Iya k'ulewa Mujahid yakai, nunasa yayi da bindigar cike da fusace yace "enough of your nonsense, hand over the d damm keys"
"Easy mehh.." Mubarak ya fad'a had'e dayin surrender, key din ya ciro ya wulla mai ya ceb'e.
Fuska ba annuri Mujahid yahau shi da mugun kallo yana cewa "dont you dare interfere, am warning you, stay out of this"
Kai Mubarak ya daga mai, tausayin Salma sosai yakama shi da takaici duk dalilin sa komai tsakanin su yakara tabarb'arewa, yana gani Mujahid ya juya da sauri yabar gurin.
Titi ya nufa bai ganta ba sai jinin daya gani kwace gurin, hannu yasa yaji jinin fresh ya tabbatar ba tayi nisa ba aduk inda take, Wayarsa ya fiddo ya kira duk polisawa dake check point din hanyoyin fita da shiga ya shaida masu lailai susa ido dakyau akan masu wucewa akwai wata wanted dangerous crimal data gudu kuma suyi making sure sun cafketa, komai na yanayin Salma da kayan jikinta saida ya kwatanta masu yadda zasu ganeta.
Sun Shiga gari, wani mugun Holdup ya tsayar dasu, hankali Jafar ne ya tashi kansancewar garin yad'an soma duhu, sauri kawai yake danya kai Salma asibiti. Wining glass yayi ya leka can gaba ya hango polisawa da sojoji tsaye suna lek'a motocin dake gaba da nashi, gabansa ne ya Fadi, da sauri yadau Jacket dinsa dake gefe ya rufawa Salam dake kwance seat din baya. Dukda baisan make faruwa ba Addua neman tsira yahau yi.
Yana isa gurin su Wani Sojo yace yayi kasa da glass din motar kasancewar sa tinted baa ganin make ciki.
"Ba matsala let him go, dan'uwan Oga ne" Wani babban dan Sanda dake gurin ya fada yana duban Jaafar, yasan shi sosai, gaisawa sukayi, police dun ya fadimai abunda ke faruwa, Tsuru Jaafar yayi danya gano bakin zaran. Hannu police din ya daga ma jaafar yaja motar ya wuce. Ajiyar zuciya ya sauke na relief, fasa kaman hanyar asibiti yayi ya wuce gidansu da ita. Da azama yayi parking ya fito yadauki Salma sukayi ciki, babu kowa palo, hajiya na dakinta, Junaina kuma tun safe taje gidan Aunty Bilki zama da yaranta... Sama ya haura da ita zuwa dakinsa ya kwantar da ita bisa godan sannan yahau kai koman yadda zai taimake ta shiba likita ba. Dabarar Kiran Aunty Bilki yayi, wayarsa yadauka ya danna lambarta...
Bayan Mujahid ya koma office, rundundar yan sanda kusan motoci hudu ya hada suka nufi gidan su Salma, tamkar wani wild vampire yake acting shi adole saiya cafko Salma aduk inda ta boye. Mom na zaune Palo tana trying no din Salma jin shuru bata dawo Shopping ba har dare yayi, kiran nambar take tana ringing baa dauka. Mai gadi ne ya kwankwaso ta mike ta bude, ya shaida mata yan sanda ke neman Salma. Hankalinta ne ya tashi ta zaburi mayafi a daki ta fito nan taga abu kaman yakin dunia..
Mujahid na zauna motarsa a gefe yana bada order, yana ganin Mom yama wani police signal ya karasa gurin ta hade da nuna mata takardar mai dauke da arrest warrant din Salma, salati Mom tayi bata gama rufe baki ba, yan sanda suka rab'a gefenta suka shiga gidan neman Salma, basu ganta ba suka fito waje, Salim ne ya iso gurin adan birkice daga inda ya biya bayan ya gama aika aika, kayan jikinsa na dazu basune jikin saba.
nan yahau tambayarsu meke faruwa, bayani suka mai, yahau ware idanu cike da kid'ima, ko Kallansa Mujahid bai ba balle ma yayi smelling rat, orders ya bawa yan Sanda suka bar gurin bayan ya dakatar da yan sanda shida suyi guarding gidan.
Mom kam kuka tafara yi ta kira Daddy a waya ta shaida mai abunda ke faruwa, Salima ma kuka yafara daya shiga dakinsa, baiyi tunanin haka abubuwa zasu kansance ba.
Aunty Bilki na asibiti tana duba patients, taga ga call din Jaafar, dauka tayi, yahau roka da magiyan taxo ta taimake shi yana cikin matsala, batagane inda zancen ya dosa ba tace bazata samu daman zuwa ba saboda dare yayi gida takeson komawa tabar Yaran, kuka jafar ya fashe dashi yanai cigaba da rokonta, ba yadda ta iya ta fito ta shiga motarta taja zuwa gidan, tana shiga sukayi Kicibis da Hajiya ta fito Palo, gaisawa sukayi tafadi ma hajiya kiran da Jaafar yayi mata, hankalin tashe duk su biyu suka haura sama.
Yana zauna kusa da Salma yana kuka suka shigo,
Tsayawa sukayi bakin kofar.
"miya faru haka.." Aunty Bilki tafada a tsorace ganin jini ta ko ina kan bedsheet..
Kasa bayani Jaafar yayi yace "plz help her, she is dieing..."
Hajiya tace "wace ce ka kawo har daki jina jina haka.."
Murya sarke yace "Ummii umman ce..".
What" Aunty Bilki ta fada, da gudu ita da Hajiya suka karasa bakin gadon.
Salati Hajiya tahau tana tab'a fuska Salma, "miya sameta, ina ka ganta.." Akid'ime hajiya ta jero tambayar.
Aunty Bilki tace bamuga ta zama ba, dauke ta muje asibiti. Nan jaafar yahau masu bayanin yadda komai ya faru kuma zuwa asibiti bazai yuyu ba.
Kowa hankalinsa atashe, Aunty Biilki kuka, jaafar kuka, da sauri tafiddo papper da pen ta rubuta mai abubuwa da zata bukata sannan ta aike shi pharmacy suyo wa, da sauri ya fice, baa fi 30 minti ba yadawo da komai, Aunty bilki tahau gyara ta da treating dinta yadda ya kamata, saukin abun Bullet din bai shiga hannu ba, allurai tai mata sannan ta hada mata da drip.
Hajiya kam tarasa shin kuka zatayi ko farin ciki, dukda tasan Ummin ce saida ta duba kirjinta dan tabbatar da Birthmark dinta wanda kowa adangin su yana dauke dashi, saidai kowa da inda aka mai shaidar, farin ciki sosai tayi bayanta gani, daukar Salma tayi ta maidata dakinta hade da kwantar da ita bayan tai mata sauyin kaya.
Palo suka dawo sukayi cirko cirko cike da jimamin abubuwa, Sallamar Junaina ce ta katse masu shuru, ganin yanayin su tahau tambayan make faruwa, babu wanda ya iya amsata, Aunty Bilki tadau jakar ta tayi waje, Jaafar kuwa mikewa yayi ya haura Sama, Hajiya tace "dare yayi, nikam na shiga" mikewa tayi ta shige daki jikin sanyaya.
Tabe baki Junaina tayi ta wuce dakin ta, aranta tana tunanin miya samesu, Wayarta ta dauka dan kaiwa Mujahid Rahoto, sau kusan shida tana kiran sa baya picking haka dai ta hakura.
Lokacin Mujahid na zaune tsakiyar Palonsa, kansa dafe da hannayansa, yana ganin call din Junaina yaki dauka, kuka sosai yake yana tunanin ina Salma ta shiga, babu inda basu bincika ba, babu ita balle labarin ta, fatan sa Allah yasa ba mutuwa tayi ba, idan har ta mutu rayuwar sa naciki hadari.
****
Har gari Allah ya waye zuwa rana Salma bata motsa ba, da yamma Auntu Bilki tazo takara mata allura sannan ta tafi. Duk shige da ficen da ake akan idon Junaina, tanason Sanin maike faruwa adakin Hajiya, takawa tayi sadaf ta leka ta hangi Hajiya zaune tana jan carbi, Jaafar zauna gefe gado iya abunda ta hanga takoma palo ta zauna.
Kallon Salam jaafar yake cike da tausayinta, fuskarta fayau kaman ka kirata ta amsa, Hannuta ya riko hade da daurawa bisa fukarsa yanai shakar dumi da kamshin hannuta, idonsa sa cike da kwalla, hannusa yakai kan kyakyawan fuskarta yanai shafawa, aransa yace "i'll protect you, til my last breath" baisan maganar ta fito fili ba, Hajiya na jinsa ta mike ta fice daga dakin..
Junai tagani palo bata iya ce mata komai ta wuce kitchen.
Kaman wasa jaafar yaji ta rike mai Hannu da hannuta dayake rike dashi, kura mata ido yayi yaga babu alamun motsi fuskan ta, da sauri ya mike, wayarsa yahau neman dan kira Aunty Bilki, bai ganta ba, ya tuna ya barta a daki, da sauri ya fito dakin Hajiya ya haura sama.
Mikewa Junaina tayi, da gudu ta shiga dakin kafin ya dawo, wata tagani kwance kan gano, karasawa tayi hade da kare mata kallo, tsaf tagane Salma ce data sace ta, "kutumar Uba, yar iskan nan ce a gidan nan" ta fada da karfin gaske, saurin kama bakin ta tayi hade da ficewa daga dakin, dakinta ta koma tahau lalubar Nambar Mujahid awayanta, sai cewa take "tab, wlh bazai yuyuba"
Dailing no din tayi.
Mujahid na zaune office da wusu yan sanda suna bashi feedback akan nemo Salma basu ganta ba, zaginsu yahau akan basu iya aikin su ba, ganin call din Junai yasashi Jan dogon tsaki, "yarinyar nan saina ji ubanta zata kyalleni" ya fada, dauka call din yayi da niyya zazzaga masifa,
"Yaya kasan wana gani adakin Hajiya, yar daban nan data sace ni kwanaki..."..
Azabure ya mike tsaya, "Uwar mi takeyi adakin Hajiyar, how comes taje Gidan...?
"Yaya nima ban sani ba, kaman dai bata da lapia, naga su hajiya sunyi jugum sai kace wata yar uwarsu.."
Katse call din yayi bai tsaya sauraran surutun taba, kallan yan sanda yayi yace ku hada motoci goma da ambulance daya kuje inda zan baku address ku daukon min ita"
Address din gidan yabasu, ya kuma cewa suje yanxu batare da bata lokaci ba yana biye dasu abaya.
Tsaki Junaina taja, tayi kwanciyar ta aranta sai tsinewa Salma take, Jaafar na daukan Wayarsa Dakin Hajiya ya koma, nan ya iske Salma na jijiga tana aman wani bakin jinin, idanuwan ta rufe, tsorata yayi ya kira Aunty Biliki ya shaida mata..
Akidmi tace "jaafar ka kawo ta asibiti, she need blood, idan ba hakaba zata iya mutuwa saboda tayi loosing alot of blood".
"Aunty yan sanda zasu iya kamamu, bakiga duk asibiti ansa securities neman taba"..
Aunty B tace "kazo da ita, zan san dabarar da zamuyi mu shigar da ita."
Hankali tashe Jaafar ya kashe Wayan, Hajiya ce ta shigo dakin, fadamata yadda sukayi yayi.
Tace "dauketa muje mota bamuga ta zama ba" da sauri ya dauki salma suka fice, haraban gidan suka fita suka ga an wangale gate, motar yan sanda mai siren suka gani suna shigowa tare da ambulance.
Cirko cirko Su hajiya sukayi suna kallon Yan sandan da already sun fito, daya daga cikin su ya nuna yace fito da gadon, ba masu aka bude ambulance aka fito da gado, inda Jafar ke rike da Salma suka nufa da niyyan karban ta, hade rai yayi hade da ja dabaya, Hajiya kuwa tsoro ne yaka mata, tahau rokonsu Allah da Annabi, ko ajikinsu, ganin Jaafar sai bata basu lokaci yasa suka nunasa da bindinga, ko gezau bashi da niyyan sakin Salma.
Gefe Oga gurin yayi ya kira Mujahid ya fadamai abunda ake ciki. Daga can karshe layin Gidan Mujahid ke zaune a motarsa yana jiran fitowar su.
Cikin fada yace "you guys are dumb, i dont care koma uban miye zakuyi agidan nidai kawai i want her out of that house dead or alive"..
"Yes sir" dan sandan yace hade da katse wayan...
Kallon sauran yayi yace, ku kwato ta da karfi da yaji...
"A"a hajiya ta fada akidime, mi yayi zafi haka kukeson karasar da ita da ranta, kaga Mujahid basu ita tunda ga ambulance samun lafiyar ta shi yafi komai yanxu. Dakyar da rokon Hajiya jaafar yabar Salma suka daurata gadon suka ja suka bar gidan.
Hajiya kaman zatayi kuka tace "jaafar ya akai suka san tana gidan nan, ina Mujahid kirashi awaya..."
Ran Jaafar ya baci ba kadan ba, sai yanxu ma ya tuna da Mujahid Police ne, magana zaiyi yaga Junaina ta fito tana kyalkyalewa da dariya.
Afusace ya karasa hade da damko wuyar ta, yace "mai kika cewa Mujahid..
Ware ido tayi atsorace, tace babu"
Yace "kin dauka bansan kina min bincike kina kaimai rahoto ba, ki gayamin abunda kika fadamai kafin nagama dake.."
Hajiya ce tayi saurin shiga tsakanin su, "miye haka jaafar, zaka kashe tane.."
"Hajiya ki tambaye ta kiji, bakin su daya da Mujahid, how comes suka san Ummi na gidan nan..".
Kallon ta Hajiya tayi tana cira amsa daga gareta.
Gunguni Junaina tahau yi tace "nifa bansan meke faruwa ba, kawai na kira ya Mujahid na fadimai yarinyar data sace ce ita"
Hannu Jaafar ya daura akai yace "ya salam, amma kin zalince ta, baki ga condition da take cika.."
"Inna ruwana" junaina tafada, wani mugun Mari Hajiya takai mata had'e da nunata da yatsa tace "son zuciya kikayi ko adalci, idan har wani abu ya samu Ummi ki tabbata gidan ubanki zaki koma.." Fuuu hajiya tayi gaba ta koma ciki.
Ihu Junaina tayi tace "na shiga uku, badai Abbana dabaya kaunata ba, wace ce Ummi ? Ta tambayi Jaafar dake tsaye, banza da ita yayi ya shiga motar sa yaja yabar Gidan.
Direct central Hospital suka wuce da Salma aka bata gado, da sauri Mujahid ya karaso gurin ganin Doctor ya fito daga dakin.
Doctor yace "tana bukatar jini, saidai bamu da type dinta, nan da 30min xaa kawo ledar type dinta"
Ahasale Mujahid yace "Kaga Doc bana son wasting tym, muje adibi nawa asamata"
Doc yace "ba matsala, inda jinin ku yazo daya muje a diba"
Da sauri suka shiga lab akayi yan aune aune jini yaxo daya aka diba sannan aka karawa Salma, bayan Doctor ya fito daga dakin yace da Mujahid suna sa ran farfadowar ta nan da awanni takwas.
Farin ciki sosai Mujahid yayi ya k"usa kai cikin dakin, kusa da ita ya tsaya yana kalon yadda ta rame farat daya, sonta sosai ke ratsa mai zuciyar saurin kawar da sonta yayi a zuciyar sa sannan ya cire handcuffs a aljihun sa ya sak'ala hannuta daya da karfan gadon, fuska ba annuri yakai hannun sa kan fuskar ta yana shafawa yace "bazaki mutu ba, bazaki gudu ba sai kin gane kuran ki......
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)
54
Yafi minti goma tsaye kanta yana taunting dinta da mugayan kalamansa marasa dad'i sannan ya zura mukullin cuffs din a aljihu ya fito daga dakin, fuska daure ya dubi yan sanda uku dake gurin sannan ya gargad'esu da karsu bar kowa shiga dakin idan ba Doctor ba.
Parking Jafar yayi a haraban asibitin bacin ya gano dakyar nan gurin ambulance din ya kawo Salma, duba girman asibitin yahau yi yana tunanin ta inda zai fara bi, juyawa yayi ya hangi Mujahid tafe daga can nesa dashi, da azama ya nufesa, Mujahid na ganinsa yakara shan kara shan mur.
Ajiyar zuciya Jafar ya sauke ya tsaya gabansa cike da tashin hankali yace "thanks Goodness you're here, kasan cewa Ummi ce yarinyar daka aika mutanan ka har gida dauko ta ?"
Cikin rashin nuna damuwa Mujahid yamai kallon banxmza yace "is dat y you're freaking out ?
Kallon rashin fahimta Jafar yamai yace "kana sane kenan ?
Tsaki Mujahid yaja, baice komai ba yayi gaba abunshi, mamaki ne ya kama jafar, ba tantama Mujahid yasan Ummi ce saidai bai san dalilin dayasa yake kokarin hunting dinta down ba, koma miye zaiso sani daga bakin Ummi, duk azuci yake magana Hanyar daya hangi yan sadan tsaye ya tabbatar nan Ummi take.
Karasawa gurin yayi suka ki bari ya shiga, haka ya hakura komawa gida saboda dare yayi.
General clinic inda aka mik'a gawar Baba nayaro nan Mujahid yanufa, police dayabar incharge din dauko gawar ya iske tare da wasu mutane zaune suna Kuka.
Yace "suwaye wannan ?
Police din yace "family din deceased dinne nayi contacting, kai suke jira tun dazu"
Kafin yayi magana daya daga masu kuka yace "dan Allah ka taimaka ka bamu Babanmu, mu mikashi gidan gaskia, bamu damu dasai an dauki mataki ga wanda ya kashe shi ba, wlh mun yafe" kuka sosai saurayin yake, daga gani ba masu hannu da shuni bane.
Tausayin su Mujahid yayi, yace yana zuwa, so yake ya amshi evidence mai karfi dazaiyi preventing Salma zuwa prison. Idan har ya karba ya boye sai randa yaga dama zai fito dashi ya ceceta.
Gurin Doctor ya shiga suka gaisa sannan yace.
"Ka gama autopsy (dissection da akeyi dan gano possible cause of sum1s death)
Doctor yace " komai anyi, zuwa gobe result will be ready.
Kwantar da Murya Mujahid yayi yace "make sure karka nunawa kowa, zan zo dakaina na karba"
Doctor bai kawo komai aranshi ba ya amsa bai da toh, fitowa mujahid yayi ya fadima mutanan cewa zasu iya tafiya da gawan, sukam kuka kawai suke.
Hankali tashe Daddy ya dawo Gidan, nan Mom ta labarta mai abunda ke faru, kuka sosai take babu labarin Salma, ran Daddy sosai yabaci ya kira Salim awaya, kaman wani majinyaci ya fado palon, duk ya fita hayyanci tsabar gulity conscious dake damu shi.
Cikin tsawa Daddy yace
" dan uwarka ina ka kaimin Salma?
Tsuru Salim yayi ji yake kaman asirin shi zai tono, yace "wlh Daddy nima neman ta nake.
"Karya kake, duk wani rashin jin Salma tare kuke yi ka dauka ban sani ba, dan haka gayamin gaskia awana dalilin ake tuhumarta da kisan mutum ?
Shuru Salim yayi baice koma ba, Daddy ya cigaba "asararrar banza tashi ka bani waje, kuma ka binciko min duk inda Salma take".
Jiki ba kwari ya mike ya fice.
Mom tace "wayarta na ringing baa dauka"
Bara na gwada atawa, Daddy ya fada hade da dailling no dinta.
Jafar na Isa gidan yayi parking, fitowa zaiyi yaji ringing din waya, dubawa yayi ya hango Pink Jakar Salma, dauka yayi ya bude yaci karo da frame mai dauke da Hoton Mujahid, kallon hoton yayi cike da mamaki, nanya tabbatar sunsa Juna, "toh make faruwa ? Ya tambayi kansa, wayarsa ya duba yaga miss call Mom hamsin saina Dad guda biyar, ajiye jakar yayi cikin motar sannan ya karasa gidan rike da wayan, dakin Hajiya ya shiga ya iske ta zaune tayi tagumi, fada mata yayi yadda sukayi da Mujahid hade da nuna mata wayan ummi da iyayanta kerlta kira, ranta sosai ya kara baci da kuma tsoro daya kamata da ganin Dad naciga da kiran Salma. Kallon namban jafar yayi kaman yaso yagane nambar, wayarsa ya danna yayi compare din nambar Dad dake kira, gabansa ne ya fadi, ya kalli Hajiya yace nasan Gidan da Ummi take, tace ai zuwa zamuyi bamuga ta zama ba, tashi tayi da sauri ta zuri hijab sukai waje.
Hankali tashe Daddy ya kira no din abokinsa head of police gabadaya, sun jima suna magana daga karshe ya yanke gobe zaiso office suyi magana.
Baa fi mintin uku ba maigadi ya kwankwaso wai sunyi baki, izini yamai dasu shigo, Su Hajiya na shiga Daddy yaga Jafar, Hajiya kam kallon Mom take wanda tasha kuka harta gaji.
Zama sukayi aka gaisa, Daddy yace "jaafar yanxu nake shirin kiran ka awaya"
Ajiya zuciya ya sauke ya mikawa Daddy wayan Salma, karba yayi, ya labarta masu haduwa su da Salma da kuma yanxu asibitin da take. Salati Mom tahau yi hade da fashewa da sabon kuka, Hajiya kam binta kawai tayi da ido, Daddy yace "amma officer in charge of this case sai yaci uwarsa, saiya fadamin yaushe yaga yata ta kashe wani dahar zaiyi babak'eran aresting one n only daughter na"
Katse shi Mom tayi da cewa, "Alhaji tashi zakayi muje mu dibo yarta."..
Jaafar yace "baa bari, saidai gobe.."
Sai sannan Mom ta dubi Hajiya dakyau sun danyi yanayi da Salma, sharewa tayi tace "mungode sosai da temakon yarmu da kukayi, Allah ya saka da alheri"
Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tace "nice da gode maku, Allah kadai yasan dami xai saka maku"
Kallon rashin fahimta Mom tayi mata, hajiya taci gaba "basan ya akayi Salma ta dawo hannunku ba, saidai kun cancanci riketa yadda naga duk kun damu" k'walla hajiya ta share tacigaba "ni yayar mahaifiya salma ce, na jima ina neman ta banganta ba"
Ware ido Mom tayi, shikam Dad baiyi mamaki ba, koda ya hadu da Salma daman neman yan'uwanta taxoyi a garin Abuja, ganinta karama lokacin yasanya ya kawo ta gida yarike ta tamkar yar cikinsa, saidai yaji dadi ganin Jaafar amatsayin d'an Hajiya, hada aura salam da Jafar yazo asauki kenan.
Kuka Mom take sosai tana rokan Hajiya karta rabata da Salma, Hajiyan ma kuka take tace "karki damu Salma takuce halak malak bazan rabaku da ita ba"
Dddy yace "ikon Allah kenan, jaafar Allah yayi bazaku hadu da Salma ba tun shekarun baya dana ma zancen auran diyata, ashe kai dan'uwan ta nema, faduwa yazo daidai da zama".
Sosa keya jaafar yayi hade dayin murnushi..
Hajiya kam jikinta ne yayi sanyi jin Daddy zai ruguza mata plans, saidai ba yadda ta iya tunda shiya rike Salma, bata isa tace Mujahid ta kamawa Salma ba, balle yadda taga Daddy yadau zafi da officer dake kokarin aika salma gidan yari....
Sun dan jima suna magana, daga bisani su Hajiya suka bar gidan bayan sunyi zasu hadu gobe a asibiti.
****
Washe gari bayan Mujahid yayi Sallar asubah asibitin ya nufa gurin Salma danso yake ta farka agaban idonsa.
Salma kam Baccinta take, wata nurse ta shigo dakin tacire roban jini sannan ta sa mata na ruwa, fita nurse din tayi, baiyi awa daya ba Salma ta fara motsi, ahankali ta bude, ganinta cikin farin daki yasata mikewa azabure, wani kara tasaki jin ta karce hannuta, duban gurin tayi taga haunta da karfen gadon makale da handcuff, kokarin cixgewa tayi ta kasa, "na shigu uku" ta fada bayan ta tuna abunda ya faru"
kuka ta soma yi, jin motsin xaa shigo yasata tsayar da kukan hade da kafawa kofar ido.
Mujahid ne ya shigo, jikinsa sanye da dagon jallabiya, tana ganinshi ta hade hade rai, tuna neman kasheta da yasoyi tayi.
Murmushi yayi mai dauke da ma'ana iri iri sanna ya karasa daf da ita ya tsaya, murya ciki ciki yace "ya jikin ki ?
Banxa tayi dashi
Yace "hope you're ready to spend 30 years a gidan yari"
Dogon Tsaki taja, tace"am ready, then after 30 years kuma i'll come back to destroy you for good".
Dariyan rainin hankali yayi yace "kina da guts dayawa" gashin kanta ya damko, saida tayi kara, daure fuska yayi yace "dan uwarki ni kike yiwa tsaki.."
Dukda ciwon da jikinta yake mai hanata kokarin cizge hannusa daka kanta ba, kaman mai shirin yi kuka tace "idan banyi tsaki ba mai kakeso nayi, apologise or beg your pardon kake so nayi, toh kasani, that will never happen, badai so kake ka kaini prison ba, bismillah, kuma point of correction uwarka badai uwata ba..."
Iya k'ulewa Mujahid ya kai, wuyanta ya damko da karfin gaske, yace " uwata kike zagi.."
Tace "uwa batafi uwa ba, idan kana nonsense dinka dont ever include my Mom."
Sakinta yayi yana Huci, juyawa yayi zai fita tace "am hungry, get me sumtin to eat".
Bai iya tanka taba ya fice zuciyarsa na zafi, baiso reaction din Salma haka ba, yaso ace kuka zatayi ta rokoshi amma dan karfin hali irin nata ba ita tayi kisan ba but she is willing to serve 30 year a prison... Tsaki yaja yana tunanin yadda zaisa a azabtar da ita a prison. Motar sa ya shiga ya koma gida dan shiryawa zuwa office.
Sai da gari yayi haske Mom da Daddy suka shirya fita asibiti gurin Salma, har sun shiga mota yan'uwan Baba nayaro suka kira Daddy suka fadimai rasuwar, hankalinsa sosai ya tashi fasa zuwa asibitin yayi ya nufi Gidan taaziya, Mom kam asibiti ta wuto nan ta iske Hajiya da Jafar na jiranta a haraban gurin, shiga sukayi wards din, sukayi saan police daya ke gurin wanda ya iso da safe baisan da order din Mujahid ba yabar Jaafar ya shiga, Mom da Hajiya sun tsaya suna magana awaje.
Bacci Salma take ya karasa ya zauna kusa da ita, kallonta yake cike da so da kauna, shafan pretty face dinta yayi har zuwa kan lips dinta yana admiring dinta, dan motsawa tayi yayi sauri cire hannusa, bude ido tayi ahankalin ta dubesa, atunaninta Mujahid ne, tace "ina abinci ? Can kasan makoshinta tayi maganar.
Murmushi yayi yace "yanxu xaa kawo, how are you feeling ?
Sai sannan tagane ba Mujahid bane, yunkurowa zaune tayi kokarin yi, yayi sauri temaka mata.
Kallan shi tayi ayayinda shima kallon ta yake, murya kasa kasa tace "thank you"
"For what" ya fada hade da rike hannuta mai sakale da handcuff, haushi ne sosai yakama shi yasan aikin Mujahid ne.
Murmushi tayi, jikin sanyi voice tace "kaman nasanka wani wuri kafin ranar da kayi saving dina?
Dariya yayi wanda ya kara fiddo kyau shi,
aranta tace "so cute dashi, ba kaman banzan nan ba kullum fuska daure"
Magana zaiyi Mom ta shigo dakin, Hajiya abayanta, da sauri Mom ta karasa gurin Jafar ya mike tsaye ya matsa gefe, kuka Salma ta fashe dashi ganin Mom, nan take ta susuce tahau rarrashi, dakyar Salma tayi shuru tace "Mom yunwa nakeji, kuma acire min wannan abun" turo baki tayi tanai mata nuni da cuffs din hannuta.
"Mun shige su" Mom ta fada cike da mamaki, kallon Hajiya tayi tace "amma babu azzalimi kaman Officer nan, ji mugunta dan Allah.."
Sai sannan Salma ta lura da Hajiya dake kallon su jiki sanyaye, shuru Hajiya tayi sanin cewa d'anta ne azzalimun da Mom ta ambata.
Maida dubanta Salma tayi ga Mom, murya kasa kasa tace "Mom matar nan kaman Hajiyar Ummata"
"Itace, tare da d'anta daya taimake ki" nuna jaafar Mom tayi,
Farin ciki ne ya mamaye Salma, duk sai taji Jafar ya kara kwanta mata, ashe dai jinin tane shiyasa ya ceceta.
"Hajiya.." Salma ta fada tana kallon Hajiya, murmushi hajiya tayi ta mike ta karasa gareta tana fadin "aina dauka bazaki gane niba" rugume juna sukayi, Salma na kukan farin ciki.
Daddy na zuwa gidan Baba nayaro taaziya yayi masu, bai samu janaizar saba, abun tausayi dayaji sanadin Mutuwarsa, tashin hankali biyu ne suka hade mai, jiki babu kwari ya wuce NPF (HQ) gurin head of police, sir Ahmad.
Kara tattauna abunda ke faruwa sukayi, Sir Ahmad yace tabbas yasan da case din saidai baisan diyar shice major suspect ba, atake ya tura department dinsu Mujahid kiran sa, baa same shiba ya aika a kira mai Mubarak sanin cewa su biyu ne witness aranar da abun yafaru.
Mubarak na zuwa, Sir Ahmad yahau shi da tambayo yi, bai boye komai ba ya zayyane masu labarin salma da mujahid tun farkon haduwar su har zuwa ranar da abunda ya faru, ya kuma jajjada wa sir Ahmad lailai Mujahid baya cikin hankalin sa, So da kiyyaya sun rufe mai ido.
Zufa Daddy yahau yi, gano cewa duk case dun revovle around Baba nayaro, "amma yaron nan ya cika dan iska, yan'uwan marigayi basu pressing charges ba saikai dan kawai wata manufarka daban zaka tsangwama d'iyata" azuci Daddy yayi maganan.
Sir Ahmad yace "zaancen banza kenan, wato personal feeling dinsa yake hadawa da aikinsa dan cimma burinsa, dan bashi da kunya kuma harda aika gawa asibiti ayi autopsy alhalin yasa ko kyankyaso yarinya bata iya kashewa"
"Kaga Mubarak, nemi wani ya amso mana autopsy din mugani"
Ba musu Mubarak ya mike ya fice, police din daya kai gawar asibiti ya tura ya amso, Doctor kam zuciya daya yabada atunaninsa Mujahid ne ya aiko.
Mujahid na Tuki ya dunga ganin call daga office, asibiti zaije amsan autopsy ya fasa ya wuce Office, yana isa aka sanar mai Sir Ahmad na kiran shi, hankali kwance ya shiga office din, wani mugun Harara Daddy yakai mai, shan jinin jikinsa yayi ya dake ya karasa gurin Sir Ahmad.
Sir Ahmad yace "yanxu M. Abdulsalam ka kyauta da abunda kayi, kaida kake daya daga cikin wanda suka san aikinsu, miyasa kakeso yin injustice ?
Kallon bangane ba Mujahid yamai, police ne ya shigo da autopsy result ya mikawa Sir Ahmad, Mujahid kaman yayi ihu.
Budewa Sir Ahmad yayi ya karanta sanna ya dubesa yace "the deceased was beating with severe blows before stab to death, yanxu gayamin ita buduwarta ka da kakejin haushi itace tamai dukan kafin ta kashe shi ko kuwa she is stupid dazata kashe shi kuma ta tsaya yimai kuka ba tare data gudu ba"
Shuru Mujahid yayi yana kallom Mubarak da wutsiyan ido, sarai yasan shiya tona komai..
Sir Ahmad yace "ka godewa Allah Mahaifin yarinya baiyi pressing charges akan attempting kashe diyar sa dakayi ba, daga yanxu nayi closing case dinnan, kai kuna you're suspended till further notice".
Mugun Kallon Mujahid yakaiwa Sir Ahmad, afusace ya ciro bage, Id da bingidar ya zubarsu kan table dinsa, hade da ficewa afusace yanai huci, mikewa Mubarak yayi yabi bayansa..
Daddy yace "hukuncin yayi tsauri da yawa.
Sir Ahmad yace "Barni dashi, so nake yagano bambancin sentimental feelings dinsa da aikinsa".
Mubarak na kwalla mai kira ko kallan sa baiyi ba,
Ya shige motarsa yaja afusace, gurin abinci ya nufa ya siya take away sannan yaja zuwa asibiti gurin Salma..
Tundaga nesa ya hangi babu police gurin, haushi ne yakamasa, yana shiga dakin mutanan daya gani yasa shi daskarewa gurin, Hajiya da Mom zaune gefe suna hira, Jafar zaune kusa da Salma yana bata tea abakin tana zuba mai shagwaban ta koshi, sai wani lallabata yake.
"Kai kuma fah, daga ina ? Mom tafada fuska ba annuri ganinsa sanyen da kayan yan sanda.
Afusace Hajiya ta mike ta kwashe shi da marin da saidai Salma ta saki ihu tsabar razana.
Bai damu da marin ba banda jafar dayake watsawa mugun kallo.
"Dan ubanka bani mukullin Handcuffs din.." Hajiya ta fada cikin karaji.
Karamin mukullin ya mikata ta amsa ta jefawa jafar ya cabe yayi sauri bude handcuffs din, mikewa yayi yabawa hajiya, "ungo tsiyar ka, kuma ka fice anan" hajiya ta fadi hade dajan haunnsa ta dunkule mai Handcuffs din ciki, Mujahid baice komai ba yayi kokarin ajiye abincin, tsawa Hajiya tamai tace ya wuce da abinci baa bukata, zuciyarsa na tafasa ya juya ya fice.
Mom tace "dan banxan yaro, waishi police, kinyi maganin shege"
Mugun Kallo Salma takai mata ba tare data lura ba, aranta adduaa take Allah yasa Mujahid ba d'an Hajiya bane, idan kuwa hakan ya tabbata she won't forgive him da boyemata shi dan uwan tane da yayi.
Mujahid na Fitowa ya Hadu da Daddy zai wuce ciki, kawar dakai yayi gefe ya wuce ranshi na kuna.
Dariya Daddy yayi yace "kaji da rashin aikin ka, Salma kuwa tama nisa".
Wayyo su oooo anyi 2 zero 😂
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)
55
Daddy na shiga d'akin yayi farin cikin ganin Salma ta warware, nan ya basu albishiri din yadda komai ta kasance. Mom kam tafi farin cikin rashin aikin mujahid sai d'ura mai zagin Allah tsine take. Hajiya kuwa murmushin dole kawai take, tana mamakin karfin hali irin na Mom, kodayake Salma diyar tace duk abunda tace daidai ne. Salma kam tagama gano komai da Reaction din Hajiya sai fama yiwa Mom ido take akan tayi shuru bata sanma tana yiba. Aunty Bilki ma tazo dubata, sun dade asibiti kafin daga bisa suka koma gida.
Kwana su Salma biyu a asibiti Likita ya sallame su. Gidan Mom suka wuce wanda ba hakan Hajiya taso ba. Bayan kwana biyu kuwa Daddy dakan sa yacema Salma ta shirya Jafar ya kaita gurin Hajiya tayi mata kwana biu, dadi sosai taji dama ta jima dason tambayarsa zataje sai Allah yasa ya furta mata hakan.
Ranar da zasu Jafar na waje parking lot yana jiranta, ita kuma tana tare da Mom a palo suna Sallama, mik'e mata wayarta Mom tayi tace
"Saura idan kinje ki manta dani"
"Haba Mom taya zamanta dake, kece fah uwa ta" ashagwabe tayi magana.
Kunnan ta Mom tajA, cikin zolaya tace "banda rashin ji, kinga Allah ya kawo maki mijin mai kirki karna kuskura naji kinma Jafar rashin Mutuncin, nasan halin ki"
Dan k'ara Salma tayi hade da cizge ruk'on da Mom tayi mata, dariya tayi sannan tace "kai Mom ina laifin wanda ya taimake ka cikin tsaka mai wuya"
Dariya sukayi atare sannan sukayi sallama, har bakin Motar Mom tarakata tanai kara mata fada, motar zata shiga ta hangi Salim bakin window dakinsa yana kallonta, dauke kai tayi tana mamaki yadda yake acting crazy kwana biyun nan. Saida Mom taga sunja sannan ta koma ciki.
Shuru sukayi kowa da abunda yake sak'awa aransa, satan kallon ta Jaafar yayi yaga tana juya wayar dake hannunta, da alamun kuma tunanin take ganin bata cikin hayyacin ta. Cikin cool voice yace "tunanin mi kenan, ko har yanzu jikin ne ?
Sai sannan ta dawo daga duniyar tunanin inda jakar ta da hoton Mujahid suke, tasan dai tare suke da wayarta cikin jakar amma Wayar kadai Mom ta bata ba jakar.
Murmushin ta saki hade da dubansa, tace "everytime i close my eye kai nake gani, kana da kirki sosai"
"Uhmm are you sure, ba wani can daban kike gani ba.." Cikin zolaya ya karashe zancen.
Dariya tayi bata ce komai ba, banda murmusawa da take.
Gabadaya duniyar tama Mujahid zafi, ba aikin fari balle na baki duk zaman kadai ce ya ishe ba, tun ranar dama bai kuma bi takan Salma ba, mugun haushi da tsanarta yake ji duk asanadin ta ya rasa komai, one thing dayafi damunsa shine yadda ya kasa yakaceta aransa, wani mugun Tsaki yaja hade da kaiwa hannusa daya haushi, gidan dayake zaune ma bakin kirin yake ganin sa tsbar takaici, mikewa tsaye yayi daga kan kujerar palon da yake zaune, kai komo yahau yi yanai nemawa kansa mafita, karshe dai ya yankewa kansa komawa Gida tunda dama ba koransa akayi ba shiya kori kasan, duban agogo yayi yaga biyar na yamma ta gota fasa tafiya yayi ya bari zuwa gobe.
Suna isowa Gidan, Salma ta jinjina kyan da girman gidan, fitowa tayi daga motan tanai karewa ko ina kallon, kallon Jafar tayi, tsaye yake bakin boot yana ciro trolleys dinta.
Tace "wow yaya this house is beautiful.."
Magana zaiyi sukaga an bude gate motar kirar avensis ta shigo, dauke kai Jafar yayi, salma kam kallon motar take har tayi parking idan suke tsaye, Junaina ce ta fito amotan hade dakaiwa Salma wani mugun kallo aranta tana fadin "i cnt believe this devil is my sister" wani mugun tsanan Salam takaraji tun ranar da Hajiya ta fadi mata ita kanwar tace, dan haushi ma ko asibiti kasa zuwa dubo ta tayi.
"Ya jafs ina wuni" tafada batare data kalle saba, tayi wucewarta
Bai amsa ba, sai kallon Salma dayayi yaga duk jikinta yayi sanyi, murya maraice tace "i dont think she will forgive me..
Yace "she is very angry but trust me she will hose down"
"I pray so" Salma ta fada hade da sauke ajiyar heart, ciki suka karasa, Hajiya na zaune palo tana kallon aljazeera, ladabce Salma ta gaidata, farin ciki mara misaltuwa ne lullube Hajiya, kasa zaune tayi ta mike tahau nannan da Salma, babban dakin mai kyau anan kasa Hajiya ta nuna mata amatsayin nata, Salma kam kin zama tayi ta nace lailai ita a dakin Hajiya zata sauka, hajiya kam taji dadi hakan, ranar kam Salma taga gata gurin Hajiya da Jaafar, sai wani narke masu take suna biyeta, Junaina kam sai binta da harara da tsaki take, zama tayi dakin tahau trying namban Mujahid dan kai masa rahota, taji wayarsa kashe.
****
Washe gari Mujahid yayi shirin sa tsaf cikin kananun kaya dayayi matukar fiddo azahirin kansa, kulle gidan yayi ya fada motarsa yaja yabar Gidan.
Bayan sun kare breakfast, wajen gidan Salma da Jaafar suka fito yanai nuna mata ko ina da garden dun gidan. Kaman masoyan juna gwanin shaawa suke tafe suna darawa abunsu ba tare da matsala tattare dasu ba, zayawo sukayi suka tsaya bakin motar sa, da alamun fita zaiyi.
Marairace murya tayi tace "yaya yaushe zaka dawo ?
Folding hands dinsa yayi a kirji hade dakai mata wani killer smile, yace "tun baje gate ba harkin fara missing dina"
Dariya tayi, sai kuma ta tsayar da dariyan tace
"Yaya you're very special,
Shuru sukayi suna duban juna for some seconds sannan tace "plz karka dade.."
Agogon hanusa ya kalla yace "i promise..
Okay bye" ta fada..
Kashe mata ido yayi, sukai smiling atare sannan ya shiga motar yaja.
Palo ta komo hade da sauke dogon ajiyar zuciya, sai sannan ta tsaya karewa ko ina na palon kallo kasancewar babu kowa..
Palon ya hadu, idanuwan ta suka sauka kan Katunan frames mai step guda biyar manne jikin bangon palan, wata farar kyakyawan Tsoyuwar mai glass ce a babban frame din, "ko wace ce wannan" ta fada.
Mai bi masa ta kalla Hajiya da late Abban su Jaafar wanda sanye yake da kayan Sojoji, sai saura kuma hoton jaafar, junaina da Mujahid, sun mata kyau sosai, kallon na Mujahid tayi ta buga uban tsaki aranta tace "to hell with you".
Afusace ta juya zata bar gurin tagan shi Tsaye bakin kofar shigowa, kusan minti daya yayi tsaye ganin ta tsaye gaban Hotonsa, baisan wace ce ba, yadai tsaya jiran ta juyo.
Harga Allah ta tsorata da ganinsa, ihu yarage batayi ba ta maze ta tsayaa mayar mai da mugun kallon dayake wurgo mata.
Magana zai yi Hajiya ta fito daga daki tanai kiran Ummi, "naam Hajiya" Salma ta amsa aladabce, ganin Mujahid yasata daure fuska tace "kai kuma daga ina ?
Sosa keya yayi ya gaidata, tabe baki tayi
Da sauri Salma ta risina tace "yaya ina wuni, sannu da zuwa" fuskar ta daure da fara'a..
Kallon mamaki yabita dashi..
Hajiya tace "bada kai take ba, mugun banxa, Allah yasa dai zuciyarta a tsarkake take shiyasa bata nufeka da shairi ba upon all abun dakai mata, idan baka sani ba toh yar'uwarka ce"
Ware ido yayi in shock.
Hajiya tacigaba "iskancin banxa au dama baka sani ba ?
"Bansanta ba, yama sunanta ? In serious tone yayi maganar
Kallon Banxa Hajiya tamai sannan ta kalli Salma tace "kiyi hakuri da abunda ya maki, Mujahid sunan sa, daga shi sai jaafar a haife.."
Shuru Salma tayi, ta mugun kuluwa da denying dinta da yayi, sai yanxu ta kara tabbata wa dagangan yaki nuna cewa yasanta tun farkon haduwan su..
Dakyar tace "ba komai hajiya ya wuce" wuce wa tayi daki, hajiya tabita abaya..
Tsaye Mujahid yayi gun hade da daura hannu akai, "yaushe tazo gidan nan ? Ya tambayi kansa..
Tifowa Salma tayi rike da Plate a hannu, ko kallan shi batayi ba ta wuce ta gabansa, fizgo hannuta yayi da karfi, ihu tasoyi yayi sauri rufe mata baki da hannusa yaja ta suka shiga kitchen, can karshe bango ya turata hade da matse ta da jikinsa har suna juwo numfashin Juna, tsuro tayi da ido, fuska ba annuri yace "What are you doing here, evil tramp from hell..
Alamun tamai da bakinta is close, cire hannu yayi daga bakinta, harara takai mai tace "the evil tramp is you, you kept me away from knowing my family and the worst part of the story you try putting me behind bars, why, do you hate me that much ?"
Cikin rashin damuwa da abunda tace yace "datx your story not mine, i need to know uban miya kawo ki gidan nan ? Cikin zare ido yayi maganar.
Dariyar takaici tayi tace "the only reason y am here, its because of your brother, he is such an Angel, so sweet, i cnt wait to be in his arms..".
Murde hannuta yayi, yanai mata mugun kallo da idanuwa sa da suka sauya launi zuwa ja, ko ajikinta saima kokarin gyara gashin kanta daya bazu gefe, hannu ya nunata dashi, "badai karuwan ci ya kawoki cikin gidan nanba, we shall cee about that.."
Tsaki taja ta kalli hannuta dayake rike dashi tace "M.u ka saki hannu karuwa mana, ko ka fara shiga tarko ne.." Cikin salon rainin wayo tayi maganar.
Haushi biyu ne ya kamashi, "wai M.u, amma yarinyar nan ta raina ni, kodan Yaya bamu" aransa yayi magana.
Rai bace yayi wurgi da Hannuta sannan ya juwa zai fita sukayi kicibis da Junaina zata shigo, "yaya yaushe ka dawo" ta fada da murnan ta, ko kallanta baiyi ba yayi gaba abunsa.
Tabe baki tayi, ganin Salma Mak'ale gurin kaman mai shirin kuka, karasawa gurinta tayi tanai kai mata kallon banxa sann tace "bawai kinzo gidan nan ba, better stay away from my boyfriend, Mujahid nawane nikadai, kodayake y am i wasting tym talking to you, very soon zaiyi kicking dinki out of this house cox he hate you so much Big sister" tsaki taja ta juya ta bude fridge tadau drink sannan ta fita tabar Salma daskare tanai kallon ta.
"Oh ma God, little sis you're too good ki falling wa M. U, na shiga uku" ta fada hade da zamewa kasa ta zauna.
Kanta ta daura kan kafafunta tahau yin kuka dani bansan dalili ba.
0 comments:
Post a Comment