kunya wai mijinta"
Widad tace "to da mijinmu ne nida ke?"
Hari tace "A'a ni Allah ya tsareni, mijinki ne ke kaɗai"
Gwaggo ta girgiza kai tace "Inda Yusufa yake ɗebo muku ruwane, ba giri ɗaya da namu ba, shi birtsatse yake zuwa ya ɗebo muku, kuma tafiyar da yake a ƙasa kafin yaje gurin ta ɓaci, da nisa sosai ita kaɗai ce burtsatse a garin nan"
"Gwaggo dan Allah meye burtsatsi?".
"Ruwan famfo, amma na tuƙa tuƙa"
"Nasan dai famfo, amma ban san meye tuƙa tuƙa ba"
Shikan sa Yusuf da yake ɗaki yana jiyosu, seda yace "Allah yasa kar Gwaggo ta gaji da wannan tambayoyin na Widad.
Allah yasa aka zuba mata ruwan ɗumi ta tafi wankanta.
Bayan ta fito daga wankanne tana shiga ɗaki, ta tarar Yusuf ya tattara kayansu na wanki ya ɗaure a guri ɗaya.
Ta kalle shi tace " wannan fa?"
"wanki zanje inyi mana"
"A ina?" ta tambayeshi
"Can wani gurine bakin ruwa, nake wankin, jira nake in ƙarasa yi miki girkin rana in tafi in wanko kayan"
Widad ta ajiye bokitin, ta ƙarasa tace "gaskiya zan bika"
"Ki bini ina?"
"Gurin wankin mana"
"No kiyi zamanki a gida inje in dawo, gurin ba kowa kuma bakin ruwane"
"gaskiya ban yadda ba, tunda muka zo garin nam ban taɓa fita ba, gaskiya ka tafi dani, nima base in koyi yadda akeyi ba im dinga yi mana"
"bana so Kisha wahala ne, ki bari inje inyi indai fitane, zam fita dake mu zaga gari"
A hasale tace "bana so tunda ba zaka dani ba shikenan"
Ya fuskanci haushi taji, dan haka ya ƙarasa inda take yace "Meyasa kike da saurin Fushi ne Masoyiyya, shikenan zamuje tare, kinsan bana son ɓacin ranki"
Tura baki tayi taƙi magana, ya juyota ta fuskance shi yace "smile mana habibty"
Tura baki ta sake yi tace "baza ai smiling ɗinba"
"In kina tura bakin nan i just feel like to kiss you"
Ɗago ido tayi da sauri cikin Shagwaɓa tace "kaga ka bari bana so"
"to yi min murmushi in ƙyaleki"
"to ai murmushin ne be zoba"
Yadda tayi maganar ne ta bashi dariya, yace "shikenan, ina bim bashi se anmin murmushin nan. To ko in ta yaki sa kayan?"
Da sauri tace "A'a bana so wallahi" tai maganar tsoro ƙarara a idonta.
Murmushi yayi, ya juya ya cigaba da haɗa kayan, seda ya kammala yayi musu girki, sannan yai waje.
Ta tsaya ta saka hijjabinta, da silifas ɗinta ɗan madina ta fito, Hindu taga Widad ta sha hijjabi, dan bata saba gani ba idan ba salla Widad zata yi ba sunyi hannun riga da hijnabi, Hindu tace "Amarya ina zuwa haka?"
"Fita zamuyi nida Yoseef, naga kamar Gwaggo wanka take inta fito ki gayamata"
Hindu tace "shikenan zan gaya mata insha Allah, sekun dawo yau zanyi wunin kaɗaici"
Widad tace "Allah sarki Hindu, nima zanyi kewarki, semun dawo"
"Shikenan Allah yasa karku daɗe"
Widad tayi hanyar fita, sedai tana zuwa ta tarar an zubawa Manyan ragunan megari harawa a hanyar fita wajen, gasu da manya manyan ƙaho a murɗe, sun kai su goma sha, suna ture ture suna cin Abinci.
Ƙura musu Ido Widad tayi, tana tunanin ta ina zata wuce.
Jin shiru Widad bata fito ba yasa Yusuf dawowa yaga ko lafiya.
Ya tarar da ita a tsaye tana kallon raguna, Yusuf yace "Madam ke nake jira fa, kim tsaya kallon raguna"
"Nifa tsoro nakeji"
"Tsoron mekuma?"
"kar inzo zan wuce su dakeni da wannan ƙahon nasu"
Yusuf ya girgiza kai yace "yanzu ragunan ne yasa kika tsaya kika kasa fitowa? Duk soyayyarki da dabbobin kuma yanzu tsoronsu kike ji?"
"To wai so kake, su dakeni da wannan ƙahon suji min ciwo, ko ance maka ni 'yar sanda ce?"
Yusuf yace "iyee au abun hadda baƙar magana, ai shikenan"
Ya ratso cikin ragunan ze kama hannunta su wuce, amma taƙi wai sedai ya koresu ta wuce, amma bazata shiga ta tsakaninsu ba.
Cak ya ɗagata ya ratsa ya wuce, sannan ya ajiyeta, hakan yayi dai dai da fitowar Hari taga abunda ya faru, ai take ta fara salati
"la'ilahaillalahu, yau nake ganin gardiyar lukutar baɗala a tsakar rana, wane irin abune haka goɗoɗo ba fasali bakomai?"
Seda Yusuf ya ƙunshe baki yana dariya, Widad har tayi shirin ramawa, ya janyo hannunta sukayi waje.
"Alhaji Haruna, nayi muku duk iya ƙoƙarin da zanyi muku, duk ayyukam da kuka sani nayi muku, yakamata ku zama masu cika Alƙawari fa"
"Kai Saleh wai baka san a halinda muke ciki bane? Wai ashe yaron da aka sace 'yar gidan Daula dashi, wai ashe ɗan sanda ne"
Hantar cikin Saleh ta kaɗa amma ya basar yace "kamar ya ɗan sanda, direba dai"
"to ɗan sanda ne, anyi bincike an tabattar mana da jami'in tsarone ma farin kaya"
Saleh yace "lallai biri yayi kama da mutum, amma yaya aka yi haka ta kasance?"
"Kai zamu tambaya, tunda kai muka wakilta a wannan ɓangaren"
Saleh yace "to ai nima ban san komai ba, ban san shi aka saka ba sam, amma gaskiya ya iya yaudara, shine yazo a matsayin direba"
Alhaji Haruna yace "to gashi nan dai, kuma bincike ya tabattar kamar maye yake akan aikin sa, idan ya saka case a gaba se yaga bayansa, kuma bimcike ya nuna ya fara gano Alhaji Musa, sannan Hajiya Halima tayi ɓarin zance a gabansa"
Saleh ya dafe kai yace "to yanzu meye abunyi?"
Alhaji Haruna yace "abunyi kam a yanzu babu, Alhaji Bukar yace mu saurare shi, ze nemo mana mafita"
Saleh yace "lallai abubuwa sun fara lalacewa, ya zama dole a hanzarta samo mafita, tun kafin su dawo garin nan in bahaka labari fa ze canza"
Haruna yace "gaskiya ne maganar ka, muna nan dai muna sauraren Bukar"
Saleh yace "Amma ya maganar ɗan uwana kuwa? Naga bakwa wani abu akan Alƙawarinmu fa"
"kai dalla ana ta kai wake ta kaya? Muna ruwa tsundum muna tsakiyar masifa kana maganar wani mutum da a yanzu bashi da wani amfani"
"Alhaji Haruna, ɗan uwan nawane bashi da Amfani, dama haka mukayi daku?"
"to ba dole ince bashi da amfani ba, tunda a yanzu ba ta tashi muke ba, muna tsakiyar masifa kana wani zance daban, ni kaga tafiyata, ina da appointment ƙarfe biyu da rabi"
Ya tashi ya bar masa falon, Saleh ya jinjina kai yace "lallai ashe kuwa an yanka, kuma zata tashi"
Suna tafe suna hira, tana yaba kyan garin dukda rashin ababan more rayuwar dake ƙauyen.
Widad ta kalli Yusuf tace "ya naga kana ɗingisawa ne, ko in goyaka ne?"
Yusuf yay murmushi yace "wai zaki goyani, kamar ba kece kika kasa wuce raguna ba ɗazu"
"to ba tsoro nakeji ba, so kake sumin illa?"
"wane ni ince wani abu ya samu Gimbiyata, ai bam san idan zan sa raina ba"
"Eh ai ka iya saurin kare kanka"
Suka cigaba da tafiya, Widad tana ta tambaye tambaye, wata tambayar idan tayi sekace wannan tsabar rainin hankali ne, nan ko harga Allah abubuwa da yawa bata sani ba, can tace "Allah sarki, wai se gani a ruɓabiyar motar ice aka kawoni garin nan, Allah sarki rayuwa"
Yusuf yace "hakane, Allah yasa hakan ya zama silar alkhairi"
"Mhmm Ameen, amma naji jiki ranar, ji nayi kamar zan bar duniya ba dan da kai ba da ban san meze faru dani ba, Nasan idan muka koma gida kana da tukuici a gurin Daddy, ka kula da amanarsa"
Yusuf yayi murmushi yace "ni bana buƙatar komai a gurin Daddy a matsayin tukuici se abu ɗaya"
"Meye abu ɗayan?"
"Ya barmin Widad in cigaba da rayuwa da ita, har ƙarshen rayuwata
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
60_61
Kallonsa ta ɗanyi tace "ina fatan Allah ya rabaka da son abunda ba zaka samu ba, na gaya maka babu Aure a tsarin rayuwata, bazan ji daɗi ba ace wani abu ya sameka saboda ni ba, amma ina fatan zumuncinmu ya ɗore nida kai"
Yusuf yayi Ajiyar zuciya yace "naga jarrabawa daban daban a rayuwata, ciki harda Jarrabawa a kan Soyayya, sam bani da sa'a a wannan ɓangaren, dukda tarin gargaɗi da kashedin da kikemin akan Sonki da nake, nakasa jin zan iya dena sonki, a kowane lokaci ina sake jin sonki a raina"
Shiru tayi suka cigaba da tafiya, ba tare da sun sake cewa komai ba.
Ta kalli Yusuf tace "ko mu tsaya ka huta ne? Saboda ƙafarka"
Yusuf yayi murmushin yaƙe yace "waye yace miki nagaji ne? Ko ance miki nima ragone irinki?"
"Nice ma raguwar?"
"Eh kece, me tsoron rago da spider ba"
Dariya tayi tace "kaikam baka mantuwa ko? Saura mu koma gida kace ga abunda nayi ka jamin raini"
"Ni na isa in faɗi abunda Gimbiya tayi, ai wannan sirrine kuma tarihi ne me matuƙar girman gaske daze zauna a zukatanmu nida ke"
Widad tai murmushi tace "gaskiya ne, wannan rayuwar ba zata taɓa gogewa a zuciyata ba"
Yusuf yace "dukda ragoncin nan naki, akwai inda na jinjina miki Gimbiya, ban taɓa tunanin samun jarumar mace kamarki ba, yadda kika sa hannu kika rama dukan da kidnappers ɗin nan sukayi miki, na jinjina miki ta wannan fannin"
Murmushi tayi tace "hakan ya samo asaline tun daga ƙuruciya ta, Allah Sarki, Allah ya jiƙan Ammi na da Baban Yoseef"
Da sauri ya kalle ta yace "Kaman Babana kikayi wa Addu'a"
Tace "Eh iyayenmu da muka rasa nayiwa Addu'a, ko baka so"
"Ni na isa imce bana so, Ameen ya Allah, ubangiji Allah yayi musu Rahama"
"Ameen"
Sunyi tafiya me nisa sannan suka iso rafin, ba kowa a gurin, gurin shiru se kukan tsintsaye, da kaɗawar bishiyu.
Widad tace "Wow masha Allah, ɗan uwa gurin nan yayi kyau sosai"
"enjoy yourself"
Yusuf ya shiga aikin yi musu wanki, yayin da Widad keta kalle Kallen tsuntsaye.
"Ɗan uwa da ruwan nan yana da kyau sosai, da swimming zanyi"
"kin iya ruwane?"
"Taɓ sosai ma, na iya ruwa sosai fa, ina shiga"
"Ai da alama kina da rashin ji, ba wanda ze gane hakan se wanda yake zaune dake"
"Wanda yake zaune da ni ɗin ma ba kowa ne ze gane hakan ba, kaima ban san yadda akayi na sake da kai haka ba, haka kurum naji kamar in yadda da kai"
"Aikin gama ya gama ai, kinma yarda dani ni ɗin"
Cigaba tayi da wasanninta a gurin, tayi nan tayi can ta Leƙa nan ta leƙa can, Yusuf yana ta wanki har ya kammala, yai shanya ya zura ƙafafinsa a cikin ruwan, kusa da Yusuf tazo zauna itama ta zura ƙafafunta a ruwan tana kallonsa.
"Meye kuma kike kallona?"
"Me zan kalla?"
"Muni mana" ya bata amsa
Murmushi tayi tace "kaine mummunan? Ai baka da muni sam"
Murmushi kawai yayi, yana jefa dutse a cikin ruwan.
Widad tace "kasan wani abu?"
"A'a sekin faɗa"
"Ban taɓa sanin a duniya akwai mutane nagari kamarka ba, da ina yiwa talakawa kallon mayun kuɗi, maciya amana, amma gaba ɗaya you proves me wrong"
Yusuf yace "dama bekamata ka yankewa mutane hukunci da laifin tsirari daga cikinsu ba, duk lalacewar zamani akwai na kirki"
Widad tace "Aikama nagani, dan yadda nake treating ɗinka a gida ban taɓa zaton zaka iya taimakona ba, nayi mamakin ganin hawaye a idonka lokacin da ni kaina na yanke tsammani da cigaba da rayuwa"
Ta ƙarasa maganar tana kwanciya a jikin Yusuf.
"Habibty, a wannan lokacin da kin mutu ban san ya zanyi ba, Nagode Allah da ya nunamin na Aure ki, dukda ba kya sona"
Shiru tayi ba tace komai ba, can Yusuf yace "Widad, yanzu idan na mutu zaki damu?"
Tsaki tayi tace "wace irin tambaya ce wannan?"
"Tambayarki kawai nayi"
"To wannan wace irin tambaya ce mara amfani, kawai muna hira ka kama wannan zancen ni bana so"
Ɗagota Yusuf yayi ya kalli idonta, ƙwallace kwance a idonta, se wani tura baki take, murmushi yayi ya maida ita jikinsa ya kwantar da ita, ya shiga shafa bayanta.
Ɗagowa tayi ta kalle shi tace "Ɗan uwa"
Yusuf yace "Yaushe na zama ɗan uwane, naji kin canza min suna'
" Gwaggo ta hanani faɗar sunan ka, kuma kaga ni bani da ɗan uwa, se gaka ka bani jini, kaga mun zama 'yan uwa tunda an samun jininka, mun zama' yan uwa kenan"
Dariya Yusuf yayi yace "wannan philosophy ɗinfa,? Lallai kam shikenan nima nayi ƙanwa tunda bani da ƙanwa mace"
Ta gyara kwanciyarta a jikinsa tace "Yoseef, idan muka koma gida zaka dawo gidanmu ka zauna kaida ummanka?"
"Ai muma muna gida" ya bata amsa
"Dan Allah ka dawo gidanmu, nasan bazaka cigaba da tuƙani a mota ba, nasan maybe ma in koma ƙasar waje, amma dan Allah ka dawo gidanmu kaji"
Girgiza mata kai yayi yace "so kike Mamansu Amal ta dinga wulaƙanta Ummana? Kuma zaman me zanzo inyi a gidanku, bayan bamu da wata alaƙa, kafin nan fa mun rabu"
"Dan mun rabu shine zaka ce bazaka dawo gidanmu ba, sannan idan na koma gida dole ta bar mana gida"
Yusuf yace "meyasa?"
"Saboda wani dalili me girman gaske, amma yanzu ba wannan maganar muke ba, dan Allah idan mun koma gida ka dawo gidanmu da zama,"
"Nida bakya sona, me zan zo gidanku inyi? Idan dai har ina ganinki zan cigaba da sonki ne, kuma ni bakya sona"
"Nifa ba tsanarka nayi ba, kawai ni bana son soyayya ne, ban santa ba kuma ban iya ba, dan bata birgeni, ƙarya ce da tarin damuwa a cikinta, amma ni bana son ko mun koma gida kayi nesa dani, na saba da kai sosai, kana iya haƙuri da dukkanin halayena, kuma kai garkuwa ne a gareni, dan Allah Yoseef ka yadda kaji ɗan uwa"
Yusuf kam murmushi yayi, a ransa yace 'sarkin taurin kai, kina sona amma kina garani'
A fili ya maze yace "Idan muka koma gidanku ace munje kwaɗayi, ni nafison in zauna a gidanmu nida Ummana"
"dan Allah, ba wanda zece muku haka, Dan Allah Yoseef kaji"
Juyowa yayi yana kallonta, har cikin ranta take maganar.
Wani abune ya dinga fizgar Yusuf game da Widad, yana jin wani irin farinciki a tare da shi, abunda bata son dai yayi mata, sedai wannan karon bata hana shi ba, sema biye masa da tayi.
A hankali ya cire bakinsa daga nata ya riƙe hannunta yace "ina sonki Habibty"
Ajiyar zuciya tayi ba tace masa komai ba.
Kawai ya tsaya ya zuba mata ido, a hankali tace "yakamata muje muci Abinci"
Yusuf ya cikata, suka miƙe ya shimfiɗa musu abu suka zauna, ya buɗe shinkafa da wake, da manja ya ɗakko tumatir da gurji ya yayyanka, ya juya suka fara ci.
Suna ci yana kallon Widad, ta kwantar da hankalinta, ta rugumi ƙaddarar rayuwarta, da farkom zuwansu ne se yayi fama kafin taci Abincin, amma yanzu hankali kwance ta dinga cin Abincinta.
"Wai meye kake kallona haka?"
"Gani nayi kina loma fiye da tawa, zaki cinye Abincin ki barni"
"Cigaba da kallona, cinyewa zan in barka"
Ya dinga jin farinciki, ganin yadda Widad ɗinsa ke nishaɗi tana fara'a, saɓanin Widad ɗin daya sani a baya, me shegen haɗe ran tsiya da koke koke, mara afuwa da tausayi.
Juyawa yayi gefensa ya tsinko wata 'yar ciwa, ya miƙo mata yana cewa
"If you ask me to be your king, i will turn around and said, you mean to tell me that I can have you when ever I want, i can tell you that I love you when you love me too, no more waiting for ever our love...
Kwashewa da dariya Widad tayi tace " Ai ba haka ake waƙar ba, kuma flower ake bayarwa, amma ni ka bani ciyawa sekace wata Akuya"
Yusuf yayi murmushi yace "A yanzu bani da wani abu da zan baki ai, shiyasa na baki wannan instead of flower"
Hannu tasa ta karɓa, ta kalli Yusuf tana murmushi.
Saleh ne a gigice ya shiga babban Ofishin dake cikin harabar gurin, Suleiman ne zaune yana danna system ɗinsa, Saleh ya shigo da sallama.
Suleiman ya ɗago tare da yin murmushi yace "Masha Allah, yau kaine a ofishin nawa? Kwana biyu"
Saleh ya miƙa masa hannu suka gaisa, yace "Suleiman ya aikin naku?"
"Alhamdilillah, ya Yusuf fatan yana lafiya?"
Saleh yace "lafiya ƙalau, yana gaisheku ina sa ran zuwa gurin mahaifiyarsa, im sake kwantar mata da hankali tare da tabattar mata yana cikin ƙoshin lafiya"
Suleiman ya gyara zama yace "hakane, hakam abune me kyau nima da week ends ɗin nan, naje gidan sedai har yanzu ta kasa kwantar da hankali ta, akwai buƙatar ka ɗakko mata muryarsa, kokuma ka haɗasu a waya su gaisa"
Saleh yace "No baze yuwu ba, ai bama zuwa garin nan da waya, kai mutanen nan fa sun shallake tunanin ka, nima ina lura da duka abunda nake yi, bana shiga da waya, haka nake zuwa in fito"
"to ubangiji Allah ya kuɓutar dasu, ina mamakin yadda abubuwan suke tafiya, kullum sake taɓarɓarewa sukeyi"
Saleh yayi ajiyar zuciya yace "yanzun ma matsala ce gagaruma ta taso"
Suleiman ya tattara hankalinsa yace
"wace irin matsala kuma?"
"mutanen nan sun gano waye Yusuf, kuma suna shirin ɗaukar mataki akan hakan?"
Suleiman yace "ya akayi suka sani?"
Saleh yace "niba wannan ba, babban abunda ya dameni shine, rashin sanin wani irin mataki zasu ɗauka akansa, gashi kuma yana can yana cikin zulumi akan ta yaya ze sanar da Widad gaskiyar waye shi, kasanta bata afuwa bata yafiya ga duka wanda yayi mata ƙarya, muddin suka dawo garin nan sannan ta gane waye shi akwai matsala "
Suleiman yace " ai tasan waye shi? "
" kamar yaya? Sannan ta yaya?"
Suleiman yace '" dukda gargaɗina da tayimin, amma bari in gaya maka yadda akayi tasan waye shi, wataran da yamma na kammala abunda nake zan bar office ɗin nan, kawai sega wata mota ta shigo gurin nan a guje, kamar zata tashi sama,
ma' aikatanmu sukayi kanta don son ganin wane mara ɗa'ar ne haka? Ko a jikin me tuƙin, Ta buɗe motar ta fito, wata matashiyar budurwa ce jikinta sanye da abaya, ta saka face mask, sannan ta rufe fuskarta da glass.
Kai tsaye inda nake ta shiga tunkarowa, da ma'aikatanmu sunyi kanta zasu hanata ƙarasowa, nace su barta ta ƙaraso.
Ko kallonsu batayi ba tazo inda nake ta tsaya ta kalleni tace "kaine Suleiman?"
Nace mata "Eh nine"
Tace "ina son muyi maganane"
Nace mata shikenan, nai mata jagora har office ɗina, muka shiga muka zauna, ta kalleni ta cire glashin fuskarta da face mask tace "kasanni?"
"Nace mata a'a"
Tace "Amma kasan Nasir Daula?"
Nace "ai duk Nigeria babu wanda be sanshi ba"
tace "sunana Widad Nasir Daula, nazo me zan maka wasu tambayoyi, kuma idan ka amsamin ba dai dai ba, ka shirya karɓar abunda ze biyo baya, bana sassauci ga mutane maƙaryata, waye Yusuf?"
Suleiman yayi ajiyar zuciya yace "wane Yusuf ɗin?"
"Direbana" ta bashi amsa
Suleiman yace "Yusuf jami'inmun ne, ɗan sanda ne na farin kaya" Suleiman ya bata amsa
"danme zaku turoshi? Me yasa kuka turoshi,? wato an haɗa kai daku a cuceni"
Suleiman yace "Yusuf bashi da laifi, jajirtaccen ma'aikacine me kishin ƙasa, umarni aka bamu daga sama akan cewar, a baki kariya sannan kuma ayi bincike akan wanda suke bibiyar rayuwar ki, amma bayan haka Yusuf be san komai ba"
Cikin isa da izza tace "akan me? Sannan kuma waye ya bada umarnin hakan? Ko kuma ni nace ina buƙatar hakanne? An haɗa kai daku za'a cutar dani, in ba hakaba meyasa Yusuf yasa hannu akan takardar zeyi aiki dani, dukda na gaya masa hakan tamkar saka hannu akan kwangilar mutuwarsane? Na kama Yusuf da bindiga"
Tun anan Suleiman ya jinjinawa Yusuf, ya yabawa ƙoƙarin sa na jure zama tare da yin aiki da Widad, saboda yadda take magana cike da izza da isa.
Suleiman yace " kamar yadda na gaya miki, Yusuf jajirtaccen ɗan sandane, kuma ba abun mamaki bane samun ɗan sanda da bindiga, sannan Yusuf baza'a taɓa bashi aiki ya dawo dashi yace ya karaya ko baze iyaba, amma sam bashi da laifi, kuma da farko bashi mukayi niyyar bawa aikinba, abokin aikinsane yace a bashi saboda jajircewarsa da haƙurinsa"
Ajiyar zuciya Widad tayi tana huci, inda Allah ya temaki Sulaiman gaskiyar data buƙata ita yake gaya mata, ta kalle shi tace "Ina buƙatar sanin waye yasa a dinga bin diddigi na?"
Suleiman yace "kamar yadda na gaya miki ne, ban saniba nima umarni aka bani daga sama, ban san komai akai ba"
Widad tace "shikenan, ni zanje in bincika da kaina, amma zan maka gargaɗi da jan kunne, Yusuf be san na ganshi da bindiga ba, kada ka kuskura Yusuf yasan nasan waye shi, idan har ka gaya masa nasan waye shi zan gane, and you know what am capable of doing"
Suleiman yace "karki damu, Insha Allah baze sani ba, bazan gaya masa ba"
Tace "and Mark you, bana son kowa yasan da nice nazo gurin nan, and zan cigaba da bibiyarka, duk lokacin da Yusuf yayi misbehaving ko wani abu na yunƙurin cin amana ta, to dasa hannunka a ciki"
Suleiman yace "ina me tabattar miki da babu abunda zeyi na cin amanarki"
Ta miƙe a gadarance, ta maida face mask ɗinta, ta saka glass ɗinta ta fito, sedai tana fitowa Abbas ya kawo kai yana shigowa, ta tsaya ta ƙura masa ido, harya shige wani office, sam Abbas be lura da kallon da take masa ba, ba tace komai ba tayi gaba da sauri ta hau motarta ta bar gurin.
Bayan wasu 'yan kwanaki da yin hakan, Widad ta kira Suleiman tace tana son ya gayamata full name na Abbas da rank ɗinsa, amma Suleiman yace hakan ya saɓa da ƙa' idar aikinsu, sedai ta gaya masa meyasa take neman hakan, bata kuma bi takansa ba bayan kwana uku, aka kawo transfer later na Abbas aka maye gurbinsa da Yusuf.
Saleh ya jinjina kai yace "wato duk inda mutum yake tunanin hatsabibancin yarinyar nan ta wuce haka, yana cam yana ta zullumi akan yadda ze gayamata, ashe tuni ta sani"
Sulaiman yace "tabbas tasan waye Yusuf, kallonsa kawai take sannan kamar yadda naimata Alƙawari ban gaya masa ba"
Saleh yace "Allah sarki, ni gaba ɗaya tausayi yake bani wallahi, bejiba be gani ba yana ta ɗawainiya da yarinyar ta bata san kimar mutane ba, duk naga ta rage wannan zafin kan nata, ta kwantar da mai tana rayuwa a ƙauyen da babu wuta, babu ruwa babu abubuwan more rayuwa, abun gaanin ban tausayi"
Suleiman yace "Allah sarki Yusuf, samun mutum me irin zuciyarsa se an tona, ina masa fatan ubangiji Allah ya kuɓutaf dashi, daga sharrin Azzaluman nan"
Saleh yace "Ameen ya Allah, amma tabbas Yusuf yana cikin jarrabawa, dan ina tunanin matakin da zasu ɗauka akansa, basu da imani sam"
Suleiman yace "Allah ya fisu kam, amma indai batun sadaukarwa ne, to tabbas Yusuf yayita"
Haka suka cigaba da tattaunawa a tsakanin su.
Se bayan la'asar, lokacin kayansu sun bushe sannan Yusuf ya tattaresu ya ninke, suka kamo hanyar gida, suna tafe suna hira gwanin ban sha'awa, Widad nata takura masa da tambayoyi dan duk abunda ta gani bata sani ba seta tambaya.
Suna zuwa gida Gwaggo tai murmushi tace "Amarya yau gidan nan ba daɗi ba kya nan, duk naji ba daɗi"
Widad tai murmushi tace "nima haka naji ba daɗi yau Mama"
Hindu tace "wallahi kuwa Gwaggo, gaba ɗaya yau gidan se a hankali ba daɗi da bakya nan"
Hari tace "Nikam naji daɗi, bakin mutane shiru yau ba neman magana"
'
Widad tace "in mutane na magana ki dena saka baki, danke ba mutum bace"
Gwaggo tace "Amarya yau wake muka dafa, ban sani ba ko zaki iyaci, dan haka na dama miki kunu gashi can da zafinsa"
Widad tace "wayyo Allah Mamana ta kaina, nagode sosai Allah yasaka da alkhairi, wakenma duk zan iyaci nagode sosai Mama"
Gwaggo tace "Babu godiya a tsakaninmu ai"
Yusuf kam bayan sun gama gaisawa, ɗakinsu ya wuce, ya bar Widad tana cigaba da neman maganarta.
Hari tana ta ƙulla gyaɗarta ta siyarwa, Widad tazo ta cika hannu ta zuba a hijjabi tayi ɗaki, Hari ta buɗe baki tace "Wudas yaseen sekin biyani kuɗin gyaɗar nan"
Gwaggo tace "yi haƙuri, zan baki kuɗin"
Seda tayi me isarta sannan ta koma ɗakin, Yusuf tun yana mamakin halin Widad har ya dena, ta kwaso kwanukan wanke wanke tayi, gaba ɗaya yau wani irin nishaɗi take ji, taji daɗin fitar da suka yi sosai, wani irin farinciki ya dinga ratsata.
Ta karɓo musu Abincin gurin Gwaggo, suka zauna suka ci, bayan sun gama ne ta ɗanyi shiru sannan tace "Naji daɗin fitar nan sosai Yoseef, ban taɓa tunanin ana samun farinciki haka ba koda babu dukiya"
Yusuf yace "aishi farinciki da jin daɗi base ka tara dukiya ba, indai zakayi tawakkali da yadda Allah ya ajiyeka, zakayi rayuwarka cikin farin ciki da jin daɗi, kuma har kafi me Dukiya walwala ma".
Widad tace "ƙwarai kuwa yau na gani, rabon da inyi farinciki haka tun Ammi na nada rai, shekara goma baya kenan"
Yusuf yace "kina nufin duk tsawon wannan shekarun, bakya farinciki?"
"tun bayan rasuwar Ammi, ban kuma samun farinciki haka ba, babu club ɗin da bana zuwa a waje, dan inyi nishaɗi, nice club ɗim wrestling stadiums na ball da sauran wasanni, amma babu sauyi, na kanji nishaɗi ne kawai idan nai wasan doki, kona kasance da dabbobi kuma idan ina Tare da Alhaji Nasir Daula "
'yar Wulaƙanci yau kuma saunan baban nata take faɗa gatsal"
Ta cigaba da cewa "nasan Daddy zeyi murna sosai, idan ya ganni cikin walwala haka, danya fidda ran faruwar hakan a rayuwata" ta ƙarasa maganar muryarta na rawa alamun zata yi kuka.
Rungumota Yusuf yayi yace "haba Jarumata, kuma Gimbiya ta, karkiyi kuka please kiyi haƙuri kinji babyna, nifa jarumtar nan taki burgeni take yi, dan haka idan muka koma gida, zan saki a aikin ɗan sanda kema"
Kwashewa tayi da dariya, tace 'kai dai kaje kaita aikin ɗan sandan, nikam a kai kasuwa "
" Zaki iya kama' yan fashi fa da ɓarayi da wannan dakakkiyar zuciyar taki Baby"
Shiru ta ɗanyi tace "da wanda suka kashemin Ammi ma ko?"
Yusuf yace "am just kidding, idan wanda suka kashe mahaifiyarki ne, Insha Allah ni zan ɗau nauyin yin wannan binciken"
Girgiza masa kai tayi tace "this the most dangerous case, don't take the risk of it, ni suke bibiya suke son ganin bayana, dan haka koni ko su, karka sa kanka a ciki, a yanzu ma kalli yadda kake wahala"
Yusuf yace "Amma suwaye suka kashe ta, kuma meyasa? '
Widad tace " nima ban sani ba"
Yusuf yace "i have to know even a little bit of your life"
"bazan faɗa ba, ban yadda da kai ba" tai maganar tana dariya.
Yusuf yace "ai yadda ta ƙare, tunda muka zama abu ɗaya, har muka kasance a inuwa ɗaya"
Hararsa tayi tace "wace irin inuwa ɗaya"
"Inuwar Aure mana Baby na, kuma gashi.... Sekuma yayi shiru
Widad tace " Kuma gashi me? Ƙarasa mana, kai ko kunyata na baka ji ko? Allah ya shiryeka, ni cikani"
Ƙara rungumeta yayi yana murmushi yace "Kunyarwa zanji? Mutum da matarsa"
"Matar ƙauye ba, dan iya nan ne, kafin mu koma gida zamu rabu'
Murmushi kawai Yusuf yayi bece mata komai ba, a hankali yace " ki gayamin mana "
" wai mai meyasa ka damu se kaji tarihin rayuwata? Ko nima binciken ake a kaina? "
Yusuf yayi dariya yace " wane ni?"
"idan kana son in baka labarin, kwanta in kwanta akan ƙirjinka"
Yusuf yace "dan dai wannan, ai shi yafi komai sauƙi"
Yusuf ya kwanta, ta kalle shi tace "kuma wallahi idan kamin wani abu, se munyi faɗa na gaya maka"
Yusuf yace "idan nai miki me?"
"Bansani ba"
"Allah ya baki haƙuri, niba abunda zanyi miki"
A hankali ta kwanta akan ƙirjinsa, tayi shiru na wani ɗan lokaci
WACECE WIDAD NASIR DAULA.....
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
60_61
Kallonsa ta ɗanyi tace "ina fatan Allah ya rabaka da son abunda ba zaka samu ba, na gaya maka babu Aure a tsarin rayuwata, bazan ji daɗi ba ace wani abu ya sameka saboda ni ba, amma ina fatan zumuncinmu ya ɗore nida kai"
Yusuf yayi Ajiyar zuciya yace "naga jarrabawa daban daban a rayuwata, ciki harda Jarrabawa a kan Soyayya, sam bani da sa'a a wannan ɓangaren, dukda tarin gargaɗi da kashedin da kikemin akan Sonki da nake, nakasa jin zan iya dena sonki, a kowane lokaci ina sake jin sonki a raina"
Shiru tayi suka cigaba da tafiya, ba tare da sun sake cewa komai ba.
Ta kalli Yusuf tace "ko mu tsaya ka huta ne? Saboda ƙafarka"
Yusuf yayi murmushin yaƙe yace "waye yace miki nagaji ne? Ko ance miki nima ragone irinki?"
"Nice ma raguwar?"
"Eh kece, me tsoron rago da spider ba"
Dariya tayi tace "kaikam baka mantuwa ko? Saura mu koma gida kace ga abunda nayi ka jamin raini"
"Ni na isa in faɗi abunda Gimbiya tayi, ai wannan sirrine kuma tarihi ne me matuƙar girman gaske daze zauna a zukatanmu nida ke"
Widad tai murmushi tace "gaskiya ne, wannan rayuwar ba zata taɓa gogewa a zuciyata ba"
Yusuf yace "dukda ragoncin nan naki, akwai inda na jinjina miki Gimbiya, ban taɓa tunanin samun jarumar mace kamarki ba, yadda kika sa hannu kika rama dukan da kidnappers ɗin nan sukayi miki, na jinjina miki ta wannan fannin"
Murmushi tayi tace "hakan ya samo asaline tun daga ƙuruciya ta, Allah Sarki, Allah ya jiƙan Ammi na da Baban Yoseef"
Da sauri ya kalle ta yace "Kaman Babana kikayi wa Addu'a"
Tace "Eh iyayenmu da muka rasa nayiwa Addu'a, ko baka so"
"Ni na isa imce bana so, Ameen ya Allah, ubangiji Allah yayi musu Rahama"
"Ameen"
Sunyi tafiya me nisa sannan suka iso rafin, ba kowa a gurin, gurin shiru se kukan tsintsaye, da kaɗawar bishiyu.
Widad tace "Wow masha Allah, ɗan uwa gurin nan yayi kyau sosai"
"enjoy yourself"
Yusuf ya shiga aikin yi musu wanki, yayin da Widad keta kalle Kallen tsuntsaye.
"Ɗan uwa da ruwan nan yana da kyau sosai, da swimming zanyi"
"kin iya ruwane?"
"Taɓ sosai ma, na iya ruwa sosai fa, ina shiga"
"Ai da alama kina da rashin ji, ba wanda ze gane hakan se wanda yake zaune dake"
"Wanda yake zaune da ni ɗin ma ba kowa ne ze gane hakan ba, kaima ban san yadda akayi na sake da kai haka ba, haka kurum naji kamar in yadda da kai"
"Aikin gama ya gama ai, kinma yarda dani ni ɗin"
Cigaba tayi da wasanninta a gurin, tayi nan tayi can ta Leƙa nan ta leƙa can, Yusuf yana ta wanki har ya kammala, yai shanya ya zura ƙafafinsa a cikin ruwan, kusa da Yusuf tazo zauna itama ta zura ƙafafunta a ruwan tana kallonsa.
"Meye kuma kike kallona?"
"Me zan kalla?"
"Muni mana" ya bata amsa
Murmushi tayi tace "kaine mummunan? Ai baka da muni sam"
Murmushi kawai yayi, yana jefa dutse a cikin ruwan.
Widad tace "kasan wani abu?"
"A'a sekin faɗa"
"Ban taɓa sanin a duniya akwai mutane nagari kamarka ba, da ina yiwa talakawa kallon mayun kuɗi, maciya amana, amma gaba ɗaya you proves me wrong"
Yusuf yace "dama bekamata ka yankewa mutane hukunci da laifin tsirari daga cikinsu ba, duk lalacewar zamani akwai na kirki"
Widad tace "Aikama nagani, dan yadda nake treating ɗinka a gida ban taɓa zaton zaka iya taimakona ba, nayi mamakin ganin hawaye a idonka lokacin da ni kaina na yanke tsammani da cigaba da rayuwa"
Ta ƙarasa maganar tana kwanciya a jikin Yusuf.
"Habibty, a wannan lokacin da kin mutu ban san ya zanyi ba, Nagode Allah da ya nunamin na Aure ki, dukda ba kya sona"
Shiru tayi ba tace komai ba, can Yusuf yace "Widad, yanzu idan na mutu zaki damu?"
Tsaki tayi tace "wace irin tambaya ce wannan?"
"Tambayarki kawai nayi"
"To wannan wace irin tambaya ce mara amfani, kawai muna hira ka kama wannan zancen ni bana so"
Ɗagota Yusuf yayi ya kalli idonta, ƙwallace kwance a idonta, se wani tura baki take, murmushi yayi ya maida ita jikinsa ya kwantar da ita, ya shiga shafa bayanta.
Ɗagowa tayi ta kalle shi tace "Ɗan uwa"
Yusuf yace "Yaushe na zama ɗan uwane, naji kin canza min suna'
" Gwaggo ta hanani faɗar sunan ka, kuma kaga ni bani da ɗan uwa, se gaka ka bani jini, kaga mun zama 'yan uwa tunda an samun jininka, mun zama' yan uwa kenan"
Dariya Yusuf yayi yace "wannan philosophy ɗinfa,? Lallai kam shikenan nima nayi ƙanwa tunda bani da ƙanwa mace"
Ta gyara kwanciyarta a jikinsa tace "Yoseef, idan muka koma gida zaka dawo gidanmu ka zauna kaida ummanka?"
"Ai muma muna gida" ya bata amsa
"Dan Allah ka dawo gidanmu, nasan bazaka cigaba da tuƙani a mota ba, nasan maybe ma in koma ƙasar waje, amma dan Allah ka dawo gidanmu kaji"
Girgiza mata kai yayi yace "so kike Mamansu Amal ta dinga wulaƙanta Ummana? Kuma zaman me zanzo inyi a gidanku, bayan bamu da wata alaƙa, kafin nan fa mun rabu"
"Dan mun rabu shine zaka ce bazaka dawo gidanmu ba, sannan idan na koma gida dole ta bar mana gida"
Yusuf yace "meyasa?"
"Saboda wani dalili me girman gaske, amma yanzu ba wannan maganar muke ba, dan Allah idan mun koma gida ka dawo gidanmu da zama,"
"Nida bakya sona, me zan zo gidanku inyi? Idan dai har ina ganinki zan cigaba da sonki ne, kuma ni bakya sona"
"Nifa ba tsanarka nayi ba, kawai ni bana son soyayya ne, ban santa ba kuma ban iya ba, dan bata birgeni, ƙarya ce da tarin damuwa a cikinta, amma ni bana son ko mun koma gida kayi nesa dani, na saba da kai sosai, kana iya haƙuri da dukkanin halayena, kuma kai garkuwa ne a gareni, dan Allah Yoseef ka yadda kaji ɗan uwa"
Yusuf kam murmushi yayi, a ransa yace 'sarkin taurin kai, kina sona amma kina garani'
A fili ya maze yace "Idan muka koma gidanku ace munje kwaɗayi, ni nafison in zauna a gidanmu nida Ummana"
"dan Allah, ba wanda zece muku haka, Dan Allah Yoseef kaji"
Juyowa yayi yana kallonta, har cikin ranta take maganar.
Wani abune ya dinga fizgar Yusuf game da Widad, yana jin wani irin farinciki a tare da shi, abunda bata son dai yayi mata, sedai wannan karon bata hana shi ba, sema biye masa da tayi.
A hankali ya cire bakinsa daga nata ya riƙe hannunta yace "ina sonki Habibty"
Ajiyar zuciya tayi ba tace masa komai ba.
Kawai ya tsaya ya zuba mata ido, a hankali tace "yakamata muje muci Abinci"
Yusuf ya cikata, suka miƙe ya shimfiɗa musu abu suka zauna, ya buɗe shinkafa da wake, da manja ya ɗakko tumatir da gurji ya yayyanka, ya juya suka fara ci.
Suna ci yana kallon Widad, ta kwantar da hankalinta, ta rugumi ƙaddarar rayuwarta, da farkom zuwansu ne se yayi fama kafin taci Abincin, amma yanzu hankali kwance ta dinga cin Abincinta.
"Wai meye kake kallona haka?"
"Gani nayi kina loma fiye da tawa, zaki cinye Abincin ki barni"
"Cigaba da kallona, cinyewa zan in barka"
Ya dinga jin farinciki, ganin yadda Widad ɗinsa ke nishaɗi tana fara'a, saɓanin Widad ɗin daya sani a baya, me shegen haɗe ran tsiya da koke koke, mara afuwa da tausayi.
Juyawa yayi gefensa ya tsinko wata 'yar ciwa, ya miƙo mata yana cewa
"If you ask me to be your king, i will turn around and said, you mean to tell me that I can have you when ever I want, i can tell you that I love you when you love me too, no more waiting for ever our love...
Kwashewa da dariya Widad tayi tace " Ai ba haka ake waƙar ba, kuma flower ake bayarwa, amma ni ka bani ciyawa sekace wata Akuya"
Yusuf yayi murmushi yace "A yanzu bani da wani abu da zan baki ai, shiyasa na baki wannan instead of flower"
Hannu tasa ta karɓa, ta kalli Yusuf tana murmushi.
Saleh ne a gigice ya shiga babban Ofishin dake cikin harabar gurin, Suleiman ne zaune yana danna system ɗinsa, Saleh ya shigo da sallama.
Suleiman ya ɗago tare da yin murmushi yace "Masha Allah, yau kaine a ofishin nawa? Kwana biyu"
Saleh ya miƙa masa hannu suka gaisa, yace "Suleiman ya aikin naku?"
"Alhamdilillah, ya Yusuf fatan yana lafiya?"
Saleh yace "lafiya ƙalau, yana gaisheku ina sa ran zuwa gurin mahaifiyarsa, im sake kwantar mata da hankali tare da tabattar mata yana cikin ƙoshin lafiya"
Suleiman ya gyara zama yace "hakane, hakam abune me kyau nima da week ends ɗin nan, naje gidan sedai har yanzu ta kasa kwantar da hankali ta, akwai buƙatar ka ɗakko mata muryarsa, kokuma ka haɗasu a waya su gaisa"
Saleh yace "No baze yuwu ba, ai bama zuwa garin nan da waya, kai mutanen nan fa sun shallake tunanin ka, nima ina lura da duka abunda nake yi, bana shiga da waya, haka nake zuwa in fito"
"to ubangiji Allah ya kuɓutar dasu, ina mamakin yadda abubuwan suke tafiya, kullum sake taɓarɓarewa sukeyi"
Saleh yayi ajiyar zuciya yace "yanzun ma matsala ce gagaruma ta taso"
Suleiman ya tattara hankalinsa yace
"wace irin matsala kuma?"
"mutanen nan sun gano waye Yusuf, kuma suna shirin ɗaukar mataki akan hakan?"
Suleiman yace "ya akayi suka sani?"
Saleh yace "niba wannan ba, babban abunda ya dameni shine, rashin sanin wani irin mataki zasu ɗauka akansa, gashi kuma yana can yana cikin zulumi akan ta yaya ze sanar da Widad gaskiyar waye shi, kasanta bata afuwa bata yafiya ga duka wanda yayi mata ƙarya, muddin suka dawo garin nan sannan ta gane waye shi akwai matsala "
Suleiman yace " ai tasan waye shi? "
" kamar yaya? Sannan ta yaya?"
Suleiman yace '" dukda gargaɗina da tayimin, amma bari in gaya maka yadda akayi tasan waye shi, wataran da yamma na kammala abunda nake zan bar office ɗin nan, kawai sega wata mota ta shigo gurin nan a guje, kamar zata tashi sama,
ma' aikatanmu sukayi kanta don son ganin wane mara ɗa'ar ne haka? Ko a jikin me tuƙin, Ta buɗe motar ta fito, wata matashiyar budurwa ce jikinta sanye da abaya, ta saka face mask, sannan ta rufe fuskarta da glass.
Kai tsaye inda nake ta shiga tunkarowa, da ma'aikatanmu sunyi kanta zasu hanata ƙarasowa, nace su barta ta ƙaraso.
Ko kallonsu batayi ba tazo inda nake ta tsaya ta kalleni tace "kaine Suleiman?"
Nace mata "Eh nine"
Tace "ina son muyi maganane"
Nace mata shikenan, nai mata jagora har office ɗina, muka shiga muka zauna, ta kalleni ta cire glashin fuskarta da face mask tace "kasanni?"
"Nace mata a'a"
Tace "Amma kasan Nasir Daula?"
Nace "ai duk Nigeria babu wanda be sanshi ba"
tace "sunana Widad Nasir Daula, nazo me zan maka wasu tambayoyi, kuma idan ka amsamin ba dai dai ba, ka shirya karɓar abunda ze biyo baya, bana sassauci ga mutane maƙaryata, waye Yusuf?"
Suleiman yayi ajiyar zuciya yace "wane Yusuf ɗin?"
"Direbana" ta bashi amsa
Suleiman yace "Yusuf jami'inmun ne, ɗan sanda ne na farin kaya" Suleiman ya bata amsa
"danme zaku turoshi? Me yasa kuka turoshi,? wato an haɗa kai daku a cuceni"
Suleiman yace "Yusuf bashi da laifi, jajirtaccen ma'aikacine me kishin ƙasa, umarni aka bamu daga sama akan cewar, a baki kariya sannan kuma ayi bincike akan wanda suke bibiyar rayuwar ki, amma bayan haka Yusuf be san komai ba"
Cikin isa da izza tace "akan me? Sannan kuma waye ya bada umarnin hakan? Ko kuma ni nace ina buƙatar hakanne? An haɗa kai daku za'a cutar dani, in ba hakaba meyasa Yusuf yasa hannu akan takardar zeyi aiki dani, dukda na gaya masa hakan tamkar saka hannu akan kwangilar mutuwarsane? Na kama Yusuf da bindiga"
Tun anan Suleiman ya jinjinawa Yusuf, ya yabawa ƙoƙarin sa na jure zama tare da yin aiki da Widad, saboda yadda take magana cike da izza da isa.
Suleiman yace " kamar yadda na gaya miki, Yusuf jajirtaccen ɗan sandane, kuma ba abun mamaki bane samun ɗan sanda da bindiga, sannan Yusuf baza'a taɓa bashi aiki ya dawo dashi yace ya karaya ko baze iyaba, amma sam bashi da laifi, kuma da farko bashi mukayi niyyar bawa aikinba, abokin aikinsane yace a bashi saboda jajircewarsa da haƙurinsa"
Ajiyar zuciya Widad tayi tana huci, inda Allah ya temaki Sulaiman gaskiyar data buƙata ita yake gaya mata, ta kalle shi tace "Ina buƙatar sanin waye yasa a dinga bin diddigi na?"
Suleiman yace "kamar yadda na gaya miki ne, ban saniba nima umarni aka bani daga sama, ban san komai akai ba"
Widad tace "shikenan, ni zanje in bincika da kaina, amma zan maka gargaɗi da jan kunne, Yusuf be san na ganshi da bindiga ba, kada ka kuskura Yusuf yasan nasan waye shi, idan har ka gaya masa nasan waye shi zan gane, and you know what am capable of doing"
Suleiman yace "karki damu, Insha Allah baze sani ba, bazan gaya masa ba"
Tace "and Mark you, bana son kowa yasan da nice nazo gurin nan, and zan cigaba da bibiyarka, duk lokacin da Yusuf yayi misbehaving ko wani abu na yunƙurin cin amana ta, to dasa hannunka a ciki"
Suleiman yace "ina me tabattar miki da babu abunda zeyi na cin amanarki"
Ta miƙe a gadarance, ta maida face mask ɗinta, ta saka glass ɗinta ta fito, sedai tana fitowa Abbas ya kawo kai yana shigowa, ta tsaya ta ƙura masa ido, harya shige wani office, sam Abbas be lura da kallon da take masa ba, ba tace komai ba tayi gaba da sauri ta hau motarta ta bar gurin.
Bayan wasu 'yan kwanaki da yin hakan, Widad ta kira Suleiman tace tana son ya gayamata full name na Abbas da rank ɗinsa, amma Suleiman yace hakan ya saɓa da ƙa' idar aikinsu, sedai ta gaya masa meyasa take neman hakan, bata kuma bi takansa ba bayan kwana uku, aka kawo transfer later na Abbas aka maye gurbinsa da Yusuf.
Saleh ya jinjina kai yace "wato duk inda mutum yake tunanin hatsabibancin yarinyar nan ta wuce haka, yana cam yana ta zullumi akan yadda ze gayamata, ashe tuni ta sani"
Sulaiman yace "tabbas tasan waye Yusuf, kallonsa kawai take sannan kamar yadda naimata Alƙawari ban gaya masa ba"
Saleh yace "Allah sarki, ni gaba ɗaya tausayi yake bani wallahi, bejiba be gani ba yana ta ɗawainiya da yarinyar ta bata san kimar mutane ba, duk naga ta rage wannan zafin kan nata, ta kwantar da mai tana rayuwa a ƙauyen da babu wuta, babu ruwa babu abubuwan more rayuwa, abun gaanin ban tausayi"
Suleiman yace "Allah sarki Yusuf, samun mutum me irin zuciyarsa se an tona, ina masa fatan ubangiji Allah ya kuɓutaf dashi, daga sharrin Azzaluman nan"
Saleh yace "Ameen ya Allah, amma tabbas Yusuf yana cikin jarrabawa, dan ina tunanin matakin da zasu ɗauka akansa, basu da imani sam"
Suleiman yace "Allah ya fisu kam, amma indai batun sadaukarwa ne, to tabbas Yusuf yayita"
Haka suka cigaba da tattaunawa a tsakanin su.
Se bayan la'asar, lokacin kayansu sun bushe sannan Yusuf ya tattaresu ya ninke, suka kamo hanyar gida, suna tafe suna hira gwanin ban sha'awa, Widad nata takura masa da tambayoyi dan duk abunda ta gani bata sani ba seta tambaya.
Suna zuwa gida Gwaggo tai murmushi tace "Amarya yau gidan nan ba daɗi ba kya nan, duk naji ba daɗi"
Widad tai murmushi tace "nima haka naji ba daɗi yau Mama"
Hindu tace "wallahi kuwa Gwaggo, gaba ɗaya yau gidan se a hankali ba daɗi da bakya nan"
Hari tace "Nikam naji daɗi, bakin mutane shiru yau ba neman magana"
'
Widad tace "in mutane na magana ki dena saka baki, danke ba mutum bace"
Gwaggo tace "Amarya yau wake muka dafa, ban sani ba ko zaki iyaci, dan haka na dama miki kunu gashi can da zafinsa"
Widad tace "wayyo Allah Mamana ta kaina, nagode sosai Allah yasaka da alkhairi, wakenma duk zan iyaci nagode sosai Mama"
Gwaggo tace "Babu godiya a tsakaninmu ai"
Yusuf kam bayan sun gama gaisawa, ɗakinsu ya wuce, ya bar Widad tana cigaba da neman maganarta.
Hari tana ta ƙulla gyaɗarta ta siyarwa, Widad tazo ta cika hannu ta zuba a hijjabi tayi ɗaki, Hari ta buɗe baki tace "Wudas yaseen sekin biyani kuɗin gyaɗar nan"
Gwaggo tace "yi haƙuri, zan baki kuɗin"
Seda tayi me isarta sannan ta koma ɗakin, Yusuf tun yana mamakin halin Widad har ya dena, ta kwaso kwanukan wanke wanke tayi, gaba ɗaya yau wani irin nishaɗi take ji, taji daɗin fitar da suka yi sosai, wani irin farinciki ya dinga ratsata.
Ta karɓo musu Abincin gurin Gwaggo, suka zauna suka ci, bayan sun gama ne ta ɗanyi shiru sannan tace "Naji daɗin fitar nan sosai Yoseef, ban taɓa tunanin ana samun farinciki haka ba koda babu dukiya"
Yusuf yace "aishi farinciki da jin daɗi base ka tara dukiya ba, indai zakayi tawakkali da yadda Allah ya ajiyeka, zakayi rayuwarka cikin farin ciki da jin daɗi, kuma har kafi me Dukiya walwala ma".
Widad tace "ƙwarai kuwa yau na gani, rabon da inyi farinciki haka tun Ammi na nada rai, shekara goma baya kenan"
Yusuf yace "kina nufin duk tsawon wannan shekarun, bakya farinciki?"
"tun bayan rasuwar Ammi, ban kuma samun farinciki haka ba, babu club ɗin da bana zuwa a waje, dan inyi nishaɗi, nice club ɗim wrestling stadiums na ball da sauran wasanni, amma babu sauyi, na kanji nishaɗi ne kawai idan nai wasan doki, kona kasance da dabbobi kuma idan ina Tare da Alhaji Nasir Daula "
'yar Wulaƙanci yau kuma saunan baban nata take faɗa gatsal"
Ta cigaba da cewa "nasan Daddy zeyi murna sosai, idan ya ganni cikin walwala haka, danya fidda ran faruwar hakan a rayuwata" ta ƙarasa maganar muryarta na rawa alamun zata yi kuka.
Rungumota Yusuf yayi yace "haba Jarumata, kuma Gimbiya ta, karkiyi kuka please kiyi haƙuri kinji babyna, nifa jarumtar nan taki burgeni take yi, dan haka idan muka koma gida, zan saki a aikin ɗan sanda kema"
Kwashewa tayi da dariya, tace 'kai dai kaje kaita aikin ɗan sandan, nikam a kai kasuwa "
" Zaki iya kama' yan fashi fa da ɓarayi da wannan dakakkiyar zuciyar taki Baby"
Shiru ta ɗanyi tace "da wanda suka kashemin Ammi ma ko?"
Yusuf yace "am just kidding, idan wanda suka kashe mahaifiyarki ne, Insha Allah ni zan ɗau nauyin yin wannan binciken"
Girgiza masa kai tayi tace "this the most dangerous case, don't take the risk of it, ni suke bibiya suke son ganin bayana, dan haka koni ko su, karka sa kanka a ciki, a yanzu ma kalli yadda kake wahala"
Yusuf yace "Amma suwaye suka kashe ta, kuma meyasa? '
Widad tace " nima ban sani ba"
Yusuf yace "i have to know even a little bit of your life"
"bazan faɗa ba, ban yadda da kai ba" tai maganar tana dariya.
Yusuf yace "ai yadda ta ƙare, tunda muka zama abu ɗaya, har muka kasance a inuwa ɗaya"
Hararsa tayi tace "wace irin inuwa ɗaya"
"Inuwar Aure mana Baby na, kuma gashi.... Sekuma yayi shiru
Widad tace " Kuma gashi me? Ƙarasa mana, kai ko kunyata na baka ji ko? Allah ya shiryeka, ni cikani"
Ƙara rungumeta yayi yana murmushi yace "Kunyarwa zanji? Mutum da matarsa"
"Matar ƙauye ba, dan iya nan ne, kafin mu koma gida zamu rabu'
Murmushi kawai Yusuf yayi bece mata komai ba, a hankali yace " ki gayamin mana "
" wai mai meyasa ka damu se kaji tarihin rayuwata? Ko nima binciken ake a kaina? "
Yusuf yayi dariya yace " wane ni?"
"idan kana son in baka labarin, kwanta in kwanta akan ƙirjinka"
Yusuf yace "dan dai wannan, ai shi yafi komai sauƙi"
Yusuf ya kwanta, ta kalle shi tace "kuma wallahi idan kamin wani abu, se munyi faɗa na gaya maka"
Yusuf yace "idan nai miki me?"
"Bansani ba"
"Allah ya baki haƙuri, niba abunda zanyi miki"
A hankali ta kwanta akan ƙirjinsa, tayi shiru na wani ɗan lokaci
WACECE WIDAD NASIR DAULA.....
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
60_61
Mahaifin Widad Alhaji Nasir haifaffen garin Kano ne, su biyu Allah ya bawa iyayensu, Shida Yayansa me suna Yusuf.
Yusuf shine babba sannan Nasir, kusan shekaru takwas Yusuf ya bawa Nasir, Nasir da Yusuf suna da matukar haƙuri da biyayya, dan har Yusuf yafi Nasir haƙuri, Yusuf yana matuƙar ƙaunar ƙaninsa, tun suna yara duk wata hidimar Nasir Yusuf ne yake yinta.
Mahaifiyar su Marainiya ce, bata da wani cikakken gata, mahaifinsu Nasir kuma, shikaɗai mahaifiyarsa ta haifa, sauran duk uba ɗaya suke, hakan yasa take fuskantar ƙalubale daga ɓangaren dangin miji, tsangwamar da suke masa ta shafeta.
Ko a unguwa ana jinjina tarbiyyar Su Nasir, saboda suna da matuƙar nutsuwa, ko tarin abokan nam basu dasu, tare suke komai nasu, kansu a matuƙar haɗe yake, Nasir yana girmama Yusuf a matsayinsa na wansa, shi kuma Yusuf yana matuƙar ƙaunar Nasir da tausayinsa a matsayinsa na ƙaninsa, hakan ne yasa duk inda me sunan Yusuf yake Alhaji Nasir Daula yake girmama shi sosai.
Lokacin da suka fara tasowa, Nasir ya fara yin abokai, saboda yafi yayansa baki da son mutane, mahaifinsu yana da rufin Asiri daidai gwargwado basu nemi komai sun rasa ba.
Sun fara kawo ƙarfi Allah ya karɓi rayuwar mahaifinsu, sunji mutuwar nan sosai, sun daɗe suma alhinin mutuwar nan, da ran mahaifinnasu dama dangimsa ba damuwa sukayi da su ba, balle yanzu ya bar duniya, dan haka suka sake yin watsi dasu, suka ci gaba da faɗi tashi suda mahaifiyarsu.
A wannan ƙadamin wasu mutane suka tare a kusa da gidansu Nasir, sedai mutanen ba masu ƙarfi bane ba, Nasir yana matuƙar tausayin Yaran gidan, saboda rashin gata, a haka ya janyo ɗaya daga cikin 'yan gidan ya zama abokinsa, Yaron sunan kakanshi ne dashi, shine ake masa inkiya da irin inkiyar kakan nasa wato Bulama, kullum tare suke cin Abinci da Bulama, suje yawon balla tare da sauransu.
Sedai halayar Bulama da Nasir tasha bamban, Bulama baya shakkar iyayensa, ga mugun rashin ji da yake fama, dan haka Yusuf ya tsani Bulama, yayi yayi ya raba Nasir da Bulama abu ya gagara.
Yusuf yana jami'a, Nasir yana babbar sakandire Allah ya karɓi rayuwar mahaifiyarsu, Sunyi kuka sosai, saboda ita kaɗai ta rage musu, wadda suke kalla suji daɗi, saboda dangin mahaifinsu dasu da babu duk ɗaya, ga mahaifiyarsu itama ba wani gata ne da ita ba, dan haka koda aka share makoki babu wanda yabi ta kansu, cewar dangin mahaifinsu ai su ɗin mazane zasu iya kula da kansu, base am ɗau ɗawainiyar su ba.
Nan Nasir ya ƙullaci dangin mahaifinsu, dama harda sakacinsu yayi sanadiyyar rasuwar mahaifiyarsu, tana rashin lafiya sun yi sintiri gidan ƙanin mahaifinsu ya basu kuɗi su kaita Asibiti amma ya hana, suka dinga 'yan uwan uban akan su temaka musu amma suka ƙi.
Haka suka tattara ɗan abun hannunsu, suka kaita Asibiti aka rubuta musu Allurara dubu saba' in, suna cikin taradaddim yadda zasu samu kuɗin rai yayi halimsa.
Tunda Allah yayi mata rasuwa, Nasir be ƙara takawa inda dangin mahaifinsu suke ba, haka Yusuf ya cigaba da buga buga da faɗi tashi, ya sai musu Abinci ya biya musu kuɗin makaranta, amma duk da haka Nasir be rabu da Bulama ba kuma be dena tamaka masa ba.
A haka da ƙyar Yusuf ya kammala karatunsa, ya dinga faɗi tashi neman sana'a, ya samu aikin banki da ƙyar ta hannun wani ɗan siyasa.
Cikin ikon Allah, Allah ya rufa masa Asiri har yayi Aure, dukda Nasir ya kawo ƙarfin daze fita ya nema, amma Yusuf be fasa ɗawainiya dashi ba, hatta sabulun daze wanka Yusuf seya siya ya bashi, akayi sa'a Nasir yana ɗasawa da matar Yayansa sosai, saboda bashi da ƙyuya, duk aikin data sashi yi mata yake, dukda kasancewarsa ya zama saurayi, wasu lokutan har zama suke suyi hira tare, ko suyi shawara.
Ɗan zuwan da suke gidan, haka Bulama yake mata 'yan sace sace, haka take shiru saboda Nasir, Yayan Nasir ya sha dunƙule kuɗi masu kauri ya bawa Nasir da nufin yayi sana' a, amma se Bualama ya ziga shi, su kewaye kuɗin suyi bushasha, aita kashewa 'yan matan Bulama, su sai kaya su sai kayan Ball ayi shagali kuɗi su ƙare, da Yusuf yaga abunda yake faruwa seya koma yake kafawa Nasir sana' a, nan ma Bulama ya bishi su ragargaje komai.
A hankali Nasir ya fara yiwa kansa faɗa, yaga asarar da yakewa Yayansa tayi yawa, gashi be taɓa nuna masa ya gaji ba, sedai yayi fushi yace baze sake bashi jari ba se yayi hankali.
Ya koma ya sameshi yace ya bashi jari, in Allah ya yarda ze alkinta, Amma Yusuf yace baze bashi suje su haɗu da sakarkarun abokansa su cinye ba se yayi hankali, haka yaita sintiri amma ya hana shi.
Da yaga hakan yaƙi seya koma ta gurin matar Yusuf wato Nadiya, watarana yaje ya sameta a falo, bayan sun gaisa yace "Anty taimako nake nema fa"
Tace "temakon mefa?"
"Anty Yaya ya hanani Jari, nayi nayi amma yace se nayi hankali, dan Allah kisa baki, nasam yadda yake sonki da kince a bani ta zauna"
Nadiya tayi murmushi tace "ai kai lamarin naka ne se a hankali, se an baka kaje ku kewaye ku cinye kai da abokai, kamar baka da wayo"
"Nidai dan Allah kisa baki ya bani, Allah bazan ɓafnatar ba zan tattala"
Nadiya tace "shikenan, rashin sana'a ga matashi bata da daɗi, bari ya shigo gidan inga ya za'ayi"
Nasir yace "Yawwa Antyna ta kaina, Allah yasaka da alkhairi, ya kawo 'yan biyu sau biyu" (da yake tunda akayi auren bata samu rabo ba"
Tai murmushi ta ce "Ameen ya Allah Nasir, Allah yasa ya baka jarin nan, daga nan ka zama babbn done"
"Ameen Anty, bari in ɗau carbi inta masa lazimi kafin ya dawo"
Tai dariya tace "idan ma be baka ba, ina sa ran a kawomin kuɗin gonata, se in baka"
Nasir yace "zema bani insha Allah '
Suna cikin hirar ne sega Yusuf ya dawo, Yusuf yace " Ashe kana nan, na biya ta can gidan in baka takalmin dana siyo maka amma baka nan"
Nasir yace "ai tun ɗazi ina nan, gurinka nazo"
"Gurina kuma? To gani"
Nadiya tace "ka zauna kaci Abinci tukuna, idan kaci se in gaya maka saƙon nasa"
Haka akayi, tare ma sukaci Abincin shida Nasir, bayan sun kammala Yusuf yace "to Uwargida, ina jinki tunda naga kun haɗa kai, nasan wataƙila wani abu akeso na bayar ko inyi"
Dariya suka yi, Nadiya tace "Yawwa ranka ya daɗe, kaga yanzu kamar Nasir ai bekamata ace seka sai masa takalmin sawa ba, kamata yayi ace duk wannan abubuwan shiyakewa kansa, dan haka yazo neman alfarma dan Allah a temaka masa da jari"
Yusuf yace "An hanashin baza'a bayar ba, in kuma bashi yake shida wancam yaron mara kunya su haɗu su cinye, gara ko meye yazo in sai masa, idan ya ƙara hankali se in bashi jarin"
Nasir yace "dan Allah Yaya, Allah nayi hankali zan tattala"
Yusuf yace "Anƙi ɗin, ai tun rannan nace bazan sake baka ba"
Nadiya tace "A dai yi haƙuri ranka ya daɗe, Insha Allah baze sake ba"
Yusuf yace "to naji, tunda haɗe mun kai zakuyi, naji zan bashi jari, amma rance zan bashi"
Nadiya tace "haba dai rance dan Allah"
"shikenan tunda bakwa so, ai bazan sake bashi kuɗi yaje yaci a banza ba, tunda besan zafinsu ba"
Nasir yace "Anty na yadda, Insha Allah zan dawo masa dasj, nidai a bani jarin"
Nadiya tace "dan Allah kace ya dawo maka da rabi, ya riƙe rabi mana"
Yusuf yace "Nifa in bakwaso kuɗina sun huta, nasan abunda zanyi dasu"
Nadiya tace "shikenan, munji mungode Yaushe za'a bamu?"
Yusuf yace "waini wace sana'ar ma zakiyi ne? Kuma nawa kake buƙata?"
Nasir yace "Yaya sarƙoƙi nake son in dinga siyarwa, zan kama shago a kasuwa sannan in zuba kayan, ance dubu ɗari biyar zasu isheni".
Zaro ido Yusuf yayi yace "dubu dari biyar? Kana da hankali kuwa?"
Nadiya tace "kana dasu fa, kafi ƙarfinsu dan Allah ka bashi"
"Gaskiya bazan bashi ba, zan dai bashi ɗari uku yaje ya nemi sauran, ɗari ukunma bashi"
Nadiya tace "Nasir karka damu, idan aka kawomin kuɗina, kazo in baka sauran, inaji a jikina wannan sana'ar ds zaka fara itace silar arzikinka, ka zama hamshaƙin Attajiri, wanda ze tara Daula ta ban mamaki"
Nasir ya washe baki yace "Allah yasa Antyna ta kaina, da duk sati sena kaiki Makka, shi kuwa yaya se shekara shekara zan dinga kai shi"
Yusuf yace "kar Allah yasa ka kainin, bana insha Allah zan tafi ai, kuma kema ban yadda ki bashi kuɗi kyauta ba, rance zaki bashi kuma tare zamu je da kaina a kama shagon"
Har zata yi magana, ya dakatar da ita, ya hanta magana, Nasir yaita godiya sannan ya tafi.
Bayan tafiyar sa Yusuf yace "Nadiya, ina jin daɗin yadda kike nunawa ɗan uwana ƙauna kamar ɗan uwanki, ni kaina ina tunanin wace sana'a zan sama mishi, saboda nasan bayan raina babu wanda ze iya ɗawainiya dashi kamar yadda nakeyi, ba ƙinsa nake da nace rance na bashi ba, hakan ne zesa ya maida ya tattala abunda aka bashi "
Nadiya tace " Shikenan tunda haka kace, Amma kana min kyautatawar dako nawa nakwa 'yan uwanka alheri dashi ban faɗi ba, amma tunda kace haka shikenan "
Bayan kwana bakwai, aka tattara kuɗi akaje aka kamawa Nasir shago, aka zuba kayan sarƙoƙi kala kala, Nasir ya maida kai sosai a tafi da shagon nan, duk yadda Bulama yaso a kassara shagon Nasir yaƙi, sedai wataran Bulama yazo ya taya shi zama koya yayi masa shara, shi kuma ya biya shi, amma a hakan Bulama yana taɓa ƙuruciyar ɓera wato sata.
Allah yasawa kasuwancin nasa albarka, nan da nan kasuwanci ya kankama, idan kuɗi suna nema su yanke masa idan ya zaga gurin Matar yayansa seta ƙara masa kuɗi, a hankali ya dinga sabawa da mutane, idan yaji labarin wani kasuwancin seya ɗibi kuɗi ya jarraba, shine ya buga nan ya buga can.
Wataran aci riba, wata ran a faɗi, Yusuf yana yi yana monitoring ɗin ƙanin nasa, idan ya tambayeshi yaushe zan dawo maka da kuɗin se yace 'ba yanzu ba, idan lokacin karɓa yayi zan karɓa'
Haka ya dinga faɗi tashi, da Nadiya ta ganshi seta fara tsokanarsa da seka gina Daula me ban mammaki babban don, a haka abokansa da maƙota suka fara kiransa da Daula kawai.
Ana nan wani hamshaƙin attajiri a kusa da gidan Yusuf, yaje ya auro wata balarabiya 'yar maroco, akayi shagali sosai' yan uwanta na can maroco suka zo Nigeria, akayi shagalin biki sosai.
Bayan wani lokaci balarabiyar nan ta haihu, aka kawo mata wata Yarinya a cikin danginta, ta zauna tare da ita saboda ta dinga tayata raino, kafin jaririn yayi ƙwari.
Nasir ya kan shiga gidan mutumin, da yake akwai babban ɗan mutumin me suna Ahmad a gidan, suna gaisawa sosai da Nasir, shi ya bashi shawarar fara sana'ar kayan sarƙoƙi na mata, dan haka Nasir yana shiga gidan sosai, dan ya saba da ita Amaryar wannan mutumin Islam wato balarabiyar maroco.
Duk lokacin da Nasir ya shiga gidan sukan haɗu da wannan balarabiyar Yarinyar me suna Huda 'yar uwar Islam , yana ɗan jin larabci dan haka sukan gaisa, kokuma suyi magana da turanci.
Huda bata da saurin sabo, amma ta saba da Nasir, ko fita ba tayi amma Saboda Nasir har gidan Yusuf take shiga nemansa idan taga bata ganshi ba, saboda Nasir yana da barkwanci, gashi ya iya hira dan haka yakan ɗebe mata kewa sosai.
A hankali mutuncinsu ya rikiɗe zuwa Soyayya, sun shaƙu da juna sosai, da farko lokacin da tazo Nigeria cewa tayi ba zata fi sati biyu ba zata koma ƙasarsu, Islam na ta fama da ita ta zauna amma fafur taƙi, amma saboda Nasir se gashi ta shafe watanni uku ba tare da ta koma maroco ba.
Ya zamana Nasir ya dena karɓar Abinci a gidan yayansa Yusuf, saboda Huda zata ajiye masa idan an dafa a gidansu, idan yaje ta kawo masa su zauna yana ci suna hira.
Kasancewar Nasir mutumin kirki ne daga shi har yayansa, yasa duk mutanen unguwa sun sanshi, kuma shi wannan Attajiri mijin islam yasan Nasir sosai, kuma yasan yana zuwa gidansa, shi ya fara tsokanarsa yana cewa
"Nifa Malam Nasiru ban gane wannan mutuncin haka tsakaninka da Huda ba, ko kaima marocon zaka ne?"
Tun suna ɓoye ɓoye harta bayyana ga mutane, Nasir da Huda soyayya sukeyi, wasu lokutan idan aka aiketa shiyake rakata, saboda wani abun bata sanshi da hausa ba, kyautar sarƙoƙi kuwa da yake bata babu adadi.
Wataran haka zata shiga gidan Yayan Nasir, gurin Nadiya ta wuni a gurinta suna hira, a haka har take sedai sam Allah be haɗa jinin Huda da Bulama ba, da tana ɓoyewa, harta kasa ɓoyewar take gayawa Nasir ita bata san ganinsa da wannan Bulaman.
Nasir yace "Hudallahi Bulama abokina ne, kuma ɗan uwanane ban san me yasa bakwa shiri ba"
Huda tace "Nifa ba hanaku hulɗa nayi ba, amma idan zakazo gidan nan ka dena zuwa dashi, yaita faman kallona, ni kuma bana so"
Nasir yace "ki kwantar da hankalinki, ba abunda ze miki, dan dai kallo ai ba cinye ki zeba"
Haka yaita rarraashinta, suka cigaba da soyayya ita da Nasir.
Watarana Yayarta ta kirata tace "Huda, gida fa sun matsa akan lallai ki koma, kinga kin daɗe sosai a nan"
Maimakon Huda tayi magana, se tayi shiru idonta ya cika da ƙwalla, Islam tace "kuka kuma? Me yasa ki kuka?"
Huda tace "ni bana son in koma gida"
Islam tace "meyasa, keda da ƙyar aka lallaɓoki kika yadda kika zauna"
Huda ta share hawayenta tace "bana son in koma saboda... Sekuma tayi shiru
Islam tace " Saboda Nasir ko? "
Huda ta jinjina mata kai, Islam tace " Amma Huda kin san bazasu yadda su aura miki shiba? Kin san irin tashin da mukayi a gidanmu, nima dan Alhaji yana da kuɗi ne suka yadda suka Auramin shi, amma kinga Nasir bashi da kuɗin daze iya biya ya Aureki, kuma a can ga Habibullah sun masa Alƙawarin bashi Aurenki"
Cikin kuka Huda tace "ni bana son Habib, Nasir nake so, dan Allah Ukty kisa baki, wallahi ina son Nasir sosai"
Islam tace "kidena kuka ukty, Insha Allah zan tayaki da Addu'a amma nasan ko zaki Auri Nasir zaki sha wuya"
Daga maroco musamman aka taso ƙanin mahaifin su Huda yazo ya tafi da ita, tayi kuka sosai saboda zata rabu da Nasir, shi kansa Nasir ya shiga damuwa sosai, ranar da zasuyi Sallama Huda ta dinga kuka, Nasir kamar ze hauka.
Dan bayan sun rabu ɗaki ya koma yaje yaita nasa kukan shima, tunda Huda ta koma ya dena zuwa gidan wansa ko karɓar Abinci, ya zamana kasuwa ma ba kullum yake zuwa ba, sedai wataran Bulama yaje ya buɗe shagon ya zauna yayi wadaƙarsa san ransa da kuɗi.
Mussaman Yusuf ya aika aka kira masa Nasir, Yusuf yace "Wato Nasir saboda wannan yarinyar kake nema ka kashe kanka ko? Ko Abinci ka dena zuwa ci, kai yanzu ko Auren ne ina kaga kuɗin da zaka iya auran balarabiyar yarinyar nan? Shikansa maƙocin nawa bakaji kuɗin da ya kashe gurin auro yarta ba, me muke dashi Nasir? Kayi haƙuri ka cigaba da walwalarka, nan gaba Insha Allah ni zan maka Auren ma da kaina, a samo maka 'yar baƙa me kyau ka Aura ko ƙanina"
Zumɓura baki Nasir yayi, ya haɗe rai ƙwalla ta taru a idonsa. Nadiya tace "Shifa farar fatar nan yake so da dogon gashi ko Nasir?"
Girgiza kai Nasir yayi yace "Ni wallahi kawai sonta nake, ni bana son wata inba Huda ba"
Haushi ne ya kama Yusuf, da ze masa Masifa, amma ganin Nasir yana kuka yasan lallai ya kamu da yawa.
Se ya koma rarrashinsa, dayi masa Nasiha da ƙyar da rarrashi da Addu'a sannan Nasir ya cigaba da zuwa shagonsa, badan ya cire Huda daga ransa ba.
Ɓangaren Huda ma tunda ta koma maroco suka kasa gane kanta, bata walwala Sam, sannan taƙi saurarar wanda akeso a Aura matan, sam baya gabanta kullum cikin tunanin Nasir take da barkwancinsa, gashi lokacin waya bata yawaita a hannun mutane ba, balle ta dinga kiransa suna magana.
Aka fara shirye shiryen bikin Huda da Habib, amma Huda sam bata saurarensa se aikin kuka, gaba ɗaya tabi ta rame suka kasa gane kanta.
Islam ta shirya taje ganin gida, domin ayi shirye shiryen biki da ita, sedai me ganin 'yar uwatta ya razana ta gaba ɗaya ta rame, bata walwala se kuka.
Gashi iyayensu sun rasu, a hannun wan mahaifinsu suke, shi kuma mutum ne me azabar tsauri kuma kaifi ɗayane baya magana biyu, dan duk wannan botsarewar da Huda take akan Auren Habib be dameshi ba sam, shirin Aurar da ita kawai yake.
Seda Islam taje ta gaya masa aiga Halinda Huda take ciki, akwai wanda take so a Nigeria.
Nan yai tsalle ya dire yace baze taɓa yuwuwa ba, in dai yana nan a raye ba zata Auri wani ba idan ba Habib ba.
Da jin wannan batu hankalin Huda ya ƙara tashi, duk 'ya' yan wan mahaifinsu ba wanda yakewa Auren dole, sesu, yanzun ma yana son ya aurawa Habib Huda ne saboda yana da kuɗi kuma yana ci.
Mijin Islam har maroco yaje, akan maganar Huda dan Islam tana ta kuka ganin tilon ƙanwarta na neman rasa ranta saboda baƙin cikin auren dole daza'ayi mata.
Alhaji Abubakar yasa baki akan su ƙyale Huda da Auren nan, ko basu Aurawa Nasir ba su ƙyaleta tunda bata son Auren amma suka ƙi, har yayi barazanar ze ɗauke Huda kuma ze haɗa wan mahaifinsu da hukuma akan abunda yake yunƙurin yi.
Ɓangaren Nasir ma, tunda yaji halin da Huda take ciki ya shiga matsananciyar damuwa, har kwanciya yayi a Asibiti, damuwa tayi masa yawa gashi kullum ƙara son Huda yake a cikin zuciyarsa, tun Yusuf yana jin haushin ƙanin nasa har ya dawo yana tausaya masa, saboda ya lura kamar jarabta ce wannan Soyayyar tasa da Huda.
Hatta dangin su Huda da 'yan uwa suma suka sako Wan mahaifin Su Huda a gaba akan ya aura mata wanda takeso taje can ta ƙarata, indai mazan ƙabilar hausawa ne da ƙafarta zata dawo, itama Yayarta dan tana Auren me kuɗi ne, shiyasa ya iya riƙeta, itama babu tabbacin baza' a sakota nan kusa ba, dama me kuɗi itama ta samo da ɗan sauƙi amma ta ɗakko talaka, kota aureshi Auren ba inda zashi, ita dai Huda tace taji ta gani taje ƙasar Hausawa ta zauna dasu ita ba taga wani aibunsu ba, duk miyagun halayen da ake faɗa bata gani ba, kuma suna zaune da iyalansu lafiya.
Ganin baki yayi yawa yasa wan mahaifinta yace "da kuɗin Auren Huda, da kayan Aure da sadaki da komai da komai ya yanke dirham dubu ɗari takwas"
Yusuf yana gida, akazo ana sallama dashi, ya fito dan ganin me sallamar hana zuwa yaga mijin Islam ne wato Alhaji Abubakar, ya fito suka gaisa da juna, Alhaji Abubakar yace "wato dama magana ce nake tafe da ita akan ɗan uwanka Nasir, naje maroco ƙasar su matata, yarinyar nan Huda tama cikin matsanancin hali, ɗan uwan mahaifinta ma shirin yi mata Auren dole, mun kai ruwa rana sosai dashi, dan haka yace idan Nasir ya shirya nan da sati biyu ya kai kuɗin Aure, komai da komai dirham dubu ɗari takwas "
Yusuf yace " Alhaji nawa kenan a kuɗin mu na Nigeria "
Alhaji Abubakar ya ɗanyi shiru sannan yace " Naira miliyan uku da dubu ɗari shida kenan a kuɗinmu na nan"
Shiru Yusuf yayi, ya yakice gumi sannan yace "innalillahi wa inna ialaihi raji'un, to zamuje muyi shawara inga inda yadda zamuyi, amma bamu da shi a ɗaka balle a waje, ni kaina yadda gaba ɗaya Nasir ya sukurkuce abun yana damuna, amma bakomai nagode sosai da ƙoƙarinka nagode"
Alhaji Abubakar yace "karka damu, ai ɗa na kowane kuma Nasir yaron kirkine ubangiji Allah ya yassare muku"
Sukayi Sallama ya tafi, jiki a sanyaye Yusuf ya shiga cikin gida, gaba ɗaya kamar an zare masa laka, Nadiya ta kalle shi tace "ranka ya daɗe lafiya kuwa?"
Ya samu guri ya zauna yace "Nadiya akwai matsala, baban Yarinyar nan Huda yace nan da sati biyu mu kai miliyan uku da dubu ɗari shida sannan a bashi ita, nikuma kin san bani ds ita, gashi ina tsoron wani ciwo ya kama min Nasir, gaba ɗaya yasa kansa a damuwa, duka abunda zan tsawatarwa Nasir ince ya bari yaƙi hanuwa to tabbas wannan jarrabawa ce a gareshi, Nadiya na rasa abunyi ina zan samu wannan kuɗin haka? "
(A wannan lokacin kuɗi suna matuƙar daraja)
Nadiya tace " yanzu meye abunyi, nikaina na fuskanci idan ba'a ɗau matakin daya dace ba, akwai yuwuwar ya faɗa mawuyacin hali "
Yusuf yace " shine abunda nake tsoro, bazan iya fitowa in nunawa Nasir gazawa taba gurin sama masa abunda yakeso ba, kinga kwanan nan kuɗin hannuna na tatike aka buɗe masa shago, idan aka saki shagon aka karɓi kuɗin idan yayi aure dame ze Riƙeta? "
Nadiya tace "ai kama bar batun a saki shagon nan, muyi tunanin wata mafitar"
Yusuf yace "bazan gaya masa halin da ake ciki ba, inaga zan rubutawa bankinmu su bani aron kuɗin, idan yaso a dinga cirewa a albashina, akai musu kamar yadda Nasir ne kaɗai ɗan uwana itama Islam Huda ce kaɗai 'yar uwatta, idan muka temakesu kinga mun ceci rayuka biyu kenan, amma kiyi shiru da bakinki karki gaya masa Nadiya "
Nadiya tace " Insha Allah bazan gaya masa ba, amma asaka gidana na cikin gari a kasuwa, idan aka siyar semu ragewa banki kuɗinsu ko? "
Yusuf yace" A'a Nadiya, ɗawainiyar da kike da Yusuf aita isa haka, ki bari kawai '
Nadiya ta haɗe rai tace "to ainima Nasir ɗan uwanane, tunda muna zaune da kai kana kula dani, meyasa zan bar ɗan uwanka cikin damuwa?"
Yusuf yace "Shikenan, ki bari in dawo se mucigaba da maganar, bari inje inyi sallar isha' i in dawo"
Yai maganar yana miƙewa, sedai yana fitowa ya ci karo da Nasir a tsaye a ƙofar ɗakin
0 comments:
Post a Comment