Ganin halin da take ciki yasa likotoci suka amsheta tare da umarta da sukai report a wajen police, matashin nan ne ya tafi dan cika umarnin, baisha wahala ba ya samo takardar izini a dubata, yana kawowa likitoci suka duk'ufa kanta, tun matashin nan na kai da kawowa harya fara zaune yana jiran fitowar likotocin, mutanen da suka taho tare ma jira suke tare da jimami, ana haka wata docteur ta fito tana tambayar wanda suka kawota, a sukwane suka rufeta suna fad'in sune, a nitse tace "kune 'yan uwanta?"
Matashin ne yayi karaf yace "a'a, muma tsitarta mukayi, ina fatan dai lafiya ko?"
Wani kallo ta masa tace "kai baka ga yanda kuka kawota bane har kake maganar lafiya, muna buk'atar dan ginta dan akwai aiki da za'a mata ana buk'atar saka hannunsu."
A raunane yace "gaskiya bamu san kowa nata ba, amma in ba damuwa mu saimu saka hannun."
A wulak'ance ta kalleshi tace "ok ina zuwa."
Juyowa matashin yayi yace "dan Allah iyayena kuyi hak'uri, ina so ku bani had'in kai mu taimakawa baiwar Allah nan."
Wani dattijo ne yace "ba komai yaro, muma fa iyayene, fatanmu dai Allah ya bata lafiya."
Fitowar docteur d'in tasa suka maida hankalinsu a kanta, matashin ta kalla tace "ka biyoni tare da wani dattijo d'aya a cikinku sai kusa hannun."
Binta sukayi ta kuma nuna musu suka saka hannu, saida suka tashi zasu fita matashin yace "dan Allah wane irin aikine za'a mata?"
"Kai baka san aikin da za'a mata ba kasa hannu, saboda ba yar uwarka bace kenan?"
Kai ya girgiza yace "ba haka bane, kawai dai muna so ne mu taimaketa."
Tsaye ta mik'e ta wuce tana fad'in "d'inki za'a mata saboda tana zubar da jini dayawa."
A haka suka kasance har rana ta take sosai amma ba wani labari, ganin haka yasa dattijawa biyu suka bar wajen ya rage sai su uku a wurin.
*Tun daren jiya* Mamie ta kasa bacci saboda ganin k'arfe d'aya tayi, a al'adar Khairat kuma bata kai wannan lokacin, kai kawo ta dinga yi a tsakiyar falo ita kad'ai duk hankalinta a tashe, *03: 17* Papa ya bud'o k'ofar d'akin ya shigo a halin daya fi shigowa, tsaye tayi tana kallonshi harya k'araso ya zube saman kujera yana maganganun dashi kanshi baisan me yake fad'a ba, durk'ushe tayi gabanshi cikin kuka tace "Alhaji, Khairat fa bata dawo gidan nan ba har yanzu, dan Allah kayi wani abu kar komai ya samu 'yata, dan in haka ta faru wallahi ba zan yafe maka ba."
Wani fizgo hannu ya fara a cikin muryarshi ta maye yana fad'in "to saime idan bata dawo ba, ita d'in yarinya ce? ki barta tayi sha'aninta taji dad'in rayuwarta, ke kad'ai ce a duniyar nan baki waye ba ai."
Cike da damuwa ta sake cewa "dan Allah Alhaji ka taimaka ka dubo min ita ko kasa a dubota, wallahi nasan Khairat ba zata jima haka kawai ba a waje saida dalili, jikina yana bani kamar akwai wani abu dake shirin faruwa, wallahi hankalina ya kasa kwantawa gabana fad'uwa yake."
Abin takaici ashe duk maganar da take yayi bacci, dole ta gyara zamanta a k'asa tana ci gaba da kiran wayar Khairat gashi tana kururuwa amma ba'a d'auka ba, haka ta kasa rintsawa har gari ya waye lokacin kuma Papa ya farka a cikin hayyacinshi, a lokacin data fad'a masa halin da ake ciki hankalinshi ya tashi sosai kuma harya fara mata fad'a wai bata fad'a masa ba, nan ta fad'a masa halin daya shigo da abinda suka tattauna kafin bacci ya d'aukeshi.
Aifa hankaline ya tashi dama na Mamie tuni a tashe yake, a lokacin kuma su Musa sunzo wajen aikinsu cikin kaki, nanfa ya sasu nemo mashi Khairat duk in da take, saboda su sun san komai kawai sai suka fara tafiya gidan rawar suna binciken k'arya, anan kuma suka samu wayarta , haka a wajen da suka jefar da ita suka tsaya suna tambayan mutanen wajen ko basu ga wani bak'on al'amari ba, saboda ganinsu da kayan soja yasa aka fad'a musu abinda ya faru, nan fa suka dawo gida da qarfin gwiwa sun samu labarinta, Papa da Mamie basu zauna ba suka rankaya zuwa asibitin, kai tsaye asibitin *Clinic Poudrière* anan suka samu mutanen da suka kawo Khairat asibitin, matashin ne ya fad'a musu halin da suka kawota, cikin fitar hayyaci Papa ya shak'i wuyan matashin yana fad'in,
"Wallahi baku isa ba sai kun fad'a min abinda kukawa 'yata, ka fad'a min me kuka mata?"
Matashin kam zare ido ya fara yi baisan me zaice ba, suna haka likitoci biyu maza da d'aya mace suka fito daga d'akin da Khairat take, da sauri suka nufi wajensu banda Mamie data zube wajen kamar gawa sai hawaye kawai dake zuba a idonta, "likita meya faru da yarinyata?"
A tsanake likitocin suka kalleshi kafin babban docteur d'in yace "kaine mahaifinta?"
"Eh nine, dan Allah ka fad'a min meya faru da ita?"
"Ok to, yallab'ai ka biyoni ciki saina maka bayani."
Kamar zai tashi sama haka ya bishi har kamar zai shiga gabanshi, sun d'auki 'yan mintuna da shiga Mamie ta dawo hankalinta ta tashi tabi bayansu dan taji abinda za'a fad'a, da isarta yayi daidai da bayan kwantar da hankalin da likitan yayiwa Papa ya kalleshi yace "kayi hak'uri yallabai, fyad'e akawa 'yarka."
Mamie na jin haka ta k'arasa fad'uwa a gurin somammiya, Papa kuma wani kuka ya saki kamar yaro yana kiran "a'a, a'a, ba dai akan 'yata, me yasa ba za'a rama a kaina ba, na shiga uku na lalace."
Likitan ne yace "yallab'ai ka saurareni kaji."
Kallonshi yayi yana goge hawaye da babbar rigarshi yace "ina jinka."
A hankali kuma a nutse likitan ya fara magana "'yarka tana cikin wani hali da take buk'atar kulawa, bawai fyad'en ne ba abun tashin hankali, yawan mutanen da suka mata fyad'en sune abun dubawa, duk da mun rasa wasu hujjoji saboda ba'a kawata da wuri ba a asibiti, amma dai munyi k'ok'arin gano wasu abubuwan, mun bata duk wata kulawar da take buk'ata a yanzu tare da taimakon wanda suka kawota, mun mata gwaje gwaje na cutuka da akan iya d'auka ta hanyar saduwa, kuma alhamdulillah a yanzu dai babu wani abu mai yiyuwa ko nan gaba, sai kuma akwai raunika da dama da aka ji mata mai yiwuwa tayi fad'a da mutanen sosai, dan mun samu karaya a hannunta da tsakanin cinyarta da k'ugunta, sai kuma gocewa a yatsunta biyu da kuma wasu raunika da suke nuna dukanta akayi, akwai ciwo a kanta daya ja mata matsala sai dai munyi k'ok'arin shawo kanta, badan ciwon a cikin gashinta yake ba da iska ya shiga akwai yiyuwar ta kamu da ciwon mantau.
"Ciwon daya bamu wahala, shine ciwon da suka ji mata a gabanta, 'yarka tana d'aya daga cikin irin matan nan masu tsukakken gaba, wasu daga ciki zaka ga ko haihuwa basa iya yi da kansu sai an masu aiki, wasu kuma ba zasu haihu da farko ba amma sai kaga cikin ikon Allah sun haihu a gaba da kansu, gaskiya 'yarka bana jin tana daga cikin masu samun damar haihuwa da kansu ko a gaba in ba wani iko na ubangiji ba, ko mijinta ne na aure zai shigeta dole saiya had'a da dabaru, amma kasancewar sun mata ta k'arfi hakan yasa sun b'arkata sosai, idan kaga gabanta kafin a mata aiki zaka d'auka *anus* d'inta da *vessie* (gabanta da duburarta) a had'e suke, amma cikin ikon Allah mun di'nketa sosai d'inki kuma ba adadi, sai kuma jini da muka d'auka a lab muka saka mata dan tana buk'atarshi."
"Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un." abinda Papa ya dinga maimaitawa kenan, hawaye taf da ido ya dag'o yace "kana ganin zata rayu ma? danni na cire rai da ita."
"Haba yallab'ai, ya zaka cire rai da rahamar ubangiji? ai insha Allah babu abinda zai sameta, zata tashi in Allah ya yarda ma."
Sake kallonshi yayi yace "to ya take yanzu?"
Cikin i'ina yace "eh...to, yanzu dai..tana kwance...insha Allahu,zata farka , amma dai har yanzu a some take bata san in da kanta yake ba, kawai muna gane tana raye da ta hanyar na'urar dake nuna mana numfashinta."
"Yanzu miye abunyi?"
"Eh yanzu kam babu wani abu, akwai magungunan da za'a d'orata ne kawai idan aka siyo, sai kuma kud'in duka aikin da aka mata, gashi nan a rubuce." ya fad'a tare da mik'a masa takardar.
A sanyaye ya amshi takardar ya mik'e ya fara takawa, yana bud'e k'ofar yaci karo da Mamie kwance a wajen, da sauri ya zube yana jijjigata yana kiran "Na'ima, Na'ima, dan Allah ki tashi, meya faru dake?"
Likitane ya k'araso ya kiran likita mace suka kamata aka shiga da ita emergency dan bata taimakon gaggawa, Papa ji yake shima kamar zai fad'i amma da taimakon su Musa ya samu ya zauna numfashinshi na fita d'aya d'aya, saida suka d'auki kusan awa d'aya sannan likitan ya tsaya gaban Papa, ganin halin da yake ciki yasa yace masa "ka kwantar da hankalinka yallab'ai, Hajia na samun sauki, zata farfad'o nan da zuwa yamma."
Cikin kuka yace "dan Allah zan iya ganinsu?"
"Eh to, sai dai Hajiar amma banda 'yarka."
Sake sunkuyar da kai yayi yana ci gaba da zubar hawaye, wucewa likitan yayi shi kuma ya bawa su Musa takardar maganin yace su duba mota akwai kud'i su siyo, saida suka tafi ya nufi wajen mutanen da suka kawo Khairat asibiti ya basu hannu yana musu godiya, wani dattijo ne yace,
"Ba komai yallab'ai, ai yiwa kaine, Allah dai ya bata lafiya."
Idon nan jawur ya kalleshi yace "ameen na gode, amma dan Allah kun shaidani?"
Murmushi sukayi d'aya yace "yallab'ai waye bai sanka ba, ai mun shaidaka tun shigowarka."
Duk da baiji dad'i ba amma haka yace "to dan Allah wata alfarma nake nema a wajenku? ina so dan Allah abin nan daya faru akan yata ya zama sirri tsakanina daku, idan maganar nan ta fita wallahi zamu shiga uku, ko yarfen siyasa saiya addabemu bare kuma jama'ar gari."
Had'e hannaye yayi alamar rok'o ya sake cewa "dan Allah, ku rufa mana asiri, kar maganar nan ta fita waje, wallahi za'a mana dariya ne ana fad'in munanan kalmomi a kanmu."
Matashin saurayin nan ne yace "yallab'ai karka damu, wallahi babu wanda zaiji maganar nan, insha Allah zamu rik'e wannan sirrin tunda ba wani abun fad'a bane, duba da zamanin da muke ciki, idan bai faru akan k'anwarka ko yayarka ba, to zai iya faruwa da wata shak'ik'iyarka."
"Na gode sosai, Allah ya saka muku da alkairinsa, Allah ya taimakeku kamar yanda kuka taimakeni."
Haka suka bar wajen suna mata fatan samun lafiya, shi kuma ya zauna zuciyarshi na tafasa, sai dai a yau yana ji har abada ya daina neman mata da kuma shan giya, kanshi qasa a hankali ya furta "in dai anyi duniya dan Manzon Allah S.A.W, to nabar giya da matan banza har abada, domin abinda nayi da yaran wasu yau gashi an ninka wannan abun akan yata, ban tab'a ma 'yar kowa fyad'e ba tunda nake, kowace mace na kusanta to da son ranta ne na kuma biyata, amma yau sai gashi namiji fiye da d'aya ya kusanci 'yata da k'arfi, wannan cin zarafi yayi yawa, Allah ina rok'onka gafara abisa zunubaina, wannan tuba tubane na gaskiya, wallahi ba zan sake ba har duniya ta nad'e."
Bayan su Musa sun kawo maganin da wasu allurai an kaiwa likitan, Papa kuma ya tara su Musa yayi tsaye gabansu yace "ku jini da kyau, ina so ku koma gidan rawar nan ku bincika min komai daya faru a wajen, ina so ku zage damtse ku samo min wad'annan 'yan iskan da suka lalata min rayuwar ya, dan wallahi ba zasu ci banza ba dole na d'auki mataki a kansu, dan haka kuyi da jiki ku gaggauta kawo min su cikin kwana uku, ina so kafin Khairat ta dawo hayyacinta su fuskanci hukunci."
D'orawa yayi da "kun fahimta?"
Da k'arfi suka amsa da "Eh yallab'ai."
"To ku motsa, ni ku barni da driver, yanzu wannan shine aikinku kuma yafi tsarona mahimanci."
Anan ya basu umarni shi kuma ya shiga d'akin da Mamie take, k'ura mata ido yayi yana tunano rayuwar da sukayi, hakika yana k'aunar Na'ima fiye da yanda yake k'aunar kanshi, abubuwan da yake kawai sabone yasa kasa dainawa duk da bata so, amma yau kam yayi tuba na gaskiya, likitace ta shigo tana fad'in "sannan yallab'ai, ya mai jiki?"
Kai ya girgiza yace "ku zaku fad'a min, dan har yanzu banga ta farka ba."
Murmushi tayi tace "zata farka yallab'ai, saboda hawan jininta yasa aka mata allurar bacci, kuma gashi jininta ya hau, amma yanzu zan sake dubawa na gani."
Sake awo ta mata sannan tace masa "mu gode Allah yallab'ai, jininta ya koma daidai, amma dole a guji abinda zai tayar mata da hankali idan ta farka."
Shiru yayi dan yasan ba lallai taso ganinshi ba idan ta farka, dan kullum maganarta kar abinda yake ya shafi yarsa, kuma yanzu yasan da bai tab'a kusantar 'yar kowa ba ba abisa sadaki ba, to da duk rashin kunyar Khairat babu wanda ya isa ya mata irin wannan cin zarafin , dan haka ya tashi ya fita daga d'akin, a lokacin 'yan uwa na kusa dana nesa har sun fara samun labarin Khairat ba lafiya da Hajia Na'ima, zuwa bayan magrib yan uwa sun fara zuwa ganinsu, Mamie kad'ai suke gani su koma hakan yasa Papa ya shawarci likitan suka k'ara tsaurara tsaro akan Khairat.
*Tun daga wannan rana*....
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgee❤: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Bismillahi walajna, wa bismillahi kharajna, wa 'allah lahi rabbina tawalkalna* _addu'ar shiga gida._
_Bismmilahir-rahman-rahim_
8⃣
*India* tun jiya Mammie ke kiran shalelenta Khairat amma bata dagawa, bayan gari ya waye ta sake doka mata kira amma shiru, abinne ya dameta dan haka ta fara kiran Mamie, amma itama ba'a dauka saboda wayar na gida, ganin itama an kasa dauka yasa ta fara kiran Papa cikin b'acin rai, shi kuma tun daren jiya yasa wayar vibration saboda kar a takura masa, nan ma ba amsa dan haka Mammie take jin in har aka sake riskar gobe a haka to tabbas zata shigo gida niger.
Wani jami'i ne aka tsayar dashi a kofar d'akin da Khairat take ba'a bari kowa ya ganta, kannan Papa da Mamie ne kad'ai suka ganta shima sau d'aya, tunda Mamie ta farka take kuka tana wa Papa Allah ya isa cikin fitar hayyaci, hakan yasa itama ta zama cikin tsaro tunda ya zama kamar suna fallasa sirrin gidansu ne, har yanzu Papa baije gida ba haka ma Mamie gaba d'aya basa cikin nutsuwarsu, hakan yasa kuma sai maganganu suka fara fita musamman daga wajen yan uwa wanda suka ga jikin Khairat d'in
Nan suka fara fad'in kila wa kala ama dai suna gani kamar fyade aka mata, dama duk abinda aka ce ya fara da jitajita to dole a samu banbancin kalamai, a cikin *kwana uku* sai gashi manganu suna yaduwa akan amma Khairat fyade, duk da tsaro da kuma boye abinda ake amma bai hana maganar fita ba.
Wasu kuma suna cewa ba wani fyade kawai dai dubunta ce ta cika watakila sun samu matsala da abokanan shekewarta ne kawai, to haka dai aka dinga yada wannan magana, kuma abu ga manyan mutane dan danan sai labari ya game gari, mutane nata tururuwar zuwa dan ganin kwam amma babu mai ganinta koda kuwa cousine d'inta ne, haka labari ya samu masana'antarta kuma suma sun zo ganinta sai Papa kawai suka ma jaje, amma manager Papa yace a barshi ya ganta saboda sun jima tare ya aminta dashi.
*Duk badakalar nan* da ake Khairat bata san me ake ba, tana kwance da na'urori a jikinta kamar wacce ta shiga halin doguwar suma, ruwa da sassaukan abinci duk ta tiyo ake bata su, duniya kenan.
*Umar Faruk* ma tun ranar bai sake zuwa masana'antar ba, sai dai ya shirya ya fita kamar ya tafi aikin saboda Babanshi amma kuma fafutukar samun wani aikin yake zuwa, dan ya riga daya cire rai da aiki a karkashin Khairat.
Yau ta kama *lahadi* Faruk na kwance d'akinshi akan kafarshi Baba ya shigo, yana ganinshi ya mike zaune yana fad'in "sannu da zuwa Baba."
Bai amsa mashi ba sai kallonshi da yake, tsarguwa yayi da kallon dan haka yace "Baba, da wata matsala ne?"
"Eh, da matsala."
Kallonshi yayi yace "subhanallah, meya faru Baba?"
Gyara tsayuwarsa yayi yace "Faruk, yanzu har kiyayyar da kake ma yarinyar nan ta kai haka, da har zata kwanta rashin lafiya amma ka kasa fad'a mana ko dai mu mata addu'ar samun sauki?"
Duk da bai fahimci Baban ba amma haka yace "kayi hak'uri Baba, wace yarinya kenan?"
Dakuwa Baba ya masa yace "ban sani ba, har ni zaka tambaya wace yarinya? aiku ku kafi kowa labarin abinda ke faruwa tunda ku ke aiki a ma'aikatarta."
Cikin mamaki yace "Baba wai, Khairat kake nufi? meya sameta to? ni bana da labari."
Shima da mamaki ya kalleshi yace "Umar Faruk kamar ya baka da labari, kai yanzu kace baka san meke faruwa ba? bayan kullum kana fita."
Ganin karya ballowa kansa wani liki kawai sai yace "a'a Baba, kasan da yake ina da aiki sosai shi yasa bana da lokacin wani shirme , amma wallahi bansan meya faru da ita ba."
Juyawa Baba yayi zai fita yace "amma Baba me yake damunta?"
"Humm, idan kaje bureau d'in gobe kaji meke faruwa."
Yana fad'a ya bar d'akin shi kuma ya fad'a duniyar tunanin abinda ya samu Khairat, gashi dama har yanzu yana ganinta a idonshi a cikin wannan shigar, tsaki yayi kawai ya kwanta amma ya kasa komai sai tunanin wannan daren yake.
*Safiya* nayi ya shirya kamar yanda ya saba ya fita sai dai yau ma'aikatar ya tafi dan jin meke faruwa, da sameshi ko sai yayi sa'ar ganin manager a farfajiyar wajen zai shiga mota da alama fita zaiyi, da sauri ya karasa suka gaisa kafin manager yace "Faruk ashe kana nan ka daina zuwa aiki?"
Kai ya shafa yace "eh yallabai ina nan, nasan ko nazo ba zata barni ba shi yasa ma bana zuwa."
"To yanzu meya kawoka?"
Nan ma kai ya shafa yace "yallabai nazo ne naji meke faruwa anan? dan jiya Baba ya sameni yana fad'an wasu maganganu da ban gane ba."
"Kamar me kenan?"
Shiru ya d'anyi sai kuma ya kalli saman ginin yace "Hajiar tana ciki?"
Da mamaki yace "Umar Faruk, kar dai kace min baka san meke faruwa ba? Hajia Khairat ai yau kwananta hud'u bata fitowa."
Dammm , yaji gabanshi ya tsinke ya fad'i, saida ya had'e yawu yace "to meya sameta?"
Ajiyar zuciya manager ya sauke yace "yanzu dai kaga ganinta ne zanje, idan zaka iya mutafi tare mana?"
"Ganinta kuma, a ina?"
"Asibiti."
Ji yayi duk ba dad'i sai kawai yace "ba damuwa muje."
Zagayawa yayi ya shiga motarshi suka d'auki hanya tare, amma ya rasa dalili sai yaji zuciyarshi na bugawa d k'arfi ga gabanshi dake ta fad'uwa babu gaira babu dalili, a haka suka isa asibitin jami'in dake tsaron k'ofar d'akin yana ganin manager ya kauce masa ya wuce amma saiya hana Faruk, manager ne yace "dan Allah abokina ka barshi ya wuce, dani dashi duk d'aya ne."
Cewar jami'in "gaskiya ba zai wuce ba wannan doka ce, kayi hak'uri ka koma."
Papa ne yaji maganarsu daga cikin d'akin dan haka ya lek'o duk da baiga ko suwaye ba amma kawai sai yace "barsu su shigo kawai."
Da sallama suka shiga amma sallamar Faruk saita tsaya cak saboda ganin Khairat a wani hali na daban, cikin sanyin jiki da rauni ya k'arasa gaban gadonta ya tsaya yana kallon fuskarta dake d'aure da bandeji , Papa kuma d'akin kusa dana Khairat ya shiga in da Mamie take kwance, a hankali ya kalli manager yace "meya sameta haka, hatsari tayi?"
Kai kawai ya girgiza masa, sake maida kallonshi yayi gareta yana k'ara jin tsoron ubangiji na shigarshi, wai wannan matashiyar mai tsiwa da girman kai da raina mutane yau gata kwance, ta sauya kamanni kamar ba ita ba duk kusan rabin jikinta bandeji ne sai jini, bin qafarta yayi da kallo wacce tayi sumtum da ita ta kunbura , kallon yatsun qafar yayi wanda suka sha akaihu da kalar pink, kallon fuskarta yayi idonta rufe gashin idonta duk ya kwanka luf kamar na kanti, wata har sharasharar rigace fara aka lak'aba mata.
Suna haka wayar manager tayi k'ara dan haka ya fito da ita ganin mai kira yasa ya fita daga d'akin dan amsa wayar, kujerar dage gaban gadon Faruk ya zauna yana kallon k'afarta dake rataye da gado tasha k'arafa saboda dorin da aka mata haka ma hannu, sosai zuciyarshi ta karye saboda ganin halin da take ciki, sama sama ya fara jiyo murya daga d'aya d'akin ko ba'a fad'a masa ba yasan muryar iyayenta ne, tsaye ya tashi saboda ji da yayi muryoyin na sake sama kuma kamar zasu fito daga d'akin.
Juyawa yayi da nufin barin d'akin kawai yaji har sun fito, muryar Mamie ce ta fara magana cikin tsananin kuka da fitar hayyaci ta nuna Khairat dake kwance tace "ka dubi yarinyar nan dake kwance waya ja mata shiga wannan halin? kaine duk kaine sila."
"Ka sani wallahi jira kawai nake 'yata ta samu sauk'i mu raba kanmu da kai , dan in har zamu ci gaba da zama da kai , to ya zama dole sai mun shirya karb'ar bala'en da suka fi wannan, bansan me yasa nayi wannan kuskuren ba duk da na karanta cewa bai hallata ba zama da fasik'i ba, yau gashi abinda ka shuka yarka ta fara girbarshi, gashi gyaran kuskurenka zai zama alhakin 'yarka, to sam ba zan yarda ba wallahi, dole ka sakeni nayi nesa da kai da yata dan mu tsira da rayuwarmu da lafiyarmu."
"Ka dubi k'ask'ancin da aka mata, nasan ko kai baka tab'a shigar da 'yar wani a wannan halin ba, amma yau gashi yarka mutum d'aya d'aya har guda hud'u ne suka keta mata haddi , yanzu haka ya maka daidai kenan? kaji dad'i?"
Duk da kuka yake amma cikin dakakkiyar zuciya yace "Na'ima, wai me yasa kike da taurin kaine? me yasa baki da yafiya a rayuwarki? tunda abin nan ya faru nake baki hak'uri amma kinki hak'ura, na rantse miki da Allah Na'ima nayi nadama kuma na tuba ga Allah, wallahi ba zan sake aikata sab'o irin wanda nayi a baya ba, dan Allah Na'ima ki sake bani dama mu sake sabuwar rayuwa, muyi fatan ganin Khairat ta samu lafiya, ni kuma na miki alk'awarin saku farin ciki sannan zan samar ma Khairat miji na gari na had'ata dashi, kuma wallahi daga yanzu duk abinda ki kace nayi zanyi Na'ima amma banda rabuwa dani."
Murmushi tayi tace "oho , kenan sai yanzu zaka fara maganar yi mata aure, kenan yanzu ne kake ganin Khairat ta isa aure? to kai a ganinka waye zai yarda ya aureta a yanzu bayan ta rasa kimarta , ai kowane namiji yana alfahari ace shiya fara sanin matar daya aura, wallahi Mani duk wanda kaga ya auri Khairat a yanzu to abu d'aya ne, shine dukiyarka, amma duk wanda ya auri Khairat dan Allah to ka sani wallahi taimakonta yayi kuma *JIHADI* yayi."
Juyawa tayi ta zauna kusa da Khairat ta fara shafar kanta tana zubar da hawaye, shima Papa hawayen yake yi yana kallonsu, Umar Faruk kuma ya kasa motsawa saboda tunanin kamar basu lura dashi ba ma a wajen, baya baya ya fara ja yana so ya sulale daga wajen kawai yaji an bud'o k'ofar an shigo, ya dauka manager ne ashe Kakar Khairat ce ta zo daga India, maida kallonsu sukayi gareta da sauri duk suka tashi kowa na fad'i "Mammie, yaushe kika zo?"
Hannu ta d'aga musu tana kallon Khairat dake kwance a tsananin mamaki, bata d'auke idonta akan Khairat ba tace "meya samu gimbiyata? me kuka mata?"
Mamie ce ta fara kame kame tace "Mammie babu komai fa, ta samu wani d'an hatsari ne."
Cikin d'aga murya tace "wane irin hatsari ne wannan? zaku fad'a min gaskiya ko saina tsine muku albarka."
Da sauri Papa yace "a'a Mama, dan Allah kiyi hak'uri, wallahi..."
Kuma sai yayi shiru, ganin Mammie ta kafe Mamie da ido yasa ta fara i'ina tana fad'in "Ma...ma wa...sune..suka , wasu ne....suka, suka mata fyad'e." ta k'arasa da fashewa da kuka.
A nitse Mammie ta k'arasa gaban gadonta ta durk'usa tana shafa kanta tana zubar da hawaye, kuka suke sosai babu wanda yake bawa wani hak'uri a cikin wannan hali Umar Faruk ya sulale ya fita, a farfajiyar wajen ya samu manager yana waya , saida ya jira ya gama suka shiga mota suka wuce in banda tunanin halin daya ga Khairat da abinda yaji mahaifiyarta ta fad'a babu abinda yake, a haka har suka kai ma'aikatar manager yace kawai ya shigo yaci gaba da aikinshi kafin Allah ya bata lafiya.
Nan ya shiga ya kuma zauna mazauninshi, abokinshi Ishaq da wasu ma'aikatan mata da maza ne suka taru suna tattauna abinda ya faru da Khairat d'in, d'aya daga ciki ne yace,
"Koda dai har yanzu babu tabbas, amma duk mai hankali ai zaiyi zaton wani abu."
"Gaskiya ne, wallahi abar tausayi, nasan tana cikin wani hali ne shi yasa ma ba'a bari a ganta."
Wata matashiya ce tace "wacece abar tausayin? Khairat d'in, ni kuma wallahi ko kad'an banji tausayinta ba, dan nasan ba wani mummunan abu bane a wajenta."
Faruk ne ya kalli matashiyar ya taso ya tsaya gabanta, duk da yana k'ok'arin tausar kanshi, amma haka kawai yaji zuciyarsa na masa zafi akan abinda suke fad'a, basu san da zuwanshi ba sai muryarshi suka ji yace "wannan maganar bata dace ace ta fito daga bakinki ba a matsayinki na mace, tausayi da jimami ya kamata a gani a tare dake, kamata yayi ace kinji cewar an tab'a kimarki kema saboda 'yar uwarki mace aka tab'a, ki tuna fa kema macece kuma bana miki fata, amma kema kina cikin wannan k'alubalen dan haka zata iya faruwa dake, dan Allah ku dinga kyautatawa juna zato."
Tab'e baki tayi ta kau da kai tana fad'in " ni dai nasan ina zaune da kowa lafiya, kuma kamar yanda na fad'a a baya bana jin Khairat wani sabon abune ya sameta bare kuma taji zafinshi."
Sake gyara tsayuwa yayi cikin b'acin rai da d'aga murya ya fara magana "bata jin zafi kike cewa? kinsan me fyad'e yake nufi? shin kin tona zuciyarta kinga me take ji? shin kin tab'a kwatanta me zaki ji a zuciyarki ace namijin da baki had'a komai dashi ba ya tursasaki ya kusanceki? kefa macece, ki misalta kona second goma kiji me zaki ji a zuciyarki."
"Shin kinsan halin da take ciki? kin ganta da idonki bare kisan me take ji? kije, kije kiga halin da take ciki, kina gani nasan dole ki yarda tana cikin wani hali, kinsan zafin karaya a hannu bare kuma a qafa? shin kin tab'a yin hatsarin da yasa kika ji raunika? to ita a sanadiyar abinda ya faru tana can kamar wacce babbar motar ta bige, dan Allah ki sawa zuciyarki tausayi kodan kasantuwarki mace."
Yana fad'a ya bar wajen ya fita farfajiya zuciyarshi in banda tafasa ba abinda take, ji yake kamar zai fashe da kuka amma kuma ya kasa, a hankali ya tambayi kanshi "wai me yasa ka damune? Khairat ce fa."
Saida yasa hannu ya goge idonshi da yaji sun cika da k'walla sannan yace "rashin imanina bai kai na kasa tausaya mata ba."
*Haka* Faruk ya kasance cikin wannan damuwa da tunani har yaje gida, haka ya dinga tunanin abinda idonshi suka gane mishi a ranar, kai da kawo yake a tsakiyar d'akinshi yana fad'in "rigarta, wannan saurayin, matashin da yazo daga baya, d'aukewar wuta, dawowar wuta bayan qanqanin lokaci, b'atan Khairat, sai kuma....sai...sai kuma me?"
Ci gaba yake da kai da kawowa har saida ya tsaya cak baki bud'e ido waje, a hankali ya furta "wannan motar, wannan *CRV Honda* d'in, tabbas akwai alamun tambaya akan wannan motar, me yasa take gudu a cikin wannan daren, sannan ina suka nufa da suka ratsi wannan jejin?"
"Dole nasan wani abu a game da motar nan, dole na koma wajen nan."
Wata zuciyar ce kuma tace "to wai akan me? ka barsu da matsalarsu mana."
"A'a, ka tuna fa kana k'annai mata dayawa, ya zaka ji idan d'aya daga cikinsu ce? koda namiji d'aya ne ba zaka ji dad'i b bare har hud'u saboda rashin imani, zanyi wannan taimakon a matsayin *jihadi* fisabilillah."
_To Umar Faruk Allah ya bada sa'a._
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgee❤: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
πππππππ
_Farin ciki auntynmu ta dawo, *ASMA'U GALADIMA* (ummu Maryam), marubuciyar *Dijah Qaya* ina miki barka da dawowa._
_Bismmilahir-rahman-rahim_
_Allahumma antas- salam, waminkas-salam, tabarakta ya zuljalali wal- ikram._
9⃣
Har gaggawa yake gari ya waye, alwala yayi ya fara tsayuwar dare kamar yanda ya saba, ya jima yana sallah har aka kira asuba sannan ya nufi masallaci tare da sauran 'yan uwanshi, saida gari yayi haske suka dawo yana zuwa shiryawa yayi ya fita ko kari baiyi ba, kai tsaye asibiti ya nufa dan yana so ya d'an samu wata makama da zai iya dafawa a matsayin k'warin gwiwarshi.
Sammakon da yayi yasa ya tarar da Papa a k'ofar d'akin da Khairat da Mamie suke tare dasu Musa bayan sun fad'a masa har yanzu basu samu wani abu ba, cikin b'acin rai da sassauta murya yace,
"Wannan ai maganar banza ce, ba zai yiwu ba, ku dubi Khairat nan fa kwance har yanzu bata farka ba, me kuke so nace mata idan ta kalleni? to kuji wallahi ku shiga duk in da zaku shiga ku nemo min 'yan iskan nan, idan ba haka ba ranku ne zai b'ace, kunji na fad'a muku."
Yana fad'a ya koma cikin d'akin su kuma suka jiyo Musa na fad'in "kaji d'an wahala, to ya zaiyi in bamu samosu ba? dole dai a qarshe ya hak'ura tunda ba mik'a k'anmu zamuyi ba muce mune muka mata fyad'en."
Da sauri Faruk ya juya yana binsu da kallo matuk'ar tsoro ya bayyana a fuskarshi sosai, yana kallo har suka shiga motarsu CRV Honda, hannu yasa ya rufe bakinshi yana fad'in "inna lillahi wa'inna ilaihir-raju'un."
Juyawa yayi ya koma ya hau mashin d'inshi dan baya da hujjar da zaice sune kai tsaye dole ya samu wata makama da zai nuna eh sune, saida ya koma har club d'in nan sannan ya fito ya d'auko hanyar, a hankali yake tafiya yana dube dube har saida ya kawo wajen da motarnan ta shiga kwana, nan yabi yana waige waige yana dubawa ko zaiga gida da makamantansu, wasa wasa dai bai samu komai ba har saida hanya ta b'illo dashi kusa da unguwar airport, ganin idan ya koma baya zai maida kansa baya ne kawai saiya shiga kwanar da zata sadashi da titi, zai hau titi kenan motar su Musa ta shigo kwanar suka nufi hanyar daya fito, da sauri ya taka birki ya juya yana kallonsu, bai b'ata lokaci ba yabi bayansu har suka tsaya k'ofar gidan da Papa ya basu duk lokacin da suke bakin aiki.
Nesa da gidan ya tsaya da tunanin ko zasu fito, amma shiru shiru su Musa basu fito ba har suka kwashe awanni uku, tun yana gyara zama akan mashin d'in har ya kai gayin kwance a sama nan ma ya gaji ya sauka ya aza takalminshi ya zauna qasa.
Su kuma suna ciki dama duk lokacin da Papa ya matsa musu lamba nan suke dawowa suyi kwancinsu su huta sannan su koma suce masa babu labari, _(rainin wayo)_, sai lokacin suka fito suka shiga motarsu sukayi gaba abinsu, anan ya bar mashin d'in ya nufi gidan, ganin k'ofar rufe take amma katangar gajera ce yasa ya tuna yarinta d'araf ya haye katangar ya haura gidan.
π€£π€£π€£π€£π€£π€£π€£
Ganin k'ofar falon itama a rufe take kawai yasa ya dinga bangazar k'ofar har saida ta bud'e da k'arfi, nan ya shiga d'akuna hud'u ne a ciki, kowane d'aki b'alle k'ofar yayi ya dinga bincikawa ko zaiga wani abu amma shiru, d'aki na qarshe daya shiga ganin bai samu komai ba yasa ranshi ya b'ace ya daki armoire (wradrob) d'in da k'arfi, abinka ga d'akin maza ba'a kimtsa komai, kayane suka zubo daga ciki.
Durk'usawa yayi zai kwashe kawai yaga wata bak'ar mask ta fuska, d'auka yayi ya kalleta da kyau yana tunanin ko meye anfaninta, zai mayar da kayan saiya sake ganin wata, dan haka ya sake dubawa saiga guda hud'u ras sun bayyana, kai ya girgiza ya mayar da kayan har da mask d'in sannan ya rufe wradrob d'in fito ya daga d'akin, maida k'ofar falon yayi ya rufe duk da bata rufu ba.
Har zai wuce kuma ya tsaya yana kallon poubelle (abun zuba shara) d'in wajen, cike da mamaki yasa hannu ya ciro rigar da koba a fad'a masa ba yasan ta Khairat ce dan itace a jikinta a ranar, duk rigar ta yage sosai ga jini a jikinta har da pant dinta da kuma takalminta duk a cikin sharar, ji yayi idonshi sun kawo ruwa amma saiya aje rigar ya da kayan ya fita ya bar wajen, gudu yake sosai akan mashin d'in har saida ya kai asibiti.
Ya samu 'yan uwa dayawa a wajen wanda ba'a bari shiga ba, mai tsaron k'ofar Umar ya cewa "dan Allah ko zan iya ganin yallab'ai?"
"Lafiya ko? yallab'ai yace kar a takura masa fa."
"Kaga wallahi magana ce zamuyi mai mahimmanci, dan Allah ka barni na ganshi."
"Ka fad'a min ko miye saina fad'a masa." cewar jami'in yana d'auke kai.
"Maganar nan sirri ce, dan Allah kace ina son ganinshi."
A hassale jami'in yace "kai, wai kai wane irin mutum ne? nace maka yace kar a takura masa ko, kai baka ga yan uwa ba duk gasu nan amma ba'a bari sun shiga ba sai kai, dallah ka b'ace min da gani."
Ganin fa ba zai barshi ba yasa dole ya yanke shawarar fad'a masa, d'an sassauta murya yayi yace "kaga abokina, wata masaniya na samo akan mutanen da yallab'ai yake nema, dan Allah ka barni na ganshi kar lokaci ya qure mana."
Ido ya zaro yace "kenan kasan mutanan da ake nema? to su waye, kuma me sukayi?"
Kallon rainin wayo ya masa yace "kana nan kace baka san akan me ake nemansu ba?"
Cike da son jin gulma yace "wallahi ban sani ba, ba'a yarda kowa yasan meke faruwa ba."
Cike da k'osawa yace "yanzu zaka iya yimin magana dashi d'in ko kuwa na tafi?"
"A'a jira ina zuwa."
Yana fad'a ya shiga d'akin dan fad'a ma yallab'ai Papa, zaune ya samesu shiru dasu abin tausayi suna kallon Khairat, sunkuyawa yayi kusan kunnen Papa yace "yallab'ai wani saurayine a waje kesan ganinka, kuma yace akan maganar mutanen da ake nema ne."
Kallonshi yayi da sauri yace "ka tabbata?"
"Eh to, haka dai yace min."
Tsaki yayi yace "yanzu haka d'an jarida ne yayi basaja ko kuma masu son sanin meke faruwa, kawai kace masa ina wani uzuri ba zanga kowa ba."
Duk abinda ya fad'a a kunne Mamie dan haka bata ce k'ala ba ba ta mik'e zunbur ta fita daga d'akin, tsaye ta samu Umar Faruk yana jira, saida ta kalleshi da kyau tace "sannu bawan Allah, kaine kake son ganin Alhaji?"
"Eh nine Mama."
Cikin muryar tausayi tace "ka fad'a min wani abu da zaisa naji dad'i dan Allah."
Ajiyar zuciya ya sauke tare da gyara tsyuwa yace "kiyi hak'uri Mama, bansan taya zaki fahimci abun ba, amma dai tabbas anci amanarku, wanda suka ketawa yarku haddi suna nan tare daku, hasali ma sune kuke sawa nemo muku masu laifin."
A jujjuye ta fahimceshi dan haka tace "ban fahimceka ba yaro? ko zaka iya yimin dalla dalla?"
"Mama ba zan iya fad'a muku komai ba, amma ku aika wasu jami'an na daban ba wanda kuke tare dasu ba, suje unguwar airport daga farkon shiga unguwar a gida mai number 8, suyi bincike da kyau karsu bar komai, ina tabbatar muku zaku samu hojojjin da suke nuna masu laifin anan suke."
Tuni hawaye suka wanke fuskar Mamie tana kallon Umar Faruk tace "jirani ina zuwa kaji yarona."
Tana fad'a ta juya ta shiga ciki da gudu, Umar Faruk na ganin haka shima yayi murmushi kawai ya juya bar wajen, tare da Papa Mamie ta fito amma basu ga Faruk ba, nan Papa ya ciro waya jiki na rawa yasa aka turo mashi wasu jami'an, dan danan asibiti ta cika da jami'an kama daga police soldier da gendarme, nan fa suka basu jawabin abinda Umar ya fad'a musu, ina Papa ma ba'a barshi ba saida ya bisu.
Suna gaf da fita daga k'ofar asibitin motar su Musa tazo shigowa, nan suka tsaya suka fito suka sarama manyansu suma wasu suka sara musu, nan Papa yace su shiga mota su tafi an samu labarin in da mutanen nan suke, ganin yanda ya masu magana bai nuna wani abu ba yasa ransu yayi fari suna tunanin wasu ne aka lak'ama sharrin, amma tunda suka ga ana nufa unguwarsu gabansu ya fara fad'uwa, babu wanda baiji gudawa ba lokacin da aka tsaya k'ofar gidansu.
Duk da unguwa ce da babu mutane sosai amma saida jama'a suka fito kallo ganin yanda jami'an suka cika unguwar, Papa na fitowa ya duba yaga kwatancen daidai ne kawai ya juya ya kalli su Musa da sukayi sukayi sharkaf da zufa, hannu Papa ya nuna musu yace "ku kama min su."
Tuni aka cika aikin yallab'ai akayi ram dasu Musa aka d'aure su , gidan suka shiga nan fa suka fara shiga kusfa kusfa ana bincike, saboda Umar Faruk ya rage musu wahala hakan yasa suka samu hujjojin da Faruk ya gani har dama wanda shi bai gani ba kamar bras d'inta da d'an kunnai, haba su Musa ai tun daga nan suka fara shan duka.
_Kuyi hak'uri jami'an mu, akwai fa zafin rai._
Kasancewarsu jami'an yasa ba'a tausaya musu ba, cikin k'ank'anin lokaci har sun canza kama wai wannan somin tab'i ne kafin su gurfana a gaban kotu, tuni labari ya karad'e gari akan abinda ya faru da Khairat da kuma kama masu laifin, duk mai zuciyar imani ya tausaya mata sosai ace har mutum hud'u.
*02: 40* na dare Khairat ta farka da ihu tana fad'in a taimaketa zasu kasheta, Mamie da Mammie ne suka rik'eta sosai suna tofa mata addu'a harta nutsu, kuka take sosai tana d'aga murya kamar ranta zai fita, haka har suka wayi gari bata daina kuka ba, tunda likitoci suka nufi wajenta ta dinga kuka tana fad'in karsu tab'a ta su saketa ta koma gida, babu abinda suke ji kamar d'orin qafarta dan yafi hatsari, ganin abin ba qarami bane yasa Papa ma yace su sallamesu kawai.
Duk da ba haka aka so ba haka aka sallameta aka koma gida da ita, a d'akinta aka sake mata wani tanadin na ci gaba da jinyarta , amma duk da sunzo gida ma ba'a bari kowa ya ganta saboda kukan da take.
*Bayan sati d'aya* jikinta yayi dama dama sai dai har yanzu bata fara taka qafar ba, qananan raunikanta ne suka warke har akaihunta guda biyu sun toho, in banda shiru da tunani da hawaye babu abinda Khairat keyi hakan kuma na damun iyayenta.
Da farko an fara barin 'yan uwa na zuwa dubata, amma ranar da Mujahhid yazo da abokanshi su uku saita firgita sosai tana fad'in sune sune, tun ranar sai Mammie ta yanke shawarar tafiya da ita india danta samu ta dawo daidai.
Umar Faruk ya ci gaba da zuwa wajen aikinshi sai dai i zuwa yanzu babu wata damuwa a tare dashi, gaba d'aya ma mantawa yake da wata Khairat bare ta dameshi , yayin da d'aya b'angaren kuma yake soyayyarshi hankali kwance da 'yar uwarshi *Zubaida* wacce suka fi kira da *Zuby*, kuma suna jiran hutun 'yan makaranta domin shi zai basu damar zama miji da mata.
An shigar dasu Musa kotu kuma sun samu hukuncin shekarun da doka ta tanadar ga duk wanda ya keta haddin wata, tun akan akan hayarsu ta zuwa sabon gidansu suka fara tuhumar juna suna dorawa Musa laifin, shi kuma yace ba gaskiya bane tunda bai tilasta kowa ba.
_Wallahi ni duk abokin da ba zai anfaneni duniyata da lahirata ba to banga anfaninshi ba, domin kuwa kamar abotar shedan da yan uwata zata kasance, bayan ya ganka cikin wuta zai kora maka jawabinsa, bayan ya muku dogon jawabi da bama fatan jinshi daga qarshe dai zai ce ._
*Karku zargeni ku zargi kawunanku.*
_Allah ka karemu da yayenmu daga fuskantar qasqanci irin wanda Khairat ta fuskanta, Allah ka shirya mana zuri'armu shirin addinin musulunci._π
Mamie da Mammie ce suka kama Khairat daga bisa kujerar guragunta suka cire mata kaya sannan suka sata cikin bahon wanka dake d'auke da magunguna na ice kala kala, suna zaunar da ita ta rintse ido saboda zafin dake da ruwan, duk da kullum ake mata tunda suka komo gida amma ta kasa sabawa , a hankali ta bud'a ido hawaye suka gangaro, Mamie ce ta fita daga ban d'akin sai Mammie ta dinga tausarta da kalaman har saida ruwan suka huce sannan ta kira Mamie suka kamata suka fito da ita.
Mamie ce ta shiryata cikin doguwar rigar kantie iya gwiwa sannan suka zaunar da ita akan kujerarta, abinci Mamie ta d'auka ta fara bata a baki, da sun had'a ido Mamie take saurin dauke nata, ganin kuma ta kafeta da ido yasa duk ta tsargu , a raunane ta kalleta tace "akwai abinda kike so ki fad'a ko?"
Lumshe ido kawai tayi ta kawar da kai, Papa ne ya shigo cikin shiri da alama fita zaiyi, saida ya sumbaci goshinta yace "shalele ya kike?"
Da ido kawai ta kalleshi, sake fad'in "ya jikin naki? da sauk'i dai ko?"
Ganin dai ba za tayi magana yasa yace "shaleleta kiyi hak'uri kinji da abinda ya faru, ina tabbatar miki hakan ba zata koma faruwa ba."
Take idonta ya kawo ruwa cikin mamakin abinda ba suyi tsammani ba suka ji Khairat tace "wane mai hankalin ne zai sake sha'awata kuma? akwai wani abinda ya rage min ne da har zan birge wani?"
Maida kallonta tayi ga Mammie tace "Mammie, ki kaini waje dan Allah ina so nasha iska."
A hankali ta tuka kujerarta ta fitar da ita kamar yanda tace, lambun dake bayan gidan ta kaita ta barota kamar yanda ta buk'ata, shiru tayi tana kallon firanni na kad'awa ga iska mai dad'i.
Papa da Mamie ne suka fito daga d'akin nata suna zuwa falo yayi daidai da shigowar manager, bayan sun gaisa ya fad'a musu tare da sauran ma'aikata yake suna so suga jikin Hajia, Papa ne yace su shigo sannan yace Biba mai aiki taje ta taho da Khairat, zaune sukayi suna jiran shigowarta, Mamie kuma ko kad'an bata lura da Faruk ba yaron da take nema danta gode masa, madafa ta nufa domin samo musu d'an abun tab'awa.
Shigowar Khairat a keken guragu yasa kowa maida kallonshi gareta, mamaki al'ajabi duka a tare da ganin Khairat, ita kam ido ta kafesu dashi tana kallon kowa, a lokacin da kallonta ya sauka kan Umar Faruk kuma sai gabanta ya mugun fad'i, duk da haka kuma bata d'auke idonta ba, shima a nashi b'angaren gabanshi ne yayi mummunar tsinkewa ya fad'i, d'auke kanshi yayi ita kuma suka k'arasa shiga falon, sannu kowa ke mata da jiki amma babu wanda ya amsa, Papa ne ya shafi kanta yana kallonsu yace,
"Sai hak'uri fa, har yanzu magana na mata wuya, muma haka muke zaune da ita."
A bazata Umar Faruk ya sake satar kallonta amma sai idonsu ya sake had'ewa , suna haka har Mamie ta fito amma da qyar wasu suka sha ruwa dan ganin Khairat ya girgizasu sosai, tashi sukayi gaba d'aya suka fita, amma Umar Faruk dake daf da barin falon sai yaji kamar muryar Khairat a bayanshi, dan haka yayi saurin juyowa ya kalleta, dama itama shi d'in take kallo dan haka suka kalli juna, d'an sakin fuskarshi yayi daga had'ewar daya mata baisan sanda ya saki wani basaraken murmushi ba, ita kum sai taji haushi ya kamata dan tunaninta yayi farin ciki da abinda ya sameta.
*'YAN TEAM UMAR FARUK.*πππ
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgee❤: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
πΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎ
*Raina Fansane gareta*
πΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎπΎ
_My sweet Heenat, ina tayaki murnar kammala wannan littafi, tabbas ya qayatar tare da nishadantarwa, ga ilima da muka samu a ciki, wannan shine labari ina fatan ubangiji ya yafe miki kurakuranki sannan ya baki ladar dake cikin wannan fad'akarwa da ki kayi._ sai mun jiki a next novel.
_Bismmilahir-rahman-rahim_
1⃣0⃣
*Haka* kwanaki suka dinga tafiya sati ma ya fara shud'ewa har aka fara lissafa abinda ya faru da sati uku, a *sati uku* kuma duk wasu qananan raunika sunyi sauk'i sosai sai qafarta da har yanzu takata ya zama aiki, har yanzu Mammie na gasata a ruwan zafi tare da wasu saiwar magunguna da zai taimaka mata, haka ma an sake maidata asibiti an mata gwaje gwaje amma cikin ikon Allah babu wata matsala har yanzu.
A lokacin data cika wata d'aya sai suka fara shirye shiryen tafiya india, a lokacin kuma Mamie ta matsawa Papa akan ya bata takardarta, shi kuma ya dage ba zai bayar ba, amma ita taci alhwashin tafiya ko babu takardar saki, Mammie bata fahimci komai ba dan basa nuna da wata matsala a gabanta, Papa kam yayi tuba na gaskiya ya daina duk abinda yake yanzu, sai dai akwai barazana da wasu matan ke kawo masa saboda suna samun arzik'i sosai a hannunshi, duk da Khairat bata cika magana ba a yanzu amma dai bata kula Papa sosai haka ma Mamie.
Yau ta kama ranar *juma'a* Papa ya fito cikin shirin massallaci misalin k'arfe *10:00*, zaune suke a falo yayin da suka bishi da ido, durk'usawa yayi gaban Mammie ya gaisheta tare da fad'in "Mama zan tafi masallaci sai a mana addu'a."
Murmushi tayi dan ita har ranta tana ganin d'iyarta tayi sa'ar miji na gari, cikin sakin fuska tace "Allah ya tsare ya kareka daga sharrin masharranta, insha Allah ba zaka tab'e ba, domin kai mutumin kirki ne, duk da ban haifeka ba amma ka d'aukeni tamkar mahaifiyar data haifeka, babu abinda zance sai dai nace Allah ya saka maka da alkairi."
"Ameen ameen Mama, na gode da addu'ar nan Allah ya bar mana ke."
"Ameen." itama ta fad'a sannan ya mik'e yana kallon Mamie yace "ni zan wuce."
Cike da murmushi tace "to abban Khairat Allah ya tsare, saika dawo."
Shima cikin murmushi yace "ameen na gode."
Maida kallonshi yayi ga Khairat ya dafa kanta yace "shalele ni zan wuce, kiwa Papa addu'a kinji."
Sanin ba za tayi magana sai kawai ya wuce, muryar Khairat yaji tace "Allah ya kiyaye, a dawo lafiya."
Da sauri ya juyo ya taho a sukwane ua zube gwiwoyinshi gaban kujerarta, cikin farin ciki yace "Khairat, yau kece ki kawa Papanki addu'a? kai Allah na gode maka."
Duk da hawaye sun fara taho mata haka tace "Papa, duk munin halinka kai mahaifina ne, Papa ku yafe min da duk abinda na muku wanda ya b'ata muku rai, nasan hada hakk'inku dana kasa saukewa da kyau shi yasa haka ta faru dani."
Hannunta ya rik'e da sauri yace "a'a shaleleta, ba laifinki bane, laifina ne duk ni na ja miki, amma ki sani Papanki yayi nadama sosai kuma ya daina duk abinda yake yanzu."
"Khairat yanzu mahaifinki ya rabu da duk wani shirme na maida al'amurana ga ubangijina, shaleleta ki yafe min domin na cutar dake, duk nine...."
"Papa" cewar Khairat tana kau da kai gefe.
Shiru sukayi babu mai magana dan haka Papa ya tashi yana goge hawaye ya fita, Mamie ce ta matso kusanta ta rik'e hannunta tana shafawa tace "Khairat, ki yafe mana a bisa kurakurenmu, nima na taka rawa wajen faruwar komai a matsayina na uwa, amma yanzu mun shirya gyara kuskurenmu."
Da ido kawai ta kafe Mamie ba tace komai ba har Mamie ta gama surutunta ta koma mazauninta, haka suka zauna shiru dan yanayin da gidan yafi zama kenan tun faruwar abinda ya faru.
Bayan Papa ya dawo daga masallaci sunci abinci Mamie taje d'akinsa ta zauna dan kawar da duk wani shakku da zai nuna basa zaune lafiya, yana cire kayan jikinsa ya kalleta ta madubi yace,
"Har yanzu kina kan bakanki na tafiya tare dasu Mama?"
Ba tare data kalleshi ba tace "kana tunanin akwai abinda zaisa na fasa ne, kayana a shirye suke ranar kawai nake jira."
Gabanta ya zo ya tsaya ya kamo hannayenta suna kallon juna, kai ya girgiza mata yace "Na'ima, ke musulma ce kuma mai ilimi, nasan kinsan ba daidai bane aibata wanda ya musulunta, haka ma bai dace ak'i karb'ar yafiyar wanda ya nemi afuwa ba, hakan nasa da dama su kasa shiryiwa saboda tunanin haka, dan Allah Na'ima ki yafe min laifina wallahi ba sani da kika min da bane."
Ganin ta kawar da kai gefe yasa hannu ya tallabo fuskarta yana kallo, a hankali cikin tsoro ya had'ata da jikinshi, πwasa fa saita fara canzawa to ni dai nayi nan, bana kallon k'aramar harka bare kuma wannan babbar harka.
Kamar yanda Mamie tayi niyyar tafiya ko babu takarda hakane ta faru, ta shirya itama kuma tace wa Mammie shine yace su tafi tare danta kama mata kula da Khairat, ya gama shirya musu komai amma banda Mamie, in da itama ta shiryawa kanta komai ba tare da saninshi ba.
Sun gama shirin tafiyarsu tsaf ranar talata kawai suke jira ta zo, yau *litinin* da dare Mamie na zaune matashin saurayin nan ya fad'o mata a rai, wayarta ta d'auka ta kira manager ta tambayeshi akan yaron da suka zo tare a ranar, ya fad'a mata sunanshi dama matsayinshi a ma'aikatar tare, ta kuma tambayeshi koda wata alaka tsakaninshi da Khairat yace a'a, amma ya fad'a mata abinda ya shiga tsakaninsu.
Nan tace da safe ya turo mata shi kafin lokacin tashin jirginsu, bayan sunyi sallama ya kira Umar Faruk ya fad'a masa, hakan yasa ya kwana yana tunanin abinda zai faru da kuma dalilin da yasa matar ke nemanshi, haka dai ya wayi *gari* sannan ya shirya ya tafi gidan.
Khairat ce zaune akan kujerarta ta kira Biba, tana zuwa tace mata ta turata ta kaita lambu tasha iska, haka akayi ta kaita can ta barota yayin da ta toshe kunnuwanta da abin sauraro tana sauraron wak'ok'i, Umar Faruk ne ya shigo gidan sai dai kafin ya shiga ciki sai wayarshi ta fara ruri, yana fito da wayar yaga Zuby ce ke kira dan haka ya d'auka ya fara tafiya ya nufi kwanar cikin gidan duk da baisan ina zata kaishi ba, a hankali yake takawa harya riski lambun dake bayan gidan, jingina yayi a bishiyar daya fara gani cikin taushin murya ya mayar da martanin abinda Zuby ta fad'a masa,
"Ina sonki, ina qaunarki , na matsu ranar nan tazo domin a ranar burina na gidan duniya ya cika, na gaji da mafarkinki a kullum, ina so mu fara rayuwar gaske."
Khairat dake sauraren wak'ok'i bata jin me yake fad'a, amma shi duk da yana magana ne amma yana jin wata siririyar murya na tashi a kusa dashi ana rera waka , juyawa yayi ya kashe wayar yasa aljihu tare da rumgume bishiyar ya lek'a kanshi a hankali dan ganin me wakar, yanda ya rumgume bishiyar yasa hannunshi ya d'an shafi kafad'arta hakan kuma yasa ta juyo da sauri, manyan idanunsu ne suka sarke dana juna suna kallon kallo, babu wanda baiji fad'uwar gaba ba a cikinsu amma sai suka basar.
Babu wanda yace wani abu kuma babu wanda ya d'auke kanshi, Khairat ce taja tsaki tare da maida kallonta ga wayarta ta ci gaba da abinda take, yana ganin haka ya tab'e baki shima ya koma hanyar daya fito, Biba ce ta masa izinin zama sannan taje ta sanar da Mamie bak'onta ya zo.
Yana cikin kallon hadadden falon yaji bud'a k'ofa, maida kallonshi yayi ga nutsatsiyar matar mai dattako, tsaye ya mike yana murmushi ita kuma ta masa izinin zama, cike da girmama juna suka gaisa kafin Mamie ta kalleshi a tsanake.
Hakika Umar Faruk ba zaka kirasa da kyakyawa ba ajin farko, amma dai dole ka kirashi kyakyawa na farko a aji na biyu, manyan idanunshi masu firgita mai kallonsu da kuma saka kwarjini, haka kuma bak'i kuma yalwataccen sajenshi ma ya k'ara masa kyau, kana ganinshi zaka san jarumin namiji dan suffarshi ma ta zaratan maza ce, daga tafiyarshi kuma zaka gane ingarman dokine mai tashen k'uruciya a jika.
Murmushi Mamie tayi tace "Umar Faruk, ranar ka taimakemu amma kuma saika tafi ba tare da mun maka godiya ba, kome yasa kayi haka?"
D'an murmushi yayi yace "Hajia ni na taimakeku ne saboda Allah, bana buk'atar ku gode min."
"Duk da haka Umar Faruk muna godiya sosai da irin taimakon daka mana, amma dan Allah tayaya akayi kasan da mutanen nan?"
Kallonta yayi yace "Hajia da mun bar duk wannan maganar, tunda dai masu laifin sun shiga hannu."
"Hakane, amma zan iya sanin meke tsakaninka da Khairat?"
Murmushin gefen labb'a yayi yace "ba komai Hajia."
"In tambayeka mana idan ba damuwa?"
"Uhum, ba damuwa."
"Dan Allah kana da aure?"
"A'a, amma dai nakusa insha Allah."
"Allah yasa alkairi."
Ya amsa da "ameen, na gode."
Kallonshi tayi tace "amma misali, idan nace zan da Khairat, kana ganin zaka yarda ka aureta?"
Kafeta yayi da ido da tsananin mamaki, ba zai iya yi mata qarya ba kamar yanda ba zai yarda ya lalata rayuwarshi ba ta hanyar auren Khairat, ko kyauta za'a bashi ita to ba zai karb'a ba, shima da ido ya kalleta yace "kiyi hak'uri Hajia, amma gaskiya ba zan iya ba, kiyi hak'uri idan abinda na fad'a ya b'ata miki rai, ina da wacce nake so kuma hutu kawai muke jira a d'aura mana aure."
Murmushin takaici tayi tace "karka damu raina bai b'ace ba, dama tunda abun nan ya faru na sawa kaina dole haka zata fara faruwa damu, nasan a yanzu ba kowa bane zai iya yarda ya aureta, amma ba komai zamu ci gaba da hak'uri har komai ya zo qarshe, kuma ina so ku sani Khairat bata da laifi, duk laifin namu ne iyayenta musamman ma ni uwa."
"Shari'a ta nuna mana yanda zamu samu yaya na gari tun kafin aure, amma sai kaddarata ta zo da tangarda na kasa samar mata uban daya dace, ba komai karka damu kanka kaji."
Tsaye ta mik'e tace "na gode yaro Allah ya maka albarka."
Shi dai baice komai ba yana kallo ta fara tafiya kuma ta tsaya ta juyo tace "bansan ko kana buk'atar kuyi ban kwana da Khairat ba, dan baifi awa d'aya daya rage mana ba mu koma India da zama tare da mahaifiyata."
Tana fad'a ta juya saboda hawayen da suka taho mata, yau gashi *halin rayuwa* yasa harta yiwa namiji tayin 'yarta a cikin wasa amma yace baya so, shi kuma jikinshi ne yayi sanyi duk yaji ba dad'i, amma kuma baiyi nadama dan ba zai yarda koda a misaline ba a dinga had'ashi da Khairat.
Tashi yayi shima ya bar gidan dan baiga wani ban kwana da za suyi ba da ita, haka ya d'auki hanya yana tunanin maganganun mahaifiyar Khairat, uwar mutuniyar kirki ce amma diyar da uban sai a hankali kam , inji Umar Faruk.
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgee❤: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀
*MARAYU MA 'YA'YANE*
π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀π€Ήπ»♀
_A gaskiya littafin nan ya ilmantar sosai, kuma da za'a dinga yin labari irinshi to za'a samu ci gaba, my Lissa na tayaki murnar kammalashi, ubangiji ya yafe miki kurakurenki ya baki ladar fad'akarwar da ki kayi._ sai mun had'u a labari na gaba.
_Bismmilahir-rahman-rahim_
1⃣1⃣
Lokaci nayi suka fito cikin shirin tafiya, Papa na ganin Mamie ya janyeta gefe cikin rad'a yace "wai me kike shirin yi ne Na'ima, da gaske tafiya za kiyi?"
Fizge hannunta tayi tace "ka rabu dani, aina fad'a maka babu abinda zai hanani tafiya wallahi, kaji na rantse."
Jinjina kai yayi yace "naji, tunda kince dole zaki tafi to ki tafi, amma ki barmin 'yata zan kula da ita."
Dariya tayi tace "'yarka, wallahi idan kaga nabar Khairat a hannunka to ka tabbata aure zaka mata, amma in ba haka to wallahi ba zan bar maka ita ba."
Wucewa taje yi ya sake rik'eta yace "naji tunda haka kika ce, ki bar Khairat anan, na miki alk'awarin samo mata miji na gari na had'ata dashi."
Kallon sama da qasa ta masa tace "idan ka samu mijin saika kirani ka fad'a min, ni kuma zan kawo maka ita da kaina."
Tana fad'a tayi gaba, haka suka tafi tare ya rakasu babu mai magana har jirginsu ya tashi yana kallonsu, haka suka tashi yana ji kamar ya bisu amma tunda bai shirya hakan ba dole ya hak'ura, haka ya juya ya koma gida zuciyarshi na tafasa kamar zata fashe, yana son Na'ima kuma yasan ba zai samu mace kamarta ba, amma hallayarshi taja mashi rasata a lokacin daya fi buk'atarta.
Ita kanta Mamie saida jirgi ya tashi sai taji kamar bata kyauta ba , kamata yayi ace ta hakura su rumgumi 'yarsu su maida hankali kan tarbiyarta, ba kuma wannan ne yafi d'agawa Mamie hankali ba shine ji da tayi kamar itama ta kamu da son Papa ba tare data sani ba, haka dai har suka sauka a india Mamie na hawaye, Khairat kuma na ganin haka saita dinga jin haushin Mamie saboda tana ganin ai farin ciki ya kamata tayi data rabu dashi na d'an wani lokaci, to amma ta rasa kukan miye take.
*SOYAYYA KENAN*π
Tunda suka sauka abokan arzik'i da aka saba suka fara zuwa musu sannu da zuwa, kuma sai lokacin suke ganin halin da Khairat ke ciki, haka dai ake ce musu hatsari tayi nan zasu mata addu'ar samun lafiya sannan su tafi.
Haka ma dai masoyin nata Raj ba'a barshi a baya ba, a sukwane yazo domin ganin Khairat cikin farin ciki tare da shirinshi na neman aurenta a yau d'in, amma ganinta a wannan hali saiya sare masa gwiwa dole ya hak'ura, amma yayi niyyar bayyana mata k'udirinshi bada dad'ewa ba koda tana cikin wannan halin ne dan yana sonta so mai tsanani.
*Daga* wannan rana sai Raj ya fara taimakawa su Mamie wajen jinyar Khairat, duk da Mamie bata so ko kad'an amma da yake mutum ne mai barkwanci da son mutane gashi da aiki ko ba'a sashi ba, hakan yasa ya shiga ran Mammie kuma ya qara girma a idon Khairat, kowace safiya saiya zo gidan ya tayasu had'a abin kari kuma da kanshi yake bawa Khairat nata , haka kuma da dare zai zo su jima suna hira da Khairat saboda kusan unguwa d'aya suke, Khairat najin dad'in haka hakan yasa yanzu harta fara canzawa yanzu tana magana sosai tana dariya in dai Raj na nan.
A haka sai shakuwa ta sake shiga tsakaninsu fiye da baya, duk da raunin dake jikinta tare da rashin tafiya hakan baya hana Raj fita da ita wuraren shaqatawa, kuma hakan na mata dad'i tana d'ebe kewa sosai.
*A b'angaren* Papa kuwa an duk'ufa an maida al'amura ga ubangiji, sallah kan lokaci tsayuwar dare yana neman gafarar ubangiji, azumi kullum sadaka da taimakawa marasa galihu duk wannan yanzu shine aikinshi, damuwar rashin iyalinshi na damunshi musamman Na'ima wacce yake ganin ta tafi kenan, duk kiran da yake mata bata dauka Khairat kad'ai da Mammie suke waya dasu amma banda ita, idan ka ganshi yanzu yayi kalar tausayi sosai kana ganinshi za kasan yana rayuwar kad'aici, sai ma'aikata kawai dake hidima da gidan.
_Allah ya karb'i tubanmu ya yafe mana kurakurenmu._
*Bayan wata uku* Umar Faruk ne a tsakar gidansu Zuby suna hira, Zuby ce ta nunfasa tace "yaya Umar, a gaskiya kaban mamaki sosai daka iya b'oye min abu mai mahimmanci haka."
Gyara zama yayi yana kallonta sosai yace "uhum, ina jinki, me nayi kuma?"
Cewa tayi "yaya Umar, jiya da naje gida wajensu Mama nake jin abinda ya faru a wajen aiki, wai matar da kuke aiki a qasanta ta mareka, a gaskiya raina ya bace sosai, ganin duk kwarjinin nan naka ace mace ta daga hannu ta mareka, ai sai dai mai zarra."
Shiru ya d'anyi na wani lokaci dan sai yanzu da tayi maganar ya tuna da wata Khairat, a hankali ba tare da sanin maganarshi ta fito fili ba yace "ko ya jikinta yanzu?"
"Wacece?" tambayar da Zuby ta jefo masa kenan.
Da sauri ya kalleta yace "a'a...ba...bb..ba komai."
Dorawa tayi da "amma ai kamar itace na gani a Whatsapp ana magana akai, wai in dai har za'a dinga keta haddi yayan manya ma to ina ga talakawa da marasa 'yanci."
Kallonta kawai yayi da ido, dan haka ta sake cewa "kuma naji ance har mutum hud'u ne ko, gaskiya ta ban tausayi, nikam yaya da zaka kaini gidansu ma na ganta wallahi."
"Keeee." tsawar daya mata tasata zabura da k'arfi.
Tsaye ya mike yana masifa "ita d'in cinema ce da za kice na kaiki ki ganta, wani abun dad'i ne ya sameta da har zaki dinga magana haka cikin shauki , to ba zan kaiki d'in ba kije da kanki saiki ganta, hada wani wai mutum hud'u, to sai akayi me dan mutum hud'u ne? zata fasa rayuwa ne ko kuma zata rasa mijin aure ne?"
Yana gama fad'a kuma ya koma ya zauna yana huci, ruwan dake kusa dashi a cup ya d'auka ya kai bakinshi , kamar dirar mikiya ya tsinci muryar Zuby tace "zata rasa mijin aure, dan a mahawarar dana gani a Whatsapp, kowane namiji yana cewa shi ko kyauta ba zai aureta ba, wasu kuma suna cewa idan za'a had'a musu da kud'i da mota da gida to zasu amince, watak'ila kaine kake ganin ba komai bane, amma wannan ba k'aramar matsala bace."
Kasa shan ruwan yayi ya qura mata ido, ita kuma tashi tayi ta shige d'akinsu wai ita ya d'aga mata murya akan wata banza.
_Lallai ruwa sun daki babban zakara , Khairat d'in ce banza?_
Ai baiko bi ta kanta ba ya fita daga gidan shima ya hau mashin d'inshi, bai zame ko ina ba sai majalisar da manage ke zama bayan an tashi daga aiki, zaune ya samesu wasu akan tabarma wasu akan benci, gaidasu yayi cikin girmamawa dan duk ba sa'anshi, manager ne yasa takalmi ya tashi suka keb'e.
"Umar Faruk lafiya na ganka cikin wannan daren?"
"Eh to, lafiya lau."
Shiru ya d'anyi shi kuma yana kallonshi kamar mai nazartarshi, kai ya shafa yace "manager wai dan Allah ya jikin Hajia Khairat ne? naga har yanzu babu wani labari tunda suka tafi basu dawo ba."
Manager daya kafeshi da ido murmushi ne ya bayyana a fuskarshi ya dafa kafadarshi yace "Umar Faruk kenan, irin wannan damuwa haka? to ka kwantar da hankalinka, Khairat na nan lafiya dan mahaifiyarta tace min ma harta fara takawa da taimakon wani saurayinta Raj, kuma da zaran ta samu sauki sosai zata turota ta dawo gida."
Da mamaki ya kalleshi yace "ta turota kuma, ita fa?"
Ajiyar zuciya ya sauke yace "wannan sirrin gidan Alhaji Mani ne, bai kamata na fitar dashi ba, amma dai ka sani mahaifiyarta ba zata sake dawowa ba sai dai wani iko na ubangiji kuma."
A tsanake ya kalli manager yace "hakan nada alak'a da abinda ya faru da 'yarsu kenan?"
"Sosai ma, faruwar hakanne ya jawo komai."
Kai Umar Faruk ya girgiza ya bawa manager hannu yace "na gode manager, ni zan wuce."
Harya tafi manager ya kira sunanshi, juyowa yayi yace masa "ko dai na baka lambarta ne saika kirata kaji."
Kamar wanda aka ba tsoro saiko yace "a'a a'a, ni kuma me zanyi da lambarta."
Yana fad'a ya juya ya hau mashin d'inshi yana fad'in "ina ruwana da ita, tana can fa ita da masoyinta."
Tafiya ya fara amma ya rasa dalilin da yasa ranshi b'acewa, da k'arfi sake fizgar mashin d'in tare da jan dogon tsaki yace "Raj d'in banza da wofi, miye matsalata dashi da zai dameni."
πππππππ
*A wannan* lokacin Khairat jiki yayi dama sosai tafiyarta ma lafiya lau, da taimakon Raj ta fara takawa dan kullum shike rik'e da hannayenta yana koya mata tafiya harta fara sosai, yanzu dai da kaga Khairat to ta baya ce dan ba zaka tab'a cewa tayi wata larura ba.
Mammie Mamie da Khairat duka suna zaune a falo suka ji ana buga kofa, Khairat ce ta tashi ta bud'e, da farin ciki ta rumgume Raj wanda ya shirya cikin pink d'in riga da bakin wando, sosai yayi kyau dan dama akwai kyau d'in, sakin juna sukayi ya shigo ciki ta rufe kofar, hannun juna suka rik'e cikin yaran india take cewa,
"Yaufa kayi kyau, da wani abu ne dake faruwa?"
Murmushi kawai ya mata ya mik'a mata flowers daya taho da ita ja mai kyau, karb'a tayi tace "na gode."
Mamie da tunda ta ganshi ta had'e rai dan ko kad'an bata san ganinshi tare da Khairat, bata musa akan cewar yaran kirki ne ba,amma tafiyarshi da Khairat bata dace ba, saboda shine namiji kuma ba musulmi ba, d'aya bayan d'aya ya sunkuya ya tab'a qafafun Mammie da Mamie d'in dan neman tabarruki, Mammie ce tace ya zauna, kallon kallon aka shiga yi har saida Khairat tace,
"Ya dai Raj?"
Kai kawai ya girgiza mata alamar ba komai, Mammie da Mamie ya kalla cikin harshenshi yace "ina neman izininku akan ku bani damar neman auren Khairat."
Khairat ce ta kalleshi da mamaki, kai ya jinjina mata dan haka ta taso ta dawo wurinshi ta zauna murya qasa qasa tace "kana haukane? nifa ban shirya aure ba yanzu."
Hannunta ya kama ya rik'e yana mata shu'umin kallo yace "me yasa Khairat? baki sona ne?"
Cikin sanyin jiki tace "ba haka bane Raj, amma ba...."
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgee❤: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Bismmilahir-rahman-rahim_
1⃣2⃣
Bai bari ta k'arasa ba ya rufe mata baki yana fad'in "shiiii, Khairat, in dai har kina sona, to ki tabbatar min da hakan yanzu ta hanyar saka wannan zoben, alamar munyi baiko dake." ya fad'a tare da fito da zobe daga aljihun rigarshi ya bud'e mata.
Da mamaki ya kalleta tana tunanin mafita, hak'ik'a Raj shine namiji na farko da take jinshi a ranta, ganin bata da wani dalili na kin amincewa yasa tayi murmushi ta mik'a masa hannunta tace "eh, na amince."
Cikin farin ciki ya fito da zoben jiki na rawa ya fara k'ok'arin saka mata, "Khairat!"
Kira da Mamieta mata yasa suka kalleta a matuk'ar razane, tsaye suka mik'e suna ci gaba da kallonta, d'orawa Mamie tayi da "ashe baki da hankali Khairat, ke yanzu amince masa za kiyi ki aureshi kike nufi kome? kinsan hukuncin kuskuren da kike shirin aikatawa kuwa?"
Maida kallonta tayi ga Raj da bai fahimci komai ba ta fara masa magana a harshen india duk da yanzu indiancin nata yayi rauni sosai amma haka ta dage tace masa,
"Kaga Raj, kai yaron kirki ne, amma ka sani alak'arka da Khairat ba mai dorewa bace domin kuwa ita musulma ce kai kuma ba musulmi ba, addininmu kuma ya haramtawa mace musulma auren namiji da ba musulmi ba, dan Allah ina so ka fita a harkarta ka manta da ita a rayuwarka, kaje ka samu mace yar uwarka ka aura, dan Khairat ma an fitar mata da miji fad'a maka ne ba tayi ba."
Duk da ta fad'i hakane danya rabu da ita, amma dai bata ji dad'in abinda ta fad'a ba saboda ba gaskiya bane, had'e hannayenta tayi tace "na rok'eka da ka tafi, ka tafi dan Allah karka sake dawowa, dan Allah."
Tunda Mamie ta fara magana ya zama kamar gunki, jin ta gama fad'an abinda take son fad'a yasa ya juya ya kalli Khairat, gefen fuskarta ya shafa yayi murmushi wanda yasa hawayenshi suka fito, da qyar ya iya furta mata "zanyi kewarki Khairat, naso na sameki, amma dole na barki, ba zanso ki sab'a umarnin addinninki ba a kaina, kibi zab'in iyayenki."
Yana fad'a yayi hanyar fita, da sauri Khairat tabi bayanshi, fizgowar da Mamie ta mata tasa ta fad'a saman kujera, a hassale ta tashi cikin harshen zarma (zabarmanci,πinji k'anwata zamarmanci) ta fara magana,
"Wai meye haka, me yake damunki ne, kinsan me kika aikata kuwa? aurena fa ya nema a gabanku, akan me zaki masa haka?"
"Khairat, kin manta ke musulma ce, bai halatta gareki ba auren wanda ba musulmi ba."
"Mamie saime, nifa zan zauna dashi bake ba, me yasa zaki min haka?"
_WAI'IYAZU BILLAH_π
A fusace ta shige d'aki ta barsu, Mamie kuma fad'awa tayi saman kujera ta fashe da kuka sosai har saida Mammie ta taso ta zauna kusanta ta dafata tace,
"Na'ima kiyi hak'uri, kici gaba da yiwa Khairat addu'a, insha Allah zata canja."
"Yaushe, Mama sai yaushe Khairat zata san mu iyayen tane, Mama munyi kuskure da bamu d'ora Khairat a tafarkin ilimin addini ba, yafi kowane ilimi a rayuwa, na tabbata da tayi karatu da zata san girman hukuncin iyaye sannan zata san girman zunubin da take shirin aikatawa."
"A gaskiya Mama ba zan jure ba, aure kawai nake so Khairat tayi Mama, akwai matsala zamanta anan dan haka gobe zamu koma wajen mahaifinta, na gaji da ganinta a gabana Mama."
Tana gama fad'a itama ta tashi ta nufi d'akinta, kwance tayi tana tunanin rayuwa da kuskurensu da kuma kuskuren da 'yarta ke cikin aikatawa, Khairat ma na d'akinta tayi kiran wayar Raj harta gaji, ganin ta aika sak'o ba amsa yasa kawai ranta ya b'ace ta fita harkarshi shima, abin sauraronta tasa a kunne tasa sanyayyen waka domin d'ebe mata kewa.
*Tunda gari ya waye* Mamie taje ta ciro musu ticket kuma tayi sa'ar samun jirgin da zai tashi da yamma, tana zuwa ta shirya kayanta dana Khairat dake bacci a d'akinta, tana gamawa ganin lokaci ya fara tafiya yasa Mamie tashin Khairat.
Da mik'a ta farka tare da hamma, ganin Mamie tsaye yasa ta gyara zamanta tana kallonta, "ki tashi ki shirya zamu tafi."
"Ina kenan?" cewar Khairat tana saukowa daga kan gadon.
"Gidan mahaifinki zamu koma?"
Dariya tayi tace "kije kawai idan kinyi kewar mijinki ne, ni nafi jin dad'in zamana anan tare da kakata."
Gabanta Mamieta tare tace "Khairat tare zamu tafi dake, kiyi sauri ki shirya ki fito ki sameni."
"Bansan me yasa kike so ki bawa kanki wahala ba, na fad'a miki ba zanje ba."
Da sauri Mamie ta fita daga d'akin ta koma falo ta bud'a jakar kayan Khairat d'in ta d'auko wata doguwar rigar atamfa ta dawo d'akin da zafinta, tana zuwa zaune ta samu Khairat akan kujerar dake gaban madubi tana kallon kanta, da k'arfi Mamie ta kamo hannunta ta tsayar da ita gabanta ta cire mata qaramar rigar dake jikinta, ganin tana kare qirjinta yasa Mamie tayi tsaki taci gaba da abinda take, saida ta barta da silip kad'ai sannan ta rataya mata wannan rigar, wani irin d'auri ne Mamie ta mata mai ban dariya sannan ta d'ora mata gyale a kafad'a dan tasan haka tafi so.
Hannunta ta fizga zasu fita daga d'akin Khairat ta tirje tace "wai Mamie miye haka, nifa ba yarinya bace?"
"Amma ni na haifeki, muje." ta fad'a tana janyota har suka fita.
Mammie na zaune taga sun fito kamar ankorosu, tsaye ta mike tace "ku kuma lafiya, miye haka kike janta kamar yarinya?"
"Fad'a mata dai kakata." cewar Khairat tana so ta kwaci hannunta.
"Mama kiyi shiru, zamu tafi ne saina dawo."
Jakunkunansu Mamie ta d'auka zasu fita Mammie tace "saikin dawo kuma, ina kuma yaushe, ki zo kiyi me?"
Saida Mamieta bud'e k'ofar fita tace "idan na dawo za muyi magana, sai kinzo bikin gimbiyarki."
Dariya Mammie tayi lokacin da taji Khairat tace "biki kuma, aure zaki min?"
Haka suka fita suka shiga taxi d'in dake jiransu a k'ofar gidan, Mamie bata saki hannunta Khairat ba har saida suka shiga jirgi sannan.
*Dare ya fara tafiya* suka shigo garin, suna cikin taxi Khairat na kallon gefen titi kwatsam ta hango Papanta zai shiga wani super market tare da wata wayayyar mata sun shiga ciki, da sauri Khairat ta daddab'a kafad'ar driven taxi tace ya tsaya, tsayawa yayi Mamie kuma tambayarta ta fara yi ko lafiya, fita tayi daga motar da sauri ta fita ta rufe motar ta lek'o kai tace wa Mamie "kije gida, zanje na taho miki da mijin naki."
Da gudu ta tsallaka d'aya titin, zata tsallaka na biyu wani mai mota da bata kula dashi ba ya danna mata wata irin oder da saida ta zabura, cak ta tsaya tana kallon motar, ganin mai motar ya tsaya yasa ta kwada tsaki zata wuce kawai taji yace "yan mata lafiya, da matsala ne?"
Hararanshi tayi tace " dallah gafara can, wai kai mai mota sai iya oder tsiya, hamago yanzu haka ma motar aro ce."
Umar Faruk ne a d'aya b'angaren data tsallako zai wuce yaga kamar idonshi na mishi gizo, amma daga ganin kayan jikinta da yanda takewa mutumin nan magana yasa yasan Khairat ce da kanta ba mai kama da ita ba, tsallakowa yayi ya tsaya daga gefe yana kallonsu kamar wasu mutanen da suma har sun fara kallonsu, mai motar nan ne yace "da alama baki da tarbiya, amma tunda kika had'u dani kin gama, wallahi daga yau ba zaki sake wulak'anta wani ba."
A zabure ta matso kusanshi tace "me za kayi, dukana za kayi, ko kuma kaima za kayi abinda kuka iya ne, to ka sani ba kaine farko ba?"
Zaiyi magana ta mashi wata irin kyara tace "tafi dallah ni bana da lokacinka."
Zata wuce ya tari gabanta ya zaro mata ido yace "ke har kin isa kice zaki ci mutunci na, kinsan ko waye ni? ke yar gidan uban waye? da alama fa karuwanci kika fito amma har kike so ki rainani, to yau sai naga uban daya d'aure miki gindi a garin nan."
Waya ya fito da ita da alama kamar wata lamba yake nema, Umar Faruk ne yaga al'amarin zaiyi tsamari dan haka ya matso tare da rik'e hannun mutumin yace "sannu abokina, dan Allah kayi hak'uri ka rabu da ita, qwaqwalwarta ce ta samu matsala tunda ta samu wani hatsari."
A hassale mutumin yace "ina so ne naga uban daya d'aure mata gindi a garin nan da har take wa mutane rashin kunya, ka bari kawai na koya mata hankali."
"Ka koya min hankali kaga yanda zamu kare da kai, wallahi sai kayi nadaman zuwanka duniya." cewar Khairat.
"Ke." mutumin ya fad'a cikin daga murya.
"Wai kinsan dawa kike magana? to mune garin nan dan mune gwamnati."
"Mtsssssss." wani dogon tsaki da Khairat taja.
Gyara tsayuwa tayi ta rik'e k'ugu da hannu d'aya tana nunashi da d'aya hannun tace "kasan ni kuma wacece, duk kasancewarka a cikin gwamnati nasan baka kai mahaifina ba, kasan koni yar wacece? to ni yar Mani Bukar ce, kuma nasan kasanshi."
Jim ya d'anyi kafin ya basar yace "to saime dan kina d'iyar Mani Bukar, cemin za kiyi ragowar sojoji, ke yanzu duk da abinda ya faru dake amma kike wannan bud'a hanci, kamar wata wacce take cike da budurci."
Ranta ne ya b'ace duk da hawayen da suka taho mata, matsowa ta sakeyi daf dashi za tayi magana amma sai Umar Faruk ya d'auka ko zata mareshi kamar yanda shima ta masa, da sauri ya shiga tsakaninta dashi yana kallonta yace "waike me yake damunki ne?"
Kallon sani tama Umar Faruk amma kuma tana ji ba zata iya tunashi ba, wani tsakin ta kuma ja ta bisu da harara ta wuce abinta, Umar Faruk binta yayi da kallo kafin yaga in da ta shiga shima ya juya ya hau mashin d'inshi yana tunanin maganganun da mutumin ya fad'a mata.
Tana shiga ta fara waige waige ta in da za taga mahaifin nata, can ta hangoshi da wata qosashiyar mace da gani kasan ba qarya babbar macece, a hankali ta fara takawa harta tsaya bayansu basu sani ba, cikin taushin murya tace "sannu da jin dad'i."
Juyowa sukayi dukansu in da jikin Papa ya d'auki rawa, matar kam a wulak'ance ta fara kallon Khairat, matsowa tayi kusan matar za tayi magana Papa ya gaggauta jan hannunta yayi gefe da ita ya fara magana cikin rad'a.
"Khairat meya kawoki nan?"
"Kamata yayi tambayi ne yaushe na shigo garin."
"Naji yaushe kika zo?"
"Papa wacece waccen matar, kenan har yanzu baka daina abinda kake ba?"
Hannunta ya rik'e yace "a'a shalele, wallahi na daina duk abinda nake, na riga dana tuba da duk wani aikata zunubi, wannan matar ma ba wani abu bane tsakaninmu a yanzu, kawai tana so ta b'ata min suna ne, shi yasa nake binta a hankali."
Kai ta girgiza tace "Papa, kamar ya kake binta a hankali? me take maka?"
"Khairat, wannan matar tace tana d'auke da cikina, kuma ta kaini asibiti an tabbatar min da hakan, kinga dole na bi a sannu."
Juyawa tayi ta kalli matar sannan ta kalli Papa tace "wannan matar bata da wani ciki, kuma yanzu zan tabbatar maka da haka."
Tana fad'a ta tunkari matar, tsaye tayi gabanta tana murmushi tace "Papana ya fad'a min na kusa samun kani , rashin yarda da banyi ba yasa nace bara duba da kaina na gani."
Tana fad'a ta kamo hannun matar ta fara kallon tafin hannunta wai ita tana so ta gano cikiπ€£, sakin hannunta tayi tana mata kallon tuhuma, k'ara matsawa tayi kusanta ta bud'a ijiyarta tana kallo, matar kam duk tsoro ya kamata dan haka ta tsaya ma, sakinta tayi ta kalli Papa tace "babu wani ciki a tare da ita, wahalar da kai kawai take yi, da alama ma kamar ba zata iya d'aukar ciki ba."
"Inji uban wa? wallahi ko banda ciki yanzu ni nasan ina haihuwa."
Kallon Papa tayi tace "ka gani ko, ko makarantar koyan likitanci ban tab'a shiga ba, amma ta bayar da kanta saboda tana tunanin ni ma'aikaciyar lafiya ce."
Soshe soshe matar ta fara na rashin gaskiya a hankali ta aje kwandon hannunta wanda take zuba kayan data d'auka, tafiya ta fara yi su kuma suna kallonta, saida ta d'anyi nisa ta juyo tace ma Khairat "kin kub'utar da ubanki."
Murmushi ta mata tace "sai dai ki kama uban wani amma ba nawa ba."
Tana fita Papa ya shafa kan Khairat yace "Allah miki albarka shalele, gashi kin kub'utar da Papanki."
Tafiya suka fara yace "ina alfahari dake gimbiyata."
Ba tace komai ba har suka shiga mota yana tuki har suka isa gida, zaune suka samu Mamie a falo ko hijab d'in jikinta bata cire ba haka ma kayansu na gabanta, zaune Papa yayi yace "ya kike zaune haka?"
Kallon Khairat Mamie tayi tace "ki shiga ciki za muyi magana."
Wucewa kawai tayi ta shiga d'akinta, wanka ta fara tana tunanin fuskar data gani, bud'e idonta tayi duk da ruwa na sauka a kanta tace "Umar Faruk ko? tabbas shine."
Tab'e baki tayi ta ci gaba da wankanta harta fito ta shirya cikin dogon wando fari da pink d'in riga mai siraren hannuwa, turare kawai ta shafa ta d'auki abin sauraronta ta makala a kunne ta fara tik'ar rawa abinta.
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgee❤: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Bismmilahir-rahman-rahim_
1⃣3⃣
Papa ne ya gyara zama yace "ina jinki, dan da alama akwai magana sosai a bakinki."
"Hakane, kuma mai mahimmanci ce maganar."
"To ina jinki."
Saida ta kalleshi tace "baban Khairat, gaskiya ina so ka mata aure, bana so yarinyar nan ta jawo mana wata magana, idan zai yiwu gaskiya bana so aurenta ya wuce wata d'aya."
"Toh, meya faru ne haka? wani abun tayi?"
"Eh, in har mukayi wasa wallahi Khairat zata iya auren wannan yaron Raj, wanda hakan kuma bai dace ba, ni kuma bana so wani abu ya faru dan yaran yanzu zasu iya yin komai akan abinda suke so, shi yasa nake so ka d'auki maganar da mahimmanci, dan a gaskiya wata d'aya ya wuce banga Khairat a d'akin mijinta ba, tofa zan koma in da na fito dan aurenka ne zai mutu."
Yanda tayi maganar ya bashi dariya, amma saiya had'eta yace "Mamien Khairat kenan, yau da alama da rigima kika shigo garin nan, amma fa karki manta abinda kike so ayi kamar za'a tilastata ne akan abinda bata so."
"Ba wani nan, ya zama dole ka kauda ganinka daga b'acin ranta, in ba haka ba dama babu abinda za kayi."
"To naji, yanzu bara na kirata naji koda wanda take so."
Yana fad'a ya fara kwalla mata kira, amma ina ta toshe kunnuwa da abin sauraro koji ba tayi, saida Papa ya tashi ya bubbuga k'ofar da qarfi sannan ta bud'e tana kallonshi, "kizo." kawai yace ya koma falon.
Bayanshi ta biyo harta zauna kujera mai fuskantar tasu, ganin sun kafeta da ido yasa ta cire abin kunnuwanta tana kallonsu, Papa ne ya kalli Mamie ya kalli Khairat yace,
"Shalele, mahaifiyarki ce ta zo da wata magana mai girma, kuma na goyi da bayanta, shine nace bara naji ko akwai zab'inki?"
Da kai ta masa alama da me kenan, d'orawa yayi da "ina so naji ko akwai wanda kike so a cikin zuciyarki? saimu tattauna dashi."
Wata shek'akk'ar dariya tayi tace "wai kun gaji dani ne da kuke son aurar dani kome?"
Papa ne yace "a'a shalele, aishi aure shine darajar 'ya mace."
Mamie kuma tace "ai kin kai munzalin da za'a gaji dake d'in, shekara ashirin da biyar ai ba shekara sha biyar bace."
Tsaye Khairat ta mik'e tace "kaji ko, to wallahi babu wanda zai min aure ban shirya ba, kuma me yasa baki fad'a masa abinda ya faru a jiya ba, baikona fa kika dakatar."
Wucewa taje tayi Papa ya kalleta yace "to baki fad'a min wanda kike so ba?"
Tsaye tayi ta kalli Papa tace "ni babu wanda nake so, har yanzu ban samu wanda ya dace ba."
Tana fad'a ta juya Mamie ta bita da ido tana fad'in "kaji kuma, jiya fa hannu ta mik'a wani zaisa mata zobe, amma yau tana cewa bata son kowa."
Papa ta kalla dake dariya tayi tsaye tace "shikenan tunda kun mayar dani mahaukaciya."
Da sauri ya tashi ya rik'o jakar data d'auka yana fad'in "haba madam, kiyi hak'uri ki bar min komai a hanuna, insha Allah za kiga auren Khairat da idonki harki saka mata albarka."
Zuciyarta ce ta karye ta kalleshi tana zubar da hawaye tace "dan Allah kayi wani abu dan ganin Khairat tayi aure, wallahi ina jin tsoron faruwar wani abun marar kyau, ka sama mata miji na gari daya dace, wanda zai d'orata akan addininta sannan ta gyara rayuwarta."
Hannunta Papa ya rik'e yana kallonta yace "zan iya baki zab'i?"
"Zab'in me?" ta fad'a tana share hawaye.
"A gaskiya Na'ima a yanzu babu abinda nake so kamar naga Khairat ta fara sabuwar rayuwa mai kyau da tsabta, in hai muna so haka ta faru sai mun had'ata da jigo, kinga kuma a duk cikin masarinta dana sani banga mai wannan nagartar ba, amma bansan ko ke zaki iya samoshi koda a cikin danginki ne?"
Shiru Mamie tayi dan sosai ta gamsu da bayaninshi, amma kuma saita kasa tuna komai dan haka tace "a'a, karfa muje wajen neman na gari kuma mu had'ata da bata gari, kawai ina ganin tunda ga Mujahhid nan d'an uwanta ai sai a had'asu."
"Umm hakane, to ki kwantar da hankalinki insha Allah gobe da safe zanje na samu yaya *Suleiman* sai muyi magana."
"Amma kana ganin Khairat ba zata bada matsala ba? danni yarinyar nan halinta sai ita fa."
"Ki barta, wannan karan dai kam zan nuna mata ni mahaifine, zan shawo kanta da yardar Allah."
Cike da jin dad'i Mamie tace "gaskiya naji dad'in haka, Allah ya k'ara mana shiriya."
"Ameen, ban fad'a miki bane, amma harna fara zuwa islamiyya ta manya, daga sallah magrib zuwa insha, kuma a yanzu babu abinda ke min dad'i kamar kasancewata a majlisi na ganni gaban malam ina d'aukar karatu."
Cikin nuna tsatsan farin ciki Mamie ta fad'a jikinshi tace "hakan yayi kyau, gaskiya ka kyauta, Allah ubangiji ya yafe kurakurenka na baya."
"Ameen." ya fad'a tare da sauke ajiyar zuciya ya sake matseta.
π _Daga nan dai na bar gidan nayi nawa gidan nima._
*Tunda safe* koda Papa ya gama kari ya fita bayan Mamie ta bishi da addu'ar fatan nasara, Khairat kuma na d'aki na bacci lokacin tashinta baiyi ba.
Yaya Suleiman yayi matukar mamakin ganinshi a bazata haka, amma kuma farin cikin ganin d'an uwan nashi wanda yake masa wuyar gani yasa bai nuna a fuska ba har saida ya samar masa masaukin daya dace sannan, yana zuba masa lemon a cup yace "gaskiya fa ka shammaceni sosai, irin wannan bazata haka kuma da sassafe."
Cikin dariya yace "gaskiya dama nasan zansha wannan maganar, wallahi kawai cewa nayi zaifi nazo da safe dan wannan lokacin ne zan iya samunka gida."
"Gaskiya kam, dan ina shirin fita ma yanzu."
Zaune yayi suka gaisa sosai kafin shiru ya biyo baya, yaya ne yace "kamar da magana ko Ousman? fad'i ina jinka, meke faruwa?"
"Babu komai yaya, ba wata matsala bace, nazo ne akan maganar 'yarka da kuma d'ana."
"Wai kana nufin Khairat da Mujahhid?"
Kai ya girgiza yace "eh su, naga kamar lokaci yayi daya kamata ace mun had'asu tunda ba yara bane."
Duk da yaya Suleiman ya d'anji wani abu amma dai kuma ba komai bane, cikin farin ciki yace "ranar daka saka kazo ka fad'a min, ko kuma ka zo kawai ka sanar danine dan nasa albarka a ciki?"
Dariya yayi yace "yaya kenan, ai kaine uban 'ya, dan haka kai muke jira kasa mana rana."
Dariya shima yayi da k'arfi yace "haba dai wasa kake, ai duk diyanka ne dan haka kasa ranar data maka kawai."
Papa ne yace "amma kafin musa ranar aida munji ta bakin Mujahhid d'in ko? dan kasan yara fa, watakila bai shirya ba ko kuma yana da wani tsarin a ransa."
"Haba dai Mani, yaranmu ne fa mu muka haifesu basu suka haifemu ba, kawai ka fitar mana da ranar, tunda yana da aikinyi kawai aurene ya gagara sai yawo a gari tare da abokai, idan kuma kai kana jin tsoronsu ba zaka iya ba ni saina saka ranar."
Dad'i Papa yaji dan haka yace "to ba komai hakan ma ai yayi, kawai ka tsayar mana da lokacin, sai muyi fatan Allah ya nuna mana ranar da alkairi."
"To tunda kace haka, yanzu mu barshi nan da wata d'aya, hakan ya maka?"
Wani sabon dad'i ne ya sake kashe Papa dan jin ansa daidai da lokacin da Mamie ta diba , da sauri yace "hakan ai yayi yaya, Allah ya nuna mana ranar, Allah ya tabbatar mana da alkairinsa."
"Ameen ameen, kawai kuje ku fara shirye shirye, muma tanan wajen zamu fara, duk da ma dai abun duk gidane."
"Gaskiya ne yaya, kuma da wannan nake maka albishir d'in dauke muku duk wata dawainiya, hatta gida da zasu zauna a ciki ni zan bayar insha Allah."
"Masha Allah, to hakan ma yayi Allah ya sanya alkairi."
*A haka* suka tsayar da maganar auren Khairat da Mujahhid, tun a hanya Papa ya kira Mamie ya fad'a mata, wai zo kaga farin ciki wajen Mamie marar misaltuwa, sai dai Papa yace karta fad'ama Khairat sai zai fad'a mata yanda zata fahimta, suna gama waya Mamie na zaune kawar Khairat ta shigo da sallama, amsawa Mamie tayi cikin daure fuska saboda tasan k'awacen 'yarta da *Rashida* ba alkairi bane, cikin ladabi ta zauna gefen Mamie tace.
"Mamie ina kwana?"
"Lafiya lau, daga gida a ke?"
Saboda jin tambayar wata iri yasa ta d'ansha jinin jikinta tace "eh Mamie daga gida nake, dama nazo ganin Khairat ne, jiya take cemin ta dawo gari."
"Ina fata dai ba fita za kuyi ba ko?"
"A'a Mamie, ai yanzu mun daina fita in ba da rana ba."
"Kice dai kun shiga hankalinku."
"Gaskiya kam Mami."
Kallonta Mamie tayi tace "Rashida, me zai ku nutsu kusan cewa annabi ya faku, Rashida zaifi muku ku fara neman ilimin addini, ku koma islamiyya tunda ba'a tsufa da neman ilimi, kuma bokon nan kunyishi keda k'awarki iya gwargwado, dan Allah ku koma in da zaku san ubangijinku da yanda zaku bauta masa domin tsiranku duniya da lahira."
A kunyace tace "insha Allah zamu koma Mamie, mun gode sosai."
Tashi tayi tace "bara na shiga ciki, nasan mutuniyar bacci take har yanzu."
"Umm." kawai Mamieta fad'a danta lura Rashida bata wani d'auki zancen da muhimmanci ba, binta tayi da kallo ganin kayan dake jikinta itama dai kamar Khairat d'in sai dai ita ta fita jiki hakan yasa matsatsin kayan ko kyau basa mata.
Kwance take akan makeken gadonta rufe ruf da zanin rufa pink saboda sanyin da d'akin ya d'auka na ac, zaune tayi akan gadon ta daddab'ata tana fad'in "macho, machota tashi gani na zo."
Dogon tsaki taja tana bud'e zanin daga kanta, saida ta tashi zaune sannan ma ta kalleta, jingina tayi da kan gadon ta kalleta cikin muryar bacci tace "infa gaki saime, me zaki min? hada wani zuwa ki tasheni."
Shiru tayi ba amsa dan tasan ta tab'o dala ba ganmo, ganin ba tayi magana ba yasa ta sauka daga kan gadon ta nufi ban d'aki tana tattare gashinta daya bazu wanda tun tana kwance aka since matashi.
Jin qarar ruwa yasa Rashida ta tabbatar wanka ta fara hakan kuma yasa ta gyara zama, dan tasan awa d'aya ce zata fito da ita daga bayin, bugu da qari itama ba zata iya barin gidan ba har saita samu abinda take so, dan in bata jira ba zata ma kanta asarar kud'i kuma tana da tabbacin zata samu.
06/08/2019 Γ 00:06 - Meerahgee❤: ππππππππππ
*JIHADI*
_Umar faruk_
ππππππππππ
_NA_
_SAMIRA HAROUNA_
_DEDICATED TO_
*MA FAMILLE*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
_Bismmilahir-rahman-rahim_
1⃣4⃣
Fitowa tayi da d'aurin qirji iya cinyoyinta taja kujera ta zauna a kai tana kallon kanta a madubi, mai take so ta shafa amma tana jin k'iwa, Rashida ce ta taso ta tsaya bayanta tasa hannu tana shafar kanta tana murmushi, ta madubi ta kalleta tayi qaramin tsaki, sun jima a haka babu wanda yayi magana, saida ta gaji da miskilancinta sannan tace "me kike so?"
Kallonta tayi ta madubi amma ba tayi magana ba, sake cewa tayi "kiyi magana macho, nasan wani abu kike so shi yasa kika zo."
Kai ta sosa ta fara magana "eh to, wallahi macho, gidane babu kudi gashi babu kayan abinci, mun shiga wani hali saboda ba kya nan, yanzu ma banso na zo wallahi dole ce tasa na zo."
Juyowa tayi ta kalleta tace "d'auko min kayana nasa."
Juyawa tayi ta nufi wajen kayan nata tana hararanta ta qasan ido, da hannu ta nuna mata wanda zata d'auko mata, tana kawo mata tace "ki kira min Biba."
Nan ma a qufule ta juya ta fita, Khairat ma nayin hakanne da gangan dan abotarta da Rashida bata da wata mamora, shi yasa wani lokacin take sata aikin ma da bai kamata tasa ta ba idan ta lura akwai abinda take so a wajenta.
Ta riga Biba shigowa kafin itama ta shigo tace "gani Hajia."
Ciki ciki tace "ki wanke hannuwanki a ban d'aki kizo ki shafa min mai."
Saida ta kalleta sannan ta shiga dan wanke hannuwan, haka ta fito ta fara shafa mata man a jiki har suka ida Rashida na zaune, da taimakon Biba tasa kaya sannan ta zauna gaban madubi ta murza powder kad'ai sannan tasa Rashida ta d'aura mata d'an kwali, masha Allah tsaf ta fito cikin riga da siket d'in atamfa wacce tasha d'inki tsadadden.
Saida ta gama kallon kanta a madubi sannan ta juya ta bud'a wani coffre ta d'auko poshet (post) ta tsaya gaban Rashida, budawa tayi ta d'auko kudi yan jikka goma goma sababbi guda biyar ta mika mata, tana sa hannu ta karba Khairat ta juya zata fita Rashida tayi saurin rumgumota ta baya tana fad'in,
"Oh, mon chouchou, na gode sosai Allah bar min ke ta wajena."
Murmushi kawai tayi ta janye kanta daga jikinta ta fice, binta tayi a baya haka ta sauka daga kan matakala kamar wata sarauniya, kai tsaye wajen cin abinci ta nufa ta zauna saman kujera, Rabi ce tayi saurin zuwa ta fara zuba mata farfesun kayan cikin rago da kuma soyayyar kaza ga kuma doya da aka mirginata cikin k'wai, fresh milk ta d'auko mata ta zuba mata sannan ta fara ci, Rashida kam an samu kud'i ko ta abincin bata bita, sallama tama Mamie sannan ta kalli Khairat tace "macho na tafi, sai mun had'u."
Ba wani sosai taci ba, dan Khairat a rayuwa bata san k'iba, dan d'an kumarin dake gareta ma yanzu jinshi take a wani babbar matsala, dan haka take kula da jikinta sosai amma bata son motsa jiki saboda ragwantaka, tana kammalawa ta komo falo ta zauna kusan Mamie, hankalinta na a wayarta Mamie kuma na kallo tana d'an satar kallonta wani lokacin tana murmushi.
*****************
*Umar Faruk* kuma tun jiya daya ga Khairat ya kwana cikin tunanin halin daya ganta, sam baiyi tunanin haka daga gareta ba, ya d'auka zata canza ko dan abinda ya faru da ita amma sai yaga akasin haka, ta wani b'angaren kuma haushin abinda wannan mutumin ya fad'a yake ji, da haka har safiya tayi ba tare da yayi wani baccin kirki ba, duk lokacin daya farka Khairat ce zata ziyarci tunaninshi da ganinshi.
Haka kawai yaji yana burin ya sameta a wajen aiki, shiri yayi sosai cikin qananan kayanshi bak'ar riga mai dogayen hannu da wando kalar qasa, yana shiga ma'aikatar ya fara duba wajen ajiye motoci ko zaiga motarta amma babu, duk da haka bai sare ba bayan ya shiga ciki ya aje jakarshi cikin dubara da sand'a ya nufi bureaunta, lekawa yayi ta madubi amma babu kowa kamar dai yanda yake, wata ajiyar zuciya ya sauke cikin sanyin jiki ya dawo mazauninshi, yana zaunawa ya fara tambayar kanshi wai me yasa ya damu da son ganinta ne, tsaki yayi kawai ya fara aikin gabanshi.
****************
Khairat ce ta 'kwalla kiran Biba, tana zuwa tace ta d'auko mata jaka a d'aki da gyale, cikin 'yan mintuna ta dawo da jaka da takalma da gyale duk kalar atamfar dake jikinta, tana sakawa tayi hanyar fita Mamie tayi saurin cewa "sai ina kuma Khairat?"
"Mamie zan lek'a bureau ne naga meke faruwa acan, saina dawo."
Harta wuce Mamie tace "zo mana gimbiyar Papanta."
Dawowa tayi ta tsaya gabanta, tashi tayi tsaye ta shafi fuskarta tace "Allah ya miki albarka Khairat, Allah ya baki yaya na gari, Allah ya kiyaye hanya kinji ko."
Cikin jin dad'i ta rumgume Mamie tace "yau dai da wayona naji addu'ar sa albarka ta fito daga bakinki, na gode Mamiena, saina dawo ba zan jima ba."
Sumbatar goshin Mamie tayi ta fita cike da farin ciki yau Mamie ta mata addu'a, ita kanta Mamie sai taji ba dad'i dan in zata iya tunawa gaskiya ta jima rabon data mata addu'a irin haka.
*Kuskure da iyaye mukeyi sakacin yiwa yara addu'a, wasu na ganin laifin Khairat data zama fitsararriya, amma bansa Khairat ta zama haka ba har saida na samu dalili, Mamie ta kasance mai zuciya da yanke hukunci cikin hushi, hakan ya janyo tun Khairat na qarama ta daina daina janta a jiki bare tasata a hanyar data dace, hakan kuma bai dace ba ko kad'an, yaro ko yana qarami kake masa addu'a zan sai kana masa, uwa uba kuma addu'ar na bibiyarsa ta alkairi ko akasin haka, mu kula iyaye Allah ya bamu ikon tarbiyantar da yaranmu.*
Da takonta na qasaita ta shigo wajen, kallon Abba yayi kowa da komai take da kyau, Umar Faruk daya duqufa da aiki, gabanshi ne yaji ya tsinke ya fad'i hakan ya tilasta masa juyowa da k'arfi, kasa dauke idonshi yayi daga kanta, duk da ba murmushi a tare dashi amma kuma fuskarshi a sake take, ganin yanda kowa ke kallonta kamar da wani abu a jikinta yasa ta tsaya waje d'aya, sake kallon kowa tayi dake wajen ta girgiza kai tayi murmushin takaici.
A hankali tace "kowa ni yake kallo saboda yanzu kuna ganin kamar na zama daban a cikin mutane, kowa so yake yaga ina cikin damuwa, ni kuma abinda nayi alk'awarin ba zan shiga ba kenan har abada."
Tana fad'a ta juya a fusace ta nufi in da ta aje motarta, Umar kuma buga tebur d'in dake gabanshi yayi tare da fad'in "kai."
Da gudu ya tashi yabi bayanta mutanen kuma suka bishi da kallo, Ishaq abokinshi ne yayi murmushi ya kalli na kusa dashi yace "dama ace duk soyayyar da aka fara da qiyayya to tafi zafi."
"Soyayya suke dama?" cewar mutumin.
"Kai ai basai an fad'a ba kasan akwai soyayya wannan wajen, watakila basu fahimci hakan ba."
"Lallai ko abokinka ya d'auko dala ba gammo, to ina had'in kifi da kaska? ai wannan qarmanje ne."
"Ban gane ba, ita kasan meye ra'ayinta to da za kace haka?"
Cewar mutumin "ai ko ban sani ba aikinta ya nuna abokinka baya da wani girma da qima a idonta, tunda nidai banga ko kallonshi tayi ba, zaifi ka bashi shawara ma tun wuri ya fitar da abinda ke ranshi, dan wahalar banza zaisha."
"Ai kuwa in dai har gaskene, to wallahi zaka sha mamaki, dan kana nan zaune za'a gayyaceka daurin aure."
"Tare dani dashi da kai za'a gayyata." cewar mutumin yana kama aikin gabanshi.
Tana daf da shiga mota Umar Faruk ya fito da gudu, juyawa tayi ta kalleshi ta tsaya saida ya karaso, tsaye yayi ya kuma rasa me zaiyi sai yanzu yake jin haushin abinda yayi, juyawa yayi zai koma ciki tace "kazo ka tambayeni me nake ji ne?"
Juyowa yayi yace "a'a, akan me?"
Dogon tsaki taja ta bud'e motarta ta shiga taja tayi gaba, shima ciki ya koma yana tsananin jin takaicin abinda ya aikata, shin me yasa yayi haka???
*****************
Tun yamma da Mujaheed ya dawo gida mahaifiyarshi ta fad'a mashi halin da ake ciki tare da zigashi akan karya yarda, bud'ar bakinshi cewa yayi "Mama bama sai kince ba, wato ni zasu rainawa wayo ko? kafin ta zama ragowa ina biyarta amma tana wulak'anta ni, su kuma sun biye mata aka su ba zasu bata wanda bata so ba, yanzu kenan sun saduda ne shine za'a kawo min ita ni d'an iska ko, to wallahi basu isa ba."
Tunda mahaifinshi ya dawo da dare suka sameshi da mahaifiyar tashi akan basu son wannan maganar auren, Baban baiji dad'i ba haka sauran matanshi guda biyu sun bada tasu shawara akan Mujaheed yayi hak'uri tunda yer uwa ce, amma mahaifiyarshi tace su rufe musu baki dan ba yayansu bane, an jima ana tattaunawa har saida Mujaheed yace in dai har aka takurashi wallahi zai shiga duniya, sanin halinshi da Baban yayi wanda dama ya ake dashi yanzu ma bare ya sake shiga wata duniyar, hakan yasa yace an fasa sai dai yana jin nauyin yanda zai fukanci d'an uwanshi.
Ganin baida wata mafita yasa ya kira Papa a waya ya fad'a masa yanda sukayi cikin raunin murya, a zahiri Papa ya nuna babu komai amma da suka gama waya bak'in cikinshi ya bayyana, bayan ya shigo gida shima bai iya fad'awa Mamie ba saboda gudun matsala, amma kuma ya kwanta da wani sabon shirin a ranshi, safiya kawai yake jira ta waye ya gudanar dashi.
_To Papa muji alkairi._
Kamar yanda Khairat tayi niyyar ba zata bari damuwa ta samu muhalli a zuciyarta ba, tunda ta dawo take d'akinta bayan tasha bacci ta tashi da yamma, da dare kuma tana d'aki tana tik'ar rawa abinta duk dan karta damu.
Ko kari Papa baiyi ba ya fita Mamie bata sani ba Khairat kuma na bacci, hanya Papa ya d'auka shi da drivenshi cikin awa d'aya suka isa fadar shugaban....fan's ku k'arasa min _(bana son tabo mukamin kowa, amma ku kuyanke hukunci ku d'auka babban Muzaffar shine qarshe a mulki baban Khairat kuma na binshi baya)._
Tarba ya samu sosai a babban falon bak'i na palace d'in shugaban , hamshakin shugaban mai dattako cikin fara'a ya kalli Papa yace "sai kuma gaka da safiyar nan, kamar da wata matsala ko?"
"Ba wata matsala shugaba, kawai dai nazo mu gaisane."
"To da kyau, ya al'amura kuma da fama da jama'a?"
"Alhamdulillah, ya naku k'ok'arin?"
"Alhamdulillah."
Shiru ne ya d'an biyo baya kafin shugaban yace "ya yarinyata da jiki, taji sauk'i ko? dan har yanzu bamu sake komawa ba."
Dariya yayi yace "shugaba ai dan mun kwana biyu bamu had'u ba, amma Khairat taji sauk'i sosai."
"Ah to alhamdulillah."
Papa ne yace "ina Muzaffar? na kwana biyu ban ganshi ba."
"Muzaffar ai yau kwananshi uku baya nan, na turashi saudi arabia dan halartar wani taro na qarawa juna sani akan yanda za'a inganta rayuwar matasa."
"Da kyau shugaba, in da kake birgeni kenan, kowane abu kana azashi a muhallinshi, Allah ya taimaka ya dawo dashi lafiya."
"Ameen ameen, fatanmu dai Allah ya mana mai kyau."
Wani shirun ne ya sake biyo baya kafin shugaba yace "'yata dai tak'i yarona, da yanzu mun gama da maganarsu."
Cikin dariya Papa yace "ah haba shugaba, taya zata k'i d'anmu, yanzu haka ma maganar aurensu ya kawoni, dan nayi tunani zamanta a gida haka yayi yawa sosai, kuma tunda suna fahimtar junansu naga zaifi kawai mu had'asu."
Gyara zama yayi a cikin lunstumemiyar kujerar yana fara'a yace "haba dai, kai amma naji dad'i sosai da maganar nan."
D'orawa yayi da "Muzaffar zaiyi farin ciki da wannan magana, gaskiya naji dad'i sosai, danni kaina burina bai wuce naga yayi aure ba."
"Hakane shugaba, dan haka yanzu wuk'a da nama na hannunku, kasa lokacin da kaga ya maka."
"Kuma dai? dad'in ai saiya mana yawa."
"A'a wallahi baya komai, idan kunsa ranar ku fad'a mana, iyakarmu addu'a kawai."
"Umm, to yanda mai zai hana asa nan da wata d'aya, tunda kaga akwai wani babban taro da za ayi 15 ga watan da za'a shiga, kuma dole mu dasu yaran duka zamu halarceshi, kaga zaifi dad'i suje a matsayin ma'aurata, koya ka gani?"
"Hakan ma yayi daidai yallab'ai, Allah ya nuna mana lokacin da alkairi."
A haka dai Papa ya baro gidan cikin farin ciki, take kuma shugaba ya dannawa Muzaffar kira, yana d'auka daga d'aya b'angaren yace "Papana ya kake?"
"Daidai yarona, albishirinka?"
"Nasan baka min albishir marar dad'i, goro fari tas Papana."
"Yanzun nan Mani ya fita daga nan, kuma bai bar nan ba saida muka tsayar da aurenku kai da Khairat."
"Wow, da gaske Papa? kai amma naji dad'i sosai, Papa yaushe kuka saka?"
"Nan da wata d'aya, aiya maka ko?"
"Sosai ma Papa, gashi dai Allah yayi zaifita zama mijin Khairat, to dan Allah Papa kuyi duk abinda ya dace kafin na dawo."
"Karka damu yarona, yanzu zan shiga ciki muyi magana da mamarka akan yanda za'a tafiyar da komai."
"yawwa Papana, a fara shirya komai kafin nazo, idan na zo zamu ci gaba da shiri, dan dole bikina da Khairat ya amsa duk gari a samu labarinshi, saboda kaga fa babbar yarinya ce nima kuma haka."
"To shikenan karka damu."
A haka suma sukayi sallama, haka ma a ciki ya fad'a ma mahaifiyar Muzaffar, sosai itama tayi farin ciki da alamarin dan a rayuwarta tana son bariki da tsare kai, hakan yasa Khairat ke birgeta sosai, dan lokuta da dama suna had'uwa a wasu tarurruka ta wakilci mahaifinta ita kuma ta wakilci shugaba, hakan yasa take sha'awar aurenta da d'anta.
Lokacin da Papa ya dawo Mamie ta gama karinta tana tunanin in da ya tafi bata sani ba, ganinshi yasa ta mike tana tambayar lafiya, saida ya zauna yace ta zauna, zaune tayi tana kallonshi kafin yace "daga gidan shugaba nake."
"Shugaba kuma? lafiya, wani abunne ya faru?"
"Lafiya lau, akan auren Khairat ne."
"Auren Khairat kuma? amma ba'a fasa ba?"
"Eh, an fasa Mujaheed sai Muzaffar."
"Muzaffar kuma, da gaske Alhaji."
"Sosai ma, kawai ke dai kici gaba da shirye shirye, Khairat kuma zan fad'a mata nan da kwana biyu idan muka ga komai na tafiya daidai."
"To Allah ubangiji ya sanya alkairi, Allah ya nuna mana ranar."
Suna gama maganar Khairat ta fito da riga da wando farare tas ta zauna, "ina kwananku?"
Kallon juna sukayi dan haka bata tab'a faruwa ba, amsawa sukayi Papa ya dora da "shalele kin tashi lafiya?"
"Lafiya lau, Biba." ta d'ora da kiran Biba a qarshe.
Da sauri Biba ta fito ta zube gabanta, cikin yauki tace "ki kawo min abinci na."
"To Hajia." ta fad'a tare da tashi.
Anan ta kawo mata ta fara cin abincin Papa kuma fita yayi gabatar da harkokinshi, Mamie ce tace "ki kammala cin abincin ki shirya zamu tafi dake gidan *Safiya*."
Kallonta tayi tace "Mamie nifa kinsan bana son zuwa gidan nan, wannan d'an iskan yaron da yake min maganar banza wai yana sona, bana son ganinshi ma."
Dariya Mamie tayi tace "ki shirya muje kedai, kinsan na jima banje ba, kuma yanzu nasan ba zai miki maganar soyayya ba."
Kallon Mamie tayi danta fahimci me take nufi da abinda ta fad'a, maida kallonta tayi ga abincinta tana tunanin yanda za tayi rayuwa a cikin mutanen da take kewaye dasu ba tare data iya tuna abinda ya faru da ita ba.
Da qyar Mamie ta lallabata ta shiga danta shirya, saida ta d'auki awa d'aya kafin ta shirya ta fito Mamie harta gaji da jira, a motar Mamie suka tafi tare da driventa suka nufi unguwar *yantala* (gidan Safiya diyace ga magajiyar mamar Na'ima, ma'ana cousine d'inta.), da sallama Mamie ta shiga gidan sab'anin Khairat dake binta kawai, da farin ciki matar ta taresu sai dai Khairat fuskarta a had'e take saboda hayaniyar gidan tayi yawa, saboda matan gidan hud'une yara kuma manya da qanana barkatai, haka suka shiga ciki suka zauna, matar ce ta fara gaishe da Khairat kafin tace "ina wuni."
Wata matashiyar budurwa ce ta shigo ta kawo musu ruwa, Mamie ce tasha ita kuma ko kallo, dama Mamie ta mik'a mata girgiza kai tayi tana b'ata fuska, ganin Mamie na janyo hirar da zata sa su jima yasa ta mik'e tsaye tace "Mamie ki sameni a mota, ba zan iya zama cikin zafin nan ba."
Safiya ce tace "gaskiyarki kam akwai fa zafi."
Kallonta kawai tayi ta fice a soron gidan suka had'u da *Aqilu*, wucewa taje yi ya tare gabanta yana fad'in "ya dai, yau kece a gidan?"
"Dallah matsa min a hanya."
"Ina zuwa mana, magana nake so muyi."
"Kar kace zaka min maganar banzan daka saba, dan bana da lokaci."
Wata irin dariya yayi yace "wai maganar so kike nufi, ai wannan tsohon yayi ne, abinda nake son fad'a miki yanzu kuma shine, dan in gaya miki cewa na janye son da nake miki ne, dan ba zan...."
Bai k'arasa ba tace "shashasha."
Wucewa tayi ta barshi nan tsaye kafin ya ida shiga ciki....
0 comments:
Post a Comment