Kallon takaici yayi mata.
"Keda ita ba d'aya bane, you're my friend ita kuma she is nothing.."
Cikin rashin gamsuwa da kalamansa ta tab'e.
"ban yadda ba saboda dazu kallon da kake mata baiyi kama da babu komai ba, kuma na tabbata ka fara sonta"
Murmushi gefen baki ya saki wanda shi kadau yasan manufarsa, yace "tabbas na kamu da sonta saidai son da nake mata baikai na kasance tare da ita ba, kin dauka zan barta taci bulus ne bayan tamin rashin mutunci "
Nisawa Faiza tayi, aranta batai na"am da koma mai yake niyyan yiba, tunda har ya furta yana sonta ba lailai ne ya rama abunda zaiyi ba
"What are you planning ?
Girziga kai yayi yace "i dont know yet, ina dai tunani gagarinmin abunda zanyi na koya mata hankali, so nake tayi kuka da idanta"
"Daganan kuma saika rabu da ita kenan ? Faiza ta fadi.
Tsaki yaja
"Kinga enough of your questions, you're just a friend banaso ki wuce limit dinki" ya fada, amshe mukulli hannuta yayi ya fada motar yaja ya barta nan tsaye baki sake cike da takaici.
Salma na shiga Gida daki ta wuce ta kwanta, zuciyar ta fal da farin ciki, tunanin Mujahid take tana tuna farkon haduwa su izuwa yau, kwata kwata takasa gane kanta, shin sonshi take komi, kullum dashi take kwana ta tashi, girgiza kai tayi, sam babu lissafi soyayya aranta, bata tab'a yi ba saidai na baya data gani sun wahalu daga karshe ma tsana ce ta biyo baya shiyasa take bala'in tsoron fadawa soyayyar wani. Tana son Mujahid amma bazata nuna mai komai ba ayanxu har saida tabbatar he won't break her heart.
****
Tun daga ranar lamari ya canza tsakanin su, soyayya da kulawa sosai Mujahid yake nunawa Salma saida bai fito yace yana sonta ba, har ilah yau bai kuma canza kudurin sa na koya mata hankali ba, ta bangaran Salma kuwa zuciya daya take zaune dashi takan yi mamaki sai kace ba kwanakin baya suke casa juna ba, aranta takanyi tunanin anya kuwa Mujahid baida wani mugun nufin akanta, saurin kawar da tunanin take saboda tsananin yadda yake damuwa da lamarinta.
Daddyn Salma ne tare da Ja'afar a office dinsa. ja'afar yana daya daga cikin lauyoyi da Alhaji Abbas ya aminta saboda tsananin rike gaskia da Tsoron Allah da yake azuciyarsa, sau tari yawan idan zaiyi harkar canji da dollars ko euro yafi yadda da damk'awa jaafar takardun shaidan komai dan yasan bazai cucu saba.
Zaune suka suna magana akan wani fili daya siya a Kaduna, copy na takardu shaida da komai ya mikewa Jaafar, karba yayi yana dubansu
Daddy yace "ka adana su da sauran"
Hade takardun jaafar yayi cikin briefcase nasa sannan ya mike da niyan yimai sallama, dakatar dashi Daddy yayi hade da cewa "ya maganar mu ta kwanaki, naji shuru baka kara waiwayar zancen ba.."
Zama jaafar yayi had'e da kirkiro murmushi dole, shikam yama manta da zancen, shuru yayi yana tunanin zancen da neman amsar bawa Daddy, bazai yaudari zuciyan saba dan kuwa yana son Junaina, saidai kuma ba damuwa tayi dashi ba ga kuma Daddy da yakeson ya hada shi da Diyar shi dako sanin ta bai yiba balle ma yasota, shi kuma auran bayama cikin lissafinsa yanzu kokarin Nemo Ummi kawai yake dan farin cikin hajiyarsu kuma baima isa ya tunkareta da sunan yana son aure ba, ana takai wa yake ta kaya.
Ajiyar zuciya ya sauke yace "Alhaji wani hazari ba gudu ba, maizai hana mu hadu da diyar taka, idan ta amicin dani saina yadda karya zamana ko tana da wanda takeso"
Farin ciki sosai ya lulube Daddy, kasancewar ta bangaran Salma ba matsala koda batason Jaafar yasan zata mai biyayyah, kuma ma baiyi tunanin Salma nada wani da takeso ba.
yace "ba matsala, gobe kazo gidana mu kara tattaunawa saika ganta
Yake jaafar yayi aranshi yace "Allah yasa karta aminci, afili yace "saidai yau nazo, saboda gobe da safe ina da aiki a Kaduna"
"ba damuwa, Allah ya kaimu zuwa dare" acewar Daddy.
Godiya yama Daddy sannan sukai sallama ya fice azama.
Tun ranar da Hajiya ta kira Mujahid tace yazo gida bai samu daman zuwa ba sai rana ta yau acewarsa aiki yamai yawa bacin kuma da gangan yaki zuwa.
Fuska ba yabo ba fallasa Hajiya ta tarbeshi, nan tahau mai fadan barin sa gida akan abunda baikai ya kawo ba, Mujahid kam shuru yayi yana sauraran ta dan ya kagara ta gama ya wuce aikinsa, tace "Bani hotunan Ummi dana baka kwanakin baya"
Sosa keya yayi alamun marar gaskia yace "mi zaai dasu, an ganta ne ?
Hajiya tace " baa ganta ba, kawai hoton zaka bani tunda ba nemo ta zakayi ba, tuni Jaafar ya dukufa da nemo ta kuma am sure zai samota aduk inda take"
Ware ido Mujahid yayi adan kidime yace "jaafar zaki bawa hoton ?
Mugun kallo takai mai, tace "ko babu hoto Jaafar yasan fuskan ta, kaida ba saninta kayiba yasa na baka hoton"
Gabansa ne ya fadi, fatan shi Allah yasa kar Jaafar ya hadu da Salma, nisawa yayi yace "Hajiya basai jaafar ya nemo taba, nida kaina zan kawota gidan nan very soon."
"Ka ganta ne" Acewar ta.
Kai ya girgiza alamun a'a, aranshi yace "ki bani time very soon zaki ganta amma saina koya mata hankali yadda idan ta shigo gidannan bazata yadda ki had'ata aure da niba".
Tashi yayi ya mata sallman zai wuce office ya fice waje, nan suka hadu da Junaina ta dawo daga gidan wata kawarta dan tuni sun gama Neco.
"Yaya kyan tafiya dawowa" ta fada tana dariya.
Tabe baki yayi yace, "ce maki akayi nadawo"
"Oh Allah, he will never change, ni ina can ina missing dinshi amma koya kula dani" aranta tayi maganar, Afili tace "yaya akwai abunda nakeso kasani, sumtin is going on in this house"
Kallon gefe yayi babu mai dubansu sannan ya jata gefe danjin wana abu ke faruwa, sau tari dama ita ke kaima rohoton abubuwan dake faruwa agidan dan ba zama yake ba.
Murya kasa kasa tace "bansan full story dinba, naji dai Hajiya na Waya da Aunty Bilkisu akan wani abu, i dunno ko kudi ne ko gida ko kuma ince sumtin is missing i dont really know, naji Hajiya tace tunda kai kaki nemo wa idan ya jaafar ya nemo shi zata
bawa ta fasa baka"
Hankalin sane ya tashi danya gane inda Zancen ya dosa, saidai bazai bari Jaafar yaga Salma ba much less ya yadda da auran suba.
Dakewa yayi yace "little sis kinsan mi zakimin"
Kur tayi tana kallon shi, yace "inaso ki sawa Jaafar ido, idan kinji yana waya akan wata mace ko bincike ki bani feedback kinji"
Kai ta girgiza alamun toh, murmushi ya sakar mata. "yauwa my beautiful sister, you know i like you alot"
Dariya tayi tace "nidai yaya kadawo gida plz, wlh i missed you alot".
"Karki damu nakusa dawowa"
Dadi sosai taji, sun jima yana biyeta sai shagwaba take zuba mai daga bisani ya lallab'a ta ta tafi ya koma motarsa yaja yabar gidan.
Tuki yake yana neman mafitan yadda Jaafar bazai hadu da Salma ba, idan yayi sake kuwa yanaji yana gani zaiga Salma a gidansu, dabara ce ta fadowa mai yadau waya hade da dailing no din Salma.
Alokacin kuwa had'e book dinta Salma tayi cikin jakarta sannan tabar dakinta, gurin Mom ta shiga ta mata sallama ta fito cikin sauri, library na skull takesan zuwa karatu saboda jibi ne zasu fara exams.
Kokarin bude motar tayi taga kiransa, murmushi tayi ta dauka.
Daga can Bangaran cikin sweet voice dinshi yace "Angel of my life, son kowa kin wanda ya rasa"
Dariya tayi kasa kasa, tace "ka fara koh, how am i even sure am your angel"
Yace "believe me, ba karya nake ba, idan ma baki yadda ba God knows it.
"Kaga ni library zani, inada exam jibi, kana ina?
Yaji dadi abunda tace, aranshi yace "perfect, nasan abunda zanyi"
Afili yace "ina driving, ki jirani nazo nayi picking dinki saimuje inda babu wanda zai dameki dan kisamu kiyi karatu, nasan ki da tsokana kar kije kiyi dambe da mutane a library" karashe maganar yayi cikin zolaya.
Shagwabe fuska tayi kaman yana ganinta, tace "nifah bani da tsokana, ko dambe ban taba yibaaa.."
"Hmm, kedin, ki jirani am coming" katse call din yayi, ta fita can bakin gate jiran shi, baafi 20 mins ya karaso ta shiga motan ya kama hanyar office dinsa, tagane hanyar, tace "lailai ma office dinka ne bazaa dameni ba?
Wani shumin kallo yayi mata da saida taji shi a kwakwalwar kanta, murya kasa kasa yace "duk wanda ya dameki cikin cell zan wurga shi..
Ware ido tayi adan tsorace, "cikin cell sai kaca a film"
Dariya yayi bai kuma cewa komai ba ganin yadan tadan tsorata, suna isa parking yayi, suka fito suka shiga elevator har zuwa cikin office dinsa, ita batama san akwai elevator ba kasancewar ta stair security yabi da ita kwana kin baya.
Office din babba ne mai shegen kyau can gefe inda Couch da center table yake takarasa ta zauna shi kuma yA karasa gurin table dinsa ya zauna kan kujerar sa hade da fara aikin danna laptop din gabansa, sosai yaci serious da abunda yake batare daya dubi Salma ba.
Itakam abunda take so kenan, bude handout dinta tayi ta dukafa da karatun General studies da suke dashi.
Bayan kaman awanni uku Mubarak ya shigo office din, ganin Salma yasashi dariya, zama yayi gurin mujahid yana zolayar shi murya kasakasa, b'ata rai Mujahid yayi, yafara magana cikin fad'a, duk ahankali suke magana, Salma bataji komai ba kuma bata damu dason jiba, sund'an jima sannan Mubarak ya fice office din.
Gyaran murya yayi, Salma ta dubeshi
Yace "bani labarin samarin ki ?
Dariya tayi
"Banda saurayi, infact ni bana soyayya"
"Miyasa ?
Ajiye pen din hannuta tayi hade da yin tagumi, amaraice tace "Sanadin So Ummata tasha wahalan rayuwa, daga karshe ma Abbana ya rabu da ita da tsowon ciki, bansan lokacin ba, bansan anyi ba amma ayadda naji labari yadda komai ya faru yasa kwata kwata na cire so araina"
Kallon tausayi yayi mata, tunda yake gida bai tabaji labarin Ummanta abakin Hajiya ba, saidai zaiso sani..
Kaman wanda baisan da rasuwan Umman ba yace "ina umman take ?
Kaman zatayi kuka tace "ta rasu, lokacin daban santa ba, i was 3years old tym din".
Maida dubansa Mujahid yayi bisa laptop din yace "bai kamata ki cire so aranki ba, tunda iyayan ki daban ke daban"
"Hmm, am sacred banso ayi breaking heart dina"
Shuru Mujahid yayi baice komai ba, bayason cikata da surutu, bari yayi sai kuma gobe ya kara jeho mata wata tambayar.
Cigaba da karatun Salma tayi, lokaci Sallah azahar nayi ya nuna mata toilet dake office din sannan yafice zuwa masallaci, bayan ya dawo ya tura aka kawo wa salma abincin take away, godiya tayi.
Karfe bakwai Daddy ya dawo Gida, nan ya tsarawa Mom batun zuwan Jaafar, sosai taji dadi da batun daddy dan kuwa ta kagara Salma tayi aure ko zata nutsu, nan daddy ya shaida mata bayan Sallah Isha'i Jaafar zaizo ganin Salma, dadi sosai taji, wayarta tadauka dan kiran Salma.
Bayan Salma ta idar da sallar Magrib, Qur'an dake ajiye a office din tadau ta karanta sannan ta ijeye ta cigaba da karatunta, lokacin Mujahid yafita masallaci bai dawo ba, kirar Mom tagani tayi azaman dauka.
Aladab ce ta gaidata, Mom ta amsa sannan tace "Salma kibar duk abunda kike kidawo gidan yanzu nan, Daddy zai baki wani Surprise"
Farin ciki ne ya kamata, tace "momy miye ne, dan Allah gayamin i cnt wait saina zo"
Dariya momy tayi tace "idan kinason sani kizo maza yanzun nan, kuma kiyi sauri" katse call din Mom tayi, cike da Murna Salma tahau tattare books dinta ajaka, Mujahid ne ya shigo, ganin tana hade komai yace "keda kika ce sai 10 zamu tafi, kin fasa ne ?
"Eh nafasa, kaini Gida" cigaba tayi da hade komai zuciyar ta fal murna.
8.20 Jaafar ya iso gate din Gidan Daddy, bai tab'a zuwa gidan ba yasa yakira Daddy awaya dan tabbar da gidan ne, nan take Daddy ya kira mai gadi aka budewa mai gate ya shigo gidan, cikin palo gidan Daddy yamai iso, ya shiga yagaida Mom aladabce, sosai mom ta yaba da hankalin sa, sun gaisa sosai, mai aiki ta kawo mai na shasha baki, shikam Jaafar gaban sane keta faduwa, har yayi dana sanin kowa kanshi gidan.
Mom kam murmushi kawai take tana saurara isowan Salma....
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
®NWA
43 - 50
Murmusawa Mujahid yayi ganin yadda take cikin walwala. Table dinsa ya k'arasa yadau wayarsa tare da mukulin mota. Ficewa sukayi daga office suka nufi ma'ajiya motar, Salma na tafe tana waya da Mom, cikin sauri tayi gaba ta tsaya bakin motar. Wayar sace tayi ruri, ya duba yaga Junaina da kuma miss call datai mai wanda bai lura ba sai yanzu, tsaye yayi nan inda yake batare daya karasa inda Salman take ba ya dauka.
"Little sis ya ake ciki ?
Kaman munafuka Junaina tahau duben ko ina a palo gudun kar wani yajita, murya kasa kasa tace "yayA naga ya jafs ya fita, kuma naji yana waya da wani zaije ganin wata yarinya, i dont know wace yarinya ce"
"Yaushe ya fita ?..
"Yadan jima kuma bai cewa Hajiya Komai ba"
"Okay Sis, ki cigaba da samai ido, i'll call you later" katse call din yayi ya karasa motan suka shiga, sai sannan ya tambayi salma dalilin tafiyar ta, bata boye maiba ta fadi mai Mom ke kiranta kuma it urgent.
Shuru Mujahid yayi yana tunani anya ba gidansu Salma yaje ba, wata zuciyar tace it cnt be possible, miye zai kaishi gidan, saidai surprise da Mom zata bawa salma ne ya tsaya mai arai, zuciyar sam bata aminta da hakan ba, kuma baiji yana son tafiyar Salma ayanzuba. Kallonta yayi da gefe ido yaga tana latsar wayarta fuska ta dauke da murmushi..
Murmushi yayi sannan yaja wani wawan burki da saida ta tsorota, afirgice ta kalle shi, gani tayi ya daura kansa bisa steering hannusa dafe kan gefen cikinsa, murkutsutsu yahau yi tamkar wanda zai mutu.
Tsabar gigita bata san sanda takai hanunta bisa bayan saba tanai tambayarsa maike damunsa, kasa magana yayi banda cije labb'a da yake, fita tayi motan ta zagayo gurin sa. Tambayarsa ta kuma tayi, murya ciki ciki yace "am sick, can you drive ?
Kai ta gigiza alamun eh, taimaka mai tayi ya koma dayan sit din sannan ta shiga taja motar.
Kaman mai shirin kuka ta kalle shi, "wana asibiti zamu ?
"Kaini gida kawai" ya fada yana lumshe ido, shingidewa yayi akan sit kaman wani marar lapian gaskia.
Hankali tashe tahau driving ba tare data tuna kiran da Mom ke mata ba, suna isowa gidanshi ta taimaka mai suka shiga ciki ayayinda sai faman cemai sannu take, shikam dariya ke cinsa yana gimtsewa. Zaunar dashi tayi kan two sitter sannan ta dube shi, murya cike da tausayi tace "sannu yaya.."
Yi yayi tamkar baiji taba saima rufe ido dayayi, itakam tanason tafiya ga dare yafara lulawa, gyara zama tayi ta fuskan ceshi tanai karemai kallon aranta tanai kara jin sonshi. Sunkai 20mins ahaka kafin nan ya bude ido, suna kallan juna, lumshe ido yayi yace hado min tea nasha magani"
Ba musu ta mike ta shiga kitchen ta hado ta kawo mai, k'insha yayi ya ajiye akan yayimai zafi da yawa, zama tayi tanai jiran tea yayi sanyi tanason tafiya saidai bata iya barin sa cikin larura.
Har kafar Tara su Daddy da jaafar na zauna suna jiran salma, shuru babu labarinta, sau kusan hudu Daddy na kiran wayarta babu respond, ransa ne ya bacci, nan yahau tambayan Mom, cemai tayi skull ta shiga karatu saboda exams da zasu fara, jin shaanin karatu yasanya Daddy yayi calming down, dan yasan lokacin exam Salma bata wasa. shikam Jaafar dadi yaji, amma aransa mamaki yake ace yarinya har yanzu bata dawo ba, jinjina kai yayi "anya ta arziki ce kuwa" azuci yayi maganar.
Hira kadan suka tab"a Daddy yace mai yayi hakuri idan ya dawo daga tafiyar sai yadawo kafin nan diyarshi ta gama exams sai ayi magana, Jaafar kam bai damuba, gaba ta kaishi gobarar titi a Jos, san samu ma kar Daddy ya kuma mai zancen. Sallama yayi masu yabar gida.
Mujahid kuwa shiriritar da Salma yahau yi, bayan tea yayi sanyi k'insha yayi wai zaiyi amai, saida ta kuma had'amai Black tea sannan yadan sha kadan da maganin bayan tasha walaha da lallaba shi sannan ya iya shan pill na magani guda daya, acewarsa daci yayi yawa. Bayan nan kuma ta tashi da niyya tafiya ya langwabe da ciwon kai, saida ta tayi zaman kusan 30 minti tanai mai sannu.. Karshe dai saida yaga 11 tayi sannan ya koma normal, tace mai zata tafi dare yayi, ba kunya yace suje ya kaita gida, itakam mamaki ne ya kamata mutum sai kace mai aljanu, tunani tayi anya ba raina mata wayo yake ba. Haka dai tabishi suka shiga mota, sai janta yake da hira, kasa magana tayi tsananin yadda taganshi garau, wayarta ta duba taga miss calls na Daddy, tsaki tayi aranta tace "Allah yasa banyi ranshi surprise dinnan ba"
Nan baki gate ya sauke ta tamai sallama ta shiga gida, Mom ta tarar zaune palo, dan tuni Daddy ya shiga ya kwanta, ganin Salma yasa hankalinta ya kwanta, fada tayi mata sosai akan dawowan dare amatsayin mace bai kamaceta ba, hakuri Salma ta bata, itadai surprise din takeson sani, tambayar Mom tayi taki fada mata komai sai ce mata tayi bayan exams zataji komai daga bakin Daddy.
***
Washegari langwabewa Mujahid yayi bayan yayi shirin sa tsaf na fita office, Salma ya kira yace ta taimaka ta kaishi office dan baya jin dadi, bata kowa mai aranta ba dukda dai zuciyar ta na kisyasta mata wani abu, kuma jiya taji dadin karatu a office dinsa. Gidan taje ta dauke sa suka tafi.
Tun ranar abu kaman wasa, kullum Salma na tare da Mujahid iyakacin taje skull tayi exam tadawo ta koma office dinsa ta zauna karatu, ko shopping zataje saidai ta zauna shi yaje yayi mata, sam bayaso ta fita ba tare dashi ba gudun kar yan'uwansa su ganta, balle jaafar da har yanxu neman ta yake.
Har azuciya Mujahid yasan ya kamu da son Salma saidai yayi alwashin rama abunda tamai dan kuwa bazai barta taci bulus ba, ganin yadda ta dukufa da karatu yasa ya bata lokaci dan gama exams dinta, ita kuwa Salma zuciya daya take zaune dashi, abu daya ke daure mata kai yadda bai furta yana sonta ba alhalin soyayya kuru kuru yake nuna mata, tanason sani mike zuciyarsa game da ita.
Ta b'angaran Junaina bata daina cusa kai gurin mujahid ba, ko tusa akai a gida saita buga ta fadimai, wataran rohoton sumai amfani wataran kuma data fara fadin abunda bai dameshi ba katse wayan yake. Kullum a rokonshin take ya dawo gida.
Yauce ranar da Salma ta gama Exams, tana fitowa Hall tayi kicibis da Faiza zata shiga next hall supervision, Hararan juna sukayi kowa ya wuce, kowane da abunda yake zak'awa game da junan su aranshi, K'wafa Faiza tayi aranta tace "yar banzan yarinya very soon zai jefar dake".
Tuni Salma tabaiwa banza ajiya, kobi takan Faiza bata kuma ba tq fada mota taja zuwa gida, karfe sha biyu ne lokacin, so take tayi wanka ta huta kafin taje gurin Mujahid tamai albishir din gama exams danba sani yayi ba.
Tana isa gida parking tayi ta fito, kokarin kulle motar tayi taji muryan Salim abayanta.
"Yau kuma baki je wajan sa karuwan ci ba ? Fuska babu annuri yayi magana.
Mamakine ya kamata, ta juyo tace "yaya karuwan ci, a ina, yaushe, ?
Mugun kallo yakai mata wanda daga gani asama yake, cikin zafin nama ya riko hannuta da karfin gaske wanda saida tadan tsaki kara, "ni zaki rainawa wayo Salma, gayamin uban mi kikeyi a office dinsa"
Kokarin kwance hannuta tahau yi takasa, bata rai tayi tace "zan kira Daddy idan baka sake niba.."
Mugun dariya yayi yace "tunda shine ke dauramiki gindin kina iskancin da kikaga dama ko, waya sani ma kokin bashi kanki"
Wani mugun girgiza Salma tayi da kalaman sa, cike da tsantsan bacin rai takai mai azababan mari da dayan hannuta, ba shiri ya saki hannuta yanai mata kallon mamaki lokaci guda kuma zuciyar sa ke tafasa, afuce ta nuna shi da yatsa "idan kana iskancin ka yakare akaina karka kuskura kasako min iyaye, banza, dan akuya kawai, kuma kasani i hate you Mujahid nakeso bakai ba wanda baisan ciwon kansa ba"
Dafe Kunci Salim yayi yana huci, tunanin abunda zai mata kawai yake, Harara ta ballamai, wucewa zatayi yasa mata kafa tayi wani mugun faduwa kasa wanwas, adan tsorace ta daga kai ta budeshi, sosai ta tsorata da yanayin, "anya Salim baya da hankali" ta fada aranta.
Nunata yayi da yatsa yace "ni kika mara saboda da wani banza, aikuwa sai kinyi danasani zan nuna maki ni ba wawan da kike tunani bane" juyawa yayi ya tafi, zuciyarsa na tafasa, shi kadai yasan makircin da zai shuka mata gurin Mujahid din da take takaman tanaso da kauna.
Salma kam tsoro ne sosai ya kamata, mikewa tayi kokarin yi ta kasa zabar azabar dataji kafar ta guda nayi, dakyar da azaba ta mike tsaye, kaman tayi ihu dan azaba, awahale ta iya jan dayar kafar ta karasa cikin gida, bata iya shiga gurin mom ba ta wuce dakinta.
Duk akan Idon Salim, yaji dadin yadda yaga ta kasa takawa, koba komai dole ta hakura da zuwa gurin Mujahid, murmurshin Mugunta ya saki afili yace "zaki gane kuran ki .............
Ni xarah nace Toh Fah, Salma duk ke daya, enemies ta ko ina.
Allah ya karemu daga sharin masu shairi.
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty cute)
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION...
Wattpad Cutexarah
Blog xarahbukar.wordpress.com
51
Tsabar rad'adin da k'afar take mata dak'yar ta cillara ta fad'a band'aki tayi wanka ta fito ta kwanta gado, sosai k'afar tayi tsami haka dai ta daure har bacci b'arawo yayi awon gaba da ita.
Mujahid ne zaune office yana danna na'ura mai kwakwalwa dake gabansa, jifa jifa yakan k'yallarawa agogon tsintsiyar hannusa kallo, guntun tsaki yaja ganin k'arfe daya ta gota bata iso ba gashi kuma ya k'agara ya ganta.
Mubarak ne ya shigo office din tare da sallama, amsawa yayi ciki ciki ba tare daya dubesa ba, Dariya Mubarak yayi hade da zama yanai kallon office din tamkar wani sabon bak'on sa, duban Mujahid yayi, cikin zolaya yace "yau matar ka bata zo ba?
Sai sannan Mujahid ya dubeshi, murmushi yayi.
"Zata zo, na tabbata ma tana hanya"
"taku salon soyayyar daban take, wai ma yaushe zaka rama abunda tama ? Mubarak ya fada ba tare daya bar kyalkyalewa da dariya ba.
Nisawa Mujahid yayi, yace" abokina ina cikin yanayin, na rasa mai zan mata kuma ma bazan iya cutar da ita ba, koba komai yar'uwa tace ta jini, na hakura, yanzu so nake na sadata da Hajiya".
Dakatar da dariyan Mubarak yayi, yace "naji dadi ka gano gaskian zuciyanka, Hajiya kuwa sai tafi kowa farin ciki da kai, yaushe zamuje mu kai amaryar mu gidan sirika.." Cike da zolaya Ya karashe maganar, mugun kallo Mujahid yamai yamike ya fice tare kokarin gitmse dariyar data zomai.
Murmushi Mujahid yayi yadau wayarsa dan kiran Hajiya yi mata albishir, dailing nambar zaiyi, Salim ya fadomai cikin office kamar wani mayunwacin zaki.
Ajiye wayar yayi yabishi da kallon waya baka izinin shigo min office, cikin rashin damuwa da kallon dayake mai Salim yaja kujerar dake fuskantar sa ya zauna had'e da dora kafa daya kan daya, sannan cikin karaji yace "Sir ba batun aiki ya kawo ni nan ba."
Ran Mujahid yakai mak'walan baci, shuru yayi yana jiran abunda zaice.
Salim ya cigaba
"Salma tawace, tare ka fara ganin mu, tun kafin ta sanka muke mu'amala, dan Allah karka shiga tsakanin mu, muna matukar son Juna, adalilin ka yau ta zubar da cikana da take dauke dashi"
Mik'ewa Mujahid yayi, fuska daure, afusace yace "tashi ka fita kafin nasa a cilla ka waje"
"Kayi hakuri sir banxo da fad'a ba" mikewa Salim yayi had'e da risinawa sannan ya fice a office din.
Tsaki yaja ya koma ya zauna ranshi na k'una, ko kadan bai yadda da abunda Salim yace ba, yasan kafin su saba da Salma kallon marar kamun kai yake mata yanzu kuwa d'an zaman da yayi da ita ya tabbatar ba abunda yake tunani bane, kuma ma yasan ba yadda zaai Salma ta kaiwan shashashan yaron nan kanta, tsaki ya kuma ja yace "Salma tafi karfin ka, baka isa ka rainamin hankali ba, wawan banza kawai". Wayarsa ya dauka yahau kiran Salma, sau biyar ya kira tana ruri baaa dauka ba, ajiye wayar yayi zuciyar sa na aiyyana mai abubuwa, saurin kawarwa yayi ya cigaba da aikin gabansa.
Bayan la'asar Salma ta farka bacci da matsananci ciwon kai, dakyar ta yunkuro zaune taji kafar tai mata nauyi, wani irin juwa take ji, sauka tayi kan gadon ta rarrafa zuwa bandaki ta dauro alwala ta fito tayi sallah zaune sannan ta koma gado ta kwanta, daukar wayarta tayi taga kiran shi, da sauri tayi dailing no dinsa.
Kaman jira yake, yayi azaman dauka yace "kina Ina ?
Murya ciki ciki, kaman mai shirin kuka tace "ina gida, tuna dazu nadawo saidai bana jin dadi"
Bata rai yayi.
"Mike damun ki ?
Shuru tayi, tanason cemai kafar ta ke ciwo tana tsoron ya tambayeta sanadi, ga kuma kanta na ciwo, wahalalliyar ajiyar zuciya ta sauke sannan tace "kaina ke ciwo".
So yage ya gasgata zancen Salim, yace "deme kuma ?
Zuciya daya bakinta ya furta "cikina"
Baice komai ba kuma bai jira abunda zata kuma cewa ba ya katse wayar, bata kawo komai aranta ba ta ajiye wayar hade da gyara kwanciyar ta.
Kasa gasgata zance Mujahid yayi, yanaso ya yadda da abunda Salim yace ya kasa, kalllon wayarsa yayi dake rike hannusa jiran ko zata kira shi yaji shuru.. Jiki sanyaye ya ajiye wayar aranshi yana fadin "Tabbas Biri yayi kama da mutum....
Masu korafin basu san ma'anar zuma sai da wuta, bara na maku bayani dalla dalla.
Shi sak'ar zuma baa iya daukan shi saboda Zuma🐝🐝 dake makale jikin sakar, komin yadda zaki ki kori Zuma bazata koru ba tsananin yadda take da taurin kai da kafiya maganin ta daya ce wato Wuta...kinasa mata wuta zata saduda ta gudu tabar sak'arta ba tare da bata lokaci ba.
Shiyasa hausawa sukace Zuma Sai da wuta.
Shin acikin
Mujahid
Salma
Salim
Jaafar
Da
Junaina waye Zuman waye wutan ??
Ina jiran Amsar ku....
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)
®NWA
Vote me on Wattpad @Cutexarah
xarahbukar.wordpress.com
52
Da Magrib Mom ta lek'a d'akinta kansacewar taji shigowarta tun rana, ganin bata da niyyah fitowa ya sanya ta bibiyar ta, kwance ta ganta can k'arshe gado akudundune, k'arasa wa gurin tayi tahau tashin ta, bude ido salma tayi, jikinta gabad'aya k'yamar yake tsabar yadda zazzab'i mai zafin gaske ya cafketa, hankali mom ne ya tashi ganin yanayi ta, ba tare da b'ata lokaci ba ta taimaka mata tasa kaya suka fita waje, kiran Salim tayi yaxo yaja su zuwa asibiti, a mota sai faman yi mata sannu yake tamkar ba shine sanadi ba, bata iya amsa shiba har suka isa asibiti aka bata gado.
Koda Mujahid ya koma gida kasa zaune yayi, kalaman Salim ke yawo a kwakwalwan kansa. Kamar wani tab'abb'e yahau girgiza kansa yana fadin it cant be possible, yana son Salma kuma yayi trusting dinta, ba zai tab'a yadda da zance salim ba" wayarsa dake ajiye kan 3 sitter yadau hade da mik'ewa tsaya yayi dailing no din Salma, har kusan sau biyar bata dauka ba, nan take wani mugun haushin ta ya dirar mai, cilla wayar yayi kam kujerar sannan ya zauna kasa hade da dafe kansa. Atakaice dai ranar dakyar ya iya runtsawa, da safe bayan yayi shirin sa na office fita yayi, bai zarce ko ina ba sai gidan su Salma, ya jima yana horn daga bisani mai Gadi ya iske shi ya sanar mai babu kowa agidan sai Salim, hajiya da diyarta kuma suna asibiti, Alhaji dama baya gari.
Komawa Mota Mujahid yayi ran sa bak'in k'irin, zuciyar sa kuwa ta gama gasgatar mai da gaskian lamarin, wani irin haushi kanshi yake ji da tun farko yayi sake har Salma ta shigo mai rayuwa, yana son salma, she's the only gal da yasan he can die for, saidai bazai taba yadda ta raina mai hankali ba much less tayi deceiving dinsa with her cute innocent face, nambarta dake wayar sa yayi deleting hade da kunna motan, kallan gate din gidan yayi yace you're dead to me" afusace yaja motar sa yayi gaba.
"Wai yaushe hakan ta faru bansani ba" acewar Mom, zaune take gefe gadon da Salma ke kwance, kafar mai targade daure da farin gyalle, Yunkurowa Salma tayi ta jingine jikinta a karfan gado, Magana zatayi Salim ya shigo rike da flask da Mom ta aikeshi gida ya dauko, Harara Salma takai mai, yace "sannu sister, ya jikin ?
Atakaice tace "lapia" duban Mom tayi tace "ina tafiya nayi missing steps na fadi"
Mom tace "tsautsayi kenan baya wuce ranar sa, Allah ya tsare gaba, ya ciwon Kan ?
Da sauki" Salma ta amsa, tashi Mom tayi ta fita gurin Doctor, kusa da ita Salim ya karaso hade da marairece fiska yace "sis am sorry, duk nina jaza maki"
Tabe baki tayi
"Ba komai ya wuce, ni yanzu kawai gida nakeson komawa, nabar wayata kan gado" kaman zatayi kuka ta karashe zance, Mujahid ne aranta, tana son fadimai tana asibiti karya jita shuru.
Mom ce tadawo dakin tana waya da Daddy ya mike ya fice, mikewa Salma wayan tayi ta amsa yiwa Daddy magana.
K'ashe gari likita ya sallame su, suna isowa gidan wayarta tadau ka taga miss call dinsa, farin ciki ne ya ziyar ceta ganin yadda ya damu da ita, kiran sa tahauyi fuskar ta dauke da murmushi.
Alokacin Mujahid zaune yake office yana danna laptop dake gabansa, fuskar sa babu annuri, shi kadai yasan yadda yake jin zafi azuciyar sa, yana ganin kiran nambarta yaki dauka, har kusan sau goma takira bai dauka ba, karshen ma wulla nambarta yayi a reject list ya cigaba da aikin gabansa yana huci.
Mamaki ne yakama Salma alamun da wayarta ya nuna mata nambarta is rejected, zama tayi tana tunanin lapia kuwa, bata saduda ba daddare tahau kokarin kirasan still abu daya yake nuna mata, hankalinta ne ya tashi, duk atunaninta ko wani mugun abune ya faru dashi. Kasa runtsawa tayi har garin Allah ya waye, da safe shiryawa tayi ta shiga motarta taja zuwa office dinsa, tana isa daga main entrance gate din wasu polisawa suka hanata shiga, mamaki ne yakamata dan kuwa sun santa duk zuwanta barinta suke, rokon su tahau yi da magiya, fir suka hanata shiga karshe ma ce mata sukai Ogan su yace karsu barta ta shigo.
Jiki sabule ta koma gida, kwata kwata batama san miya faru hakan ke faruwa ba, batai kasa a gwiwwaba saida tayi kwana uku tana zuwa basa barinta ta shiga, hankalinta sosai ya tashi, a kwana na hud'un ne ta kuma komawa, tana cikin rokonsu Mujahid ya iso gurin cikin motarsa zai shiga, ajiyar zuciya ta sauke ta nufesa da sauri, saidai mi, ko kallanta bai yiba yakara baiwa motan wuta ya shige ciki yabarta nan tsaye cikin tsananin tashin hankali marar mitsaltuwa, nan take zuciyar ta ya fadi mata somthing is not right, kai komo tahau yi agurin tana tunanin. Horn taji bayanta da azama ta juwa, tagane shi, Mubarak ne da take gani office din mujahid, karasa gurinsa tayi hade da gaidashi, yace "mai kikeyi anan, ki shiga mana".
Kai ta girgiza, tace "Mujahid ya basu order karsu bari na shiga, dan Allah ka taimaka ni, i need to talk to him".
Tausayi sosai tabashi, saidai yasan Mujahid da kafiya koda ya shigar da Salma bazai yadda ta shigar mai office ba tunda har yasa doka a entrance kar abari tashigo, ko miya hadusu kuma, duk axuci yake zancen.
Yace "why not ki hakura da ganinshi ki tafi gida, i dont tink zai kulaki"
Kaman zatayi kuka ta marairace fuska tace "dan Allah ka tamakeni, yaki kulani for d past 4 dayx, i need to talk to him, inason sanin miyasa yake ignoring dina all of a sudden"
Shuru Mubarak yayi yana naiman mafitan yadda hakan zai yuyu, ajiyar zuciya ya sauke yace "kinga abu daya zan iya maki, ki fadi inda kikeso ku hadu, ni kuma na maki alkwarin kawo maki Mujahid"
Nisawa Salma ayi, taji dadin abunda yace, hakan kadai zaisa ta hadu da Mujahid harya saurareta.
Risinawa tayi tace "nagode sosai"
Dariya yayi
"Baki fadi inda zan kawo miki shi ba"
Murmushi tayi tana tunanin peaceful gurin da yakamata su hadu, can ta tuna da plantation garden na Daddy, gurin nada matikar girma, kyau da shaawa uwa uba akwai flawowi da mayan bishiyoyi gwanin shawaa.
Tace "kasan A & M gardens na hanyar Dikkoh ?
Yace "uhhm nasan gurin, can kike so ku hadu".
Cike da farin ciki tace eh, dariya yayi yace ba matsala gobe by 4.30 zaki ganmu"
Godiya sosai tamai sannan ya wuce, motarta taja ta wuce Garden din.
Tana isa Baba nayaro ta iske, mai kula da shuke shuke gurin, gaidashi tayi aladabce ya amsa cike da fara'a, suna shiri sosai da Salma kasancewar yawanci idan damuwa tayi mata yawa gurin take zuwa shan iska.
Gurin da pink da yellow flowers suka fi yawa nan Salma tacemai ya gyara gurin yayi kyau dan tana da bako, so take idan yazo duk wata bakin cikin sa ya yaye, shikam Baba nayaro dariya sosai tabashi yahau zolayan ta yayi sirki.... Sun dan jima suna magana daga bisani Salma tamai sallama ta koma gida..
Salim ta tadda ya fito daga motar sa, da alamun shigowar sa gidan kenan, "Salma daga ina kike da yamma haka ? Ya fada cikin salon kulawa kaman gaske, deep down kuma so yake yasan ina taje dan kwana biyu baya ganin ta a office din Mujahid.
Ganin yadda yake mata kirki kwana biu yasa ta saki fuska tace "ya salim Ogan ka naban Tough tym, kwata kwata nakasa gane kanshi, yanxu baya kulani"
Murmushi yayi wanda shi kadai yasan maanar sa yace "kin manta The boss is always d boss, fadin Sakon ki saina kaimai".
Tabe baki tayi "no need gobe zamu hadu a Garden din Daddy by 4pm suprised visit zamu ma juna.."
Ware ido yayi in shocked, "yasan Garden dinne ?
Dariya tayi, tayi gaba tana fadin "a'a, gobe zai sani" tafiyar ta tayi..
Tsaye Salim yayi zuciyar shi na kuna, aranshi yace "muje zuwa, mahaukaci yahau kura", naushin iska yayi ya wuce part dinsa.
*****
Washe Gari.
*Kaduna*..
Jaafar ne tsaye bakin motar sa bayan su kammala shari'a da sukai tayi kusan kwanakin da suka shud'e a Supreme court. Bude motar yayi ya ajiye tilan takardu dake hannunsa sannan ya shiga motar, yaja komawa Birnin tarayya (Abuja).
*Abuja*
Tun Safe Salma ta birkice kayanta gabayada tanai neman wanda ya dace tasa, karshe dai white jean da pink top ta ajiye gefe sannan tadau Hoton Mujahid wanda tuni ta wulla a trash can kwanakin baya saidai daga baya tacire ta adana shi, daukon hoton tayi tana kalla hade da lumshe ido, daga bisani ta bude pink cluth bag dinta ta ajiye frame din ciki, wanka tayi ta fito ta sannan ta zauna jiran karfe hudu ta cika.
K'asa Zaune Salim yayi a office, duk mintina kallon agogo yake, yana fitowa sallah azahar, joint dinsu na yan shaye shaye yaje, saida yayi tatul sannan yahau kuka yana tunanin yadda zai raba Salma da Mujahid, rasa mafita yayi daga karshe ya yanke shawaran zuwa Garden din Kidnapping dinta kafin su hadu da Mujahid.
Karfe uku da rabi nayi Motar sa ya shiga yaja yanai wani reckless driving har ya isa Garden din, black Face mask daya siya na musamman yadau ya sanyawa fuskar sa sannan ya shiga Garden din cikin sadaf ya boye cikin wata bishiya.
Katon Scissors ne Hannu Baba Nayaro, sai gyaran wasu flowers yake cikin sauri yana duba lokaci kar Salma ta iso ta iske bai gamaba, aiki yake sosai yaji alamun saukar Numfashi daga ina yake, dakatar da aikin yayi yafara takowa gurin yana fadin "waye anan...?
Tsoro ne ya kama Salim, da sauri ya fito yakama wuyan Baba nayaro, yace "sshh kamin shuru karka kuskara kayi ihu"
Kokarin kwace kansa Baba nayaro yahau yi, yakasa, iya karfinsa ya take kafar Salim, da sauri Salim ya sakarmai wuya, Guduwa Baba nayaro zaiyi Salim yayi saurin rikosa hade da kwashe tsoho da mari, nan take fada ya kicibe tsakanin su, sukahau dambe, duka sosai Salim yama baba nayaro, ganin yana kokarin guduwa yasa ya dauki scissors din zuciya daya ya caka mai atsakiya cikinsa, ihu Baba yayi ya fadi kasa bakinsa na ambato kalmar shahada, tsoro da firgice ne yakama Salim ganin yadda jinin Baba ke bulbula, hankali tashe ya cire mask din fuskarsa yahau yiwa Baba sannu, nunasa Baba yayi da yatsa yace dama kaina....,
Tsorata Salim ya kuma yi da sauri ya ruga da gudu yabar gurin cike da tsananin fargaba.
Fuska dauke da seriousness Mubarak ya iske Mujahid, yace "Mjay tashi muje na nunama wani abu"
Dubasan Mujahid yayi kaman bazai kulasaba ganin yadda yaci serious first tym in his life yasa shi cewa "miya faru ?
Mubarak yace "it urgent, plz tashi muje banaso ka cikani da tambaya"
Kaman bazai tashi ba, daga baya kuma ya mike bayan Mubarak ya fice a office, "this is not good" Mujahid yafada aransa, atunanin sa ko batun wani crime ne Mubarak yakeso suje sugani, drawer na table din ya janyo yadau bindigar sa da Handcuffs yasa a ajihunun sannan ya fita, gurin mota ya iske Mubarak, shiga sukayi Mubarak yaja motar.
Hudu na cika Salma ta kammale shirin ta, jakarta da hoton ke ciki ta dauka sannan ta fita palo, dakin Mom ta nufa da sauri tai mata sallama akan zataje shopping sannan ta fito, bata dau motar taba acewarta kar Mujahid yagani bakin garden din yafasa karaso wa ciki, Fita waje tayi ta Tari Taxi ya kaita Garden din.
Tana shiga Garden din wani irin fresh air taji da farin ciki, fatan ta Allah yasa Mujahid yace yana sonta da sai tafi ko wace farin ciki.
Taku daya biyu zuwa uku tayi tafara ganin d'ison jini, bin jini tayi har inda Baba nayaro ke kwance, cike da tashin hankali ta tsugunna gaban sa takiran sunansa, jini sosai ke zuba saman cikinsa, hannu ta tasa ta tari jinin tana ambatan innalillahi wa inna'ilaihi rajun, jijji gashi tahau yi ko motsi baya yi, tuni hannuta da farin wandonta suka kwashi jini, ihu take tana kiran sunan baba.
Parking Mubarak yayi, kallan sa Mujahid yayi yace "wai miye zan gani anan ne, nifa ban ciki da wasan ka na banza.."
"Fito muje" Mubarak ya fadi, fito wa sukayi suka shiga Garden din, suna tafiya Mujahid yaji ihu, kallon Mubarak yayi yace "whats going on ?
Kafin Mubarak yayi magana sukaji wani ihu, atake maza suka rafta da gudu inda ihu ke tasowa.
"Na shiga Uku" Salma ta fada, tanai kokarin cire Scissors din dake makale jikin cikin Baba, kasawa tayi ta mike hade dasa duka hannunta biyu akan scissors din da niyyan cirewa.
"Mi kikeyi anan ?
Muryan Mujahid taji agabanta, sam bata lura da tahowar su da gudu ba, adan tsorace tayi Baya ganin mugun kallon dayake mata, "ba komaii" ta fada cikin inda inda.
Tsayawa gefe Mubarak yayi, Mujahid ya karasa hade da Taba wuyan Baba, babu alamun rai tattare dashi, kallon Salma yayi, cikin karaji da zare ido yace "Uban mi kika yimai ?
Kaman zatayi kuka tahau fadin "nima haka naganshi.."
Mujahid ya gama kulewa, ko daya bai yadda da abunda tace ba, yace "ni zaki rainawa wayo, munafuka, yar daba, karuwa yar iskaaa..."
Katse shi Mubarak yayi da cewa "mjay stop it mana, baka da hankaline kake tunanin karamar yarinya da kashe tsohon mutum haka..".
Kallon banza yama Mubarak sannan ya dube Salma hade da ciro bindigar da handcuffs, nunata yayi da bundigar, fuskar ba annuri yace "you're under arrest ..."
Katse shi tayi da cewa "yaya dan Allah kayi hakuri, wlh bani bace, believe me.."
Tsawa ya bugu mata dasaida yan hanjin ta suka kada yace "shut up, you have the right to remain silent, anything u say can and will be used against you in a court of law..."
Iya kuluwa Mubarak yakai, ganin Mujahid da gaske yake arresting salma zaiyi yasahi, riko hannusa "Mjay, calm down mana, kar kayi using personal issues dinka da aikin ki, we both know ba ita ta kashe shiba".
"Karya kake, am sure itace tayi kisan kuma abunda yasa ka kawo ni nan kenan danna gani da idona"
Kallon Salam Mubarak yayi yamata sign din ta gudu, tagane da sauri ta juya zata gudu, mujahid yace "don't you dare walk out on mee"
Tsayawa tayi chak, kuka takeson yi dan taji dadi takasa, kwata kwata ba mujahid din data sani ne wanan ba saidai she isn't stupid dazata tsaya yayi arresting dinta abanza.
Tana jin yafara taku daya biyu a bayanta tayi sauri afkawa da gudu, Tsayawa Mujahid yayi yana kwalla kiran sunanta, ganin bata da niyyan tsaya wa yasanya shi pulling trigger, daidai kafardar hannuta Bullet din yabi ya karce ta, ihu tayi sosai, wani mugun jiri yafara daukar ta, bazata iya tsayawa ba ta cigaba da gudu hade da rike gurin wanda tuni jini yafara zuba.
Ko ajikin Mujahid saima kokarin kara kai mata harbe da yake, wani Mugun Mari Mubarak ya tsakar mai, suka haure da Dambe...
Hankali tashe Salma ta fice a garden din, kan titi tayo da gudu tana neman madafa, kasancewar titi high way ce yasanya motoci daidaiku ke wucewa aguje batare da sun lura da ita ba, titin ta kalla da idanuwan da sukayi dishishi, kallon bayanta tayi taji tsoron kar Mujahid ya kamata, da sauri ta ruga tsakiyar titin, kafin takai ga gangarawa kasa wata BmW ta kunno kai, kiris ya rage bai kwashe taba yayi saurin taka burgi, itakam stars tafara gani nan take jira ya kwasheta kasa...
"Subhanallahi" Jaafar ya fada ganin yadda ta zube kasa, ga jini ta ko ina ajikinta, fitowa yayi da sauri ya karasa gurinta, kallonta yayi gabansa ya fadi, "Ummi.."
Ya kira sunanta a akideme, daukarta yayi yana jijjiga, yana kiran sunanta, ahankali ta bude ido ta kalle shi, "Help me..' Ta iya fada, kanta ya fado bisa Kirjinsa alamun babu rai tattare da ita...
Innalilahi wa inna'ilaihi rajun yahau furtawa, Ummi bazaki mutu ba dayardar Ubangiji... Ya kuma fadi, da sauri ya karasa da ita mota yasata abaya sannan ya shiga gaba motan ya zaune hade da cire suit jacket dinsa daya shafi jini ya ajiye gefe sannan yaja motar.....
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)
Wattpad @Cutexarah
Blog xarahbukar.wordpress.com
0 comments:
Post a Comment