Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima.
Casuke ALLAH dai ya infanta mana, ranki ya dad'e ALLAH ya saukeki lafiya.
Cikin tsantsar farinciki yake amsa musu, murmushi yak'i barin fuskarsa.
Nikam zuciyata Ce ta shiga tsitstsinkewa, idan har Na fahimci inda zancensu ya nufa cikine dani kokuma wani keda cikin? Galadima Na kalla, amma saiyamin wani miskilin murmushi yana kauda idonsa, alk'yabbar jikinace kawai taima mutane katanga da ganin zufar data gama jik'emin jiki.
Tun a falon farko Na dakatar da kuyangin da damuke tare, handbag d'ita Na kar6a nace suje nagode. cikeda girmamawa suka amsamin suka fita suna min addu'ar k'ara samun lafiya. suna fita na juyo ga Galadima, amma tuni ya shige d'akinsa. handbag d'in Na dungurar saman kujera nabi bayansa, hankalina bazai ta6a kwanciya ba sainaji gaskiyar lamarinnan.
Na iske babu kowa a falonsa, Dan haka nashiga bedroom d'insa, ranar farko kenan dazan fara shiga bedroom d'in. babu kowa nanma, sai motsin ruwa dana jiyo a bathroom.
Waige-waige nafarayi ina k'arema d'akin kallo, komai ya birgeni a d'akin, sai k'amshin mayen turarensa da ya mannema d'akin. karaf idona ya sauka ga takarda kusada kayan daya cire, mik'ewa nayi Na d'akkota, Na dawo Na zauna. cikin nutsuwata nafara karantawa, nai mugun waro idanu ina fad'in “wlhy impossible, abindama bazai ta6a yuwuwaba kenan” sai kuma Na fashe da kuka.
Dai-dai lokacin Galadima ya fito daga bathroom, sanye yake da rigar wanka fara, ahankali ya ringa takowa idonsa a kaina, sai dai fuskarsa a d'aure take tamkar bashine cikin walwala ba a asibiti.
Bai k'araso inda nakeba ya tsaya a tsakkiyar d'akin ya cigaba da goge ruwan kansa zuwa fuska hankalinsa kwance. a harzuk'e nayo Kansa ina cigaba da kukana, naja birki a gabansa, da d'anyatsa Na nuna masa takardar, har yanzu kuma kukan nakeyi, nace “wannan cikin a jikin wa ake nufin yake?”.
d'auke fuskarsa yayi daga kallona yana wani lumshe idanu, batare daya bani amsa ba ya taka zuwa wajen mirror, cikeda izza yace “sunanwa kika gani a jikin takardar?”.
Da sauri Na ruk'o bathtub d'in jikinsa, cak ya tsaya, murmushin gefen baki yayi, saikuma ya kuma d'aure fuska sannan ya juyo yana fuskanta ta, inda Na rik'e ya kalla yana fad'in “kona kwance miki igiyar ne?”.
Sakin rigar nai da sauri ina share kwalla, cike da tsiwa nace “aini ba 'Yar iska bace ba”.
Shikuma cikin gatse yace, “amma kikayi ciki?”.
Hannu na aza akaina nakuma fashewa da kuka, “wlhy koma mi za'ayi sai dai ayi bazan haifi wannan cikinba, aiba haka mukayi da kaiba, kawai daga auren Contract sai aganni da ciki? ka tabbatar saina zubar dashi yau d'innan, dan bazanje gidan miji da agola ba, ba kuma zan haifi d'ana Na bari gidan wani ba matar uba ta kashemin”.
Da k'yar ya iya danne dariyar dake k'ok'arin kufce masa, yay saurin cafko hannuna saboda zaburar danayi xan fita.
“k yi ahankali karkimin asarar abin cikin kwan fa”.
Wani bak'in cikine ya turnuk'omin, Na harzuk'o masa da masifa amma saiya wani tsare gida, dolena Na had'iye maganar nacigaba da kukana.
Shikuma ya watsa mini harara yana jan tagwayen tsaki, sannan yaja da baya yakoma bakin gadonsa ya zauna.
Durk'ushewa nayi saman carpet d'in gaban gadon Na fashe da kuka mai tsuma rai ina rok'onsa. “dan girman ALLAH ka kaini a zubda cikinnan, kafa tuna da Girman alk'awari, a auren yarjejeniyarmu babu wannan, aikin had'in guywa ka nemeni muyi, kaifa ka tabbatarmin da zaka kasance mai cika alk'awari aranda Na kwana biyu a masarautarnan, miyasa yanzu zaka kasa cikawa? kacemin a matsayin kuskure abinda yafaru ranar ya faru, dukda zuciyata Na cike da bak'in cikin faruwar tasa haka Na hak'ura Na danne Na yarda dakai, ka taimakeni mu rabu cikin salama batareda d'ayanmu ya cutuba, karka k'ask'antar da rayuwata saboda kana ganina mace kuma talaka wadda take k'ark'ashin mulkinka, kamin adalci Dan girman ALLAH Muhammad Sameer”.
Tunda munaya tafara magana Galadima ya tsaya daga k'ok'arin fara shafa man da yakeyi, idanunsa ya tsura mata, dukkan maganarta ta shigesa, dukda yana k'aunar cikin dake jikinta shima baiso gudan jininsa yazo ta wannan hanyar da babu soyayya tsakaninsa da mahaifiyar d'ansa ba, sai dai wayonsa ko dabararsa bazai ta6a canja k'addararsu ba shi da ita. da k'arfi ya cije lips nashi tamkar zai hudasu da hak'ori.
Ya mik'e tsaye yana mai fidda huci mai zafi, takawa yay zuwa jikin window n d'akin, ya zuge labilan yana kallon waje, bayi keta kaikawonsu hankali kwance, dukda kasancewar rana ta take. ya maida labilan ya rufe Yakoma takowa tsakkiyar d'akin yana fad'in “tabbas ni Muhammad Sameer mai cika alk'awarine, kuma dukkan alk'awarin Dana d'auka miki ina k'ok'arin cikasu, sai dai nayi kuskure d'aya a cikin AUREN YARJEJENIYA, Na manta da babbar rahamar da ubangiji yake shinfid'awa ga dukkan wasu ma'aurata dazasu iya killace Kansu a matsugunni d'aya, Na manta da ko babu aure tsakanin mace da namiji inhar zasu kasance waje d'aya shaid'an yakan iya zama Na ukunsu ya sakasu aikata sa6o, balle mu da Muke ganin akwai igiyar aure a tsakaninmu, gaskiya kika fad'a, munyi yarjejeniyar aure domin gano mak'iyanmu bata zama Abu d'aya ba, amma kuma sai bamu d'auki matakan dazamu nisanta kawunanmu ba, daga ni har ke bamu Isa hana ubangiji ikonsa ba akanmu, tabbas ALLAH shidane bada gangan Na kusancekiba a wancan lokacin, sannan bansan ciki ya shiga jikinki ba, to mizaisa kizo ki titsiyeni kina min bore akan zubda shi. Bara kiji Na tabbatar miki yarinya, koda ace ta hanyar aikata zina Na Samar da wannan cikin inason abuna, kuma baza a zubarmin ba, ballantana sadaki Na biya d'unbin mutane suka shaida ke matata ce, mu uku kad'ai mukasan da wani Auren Contract. Dan haka kima nutsu idan zaki nutsu, kamar yanda kikace Duk abinda za'ayi saikin zubar da ciki ko? to Nima duk abinda zai faru saidai ya faru, babu ubanda ya Isa yasaka a zubar da cikinnan, sai dai idan Wanda yabani ne ya kar6a banida ikon hana wannan, idan kin gadama kici gaba da duk abinda kikeso har k'udirin zubda cikin, ni kuma Muhammad Sameer ina mai miki rantsuwa da ALLAH saina nuna miki ainahin color d'ina”. ‘ya k'are maganar da buga yatsunsa biyu suka bada sautin d'ass! d'ass!! A saitin fuskarta’.
Fita munaya tayi da gudu daga bathroom d'in tana kuka, ahaka ta isa bedroom d'inta ta fad'a saman gado.
Shi kuma tana fita yaja wani wawan tsaki ya fad'a kan gado yana dafe kansa dake sara masa. ga wata yunwa dake cinsa, shi saima yanzu ya tuna ko breakfast basuyiba suka fita, tsaki kawai yaja yana jawo wayarsa. number Nuren ya kira, bugu biyu ya d'aga yana tsokanarsa da fad'in “ho angon k'arni”. Galadima ya danne 6acin ransa, dan baya buk'atar kowa yasan wannan matsalar data kunne kai tsakaninsa da Munaya, muryarsa a sake yace “kun gama ne?”.
“eh mun kammala, saidai kuma baka fad'i dawa-dawa za'ama visa ba cikin 'yan gidan nasu?”.
Ya cije lips nashi yana gyara kwanciya, “tokai dawa yaka mata kake ganin zasu tafi?”.
“eh, indai tanine gaskiya yakamata ace cikin k'annensa d'aya yaje, sai kuma mummynsu gimbiyarmu itama, tunda kaga itace first wife nashi”.
“Okay hakan yayi, zuwa dare sai muje gidan muji yanda zasuyi, nasan kai dai bazaka shigo nanba, please kabama Sauban Abinci ya shigo mana dashi, dan ko breakfast My mata batayi ba”.
“kai brother amma wannan sakacine ai, gashi ba ita kad'aiba?”.
“wlhy Na mantane, saboda kaga ai yanayin da take tun barinmu gidan, inaga zanma inno magana a bamu mai abinci kawai”.
“hakan zaifi kam, bara Na bashi ya taho yanzu kawai, amma zuwa anjima fa saika fito mun had'u”.
“okay babu damuwa”.
Yana yanke wayar kiran papi Na shigowa, fuskarsa d'auke da murmushi yay picking. cike da girmamawa yace “ran papinmu ya dad'e tare da k'yak'yk'yawan aminci”.
“tunda kamin laifi fa ai dole ka faramin da dad'in baki”.
Murmushi Galadima yayi har sarki Abdul'fatah na jiyo sautinsa, yace “a gafarceni ranka ya dad'e. ina fatan kuna cikin k'oshin lafiya kaida inno da dukkan ahalin masarautarka?”.
“Alhmdllh Muhammadu. sai kuma wasu k'yawawan albishir suka riskemu a wannan rana. to ALLAH ya inganta, ya sauketa lafiya, shi kuma mahaifinka ALLAH yaci gaba da d'orar da lafiyarsa”.
“Amin ya rabbi ranka ya dad'e ”.
“Muhammad mikuma ya faru da sirikinka haka mara dad'in ji?”.
“humm, ranka ya dad'e bansan miya sakoshi cikiba shi kuma?”.
Murmushi mai sauti papi yayi, ya gyara zamansa akan kilisarsa, cikin nuna kulawa yace, “akwai abinda bamu saniba ne kawai, amma a fiddashi daga k'asar kafin mu fara wani yunk'uri”.
Kamar Galadima na gabansa yashiga jinjina kansa, “to insha ALLAH zuwa gobe da daddare idan ALLAH ya kaimu zasu wuce".
“hakan yayi, aci gaba da hak'uri dai kaji Muhammad, hak'uri jarine, jarabawa kuma tsanice ta zuwa wajen nasara, ALLAH yayi muku albarka”.
“amin ranka ya dad'e, nagode sosai”.
“yaushe zaku shigo?”.
Murmushi Galadima yayi, hakan yana nufin kakansa nason ganinsa kenan, a ladabce yace “dasun tafi insha ALLAH ”.
“ALLAH ya kawoku lafiya”.
Tunda suka katse wayar saiyayta sauke ajiyar zuciya, koba komai ya sami nutsuwa akan wayar dasukai da papi. tashi yay ya k'arasa shafa man, sannan yasaka kayan da bazasu takurashi ba.
Falonsa ya fito, abinda ake nunawa a tv ya d'auki hankalinsa sosai, ana cigiyar d'iyar Minister Ce, wai an nemeta an rasa tun a daren jiya. Akan la66ansa ya furta “Nuren!” Sai kuma yayi murmushi kawai ya kwanta saman doguwar kujera.
A haka Sauban ya shigo ya sameshi da sallama, sai bayi buyu dake binsa a baya d'auke da ledoji.
Galadima ya bud'e idanunsa yana kallonsu amma bai tashiba, bayan bayin sun ajiye suka zube sunama Galadima barka da hutawa, murmushi kawai ya musu ya d'aga musu hannu.
Sauban yabasu izinin tafiya.
Zama Sauban yayi a kujerar dake kallon Galadima, “kai yau ina cikin nishad'i wlhy yaa Sam...”
Kallonsa Galadima yayi yana d'an murmushi, amma baice komaiba.
Sauban yace “yaa Sam... Aunty gimbiya fa?”..
Galadima yace “barci takeyi”.
“tofa Unborn babynmu yazo da sabon salo kenan”.
Hararsa Galadima yayi, ya mik'e yana dariya ya shige bedroom.
Galadima ya girgiza kai kawai yana tashi zaune. ledojin ya duba dan ganin mi suka sayo?.
Abinda yasan zata iya ci ya d'auka ya fita.
Saida ya d'anyi jimm a k'ofar d'akin sannan ya shiga da sallama, har yanzu tana a kwance tana kuka, lips d'insa ya d'an cija sannan ya ajiye abin hannunsa saman table d'in dake gaban gadon, idanu ya tsura ma bayanta nawasu 'yan seconds, ko alk'yabbar bata cireba, zama yayi a bakin gadon kusada ita, amma ya juya mata baya.
Tun daga shigowarsa har zamansa tana jinsa, amma ko motsi batayiba, kusan mintuna 3 suna zaune a haka, ganin batada niyyar tashi ko kulashi ya sakashi juyawa yana kallonta, gyaran murya yayi sannan yace, “tashi kici abinci”.
Shiru tayi ta shareshi, ko motsima bata yiba.
Tsawa ya daka mata, babu shiri ta tashi zaune, jikinta sai rawa yakeyi, tunba yanzuba munaya akwai tsoron tsawa, bata barin saita kwana amma batason amata tsawa. Shi kansa yayi mamakin tsoratar tata, ya watsa mata harara yana kwafa, sai kuma yaja tsaki, alk'yabbar yacire mata, sai hawaye take zirarwa, bai kuma cemata uffanba ya bud'e abincin ya ajiye a gabanta, kafeta kawai yayi da idanu, hakan saiya tasirantar da tsoronsa a zuciyarta, dan haka tafara cin abincin, tanayi dai hawaye na zurara, cikin nata bamai tsurfa baneba, komai ci take hankali kwance, sai dai laulayi na ciwo.
Dolenta ta saki jiki taci abincin, danya kafeta da idanu ga fuska cid'in-cid'in, duk jarumtarka dolene kaji shakkarsa.
Kallo d'aga tamasa ta janye idonta, shi kuma ya harareta yana fad'in “kin k'oshi ne?”.
Kanta ta jinjina masa tana matso kwalla. baice komaiba ya sauke sauran abincin k'asa, sannan yace “sauka kije kiyi wanka”.
Baki ta bud'e zatayi magana ya dalla mata harara. sauka tayi tana k'unk'uni akan la66a. yana kallon motsin la66an nata, sai dai bayajin mi take fad'a.
Yau kam Alhmdllh taji dad'in jikinta, ko k'arin ruwan da aka saka matane yasakata jin kwarin oho, ruwa mai d'an d'umi ta tara tayi wankan, tanayi tana hawaye, itafa ko mi zaiyi ba masifaba bazata bar cikinnan ba, babu yanda za'ayi ta reni ciki ta haifeshi sannan yazo daga baya ya saketa, bazata d'auki wannan rainin hankalinba, su maza a kullum d'aukar mace suke mai k'arancin tunani, kowane yayin rashin mutuncinsu suka kwaso saiya k'are akan mata, wlhy akan cikinnan tata d'aga masa hankali kenan harsai ya amince an zubar dashi sannan, kuma ana zubarwa zata k'ara gaba, mahaifinsa kam kobasa tare insha ALLAH zata cigaba da masa addu'oi ana aika masa.
Jin shiru tak'i fitowa ya sakashi mik'ewa, bai wani kwankwasa ba ya bud'e k'ofar bathroom d'in kawai, danshi zatonsa ba wankan takeba ta tsaya kukane.
A birkice munaya ta kalli k'ofar, ganin Galadima tsaye yana kallonta ta fasa k'ara, yay hanzarin ida shiga bayin ya rufe bakinta da tafin hannunsa dankar ta tara masa jama'a.
Juyawa tayi ta ruk'unk'umesa, tare da saka hannayenta ta zagaye bayansa ta manne k'irjinta da nasa, ita duk bata son yaga jikinta ne😂😝.
Shima fuskantar hakan da yayi ya sakashi sakin murmushi, saiya saka hannunsa biyu ya zagaye bayanta ya manneta sosai a jikin nasa.
Shiru sukayi nawasu seconds, tana sauke ajiyar zuciya shima yana saukewa, saboda yanason ganin yanda zatayi saiya fara k'ok'arin janye jikinsa itama zai janye ta.
K'ank'ameshi tayi ta fashe da kuka, jiyay tamkar ya kwashe da dariya, amma saiya daure, cikin dakiya yace, “malama sakeni mana? konaci bashinki ne wai?”.
Cikin dasashshiyar muryarta datasha kuka tace, “to kabani zanina da hijjab na saka”.
“to kin k'udunduneni ta ina zan iya baki wani zani? sakeni saina baki”.
Kafad'a ta nok'e alamar tak'i.
Murmushi Galadima yayi, ya shafa bayanta cikin murya k'asa-k'asa yace, “idan an hanani ganin can ai gashi ina kallon nan”.
Da sauri tayi wata wulk'itawa ta koma bayansa ta 6uya.
Kansa ya dafe yana fad'in “yau Sameer kaga ta kanka, ranar farin cikinka sai saka maka ciwon kai da zafin kai akeyi, wai ke yalla6iya mikike 6oyemin daban saniba ne?”.
Baki ta murgud'a masa tana fari da idanu, dayake ba ganinta yakeba baisan hidimar datakeyi ba.
K'ok'arin juyo da ita ya farayi amma tabi ta kanannad'e shi, rasa yanda zai mata yayi. yakula yarinyarnan 'Yar daruce kawai. zaninta ya jawo ya mik'a mata, saida ta tabbatar ta d'aura sannan ta sakeshi, yana juyowa ta juya masa baya ita kuma.
Baice komaiba ya ta6e baki ya fice daga bathroom d'in.
Harar bayansa tayi ta na fad'in “ALLAH ya isana”.
Nace Humm.😏
Fita yay daga d'akin gaba d'aya, tunda dai yasamu taci abincin, harya kai k'ofarsa ya tuna batasha maganinta ba, dawowa yayi da baya.
Ita kuma motsin fitarsa dataji yabata kwarin guywar fitowa.
Shigowarsa tasata kwakumar hijjab ta saka, bakinsa ya ta6e ya wuce wajen handbag d'inta batare daya kalleta ba.
Magungunan ya fido, ya zauna bakin gadon, “kizo kisha magani”. ya fad'a cikin k'asaitarsa.
6ata fuska tayi, tace “babu amfanin tattalin abinda za'a zubar ai”.
Lips d'insa ya cije, sai kuma ya ajiye drugs d'in yana kallonta, mik'ewa yayi ya taka inda take, a bayanta ya tsaya, fisgota yayi ta fad'o saman k'irjinsa, saida ta rumtse ido dan zafin dataji, ya matso da fuskarsa daf da tata, a wani yanayin data kasa fassarawa yace “adadin nawa kike buk'atar na biyaki danki barsa?”.
Rik'esa nayi da k'yau gudun karna fad'i, na janye idona dake cike da kwalla daga cikin nasa, “Bana buk'atar ko sisinka yalla6ai, cikinne kawai bana buk'ata, kuma bazan raineshi ba balle nakai ga haifeshi”.
Wani murmushi mugunta yayi, sanan ya sakeni tamkar zai hankad'ani, mikuma ya tuna oho masa, saiya kuma damk'e hannuna, muryarsa a kausashe yace “wlhy idan kinga baki haifi cikin nanba to sai dai idan wanine a cikinmu numfashinsa yabar gangar jikinsa, sai kuma idan ubangiji ya kaddara Shiba mai Shak'ar iskar duniya bane, dan bani da hakk'in kowa, ubangiji kuma bazai barki ki shiga nawa ba”.
yana gama fad'ar haka ya saki hannuna yafice daga d'akin baki d'aya.
Yariga yasan zai fuskanci abindama yafi haka daga munaya, shiyyasa bai zafafama zuciyarsa akan wannan rikicin nata ba, shi babbanma burinsa yanzu Abbanta yabar k'asar nan, danya samu damar gudanar da aikinsa yanda ya kama ta.
Da wannan tunanin ya dawo d'akinsa, ya iske Sauban kwance wai zaiyi barci, hararsa yayi yana fad'in “ kama tashi, time d'in zuhur yayi.
Yana fita na raka bayansa da harara ina murgid'a baki, “oho dai, koma mizaka fad'a ka fad'a, nima ai bani tare da hak'k'in kowan, ALLAH kuma bazai baka damar danne nawaba, sokake nazama shashar mace ko? munyi auren contract batare da sanin iyayena ko naka ba, kazo kamin ciki na haifa maka ka sakeni na koma gidanmu, katashi da riba biyu kenan, nikuma babu ko d'aya sai bak'incikin danakema iyayena tanadi da kaina, Galadima ko a matanma ai _AKWAI BANBANCI?_ wlhy.
gaskiyane Munaya, rik'e darajarki shine 'yancinki😄👍🏻.
*******
Bayan sun fito massalaci sukejin labarin wai an rasa inda Muftahu yake, a safiyar yau aka samu motarsa a bud'e, sai kuma agogonsa da takalminsa d'aya a k'asa alamar da k'arfin tsiya aka saceshi.
Hakan yasaka aka kama dogaran dake tsaron k'ofa ta uku, dan anga alamun tanan aka fita dashi.
Dukda Galadima najin haushinsa saida hankalinsa ya tashi, dan haka suna shigowa ya d'au waya ya kira Nuren.
Nuren na d'aga wayar Galadima yace, “Nuren Muftahu, kaine ko?”.
“Muftahu kuma? nine naimi?”.
“A daren jiya an rasa Wanda ya bar masarauta dashi”.
“humm brother, dukda muna ganin Muftahu cikin masu mana zagon k'asa banta6a tunanin saina d'aukeshi zan gane hakaba, wlhy bani bane”.
“ya salam”. ‘galadima ya fad'a cikin dafe kai da cije lips, wayar ya yanke ya Shiga safa da marwa, yarasa wazai hararo.
Yana cikin wannan halin saiga harun shima a rikice, kowa yasan su ukunnan abokan junane, kuma akwai shak'uwa tsakaninsu, matawalle ne dama bai cika shiga cikinsu ba, saboda mama Fulani Na hanashi tun yana yaro, a cewarta shine d'an Sarki mai mulki, kuma shine mai jiran gado, darajarsa datasu Galadima ba dai-dai takeba, wannan hud'ubar ce tamasa tasiri sosai, amma yanason 'yan uwansa har zuciyarsa.
“galadima shin kaji kuwa mike faruwa a masarautarnan?”.
Cikin damuwa Galadima yace, “Harun su waye da wannan aikin?”.
“kowa abinda yake tambaya kenan Sameer, Muftahu bashida wani abokin fad'a”.
Hankalin Galadima kuma tashi yayi, shi duk damuwarsa karda a cutar da Muftahu ta dalilinsa, tunda ya kula duk wani makusancinsu shine abin harin mak'iyansa. shifa baima yarda ba Nuren bane da wannan aikin, dan yasan halinsa sarai, dolene kuwa yafita wajensa yanzunnan.
Harun yace bara yaje, suna son akai report gidan radio da television.
Jin jina kai Galadima kawai yayi, shima ya shige ciki danya shirya.
Tun safe an sanarda jami'an tsaro 6atan Muftahu n, kuma suna a kan aikinsu.
★★★
Yunwar da yakeji tasashi bayan yayi shiri ya samu fresh milk yasha kawai, sannan yafito, d'akin Munaya ya lek'a, saiya isketa baje a gado tana shak'ar barci, baiyi yunk'urin tashinta ba yafito.
Har dogaransa sun taso yace suyi zamansu su huta, zai fita shida Sauban, cikin damuwa sarkin mota yace, “kayi hak'uri ranka ya dad'e, koda nine kawai mu fita, Mai martaba ya sanar yau a fada kar'a sake barin wani d'an gidannan yafita wani waje shi kad'ai”.
Kallonsa Galadima yayi, kamar zaiyi magana saikuma yafasa ya bud'e mortar da kansa ya shiga, batare da ya jira an bud'e masa ba.
Da hannu sarkin mota yayma sauran dogaran nuni da su biyosu a baya idan sun tafi.
A wani waje suka had'u da Nuren, Nuren ya fito daga motarsa yadawo inda Galadima yake, sai sarkin mota yafita yabasu waje kawai.
Galadima yace “please idan kaine ka sakeshi”.
Da mamaki Nuren yace, “wai Muftahu n dai? am telling you banida alak'a da d'aukarsa. yarinyar Minister ce kawai a hannuna”.
“innalillahi, wlhy Nuren inajin tsoro, karsuje su cutar dashi”.
“Sameer! nifa ina zargin kawai ya had'a baki da wasune suka kamashi dan yayi wasa da hankalinmu”.
Idanu Galadima ya tsurama Nuren tamkar yana hango gaskiyar maganarsa, ya saki wani guntun murmushi, sannan ya gyara zamansa yana fad'in “well, koma minene dai zai fito ai”.
Nuren yace “ni kaga dama kabar zancen wani Muftahu n banza can, way note mu wuce gidan sirikanka kozamu samu wasu evidence daga canma akan Accident d'innan”.
Agogon hannunsa ya kalla, sannan ya kalli Nuren d'in alamar suje.
Anan Nuren yabar motarsa suka tafi ata Galadima, saida suka fara tafiya Galadima ya lura da mototin dogaransa a bayansu.
d'an murmushi yayi yana kallon Sarkin mota, yace “sarkin mota an karya min doka kenan?”.
Sarkin mota daya fahimci Galadima yagane dogarai Na binsu sai yayi 'yar dariya, yace “ka gafarceni ranka ya dad'e, bazai yuwu mu barka ka fita kai kad'aiba ai, dan fitarka babu kowa tafi ta kowa had'ari a masarautarnan, mai martaba ma nasan saboda kaine ya saka dokar ai”.
Galadima baice komaiba sai murmushi dayayi, Nuren ma murmushin yayi, sannan yace “amma kamar bayan motar dogaranka akwai wata bak'ar mota Na bin tasu?”.
Galadima ya juya shima, tabbas anabin motar dogaran a baya, “sarkin mota su wucemu, karsu tsaya”.
“To ranka ya dad'e”.
Bayan sarkin mota ya sanar musu suka wuce su Galadima, motarma ta wuce, da kallo Nuren da Galadima suka bita, Nuren yay hanzarin d'aukar motar hoto a wayarsa. “humm da alama suna zaton kana d'aya daga cikin motocin canne”.
Murmushi Galadima yayi, a k'asaitarsa yace, “kokuma suna son wasa da hankalinmu ba”.
Da mamaki Nuren yace “kamar ya?”.
Murmusawa Galadima ya kuma yi, ya kwantar da kansa jikin seat yana lumshe idanu, “Nuriddeen! Sameer ya wuce tunanin dukkan mai tunani, kai tsaye ba'a gane manufar zuciya, kwanji ko dama basu ke nuna k'arfin ikon mai ikoba, nazarin komai daki-daki da iya sarrafa duniya a yanda tazo shike nuna k'arfin gwarzan taka, mazantaka ba'a shaidata a fuskar namiji, duk lokacinda kai gamo da nama, kud'i, mata bisa hanya, karkayi rawarkan d'auka ko murnar ALLAH ne ya baka, zata iya yuwuwa tarko aka d'ana maka, shi k'yawu had'arine, 6oyeshi kuma nagartace, maiyi baya fad'an zaiyi, sai dai aga aikinsa a k'asa, tasowar iskar hadari bashi ke nufin ruwan zai zuba ba, watak'il sunan wannan iskar gyara kayanka. Dalili da dalilai basa ta6a saka zuciyar Wanda yake nema ta raunana, time d'in da zan nunama mak'iyan mahaifina d'an zaki ya girma yayi, sun durk'usar da shi a k'asa batareda tunaninsu yabasu ya haifi Raina kama ba, Su cigaba da raina aikin Muhammad Sameer daga k'arshe kuma saisuga gayya, tafiyar hawainiya bashike nufin gazawar kuzarinta bane, lokuta da dama hanzari kan katse igiyar cikar buri, a sannu kowa zai fahimci wanene *_RAINA KAMA....._*👎🏻
Ba Nuren ba hatta da sarkin mota maganganun Galadima ya shigeshi, tabbas mutane dayawa sunama Galadima kallon mutum mai yawan sakaci da rashin ho66asa, koshi yana d'aya daga ciki, amma wannan zantukan nasa sai suka sakasu a rud'ani, kenan akwai abinda sud'in basu saniba...........
Dole tunaninsu ya katse saboda isowarsu gidansu Munaya.
Fita sarkin mota yayi yanema musu iso, babu dad'ewa saiga baba k'arami ya fito, sarkin mota ya bud'ema Galadima, yayinda Nuren ya bud'e da kansa, zuciyarsa sai jujjuya hannunka mai sandar Galadima yakeyi.
Dukda baba k'arami yayi mamakin zuwan Galadima haka ya danne, yaymusu k'ar6a ta girma, sannan suka shiga cikin gidan.
Gidan tsitt tamkar babu mutane, saikace ba gidannan bane mai kama Dana 'yan dambe😂, (yo kowa Na tsoron a korashi gidansu🤣😝).
A falon daddy aka musu masauki, dan danan aka cika musu gaba da kayayyaki, baba k'arami ya fita domin basu damar cin wani Abu.
Babu abinda suka ta6a, dukda kuma Galadima ma yunwa yakeji, a haka daddy da baba k'arami suka dawo.
Daddy yace “anya kuwa wannan d'an namu yana d'aukar gidannan matsayin nasu?”.
Murmushi Galadima da Nuren sukayi, Galadima yace “sosaima daddy”.
Baba k'arami yace “ta INA zamu amince da haka kuwa, bayan inada tabbacin ko ruwan gidannan Baka ta6a sha ba”.
Kunya Ce ta kama Galadima, sai kuma yaga bai k'yautaba, ya rissinar da kai yana fad'in “amin afuwa zan gyara”.
Mik'ewa baba k'arami da daddy suka kumayi, “to mun bada dama ta biyu”. cewar Dady yana dariya.
Bayan fitarsu Nuren ya bud'e kulolin shima yana dariyar, danbun shinkafane daya samu nutsuwa ta musamman, sai k'amshi mai dad'i yakeyi, daga Galadima har nuren saida kwad'ayin cin abincin yazo musu.
Kallon Galadima Nuren yayi yana d'aga gira, Galadima yay murmusa tareda fad'in “kadaiji kunya”.
“kaima jinta zakayi yanzu, dan nasan ci zakayi”.
Yau dai kam Galadima yaci abincin gidansu Munaya, kuma gashi girkin innarsu, babu kunya sukaita zuba Santi shida Nuren sunama juna dariya, Galadima harda su6utar baki yana fad'in “amma my mata muguwace, bata ta6amin irin wannan ba”.🙀
Mi Nuren zaiyi inba dariya ba🤣, su Galadima anji dad'i har kwalwar kai Baki ya bud'e😂😝.
Saida suka mammala tsaf sannan su baba k'arami suka dawo, sunji dad'i dasuka iske sunci.
Daga nan sukayi gaisuwa, su baba k'arami suka d'ora da godiyar d'awainiyar Abba da Galadima ya d'auke musu.
Murmushi kawai Galadima yayi.
Nuren ya gyara zama, a ladabce yamusu bayanin son fidda Abba da Galadima kesonyi, dan likitoci sunce ana buk'atar kulawa saboda karayar hak'ark'arinsa data k'ugu, “to yanzu haka dai angama setting d'in komai gameda tafiyarsa, har asibitin daza'a kaisa, visa d'insa da komai, sai dai anason tafiya da mutum biyu a cikinsu, mi kuka gani akan Wanda za'aje da shid'in?”.
Daddy da baba k'arami suka kalli juna, summa rasa wane irin farin ciki zasu nuna dan Galadima yasan sunji dad'i? sunta jero masa k'yawawan addu'oi, kafin daddy yace “ai kawai sai atafi da jafaru da Ai'sha, dan bai kamata mutafi mu duka ba gida babu kowa, dukda akwai su Anas, gakuma su Hameed zasuke zagayowa, amma hakan yafi dai.
Duk sun gamsu da hakan, dan haka suka buk'aci passport d'in baba k'arami da inna, ita inna babu, sai sunje an mata, amma baba k'arami an samu.
Sun bari akan zuwa anjima za'azo akai inna tayo.
Daga nan Galadima ya buk'aci number da aka kira aka sanar musu da accident d'in Abba.
Daddy yace Ai'sha aka kira, saidai akawo wayar tata. Kiranta yay yace tabama cikin su Aryaan ya kawo wayarta.
Babu dad'ewa saiga Aryaan d'in da ita, yanda yaron ya gaishesu saida abin ya birge Galadima, ya yarda yaran gidan akwai tarbiyya babu laifi kam.
Galadima yace, “amma Dady ko numbers nawa Abba ke amfani dasu?”.
baba k'arami ya bashi amsa da cewar “uku ne”.
Nuren yace “kozamu samesu dukansu?”.
Dukda baba k'arami da daddy sunshiga mamaki, dansu zukatansu basu kawo musu akwai wani Abu a k'asa ba, sun d'auka kawai Abba yayi Accident ne dai.
Baba k'arami yabasu Numbers d'in duka.
Bawani bincike Galadima yayi a wayar innarsu Munaya ba, wani Abu kawai ya saka (Wanda Nima ban saniba😱) yabama Dady wayar yana fad'in “zata bar wayar anan dan a can bazatayi aikiba, kuma gashi muna buk'atar wayar, dan haka daddy saika rik'e a hannunka tunda kai kana gida”.
Dady ya amsa da to, duk su Galadima sun kuma sakasu a duhu.
Sallama sukai musu suna fito domin tafiya.
Harsun Shiga mota saiga Aiyaan da gud'u d'auke da wata Leda.
Sarkin mota ya tareshi yana fad'in yaro miya farune?”.
“Auntynmu za'a kaimawa inji innarmu”.
Galadima yayma sarkin mota nuni da yabar Aiyaan d'in ya k'araso.
Bud'e murfin Galadima yayi, Aiyaan ya k'arso, Galadima ya kamo hannun Aiyaan yana murmushi, “my friend ya akayi?”.
'Uncle innarmu ce tace akaima Auntynmu dan ALLAH”.
murmushi Galadima yakumayi, sannan ya kar6i ledan yana fad'in “ita kad'ai banda ni?”.
Aiyaan yad'an zaro ido waje, sai kuma yace “to bara naje Na fad'am innarmu kaima ta baka naka”.
Da sauri Galadima ya kamo hannunsa dan yana neman tsillawa da gudune, “kaga dakata, idan naje saimu raba wannan da ita, yanzu dai ka fad'ama innarmu ta shiryaka gobe zan aiko a d'aukeka kazo ka zauna damu tunda kuna hutu ”.
Cikin murna Aiyaan yace, “wajen auntymu?”.
Galadima ya jinjina masa kai.
“to amma kuma Aryaan fa?”.
Cikin mamaki Galadima yace, “wanene Aryaan d'in?”.
“lah baka San mu 2wins bane ba?”.
“da gaske?”.
“ALLAH kuwa”.
“to shikenan, kacema innarmu ta shiryaku Ku duka biyun zakujema Aunty hutu”.
Cikeda murna Aiyaan ya shek'a da gudu gida danya kai labari.
Galadima yay murmushi yana rufe k'ofar motar, Nuren ma murmushi yakeyi, a fili yace, “yara sunyi wlhy”.
Galadima ya kalleshi, cikin d'age gira sama yace, “kayi aure”.
Sosai Nuren yay dariya.
******
A inda suka d'auki Nuren anan suka ajiyeshi, su kuma suka koma masarauta, sun iske tuni dogaran sun dawo abinsu.
d'akinsa ya Shiga, ya iske Sauban nata barcinsa.
Bai tadashiba, yadawo falo ya zauna.
_____________________________
Da daddare Galadima Na falonsa zaune yana aiki a system akayi knocking d'in k'ofa, izinin shigowa ya bada, sarkin mota ya shigo hannunsa d'auke da leda.
Galadima dake aikinsa bai d'agoba, a haka ya amsa gaisuwar sarkin mota.
Sarkin mota yace “ranka ya dad'e kayi mantuwane a mota ”.
d'agowa Galadima yayi ya kallesa, ganin ledar da Aiyaan ya kawo yatuna masa sak'on munaya, nuni yama sarkin mota daya ajiye.
Sarkin mota ya ajiye yana masa saida safe.
Nanma bai tankaba, kansa kawai ya jinjina masa.
Bayan fitar sarkin mota ya mik'e d'auke da laptop d'insa da ledar, dama tunda ya shigo baima lek'a ta ba, dan Sauban yace yakai mata abinci, kuma tun d'azu suna tare suna hira. Hakan yasa yagane shine ta raina kenan. wannan haushin ya hanashi Neman inda take.
A bakin gado ya isketa zaune tagama waya da Munubiya, k'in d'agowa tayi ta kallesa, tadai amsa masa sallama.
Shima bai kula taba ya zauna bakin gadon d'an nesa da ita.
Shiru kowa yayi suka share juna, haushi ya turnuk'e Galadima, lokaci yayi dazai daina d'agama yarinyar nan k'afa, yakamata su goga raini shi da ita. ta gefen ido ya saci kallonta, sai wani cika da batsewa takeyi, ya cije lips nashi.
“k baki iya gaisuwa bane?”.
Saida takuma tura bakin sannan tace “ina yini” tana mik'ewa da nufin bar masa d'akin, tana k'unk'uni
Bai amsata, sai mik'ewa da yayi shima, matsawa tashiga yi baya yana binta, fuskarsa a matuk'ar d'aure, da jikin bango ta manne, shikuma ya mata runfa, hannunsa d'aya a dogare da bangon yayinda yasaka d'aya ya rik'o hannunta ya matsa da k'arfi, zatai magana ya jawota tafad'o jikinsa, ya manne bakinsa kan nata, duk yanda taso kwatar kanta hakan ya gagara, dan ya kama hannuwanta biyu ya murd'esu ta baya yanda ta kasa koda motsi. A haka ya wulk'itata takoma saman gadon, shima yabi bayanta.
Ya d'ora hannunsa kan bakinta dan karta ishesa da tsiwa, idonsa ya saka cikin nata ya hanata kata6us, cikin tsare gida yace “dolene yau Na kora miki warning na musamman danki ringa banbance inda zakiyi tsiwa”.
Bai bata damar dazata fad'i nata ba yashiga aikata yanda yakeso da ita🤥🙆🏻.................✍🏼
Kutttt Galadima auren Contract nefa😱😂, ba ruwana kaida masoyan Munaya aradu🤣⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀🤧.
i miss you wujiga-wujiga my sweet fans😂😜😜😜🥳.
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*🙏🏻😭
*_Typing📲_*
*_Haske writer's asso...._*💡
*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻
~Book 2~ 👉🏻9⃣
.................Salon nasa yasani bashi ragama, dan Galadima yazo min da sabon salo mai tafiya da gudun jini dana zuciya.
Duk da kasancewata farin shiga, hakan bai hanani gane Galadima Na daban bane, kamar yanda kuka sanshi mutum mai izza da k'asaita, hakan bai canja ba ta wannan fanin, komansa a nurse da izzar k'asaita yake gudanar dashi. ban tashi farga nayi kuskure ba saida labari yafara nisan zango, anzo wajenda tsorosa yafara tasiri a gareni, Sai dai kuma nayi sakacin da Galadima yazama kurman dutsen dabaya ji baya gani. Sai lokacin hawaye suka fara ambaliya ga fuskata, hannayena na k'ok'arin d'agawa domin rok'o, sai dai ya hanani wannan damar gaba d'aya..........
🤥🙆🏻kai babu ruwana, iya nan nagani nima🤫 aradu aunty Magajiya da aunty Ni'ima zasuci k'aniyata ne idan na k'arasa fad'a😱🤭⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀.
Tabbas na gurzu, dan yau na banbance tsakanin aya da tsakkuwa, banbancin baya cikin hayyacinsa da yau d'inma kad'anne, dukda babu yanda za'ayi daren farko yayi dai-dai da kowacce rana ta bayansa.
Duk ajiyar zuciyar danake saukewa yana jina, amma yay luf a gefena, hakan ne Yakuma tunzurani, a zalinceka akasa lallashinka saboda jin kai, wlhy kasaitar bawannan tayi masa yawa, duk randa yazama sarki kam fadawa sunga takansu, dan magana dai idan sarki na uku a fada toshi bazaiyi ko guda d'aya ba😏.
Galadima daduk yake sauraren kukan nata da ajiyar zuciya ya juyo kad'an yana fuskantarta, hannu yasaka ya tallafo fuskarta ta matso dai-dai da tasa, jinai kawai ana huramin iska saman ido, tsaf na fahimmci iskar bakinsa yake huramin, amma saina dake nak'i bud'e idona.
Muryarsa can k'asan mak'oshi ya furta “my friend are you okay?”.
Banza na masa, nakuma k'i bud'e odon, lallai mutuminnan yacika d'an latsin rainin wayo number 1, yanzunan Galadima har yanada bakin yimin wannan banzar tambayar?, idona a rufe har yanzu na bud'e baki cikin salon tsiwa zan maka masa bak'ar magana, amma saiya d'ora yatsansa saman bakina yana fad'in “shiiii!🤫” da bakinsa, shirun kuwa nayi kamar an rufemin bakin Dan Nina Na tuna illar yin tsiwar.(😝😂)
Ya matso dani jikinsa ya rungume, hannunsa na buga gadon bayana k'ad'an-k'ad'an, ya d'ora bakinsa saitin kunnena, “yanzu kin gane banbancin Sameer da Munaya right?, idan kuma har yanzu baki fahimta ba to bakinki ya cigaba d'amin tsiwa OK?, nikuma bazan gaji da punishment nashi ba sala-sala yalla6iya💋”. ‘ya k'are maganar da sumbatar cikin kunnena’.
Babu shiri na k'ank'amesa dan har cikin kwalwar kaina naji sumbar nan.
Kad'an ya buga bayana sannan ya janyeni daga jikinsa ya sauka daga saman gadon.
“hasbinallahu wani'imal wakil” na iya maimaitawa kawai, na k'ank'ame pillows d'in gabana ina rintse idanu da cije lips (copy copy😝).
Kusan mintuna 15 duk nazata yama fitane, sai kawai jinai an d'aukeni. a razane na bud'e idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, da matuk'ar Sauri na maida nawa na lumshe.
Wani muskilin murmushi Galadima yayi yana cije lips.
Ba shiri na bud'e ido, saboda jina cikin ruwan zafi, yunk'urawa nayi zan mik'e cikin 6ata fuska ya maidani ya zaunar yana fad'in “za6i ya rage naki, zama kiyi da kanki, kokuma ni nayi miki..”
Banma bari yakai k'arsheba na koma na zauna ina kare k'urjina.
Kafad'a ya d'age sama yana ta6e baki da fad'in “hummm”.
Fita yay daga bathroom d'in ya rufe mata K'ofar.
Na kai tsawon lokaci a bayin ina Gasa jikina, dan nasan idanma banyiba kaina nama mugunta, saida naji ko ina ya saki sannan nayi wankan tsarki ina hawaye, bansan yanda zan fassara wannan muguntar ta Galadima ba kuma, wannan karon kuma tsautsayin zaice kokuwa ba yin Kansa bane?.
Haka dai na kammala na d'aura towel d'ina, a zuciyata ina addu'ar ALLAH dai yasa ya fita, dan towel d'in guntune, bai gama rufe cinyoyina bama baki d'aya.
Da sand'a na fito, yauma inajin zafi kad'an-kad'an, amma ba kamar na ranar ba. ganin baya d'akin saina ida rufe k'ofar na tako cikin d'akin sosai.
Ina neman kaya a wardrobe ina share hawaye, indai rashin tsiwar dayake fad'ace na daina masa, dan bazan zauna ya illatani a banza ba, wannan k'addararren cikinma daya hanamin gangar jiki hutawa da ciwuka ya isheni, basai na cigaba da 6alloma kaina wata muguntar tasa ba.
wata 'yar riga mai d'an nauyi-nauyi na samo, na cirota dan sanyi nakeji, juyowar da zanyi saina gansa zaune bakin gado yana danna laptop, hannunsa d'aya rik'e da glass cup yana shan fresh milk hankali kwance.
Saida nad'anja baya, nakuma bud'e rigar ina kare jikina.
Duk abinda takeyi yana kallonta ta gefen ido, amma yawani share kamar baima San da itaba.
Da bin bango da sand'a na koma bayin, ta gaba kuma ina karewa da rigar.
Saida ta shige ya d'ago kai yana kallon k'ofar bayin, saikuma ya girgiza kai yana murmushin gefen baki. cigaba yayi da aikinsa a nutse.
Barci nakeji, ga zazza6i yafara rufeni, hakan yasa ina gama saka rigar na fito, naci serious kawai sannan na fito.
d'ago idanu yayi muka had'a ido, da sauri nad'an rankwafa inajan rigar barcin k'asa wai danta rufemin cinya zuwa kwauri.
Baki ya ta6e yana wani janye ido cikeda basarwa. Irin shi baiga abin kallo d'in nanba.
Ni kuma na dalla masa Harara ina k'ok'arin hayewa gadon.
“ji mana”. ‘yafad'a cikin izza’.
Banza na masa zan haye gadon.
Yace “iyim, bakije daddarawa ba kenan yarinya, saina sake kaiki yanzunnan....”.
Kafin ya rufe baki nama iso gabansa na tsaya.
d'agowa yayi yana kallona yana kur6ar fresh milk nashi, ya d'agamin gira d'aya.
Baki na turo masa ina share hawaye.
Ya kamo hannuna ya zaunar kusa da shi, “nikam yalla6iya karki haifomin abin cikin kwan da halin kuka, bana son ragwan taka, 'yata ko macece jaruma za'ayi, irin wadda labarinta zai zaga lungu da sak'o na duniya”.
Harara na balla masa, yay saurin rik'e cup d'in hannunsa dayake zuba frash milk a ciki, “eh me, malama karkisa hantar cikina fitowa, irin wannan harara haka”.
Kad'an yarage banyi dariya ba, da gaskiyar Momma, halin Galadima d'aya da Sauban, tsantsar harmutsine da sanya damuwa a rai ya lullu6e halinsa na barkwanci, hakan kuma yanada nasaba da rashin samun mai jansa a jiki yana d'auke masa kewa da rage masa rad'ad'in damuwarsa. Momma hankalinta nakan jiyyar Abie, Aunty mimi kuma rainon Sauban, mom kuma tayi aure lokacin dayake buk'atar makusanci, s.......
Firgigit nayi saboda hancina da yaja, na kalleshi ina tura baki.
“maida wuk'ar yalla6iya, abin bana fusata bane, wace duniyar kika tafi hakane da nisa inata magana?”.
Marairaice fuska nayi ina shirin fara kuka, “please ka barni na kwanta barci nakeji”.
Kofin hannunsa ya mik'amin, na waro idanu ina girgiza masa hannu alamar a'a”.
Shima saiya waro nasa idanun yana fad'in “why?”.
“kawai ni bazan sha bane, aje a zubamin wani abu”.
“hakane kuma”. ‘ya fad'am yana kamoni ya jawoni jikinsa’.
Saman cinyarsa na zauna, da hanzari nafara k'ok'arin mik'ewa. shima saiya kama hannayena ya maidasu baya yanda bazan iya kata6us ba, madarar ya d'auka ya guntsa da yawa a bakinsa.
Waro idanu nayi ganin ya nufo bakina gadan-gadan, duk yanda naso kauda fuskata ya gagara, na datse hakwarana da sauri, shi kuma saya toshemin hanci, hakan yasa ni bud'e baki dole, dan ina buk'atar shak'ar numfashi. Tas ya juyemin fresh milk d'in abakina, sannan ya kuma rufe hancina saida na shanyeta sannan ya janye bakin, ni dashi duk muka hau sauke numfashi, kuka na sanya masa, amma hakan bai hanashi kuma guntsar madarba ya kuma juyemin a baki na, haka yayta min, ya kuma k'ara rabin kofi kuma, saida yaga ta kwalin ta k'are sannan ya sakarmin hannu na tashi zaune.
Bansan kawai na fara kaima k'urjinsa k'ananun dukaba, ina fad'in wlhy sai ALLAH ya sakamin, kai bama zan yarda ba fa, saboda k'azanta kaita had'a yawunka da fresh milk kana d'uramin, ni bazan yardaba”.
Shagala kawai yayi yana kallona, yakasa kare kanshi balle yunk'urin hanani, saida nayi mai isata sannan na fad'a k'irjin nasa ina raira kuka.
Lumshe idanunsa yayi yasaka hannayemsa ya zagayeni sosai yana kuma sakani jikinsa sosai. Nima sainayi luf Ina shak'ar k'amshinsa da yariga ya mannema fatarsa.
Munja wasu times a haka, ni ina kuka shi kuma idonsa a lumshe yana shafa kaina da saurarena.
Jiyay kawai jikinta ya saki, alamar barci ya d'auketa, sai ajiyar zuciya da take ta saukewa, bud'e idonsa yayi, sannan yakai bakinsa a hankali ya sumbaci sumar kanta dake tare da danshin ruwa har yanzu. zafin zazza6inta dake ratsa 6argon jikinsa ya sakashi fidda huci yana kuma sumbatar kanta.
Dr Farida ta sanar masa babu abinda zai hanata wannan zazza6in, koda tasha magani ya sauka saiya dawo, sai idan cikin yayi kwarine maybe ta daina ma gaba d'aya, amma mai juna biyu ba'a rabata da k'ananun ciwo makamantan haka. jiyay ya kuma k'aunar Momma d'insa a ransa, a hankali ya furta I love you my Momma”.
Tashi yay d'auke da Munaya a hannu, ya kwantar da ita sannan yaja bargo ya lullu6a mata. tare da sunkuya wa ya sumbaci goshinta ya shafa cikinta da hannunsa sannan ya mik'e ya koma inda yake.
Ya cigaba da aikin dayake a laptop Wanda ban fahimci komaiba a ciki, tsawon lokacin yana aikin, saida ya fara hamma sannan ya kashe. bayi ya shiga ya d'auro alwala, ya gabatar da nafila kafin yay shafa'i da wutiri yaja doguwar addu'a da kirari wa Ubangijin talikai, harda hawayensa sannan ya mik'e.
Ya kuma daidaita hasken fitilar d'akin sannan ya hau gadon shima ya kwanta, yay musu addu'a ya shafe cikin munaya (😂Galadima saboda tsaro ba tsoroba ko🥺).
a zatona zai rungumeta, sai naga ya gyara kwanciyarsa kawai a gefenta yaja bargo shima.
Galadima asuba ta gari, (ni dai rungume nawa mijin zanyi aradu🤫🙈⛹🏻♀).
Ga bannin asubahi zazza6in munaya ya sauka, hakanne ya sakata samun dad'in barci sosai, ta kuma kanainaye Galadima, wanda shi da kansa ya mirgino har inda take cikin barci ya rungumeta, dukda zafin zazza6inta nata ratsa nashi jikin yakasa barinta. ahaka kiran sallar farko ya riski kunnuwansu.
Kusan a tare suka farka, ganinsu manne da juna yasaka kowa barin jikin d'an uwansa da sauri, munaya dai kunya ta sakata juya baya, amma boss ko a kwalar rigarsa, saima tashi da yayi yana wani ciccin Magani ya shiga toilet.
Alwala ya yo, baiyi mata magana ba ya fice abinsa.
Munaya ta raka bayansa da harara tana fad'in Girman kai dai rawanin tsiya wlhy. tashi tayi itama ta shiga bayin, amma sa6anin shi ita harda wankan gasa jiki (lallai kinji basawa Munaya🤭, wannan gasa jiki dabaya k'arewa haka🤥😂).
Fitowa tayi tanata kumbura fuska, ni dai na lalla6a na shige bayinta danna dandalo arzik'i😝 lol (koya kukace fans🤷🏻♀😂?).
****************************
Ban sake jin d'uriyarsa ba sai around 9:30am.
Tashina a barci kenan na rarrafa zuwa bayi da k'yar nayo wanka, dan banajin dad'in jikina gaba d'aya, danan ya saki sai nan ya kama ciwo.
Motsin mutum naji a bayana dan haka na waiga, Galadima ne cikin Farin wando da t-shirt itam fara tas, ya d'aure k'ungunsa da Navy blue d'in belt, sannan ya kawo jacket navy blue itama ya saka, babu takalma a k'afarsa, sai dai k'afar fes tamkar ba'a takata a k'asa, sai agogon azurfa mai k'yau d'aure a tsintsiyar hannunsa.
hummm dan k'yau kam dai yayishi, sai dai ni bawai ya birgeni bane😏 (ho Munaya banda zuk'i ta malli dai🤥🤣😝🙆🏻).
Janye idona nayi na maida kan gyaran gashina da nakeyi.
Shima baice uffanba ya wuce wajen frigate, fresh milk ya d'akko yatako gaban mirror inda nake zaune. a saman mirror ya ajiye kwalin madarar ya jingina bayansa shima, idonsa a kan gashina danake gyarawa. ya d'au madarar ya zuba a cup d'in daya d'akko tare da mik'omin.
“ni ba ita zan shaba”. na fad'a ba tare da na kalleshi ba.
“mikenan?”. shima yafad'a cikeda k'asaita.
Yanzunma ban kalleshi ba nace “tea”.
Kofin ya dire saman mirror yana tattare hannun rigarsa, “salon ki k'onamin idon abin cikin kwan kenan, to za6i ya rage naki, sha da arzik'i ko kuma d'ura”.
Babu shiri na d'auki kofin na kwankwad'e, dama iyayine inajin yunwar.
Kofin na mik'a masa ina 6ata fuska tamkar zan fasa ihu.
Ya d'agamin gira yana fad'in “taimakon kai my friend”.
Gefe nayi da fuskata ina fad'in “kai duk salon mugunta ka sani ai”.
“martabar gudan jinina nake karewa”. yay maganar yana k'ok'arin ficewa.
Baki na na ta6e ina harar bayansa, su gudan jini anji jiki kuwa.
Ganin zai fice nai saurin cewa “nifa inason zuwa kitso, kuma zan koma school”..
Tsayawa yay cak daga yunk'urin fitar da yakeyi, Batare daya juyoba yace “babu wannan tsarin a masarautar gagara badau”.
Yana gama fad'a ya ida ficewarsa.
Tamkar zan fasa kuka nayi jifa da cumb d'in hannu na ina fad'in “ina ruwana dawani tsarinku ni, makaranta ta nakeson komawa ehe”.
Yana jiyota amma ko'a jikinsa yaci gaba da k'ok'arin fitarsa hankali kwance.
★★★★★★★★★
Tunda Aryaan ya shigo da gudu inna ta tareshi tana fad'in “kai lafiya? minene na gudu?”.
“innarmu wlhy Uncle ne yace ki shirya mana kayanmu ni da Aiyaan zai aiko gobe a kaimu wajen Auntynmu”.
Inna tayi d'an murmushi kawai, dan ita bata d'auki maganarma serious ba.
Su dai su Aiyaan sunata murnarsu, sun tafi d'aki sun hau had'a kaya.
Babu dad'ewa da yin haka saiga daddy ya shigo da sallama, inna ta amsa masa tana gyara zama, shima zama yay kujerar dake kusada k'ofa, ganin haka inna ta fahimci da magana yazo, dan haka ta maida dukkan hankalinta Kansa.
Bayani yamata dalla-dalla akan zancen da su Galadima sukazo dashi, ya d'ora da fad'in “saiki shirya dan zamuje ai miki passport”.
Inna tace, “amma dadynsu nake ganin ai da kud'in kukaje kamar zaifi”.
Murmushi Dady yayi, yace “Ai'sha nasan miyasa kikeso zamewa, to ai kaf cikin matan yayan kece ya cancanta kije koda ace bawai Galadima ne ya biyaba, maganar ciwo Muke bawai jin dad'i ko gutsiri tsomar wasu ba, ki shirya dan zai turo wanda zamuje immigration office d'in”. daga haka ya tashi ya fice.
Shiru kawai inna tayi, itadai inda ta itace da antafi da ko innaro, dan tasan wannan tafiyar dukda ta ciwoce sai ta janyo 6acin rai a gidan.
Aiko tamkar inna tasani, dan ana fad'ama innaro tace “bata amince ba, ita ta haifi auwalu kuma da ita za'aje tayi jiyyar yaronta, bazata bama kowacce mace acikinsu wannan ragamarba.
Shiru baba k'arami da daddy sukayi, taci masifarta ta gama tayi shiru.
Baba k'arami yace, “amma dai inna kinsan jinyar Yaya sai da matarsa a kusa, kekuma k'arfinki ya k'are ya za'a d'ora miki d'awainiyar da matansa ne keda hakki a kai?”..
“yo d'awainiya ba tare da kai za'a tafiba? Kai basai kamasa ba. ni dai fa ban amince Ai'sha tajeba, dan wlhy bazan ta6a son Ai'sha ba komi zata zama, tunda dai ta silar jikokinane balle amin ilimi. k'ilama itace ta jefeshi dan taga ta kama k'asa 'yarta Na auren d'an Sarki, t........”.
“innaaaa! haba mana, dan ALLAH karma ki bari maganar nan ta fita, waishin minene laifin Ai'sha a gareki? duk cikin matanmu banga wadda take girmamaki da d'aukarki matsayin uwaba irinta, inna ya kamata wannan k'iyayyar ta koma soyayya hakanan, a baya kince dan basuda asali, kin dawo kince juya ce bata haihuwa, gashi kuma yanzu har ALLAH zai fidda jikoki daga tsatsonta, to miye kuma matsalar?”.
“toko zaka shak'eni Na fad'a makane Hameesu?”.
“a'a inna, ALLAH yabaki hak'uri”.
“kaidai ka Sani, ni yanzu bara Na tashi Na shirya Ku kaini inama kace, imagesa nema ko uwarmi oho”.
Daga Dady har baba k'arami babu Wanda ya tanka mata, tana shigewa baba k'arami ya mik'e yana cema dady “yaya ka jireta, bara naje mutafi da maman 'yan biyun, kota fito kace naje shiryawa ne”.
Kai Dady ya kad'a masa yana murmushi, baba k'arami ya fita da hanzari.
Bayan wasu mintuna saiga innaro an fito ana warware gyale za'a yafa, “yauwa jafaru muje Na shirya”.
Habiba dake kitchen tana girki duk diramar da ake tana saurare ta tuntsure da dariya, lallai tsohuwarnan akwai daru, mama Na hanya ai, itace maganinki (gwaggo Safiyya mamarsu).
Kallonta Dady yay yana murmushi, yace “to inna mu jira jafar d'in yaje shiryawa”.
“ato shikenan bara kafin ya dawo nad'anci abinci, k! Habiba zubomin idan abincin nan ya tsotse, gara Na fita cikina da d'an nauyi”.
Habiba ta had'iye dariyarta sannan tace “innaro bai tsotseba, amma nanda kamar dai minti 5”.
“babu damuwa ai, nasan jafaru ma bai dawoba harnaci, kinsan shi da dak'undar shiri, ya tsufa amma kullum kallon kansa yake sa'ar Abdul-hameedu”.
Dariya Dady ya had'iye da k'yar, yasa handkerchief yana toshe baki dan karta fito.
★★★★★★★★
Tsaf na kammala shiryawa sannan Na kimtsa d'akin, ni dukfa a nufina nayi shirin asibitine.
Fitowa nayi dan naga ko yana falone, wayam babu kowa, sai sallama da nakeji a bakin k'ofar, amasawa nayi na bada izinin shigowa saboda naji muryar matane.
Su 10 ciff suka shigo, k'asa suka zube suna gaisheni, Na amsa musu da 'yar sakewa, “lafiya dai?”.
“lafiya lau ranki ya dad'e, mune zamu kasance hadimanki, masu miki dukkan hidima.
Nifa wlhy banason wasu bayi, amma dolene Na barsu tunda wad'ancanma Galadima ne yace su tafi, yanzu kuma baya wajen, ni kuma banida ikon korarsu tinda bansan kan abinba.
Amsa musu nayi da “to” sannan nawuce Na zauna a kujera.
Tasowa sukai suka biyoni, a tsanake suka dinga fad'amin sunansu da aiyukan da zasuyi.
Wad'anda naga bazan iya yarda suyiba Na canja musu aiki. Sallamarsu nayi, Ina k'ok'arin tashi Na shige ciki saiga Sauban ya shigo, duk zubewa sukayi suna kwasar gaisuwa a gareshi, ya amsa musu yana wani yatsine face, sai kuma ya basu izinin tafiya, fita sukayi harabar sashenmu.
Na kalleshi ina murmushi, “ashe kaima dai sarautar Na jininka yaa Sauban? Wanda bai saniba saiya d'auka duk bazaka iya wani Abu daya shafi sarautaba”.
Dariya yayi yana zama, “aunty gimbiyar mu kenan, wannan ai sai mijinki”.
Nima murmushi nayi kawai.
Ya mik'omin kayan hannunsa yana fad'in “ga break fast d'inki”..
“wayyo yaa Sauban, nikam dai nagaji da ciye-ciyennan ma, zuwa zanyi Na fara abinci da kaina”.
“wlhy dakin taimakemu Aunty gimbiya, mijinki shiya saba da cin abincin waje shiyyasa bai damu ba, ya kamata kafin Na wuce gobe naci girkinki”.
“kamarya gobe? Kana nufin zaka koma kenan?”.
“tab da gudu kuwa, aini bazan iya zaman k'asarnanba Na tsawon lokaci, tarema zamu wuce da Abba ai, harma da innarmu, yaa Sam bai sanar dakeba kenan?”.
Baki bud'e Na girgiza masa kai alamar a'a.
Sauban yay murmushi, “kinsan halin Galadiman namu ai, soyake yamiki surprise maybe, yanzu hakane yaje cuku-cukun visa d'insu ne. waito miyasa bazamu koma tare da kubane?”.
Murmushin yak'e nayi, nace, “maybe akwai ayyukan dabai gamaba shiyyasa”.
“inaga hakanne kam, ni bara naje, yace Na iskeshi birnin gayu, ga mahfuz can Na jirana”.
“ok sai kun dawo” Na iya cewa, danni daga 'yan matan masarautar har samari ba kowa Na saniba, tunda time d'in daya kamata nad'an San mutane sai muka tafi India. ni bama nason Na saba da kowa, ni da ba zama ya kawoni ba.
Maganar fita da Abba da Galadima yakeyi sai yayta cin zuciyata, kimar Galadima da darajarsa saita cika zuciyata, inason mahaifana, kuma dukkan Wanda zai nuna musu kulawa bazan manta da shiba, harda 'Yar kwallata Na share, Na tashi Na koma bedroom ba tare da nayi break fast d'inba ma.
*****************************
Innaro dai tun ana jiran dawowar baba k'arami harta fara gyangyad'i, habiba data kammala abincin ta d'ebo ta kawo mata, nuni Dady yay mata akan ta koma.
Habiba ta koma da baya ba tare da ta k'araso falonba.
Tun tana gyangyad'i harta 6ingire a kujerar barci mai nauyi ya d'auketa (ho innaronmu ta mutunci🤸🏻♀😜).
Baba k'arami da innarsu munaya kam tuni sunyi ficewarsu, dayake Abu Na kud'i dandanan aka gama cuku-cukun komai, Nuren ne tsaye, saida komai ya daidaita suka samu visa d'insu a hannu sannan suka fito.
Har gida ya maidosu ya koma suna jera masa godiya da addu'a shi da Galadima.
Innaro daga gyangyad'in jiran abinci ya tsotse aka zarce da barci mai nauyi, shima Dady lalla6awa yay ya fito dan asibiti zaije.
Tafiyarsa babu dad'ewa saiga gwaggo Safiyya ta iso da yaranta biyu.
Hayaniyar su Dahiru ita ta tada innaro, ta mik'e zumbur tana fad'in “yauwa Jafaru kadawo mu tafi ko? Habiba bar abincin kawai idan muka dawo naci.
Mi Dahiru da Naja'atu zasu ba dariya ba, suka shiga shek'ama innaro dariyar shak'iyanci. Wai kota kwanta da yunwa ne.
Zaginsu ta hau yi ta d'auki filon kujera tana dukansu.
Sai da gwaggo Safiyya ta musu magana sannan suka nutsu, “inna ina zakuje da Jafaru ne?”.
Gyara zama innaro tayi tashiga bama gwaggo Safiyya labari.
Murmushi kawai gwaggo Safiyya tayi, danta gane wayo suka mata suka gudu kawai, itama sai tace “to inna ki cigaba da jiransu, k'ila dan sunga kina barcine suka jira ki tashi sannan Ku tafi.
Da wannan gwaggo Safiyya ta rufe bakin innaro ta zauna jiran su dady.
Aiki🤣🤣😝.
**********
Galadima daya fita kai tsaye asibiti ya nufa, su yaa hameed kawai ya iske can, dan dady ya hana matan gidan zuwa sai anjima, doctors Na complain akan suna cika wajen da yawa.
Cikin mutunta juna Galadima ya gaisa dasu yaa sabi'u sannan yashiga yaga daddy.
Yau kam Alhmdllh dan ba barci yakeba, kumbirin fuskarsa kuma yad'an sa6e kad'an, saidai baya iya magana sai dai yayta bin mutane da idanu.
Dukda bazai iya amsawa ba haka Galadima ya risinna ya gaidashi, tare da masa fatan samun lafiya sannan ya fita office d'in doctor.
Bayan sun gaisa doctor ya bama Galadima file d'in bayanan Abba dasuka tattara.
Kar6a Galadima yayi ya duba, dukda bawai ya fahimci bayanan bane, ( kusan dai rubutun doctors sai su). Suka d'an tattauna akan cigaban da aka samu sannan Galadima ya fito.
Ya iske daddy ya iso, suka gaisa sannan yamasa dukkan bayanan da doctor yamasa shima. Dady ma yaji dad'in cigaban da aka samu.
Galadima yay musu sallama ya fito.
Guntun tsaki yaja saboda yanda jama'a suka wani zuba masa idanu tamkar sunga magiji, da sauri wani dogari ya bud'e masa motar ya shiga, sannan suma suka shiga.
Daga asibiti Galadima yace su wuce birnin gayu plaza.
Cike da girmamawa sarkin mita ya amsa da to.
Maida kansa yayi jikin seat ya kwanta tareda lumshe idanu ya fad'a duniyar tunani................✍🏼
Barkanku da juma'a💋💋💋🤝🏻.
Musha weekend lafiya sisters⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀😄.
*_ALLAH ka gafartama iyayen mu_*🙏🏻😭
*_Typing📲_*
*_Haske writer's asso...._*💡
*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻
_________________________
_Duk marubucin daya kafa alk'alaminsa bisa takarda tabbas yagama tanadar yanda labarinsa zai kasance ne, amma sai wasu wabubuwan mamaki kaga sun gaza k'arewa a social Media, ban saniba ko samunmu available ne yakesa a kullum kuke mana kallon marasa aikinyi?, ni dai nasan time d'in dana shirya labarin RAINA KAMA ban zauna tebirin shawara da kowaba a online, inkuwa hakane tayaya wasu har suke tunanin nafara sauka akan layin labarin?, to magana d'aya zanyi a wannan ga6ar, ban gina labarin Raina kama akan kwanciyar aure bane, dan haka masu maganar munaya bata da aiki saima Galadima rashin kunya saisu jira saina kai k'arshen labarin kafin su k'alubalanceni, abin dariya, (wai aikina kenan daga nasa munaya ta murgud'a baki sai ta harari Galadima da masa k'unk'uni) tunda aikina kenan babu lallai wajen 6ata lokaci karantawa, haka Na tsara labarina tun farko kuma haka zanyi, duk wanda yaga bai masaba zai fara iya rubuta nashi shima kawai. wannan abun da kukema writer's yana 6ata mana rai, bai kamata ku dinga k'alubalantar writer's ba, bayan su suke da masaniyar yanda suka shirya labaransu, idanma zakuyi saiku ringa tanadar lokaci har zuwa bayan mun kammala, hakan zaifi tasiri fiyeda katsalandan a tsakkiyar labaran mu, akoda yaushe kuzama masu kula kafin Ku k'alubalanci mutum🤷🏻♀._
*Ba akan kaina kawai nayi wannan bayaninba, harda sauran writers da yawa da akema makamancin hakan koma fiye da nawa.🙅🏻*
_____________________________
~Book 2~ 👉🏻1⃣0⃣➖1⃣1⃣
...................Koda motocin suka tsaya sarkin mota ya bud'e masa k'ofa yakai tsawon lokaci baiko motsaba, saboda tsantsar tunani da zuciyarsa ta lula, aduk sanda zuciya take cikin matsanancin matsi gangar jiki ma gazawar karfin ikon jini dana 6argo sukan mata k'aranci, shi kansa yasan yanada buk'atar mataimaki a kan wannan lamarin, amma k'arancin rik'on amana Na d'an Adam ne yake yawan gargad'arsa da taka masa birki, ba kowane zai fahimci ma'anar nok'ewar tasaba, sai mutum daya tsinci kansa a makamancin halin da yake ciki.........
“Ranka ya dad'e mun iso”. Sarkin mota yasake fad'a cikin taraddadi da taka tsantsan.
A hankali Galadima ya bud'e idanunsa da suka koma launin jaa saboda damuwa a kan sarkin mota, batareda yace uffanba ya ziro k'afarsa k'asa yana cije lips da had'iye wani kududun damuwa a mak'oshi.
Tunda ya fito ma'aikatan wajen suketa masa sannu da zuwa, dan tunda ya shigo k'asar sai yanzu ne zai shiga cikin plaza d'in.
Hannu kawai yake iya d'aga musu, amma bakinsa yay masa nauyi, kallo d'aya kuma zaka masa ka nazarci damuwa da buk'atar hutun dake tartare da kuzarinsa.
A cikin plaza d'in ma bata sauyaba, d'aga hannu agaresu shine yazama linzamin amsa gaisuwar dasuke masa.
Da hannu yayma d'aya daga dogaransa nuni da amso masa key.
Da sauri dogarin ya amsa yana mai nufar sashen da zai kaishi office d'in Saleem mai kula da CCTV camera's.
Sai dai kafinma yakai ga k'arasawar suka had'u da saleem, Wanda tun shigowar motocin Galadima ya gansa.
Keys d'in ya damk'ama dogarin, sannan ya k'araso domin mik'a gaisuwa ga ogansa na wajen aiki kuma magajin garinsa.
Shima d'in dai hannu Galadima ya d'aga masa, hakan kuma ya saka Saleem fahimtar akwai damuwa kenan.
Koda aka bud'e ya shiga saiyayma dogaransa nuni da suje kawai, sannan ya maida idanunsa ya lumshe tareda kwanciya jikin kujerar yana lilawa a hankali.
Shi kansa baisan tsawon lokacin daya d'auka a hakanba, amma tabbas yasan yashiga kudin nazari mai zurfin gaske. Knocking d'in k'ofar da akayi yasakashi bud'ar baki da k'yar ya bada izin a shigo.
Nuren daya shigo ya maida k'ofar ya kulle, kafin ya ida takowa cikin office d'in, idonsa nakan d'an uwannasa.
Zama yay a d'aya daga kujerun dake fuskantar Galadima, “brother what happen?”.
“Northing”. Galadima ya fad'a batare da ya bud'e idonsa ba.
Shiru kawai Nuren yayi shima, ya d'akko laptop a briefcase d'in daya shigo da ita, kunnawa yay, kusan mintuna biyu ya d'ago ya kalli Galadima, sai kuma ya maida kansa ga laptop d'in. “Sameer nasan kaga cigiyar da akeyi takowacce kafar yad'a labarai ta k'asarnan akan d'iyar minister, sannan jami'an tsaro tsaye suke akan binciken inda take. yakamata musan abinyi kafin lokaci ya k'ure mana”.
Guntun murmushi Galadima yayi, batareda ya bud'e idanunsa ba yace “Nuren indai har babu wata waya datake aiki inda kakai yarinyarnan, kuma ka cire sim card d'in phone nata a lokacin daka d'auketa, to babu wata hanya dawani jami'in tsaro zai ganota, dama hanya d'ayace da kuskure zai basu damar bibiyarta, na d'aya lokacin daka d'auketa yazam wayarta na aiki, tabbas zasubi ta wannan hanyar su gano har iya inda ka kashe wayar, hanya ta biyu itace ka kashe wayarta baka cire sim card d'in ta ba daga phone nata, koda wayar a kashe take zasu bibiyeta ta hanyar 📡 su ganota” ya tashi zaune sosai yana bud'e idanunsa akan Nuren, “wannan hanyoyin biyu kawai ke garesu saikuma idan da camera tare da ita, idan duk babu wannan basuda wata hanya, ka kwantar da hankalinka my brother, komaina da tsarinsa right?”.
Murmushi Nuren yayi, kafin ya salute d'in Galadima yana fad'in “I thrust to you my dear broth”.
Shima galadima salute d'in Nuren d'in yayi yana murmushi.
Komawa yay ya sake kwanciya jikin kujerar, “yanzu inaga time d'in turama minister Massage yayi?”.
Cikin zaro idanu Nuren yace “baka kallon hakan a matsayin ganganci kuwa?”.
Baki Galadima yad'an ta6e yana crossing k'afarsa, cikeda izzarsa yace “sai idan nabama wani damar hakan ai”.
Nuren baice komaiba, dan yagama sanin hatsabibancin Galadima wajen iya sarrafa Computer, dan haka ya bar wannan zancen ya d'akko wani. “yauwa to maganar Malam Saminu fa? Kasan yana hannunmu fa har yanzu?”.
“wannan barsa saiya kuma magantuwa, dan da alama yasan wani Abu, saidai akwai abinda ya sakashi za6ar 6oyewa. ni yanzu damuwar 6atan Muftahu yafi damuna, nasaka camera's jikin mutane 10 danake iya zargi a masarauta amma banga alamun da hannun koda mutum d'aya ba, hakan ya tabbatar min da gaske Muftahu na bibiyar lamarina, sai dai bansan dalilinsa ba, ko kuma waye sakashi?”.
Nuren ya jinjina kansa, “brother aini da Harun dama mun dad'e da zargin Muftahu, Kaine kawai kake masa kallon mutumin kirki daman”.
Lips kawai Galadima ya cije, amma baice uffanba, Nuren yaci gaba da 'yan danne dannensa a laptop d'in, zuwa wasu mintuna batareda ya d'agoba yace, “maganar Sirikinka fa?”.
Shiru Galadima ya masa, saida ya mula dan kansa sannan ya murmusa tareda maida idonsa ya lumshe, “a daren jiya nagama da wannan matsalar, sim card d'insa 3, akwai Contact 300 da 38, mtn yanada mutum 172, ya fara saka credit a layin shekaru 15 kenan, ranar 3/6/2005, glo 107, ya fara amfani dashi shekaru 8 kenan, wad'annan sune Sim card d'insa da yake mu'amulla da kowa a ciki, kuma anfi saninsa da su, akwai 6oyayyen layinsa Na mtn shima, yafara aiki dashi shekaru 13 kenan, kuma mutane 59 ne kawai acikinsa, sannan ba kowane yasan layinba, dan dukkan family nashi basu San da zamansa ba, ita kanta mahaifiyar su Munaya batasan anyi saving number a phone nata ba, suma da suka kirata basusan da number a wayarta ba, dan baita6a kiranta da shiba, akwai matakan tsaro dake tattare da Layin, hakanne ya tabbatar min da akwai abinda yake 6oyewa a Sim card d'in, dan sai time to time yake amfani da shi, kiran matarsa da sukayi da layin wannan shine kuskuren farko da suka tafka da Sameer ya samu hanyar musu takun sauro. zan fara aiki akan layin na shigesu ta hanyar da basu zataba”.
Jinjina kai kawai Nuren yakeyi dan mamaki, Galadima da banne, kamar yanda basirarsa take daban, ya sauke ajiyar zuciya yana kama hannun Galadima da idonsa ke a lumshe har yanzun, cikin karsashi yace “lallai kai RAINA KAMA ne Sameer”.
Murmushi kawai Galadima yayi, amma baice uffanba.
Knocking akayi, Nuren ya kalli k'ofar yana bada izinin a shigo, Sauban ya shigo da sallama, su duka idonsu a kansa, Nuren yace “lafiya kuwa?”.
Zama Sauban yayi yana sauke Numfashi da k'yar, cikin magana d'ai-d'ai da alamar a birkice yake yace, “wlhy Yaya binmu aka ringayi da wata bak'ar Jeep, da k'yar mukasha wlhy, ni dai yau zanbar k'asarnan gaskiya”. Sauban ya fad'a tamkar zaiyi kuka’.
Gani kawai sukai Galadima yana dariya, saida yayi mai isarsa sannan ya tsagaita.
Nuren da Sauban suka tsaya kawai suna kallonsa.
Tashi yayi tsaye yana takawa cikin izzar k'asaita, ya dafa bango yana lek'en waje ta window d'in office d'in, yakai wasu adadin lokuta a wajen, sai kuma ya juyo yana kallon Nuren d'in da Sauban da suma suka zuba masa idanu.
“my dear brother! daka tsaya sun kamaka ai, tabbas da wannan shine kuskuren da zasuyi Wanda bazasu ta6a mantawa da waye Muhammad Sameer Saifudden ba a tarihin rayuwarsu. Waya gaya maka kana yawo cikin 9ja ne batareda idon Sameer ba a kanka?”.
Sauban ya sauke ajiyar zuciya yana share gumin daya jik'a fuskarsa, “wlhy yaa Sam daka fad'amin da bazan tsorata ba”.
Daga Galadima har Nuren dariya suka kwashe da shi, Nuren ya dafa kafad'ar Sauban yana fad'in “matsoracin banza”.
“uhm-uhm yaa Nuren bazaka ganeba wlhy, tsoro halak ne fa”..
Galadima dai baice komaiba ya koma ya zauna yana murmushi.
★)))*(((★)))*(((★)))*(((★)))*(((★
Ganin har anyi sallar Magriba babu baba k'arami balle Dady ya saka Innaro d'aukar gyale ta fito, lokacin gwaggo Safiyya tana salla, shiyyasa batasan innaro ta fitaba, habiba da Naja'atu dake tsakar gida suna tattare kaya saboda hadari na farkon damina dayake nuna alamar zai zubda ruwa. suka kalli juna, Naja'atu tace “yaya habiba tsohuwarnan fa bata da dama wlhy”.
Dariya habiba tayi, “ai kad'anma kika gani Naja'atu, yanzu dai zataje ta tadama baiwar ALLAH hankali”.
“to ALLAH ya k'yauta”. ‘cewar Naja'atu tana rik'e ha6a’.
Lokacin da Innaro ta shigo gidan d'akin Innarsu Munaya ta nufa kai tsaye, sai dai ta iskeshi rufe, kwala kiran sunanta ta shigayi cikin masifa, “Ai'sha!! Ai'sha!! Nasan kina jina, wlhy ki fito kafin yau d'innan igiyar aurenki ta tsinke”.
Mamansu yaa Hameed da gwaggon Haleematu ne suka fito, mamansu yaa hameed tace “aiko tafita fa inna, dan gab da magribar nan naga Fadeel ya shigo sun fita, bansan mike faruwa ba dai”.
“yaza'ayi kusan mike faruwa tunda anyi k'ulle-k'ullen munafunci, lallai jafaru, wai yau da kaine za'a muzantani hannun mak'iyana, to nikuma naga ta yanda Ai'sha zataje wata k'asa jiyyar Auwalu da raina”........ haka taita zuba banbamin masifa matan gida na saurarenta, daga daddy har baba k'arami suna gidan amma sukak'i fitowa. Jarabar Innaro ta saka kowa na gidan fahimtar mi ake ciki, nanfa hassada da bak'in ciki suka kume zukatansu, dukda kuwa sunsan tafiyar bata dad'i baceba, maman fauziyyace kawai hakan yamata dad'i, koba komai inna ta huta da cin zarafin Innaro koyayane.
Sai da Gwaggo Safiyya ta shigo tama Innaro magana sannan ta tafi gida, su matan gidanma sai yanzu suka San da zuwa gwaggo Safiyya d'in.
Amma sunso ace innarsu munaya na gida Innaro tayi wannan rashin mutuncin.
Hummm😕.
****************************
Bayan fitowar su Galadima daga birnin gayu, sun wuce gidane, Nuren kuma yakoma hotel d'in daya sauka.
Galadima kawai ne ya shiga sashensu, amma Sauban 6angaren mai martaba ya nufa neman yarima Mahfuz.
Munaya na zaune a falon farko tareda sabbin kuyanginta guda uku, (dan bata amince su shiga falonta ba, saita gama tantance su sannan) ba wani hira sukeyiba, d'ayace a cikinsu ke sak'a shine abin ya birge Munaya take kallo, tana kwance cikin doguwar kujera ne, yayinda su kuma su ke zaune a k'asan lallausan carpet d'in falon.
Dogarai biyune suka fara shigowa hannunsu d'auke da ledoji, sai kuma mai gayya mai aiki Galadima.
Da sauri bayin suka mik'e tsaye, saida ya ida shigowa sannan suka d'urk'ushe a k'asa suna kwasar gaisuwa.
A la66ansa ya amsa yana d'aga musu hannu, yayinda idanunsa ke kan munaya da itama ke satar kallonsa
Duk d'insu kowa janyewa yayi, yayinda bayin da dogaran suka fice bayan sunkai ledojin falon Galadima.
Baice da ita uffanba yafara takawa zai shige, tamkar mai tsoron fad'a tace, “sannu da zuwa”.
Ysayawa yayi cak, sannan ya juyo da kansa tamkar mai ciwon wuya ya kalleta, bata yarda sun kuma had'a idoba takuma fad'in “nagode sosai”.
“for what?”. ‘ya fad'a cikin isa’.
Shiru munaya tayi, ta kasa cewa komai.
Shima bai sake cewa komai ba ya taka ya shige abinsa.
Harara munaya ta raka bayansa da shi, sai kuma ta sauke numfashi tana tashi itama, bedroom d'inta ta koma, a saman sofa ta zauna tana dafe kai, sosai take buk'atar zuwa sake duba mahaifinta, amma ta kula Galadima bashida niyyar cemata taje, kai itako wannan wane irin abune haka? shi dama gidan Sarautar haka yake bakada 'yancin kanka?, komai saida k'a'ida. tun d'azu kuma take kiran number inna bata d'agaba, tadai kira baba k'arami da daddy sun gaisa ta tambayi jikin Abba, shine ma har suke kuma sanar mata k'ok'arin da galadiman keyi. tabbas hakan da yayi yasata jin farin ciki, koba komai tasan shi adaline, ko anan gaba ragamar shugabanci ta riskesa zaiyima na k'asa da shi adalci.
Galadima daya shiga tun a falo yafara k'ok'arin cire navy blue d'in jacket d'insa, ya wullata saman kujera, sassauta belt d'in yayi shima amma bai cireba, ya zauna cikin tsantsar nuna gajiya yana furzo iskar bakinsa, remote ya d'auka ya kunna tv, tamkar ya saita lokaci saiga hoton d'iyar minister mai amsa sunan Farhat ana nunawa, an saka 2.5 millions ga dukkan wanda ya kawota koya bada bayanan sirri akan wanda yasan wani Abu akan 6atanta.
Wani mugun tsaki Galadima yaja a zuciyarsa yana fad'in wawaye, saiku k'ara yakai 100millions ba 2 ba, idan ubanta ya shirya kawo kansa gareni nima a shirye nake nabashi shashashar 'yarsa mai zubin ta6arya, ya kashe TV d'in kawai ya mik'e ya shige ciki.
Ko ina fes da shi, yasan baida Matsala da Sauban a 6angaren tsafta dama. kayan jikinsa ya ida cirewa ya shiga wanka.
Bayan ya fito samu yay yad'an kwanta, dan ya samu Hutu kona 2hours ne, dan yanzu akayi sallar zuhur. aiko kwanciyarsa babu dad'ewa barci yay gaba dashi.
Munaya ta jawo wayarta da nufin kuma kiran inna, amma sai taga Ashe credit d'inta yama k'are, kanta ta dafe dan haushi, zuwa can tamik'e domin bin shawarar zuciyarta. turare ta kuma fesama jikinta ta d'auki gyale ta yafa.
Ta d'an dad'e a k'ofar d'akin tana tunanin idan kuma ta shiga hasashenta bai zama gaskiyaba ya kenan?, wata zuciya tace kije abinki k'ilama wanka yake.
Da sand'a na ida shiga tamkar wata 6arauniya, sai kuma na tuna ai yanada CCTV camera, nutsuwa nayi na daidaita kaina, na koma normal saboda tsaro. Ganin babu abinda naje nema d'in a falo saina zarce bedroom ina wani ciccijewa.
Mamaki ya kamani ganinsa kwance a kan gado yana shak'ar barci hankali kwance, hakan yamin dad'i kam.
Saida nabi ko'ina na bedroom d'in da kallo, ganin babu alamar akwai camera a nan saina ida shiga, wayoyinsa biyu na ajiye gefen filon dayake kwance, rabin hannun damarsa ma nakan d'aya ya d'ora cikin barci halan?.
Dole saina hau saman gadon, dan haka na tsaya tunanin yanda zanyi, banida wata mafita dan haka nahau a hankali, kai kace wata hawainiya ce.
Cikin rintse ido da cije la66a nakai hannu zan d'auki wayar d'aya.
Caraf aka rik'emin hannu, babu Shiri na bud'e idona zuciyata nawani tsitstsinkewa.
Fisgoni yayi na fad'o jikinsa, zafin danaji ya sakani sakin k'aramar k'ara.
Ya matseni a jikinsa batare da ya kula miya aikata ba. nikam jikina sai rawa yakeyi, tsorona karya d'auka ko cutar da shi zanyi ma........ maganarsa cikin yanayin barci ta Sani kallonsa.
Kad'an ya bud'e idonsa dake jajir, alamar da gaske barci yakeyi, muryarsa a sark'e irinta barci yace, “sata kika koma?”.
Baki na tunzuro ina marmar da idanu da suka cika da kwalla, nace “ALLAH ya kiyaye, arafa zanyi”.
Kuma matseni yayi har saida na rik'e hannunsa,, yace “wannan ba aro bane sata ce yalla6iya, dan haka dolene ki kar6i punishment”.
Jin ya ambaci punishment saina kuma rikicewa, nahau k'yarma ina rantse-rantae da matso kwallan idona.
Bai wani saurareni ba ya hau sumbatar wuyana, tureshi nafarayi amma saina gaza, dan haka na koma mintsini, shima a banza man kare😩.
Dukna d'auka wasa yakeyi kawai farfaganda Ce danna tsorata, amma saina tsinci ya fara sakin layi, iya yina da rok'o, yakushi, mintsini, ban samu ku6uta ba, saima salonsa yafara tasiri a kaina, nima nai luf harda k'ok'arin maida murtani. saida naji zai kama wata tashar nai azamar tsaidashi ta hanyar fad'in “please yalla6ai camera”.
Maganinki ai baby😝, su Galadima akwai bak'in wayo dai🤥😂, idan ta gaskiya za'abi ni banga abin punishment anan ba🤣, dama yadawo 'Yar matsalarsa dai tsautsayi ya kawo mai karanbani dason banza ta fad'a tarko😜🥳😆.
**********★********
Koda inna ta dawo saita had'ama su Aryaan kayansu, da nufin su koma wajen mamansu yaa hameed harta dawo.
Amma suka tibire akan bazasu jeba, su Uncle yace zaizo ya kaisu wajen Auntynsu.
Tun inna na lallashinsu harta kai ga mammakesu suka fara kuka, daga nan sukai barcin dole.
Bata fasa had'a kayanba, tagama tsaf ta d'auki akwatin zuwa d'akin mamansu yaa hameed.
Su Bintu kawai ta iske a falo suna kallo, Aminu ne yace “innar 'yan 2 ina zaki da daddare?”.
Murmushi inna tamasa tana fad'in “kayansu Aryaan ne Aminu........”
Bata gama rufe bakiba mamansu yaa hameed ta fito. ganin innarsu munubiya da kaya saita had'e fuska. Inna bata damuba tace “ga kayansu Aiyaan, saisu dawo nan da zama kafin na dawo”.
“to”. Kawai mamansu yaa hameed tace tana kauda kai gefe.
Ran inna ya sosu, amma sai batace komai ba ta ajiye ta fice jiki a sanyaye.
Da murnar Haneeff ya tashi zai d'au jakar yakai d'akinsu, amma sai Maman ta watsa masa harara. babu shiri ya koma ya zauna. Jakkar dai sai anan ta kwana, bata d'auka ba, bata bar 'ya'yanta sun d'auka ba saboda bak'incikin inna zataje jiyyar Abba ba itaba.
ALLAH ya k'yauta😡.
****************************
Dakatawa yay daga abinda yakeyi, ya bud'e idanu a hankali akan fuskata, murya k'asa-k'asa ya furta “camera?”.
Kaina na d'aga masa batareda na bud'e idoba.
Bai kuma cewa komai ba ya koma ya kwanta yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa, sai kuma ya cije lips yana gyara kwanciya da sake rungumeni kawai.
Idona na bud'e a tsorace, azatona zai cigaba ne, sainaga ba haka bane.
A cikin kunnene ya furta “barci please”.
Kallonsa nayi ta gefen ido sai naga idonsa a rufe, nima banida za6in daya wuce na rufe nawan, dan haka na lumshe kawai.
Ni sai barcin ya d'aukeni, amma shi ya k'auracema idonsa, mamakin furicina ya dami zuciyarsa, dama yadad'e yana zargin akwai camera a d'akin nan nasa, sai dai bawai ya tabbatar bane, kuma bai ta6a yunk'urin dubawa ba. da wad'annan tunanin ya cinye lokacin barcinsa har aka kwala kiran sallar la'asar.
Bud'e idanunsa yayi akan fuskata, yad'an tsuramin ido nawasu time's, sai yaga barcin yamin k'yau, kauda idonsa yayi cikeda basarwa, saikuma ya janyeni daga jikinsa yana yunk'urin tashi, hakanne ya sakani farkawar nima, na tashi da hanzarina ina gyara rigata, sai kuma na sauka na fice batareda nako waiwayoshi ba.
Bina yay da kallo harna fice sannan ya janye yana ta6e baki.
Ban kuma jin labarin Galadima ba har dare yayi, nafito wanka ina shirin barci ya shigo, yau dai babu laptop d'in kaddara, dagashi sai phone guda d'aya ma, yana sanye da kayan barci kalar gwaiduwar kwai masu duhu.
Zama yay a kujerar dake cikin d'akin, yayinda ni kuma na k'arasa saka hijjab d'in dana jawo, babu walwala ko alamar wasa kwata-kwata a face nashi, dan haka nima saina kama kaina.
cikin k'asaitarsa yace “muyi magana mana”.
Kallonsa na d'anyi, saikuma na amsa da “ina jinka”.
d'ago ido yay muka kalli juna, da ido yay min nuni da bakin gadon.
Ban musaba nazo na zauna, amma sai nayi k'asa da kaina ina wasa da zoben hannuna.
Maida kallonsa yayi ga zoben danake jujjuyawa, kusan mintuna 4 harna d'auka ya ma fasa maganar, na d'ago na kalleshi.
Ya kauda kai gefe yana fad'in, “waya fad'a miki da CCTV camera a d'akina?”.
Nima ban kalleshi ba na bashi amsa a tak'aice, “bakai ka saka kayarka ba danni?”.
Da mamaki ya kalleni, sai kuma ya kausasa muryarsa, “Munaayaa seriously nake miki magana!”.
nad'an razana, amma saina dake, nace “kana nufin bakasan da itaba?”.
“idan nasan da ita mizai sani aikata wani Abu na sirrina a d'akin”.
da mamaki na kalleshi domin tabbatarwa, tsantsar gaskiya na hanga a idonsa, dan haka na danna yatsun hannuna da k'arfi suka bada sautin “k'asss!, k'asan zuciyata na tunanin minene sirrin nasa?”.
Idonsa a kaina ko k'yaftawa bayayi, nima na d'ago mukaima juna kallon ido cikin ido, dukda tsorata danai da hango masifa cikinsu ban janyeba, nafara fad'in “tabbas naga camera a falonka, tana nan saitin hotonku kaidasu momma, inda flower d'in nan take, hakanne yasani zargin kai ka saka kayarka saboda tsaro”.
“hummm”. kawai yafad'a yana janye idanunsa, sai kuma ya taso ya dawo inda nake zaune, ganinai kawai ya rungumoni jikinsa, na waro idanu dan mamaki, shikuma ya lumshe nasa tareda sumbatar goshina a hankali, shigar sumbarce tasakani lumshe nawa idanun nima tareda k'ank'ameshi.
Cikin kunnena ya furta “i'm proud of you my friend”.
Da sauri na waro idanu ina kallonsa, saiya d'agamin gira d'aya yana wani miskilin murmushi, sannan ya tadani zaune shima ya tashi ya fita.
Baki da idanu da hanci duk na saki ina binsa da kallo, a k'asan raina ina tambayar mike damun guy d'innan ne wai?.
Banida mai bani amsa, dan haka na mik'e na cire hijjab d'in nai kwanciyata.
d'akinsa ya koma ya d'akko wani Abu kamar k'aramar ball🎱 ya ajiye saman table d'in gaban gadon, sannan ya manna wani dogon Abu a jikin 'Yar ball d'in, ya d'akko laptop d'insa ya kunna. shiru na kusan mintuna uku ya k'urama abinnan ido, zuwa can yafara wata k'aramar k'ara d'i! d'i! d'i!, sai kuma k'aramar danja ajikin abinda ya manna d'in shima tana kawo haske jaa da d'aukewa.
Murmushin takaici kawai yayi, a zuciyarsa yanama ALLAH godiya dabai ta6a kusantar Munaya a d'akin nanba. dan tabbas ga CCTV camera ya gani a d'akin, an sakatane can ta saman wardrobe, yanda ko alama hankalinsa bazai kaiba, baiyi yunk'urin cirewa ba, ya d'auki kayan aikinsa ya koma parlour, dan yaga itakuma tanan a ina take?. yanama shigowa tun'a k'ofar tsakanin bedroom da falon ya gani, baima k'arasaba ya koma ciki, kashe laptop d'in yayi ya d'auke k'aramar ball d'in ya 6oye.
Duk wannan hidimar da Galadima keyi Sauban na kwance bisa gadonsa yayi d'ai-d'ai yana kwasar barci.
Gyara masa bargo yayi saboda tasowar hadarin farkon damina da iska tafara kad'awa sanyi ya busa. daga nan ya kashe masa fitila ya fita zuwa d'akin Munaya.
Ita harma tayi barci, tana k'ank'ame da fillo saboda sanyin hadarin dake busawa, gadon ya hau tareda warware bargon ya lullu6a musu. dai-dai iska ta taso mai azabar k'arfi, a rikice Munaya ta juyo ta k'ank'amesa saboda tsorata.
Rik'eta yay sosai yana fad'in “uchh! Karki karyani”.
Babu shiri munaya ta bud'e idonta, tana k'ank'ame da shi tace, “wai miyasa bazaka ke kwana naka d'akinba ne?”.
“k miyasa time d'in da kikaje India kika gajemin d'akina?”.
Shiru tamasa bata amsaba, amma yanajin alamar murgud'a bakinta akan k'irjinsa.
“punishment ya tabbata agareki yalla6iya”.
Da sauri nace “wlhy a'a, inba hakaba zaka koma saman sofa ne, ai kaima haka kamin a d'akinka”.
“uyim Madan tsiwa, to ai nima dankar ki murk'ushemin abin cikin kwan cikin barci yasani kwantawa anan?”.
Zan bashi amsa aka kwad'a wata tsawa data sakamu ruk'unk'ume juna babu shiri, sai kuma ruwa ya 6alle.
Da wannan damar Galadima yay amfani wajen canja salon kwanciyar tamu, tun ina nuna banaso har salonsa ya sakani sakin layi, (😆anya munaya wannan cikin naki bashine tarkon da Galadima ya d'ana miki ba?😜).
Da asuba tashi nayi inata zum6ure-zum6ure, baice dani uffanba yashiga toilet ya tsarkake jikinsa. Bayan yafito nima na shiga.
Baki ya ta6e yana wani d'age gira d'aya tamkar ina kallonsa ya fice.
Saida nasha kukana sannan nayi wankan tsarki, narasa mike sakani biyema Galadima? insha ALLAH zan d'auki mataki (🤣idan babu abin cikin kwan ba😂, nasan inhar yana nan babansa zaita samun bonus😜).
Bayan na idar da sallar ban koma barciba, saina gyara d'akin nayi wanka, shirin fitarma na sake yi yau, dan baba k'arami yacemin k'arfe goma na safe zuwa 11 zasu tafi.
Kammalatawa kenan ya shigo, ko kad'an banji alamar shigowarsa ba, saida na gama fesa turare ina k'ok'arin ajiyewa na hango kamar mutum tsaye a bayana.
Da sauri nayi azamar juyowa, dayake yana gab dani kad'an ya rage na fad'a masa a jiki, na dai samu nad'anyi baya na jingina da mirror ina tura baki.
Ko motsi baiyiba shikam, bai kuma janye idonsa daga kallona da yakeba.
Haushi ya kamani, nima nabi jikin nawa da kallo kozanga abin da yake kallon, ganin babu wani Abu daya faru na d'ago na kuma kallonsa, “wai yalla6ai mi kake kallone haka?”.
d'an yatsansa d'aya yasaka yad'an shafi girarsa yana gyara tsayuwa, “abin cikin kwan mana”. ‘ya fad'a cikin basarwa’.
“ta gefensa na ra6a zan wuce ina fad'in “ai lokaci kad'an ya rage maka ka bar ganin nasa”.
Da sauri ya rik'o hannuna, na juyo muka kalli juna, mayun idanunsa ya saka cikin nawa, “kina zaton idan nabar ganinsa kema za'a cigaba da ganinki?”.
Guntun murmushi nayi ina janye idona daga cikin nasa, nace “kana zaton kasheni zakayi nima?”.
“cire maganar ma zato”.
Kallonsa na kuma yi, cikin yanayin da shi kansa bai ta6a zaton ina dashiba nace “saika fara shiri”.
Shima a dake yace “dama a shirye nake kullum”.
Na murmusa ina k'ok'arin cire hannuna daga cikin nasa, amma ya hanani damar hakan, kallonsa na kuma yi nace “ko har lokacin yayi ne?”.
Fisgoni yayi na koma da baya, ya mannani jikin mirror d'in tare da maida hannuna baya ya rik'e, ya matseni da jikinsa, fuskarsa gab da tawa tamkar zai had'a bakinmu, yayinda idonsa ke cikin nawa, wani miskilin murmushin gefen baki yayi, yasaka yatsansa yana zagaya janbakin dake kan la66ana a hankali, cikin muryarnan tasa mai kama da an masa dole ya fara magana cikin karsashi “ko Ubangiji yakanyi hukuncine ga bawan daya bijirema umarninsa, koda ace zubarda wannan cikin kikayi dolene saikin kuma d'aukar wani, zubar da shi na dai-dai da haihuwar yara goma anan gidan kafin na aikaki inda shima ya tafi” ya matsa la66ana da k'arfi, wani zafi ya ratsani saiga hawaye a kumatuna, murmushi yayi, yasaki la66an ya dangwali hawayen a d'an yatsansa, nunamin yay yana fad'in “lallai momcyn abin cikin kwan kin cancanta 100%, amma bayan abin cikin kwanfa akwai k'annensa, please bar kuka my dear friend”. ‘ya k'are maganar da sumbatar la66ana sannan ya sakeni yaja baya.
Koda ya sakeni sainayi murmushi kawai, sannan na juya ina fuskantar mirror, foda na d'auka na gyara fuskata, na sake saka jambaki kad'an kamar yanda na saka d'azun.
Tsayawa yay cikeda mamakin abin da nayi na ko inkula yana kallona, mi wannan yarinyar take shiryawa ne haka?.....
Kafin ya samu amsa Na juyo gareshi, fuskata d'auke da murmushi na ra6a zan wuce sa, bina kawai yay da kallo, naje gaban wardrobe na bud'e, alk'yabba na d'akko na sanya, sannan na d'auki handbag ina kallonsa har yanzu fuskata d'auke da murmushi.
Gira ya d'agamin shima yana wani k'asaitaccen murmushi, ya juya ya fita batareda yakuma magana ba.
Yana fita na sauke ajiyar zuciya ina dafe k'irji, wlhy ni kad'ai nasan dukan da zuciyata takeyi, kad'an yarage ya ranfo a tsorace nake, kalamansa ne suka shiga dawomin cikin zuciyata, mi wannan yake nufine wai..........?
“Shin bazaki bane?”.
Muryarsa ta daki dodon kunnena, da sauri na gyara yanayina na d'ago muka had'a ido, Ashe yana bakin k'ofar bai tafiba.
Bance komai ba na biyo bayansa.
A falon farko na iske kuyangina suna gaidashi, hannu kawai ya d'aga musu ya fice abinsa.
Tsayawa nayi muka gaisa, d'aya a cikinsu ta yunk'urin k'ar6ar handbag d'ina.
Na iske harya shiga mota, nima aka bud'emin na shiga, handbag d'ina ta mik'omin tana fad'in “ranki ya dad'e ana buk'atar rakkiyarmu ne?”.
Murmushi namata, na juya na kalli Galadima danjin mizaice, kansa ya girgiza alamar a'a.
Juyawa nima nayi na girgiza mata kai, tamana addu'a tana rufe k'ofar.
Tunda muka tafi babu wanda yace uffan, yanata latsa wayarsa.
Airport muka nufa kai tsaye.
Bayan motocin sun tsaya sarkin mota na yunk'urin fita yace “2 minutes ”.
Sarikin mota yace “to ranka ya dad'e”.
Ni ban fahimci mi suke nufiba, naga dai sarkin mota ya fita mukuma ba'a bud'e mana ba, sai kawai nakai hannu zan bud'e.
Hannuna ya rik'o, na juyo ina kallonsa, har Yanzu idonsa nakan waya,, ajiye wayar yayi ya juyo yana fuskantata, ina yunk'urin tambayar lafiya naji la66ana cikin bakinsa.
Ya salam, na fad'a a zuciyata, saida ya shanye janbakin la66ana tas sannan ya sakeni. yanda kukasan gunki haka na koma masa, ya buga yatsunsa biyu saitin fuskata suna bada k'arar d'as d'as yace “gargad'i, first and last dazanganshi abakinki yayin fita”.
Harya fita ban iya motsawa ba, saida aka bud'e murfin 6angaren danake sannan na iya sauke numfashi, na kasa fahimtar damuwar guy d'innan kwata-kwata. fita nayi nima, yana tsaye yana jiran fitowata. a tare muka jera muna tafiya, yayinda dogaransa ke take mana baya. ya wani miskile fuska tamkar bashine yagama ta6argaza ba a mota yanzun.
Mutane sai kallonmu suke, masu gulma nayi masu nunamu nayi, ni dai duk sainaji wani iri, shima tsaki yayi danya tsani kallo.
A mamaki na duk sai naga 'yan gidanmu ma a wajen, gaggaisawa muka shigayi, muka rik'e hannun juna nida munubiya muka k'arasa inda innarmu take, gaisheta nayi, nace “su Aiyaan fa?”.
“suna gida zasu zauna da mamanku mana”.
“kai innarmu, ya zaki barsu wajen muguwarnan, bama gara Maman fauziyya ba komu suzo wajenmu”.
Murmushi kawai innarmu tayi, tace, “ashe bazaki canjaba Munaya?”.
6ata fuska nayi, ina fad'in “kai inna, duk canjawarnan danayi”.
Murmushi sukayi itada Munubiya. akuma dai-dai time d'in Ambulance ta shigo airport d'in, sai mota biyu a bayanta sai motar police guda d'aya.
Gaba d'ayanmu hankalinmu saiya koma can, Galadima ya k'arasa wajen Ambulance d'in, yayinda sauran motocin biyu Sauban da Nuren baba k'arami Dady ya Shafi'u da yaa Naseer yaa hameed suka fito.
Zuwansu baifi da mintuna 15 ba aka fara kiran sunan wad'anda zasu tashi a jirgin.
Sai kuma ma'aikatan wajen mutum uku suka iso wajen Ambulance d'in aka fara k'ok'arin fidda Abba. Hankalin jama'a da yawa ya tashi a airport d'in nan saboda tausayin Abba, mukam kuka ma wasunmu sukeyi ai, muna kallo aka gungura gadon da aka d'oroshi har zuwa ga jirgin.
Suma su innarmu suka shiga itada baba k'arami da Sauban.
Rungume juna mukayi nida munubiya muma muna kuka.
Galadima bai fito cikin jirginba saida yaga komai ya dai-daita. yana fitowa babu dad'ewa jirgin ya d'aga zuwa sararin samaniya, yayinda mukuma muke binsu da addu'oin fatan alkairi da samun sauk'i.................✍🏼
🤥kutt harda na gobe nayi🙄⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_typing📲_*
💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._*
*_♦RAINA KAMA.....!!♦_*
_(Kaga gayya)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
~Book 2~ 👉🏻1⃣2⃣
...............Maman Fauziyya tamatso ta kama hannunmu ni da Munubiya tana lallashinmu, da fad'a mana mu bisa da addu'a, insha ALLAHU da k'afarsa zai dawo.
Ganin mun fara shirin tafiya na taka inda Galadima yake tsaye da Nuren suna magana, tun d'anzun ina lura dashi ya kafeni da idanu, yanzunma suna maganar amma idonsa na kaina na k'araso garesu.
Nuren daketa fara'a yace, “gimbiyarmu barka da hantsi”.
Murmushi nayi sannan na gaisheshi, ya amsa yana tambayata yaya jikina?.
Nace “Alhmdllh na warke ai”.
“to ALLAH ya k'ara afuwa gimbiya”. ‘yafad'a yana matsawa gefe domin bamu waje.
Galadima dake kallona hannunsa duk biyu cikin wandon sky blue d'in shaddarsa da tsawon rigar iyakarsa rabin cinyarsa, yace, “Lafiya?”.
Dakewa nima nayi, cike da jan ajina nace “k'alau. Dan ALLAH zanbi Munubiya please yalla6ai”.
Janye idanunsa yayi daga kaina yana fad'in “awane farashi?”.
“kamarya farashi? ciniki mukeyi?”.
Hannunsa d'aya ya fiddo daga aljihu ya shafa sajensa zuwa gemu, cikin kafeni da idanu yace “kusan haka, kinsan rayuwar bani gishiri in baka manda akeyi yanzun”.
Cikin son tura masa haushi nace “Ai ni bana gane Hausa cikin hausa”.
“really? lallai kin fad'o kuwa, kuma saiki ce ke bahaushiyace?”.
Baki na tunzura masa saboda haushin rainin wayon da yake min, gasu Munubiya kuma shirin tafiya sukeyi.
“Kinsan wannan bakin kika bari na kamashi a airport d'innan....., hummm”.
Idanuna na waro, “mi kake tunanin zakayi kenan?”.
“kuma turowa saina nuna miki”. ‘yafad'a yana matsowa’..
Baya na matsa da sauri zuciyata na harbawa, anya kan Galadima d'aya kuwa?.
Kwafa yayi yana kallon agogon hannunsa yana k'ok'arin zaro waya daga aljihun gaban rigar datake ring.
Nikuma na hararesa a zuciyata ina fad'in mara kunya ai nasan zaka iya. A fili kuma nace “please yalla6ai nidai badan halina ba”.
Bai bani amsaba, sai sallamar danaji yayi wayarsa akan kunne.
Jinai kawai yace, “Harun kana inane?”.
Bansan wace amsa ya bashiba, naji yana fad'in “ok idan ka tashi saimu had'u”. daga haka ya yanke wayar sannan ya kalleni.
“uhm mikike cewa?”
Haushi tamkar zai karni nace “please mana autan Momma”.
Murmushi yayi yana cije lips, “wlhy yarinyarnan kin gama rainani, ninema Autan?”.
“lah nama manta ashe kaifa na tsakkiyar momma ne, karma Yaa Sauban ya jini”.
“kinsan ALLAH na damk'eki a airport d'innan saikin fad'amin dawa kike”.
Dariya nayi ina d'aga masa yatsu biyu, “karka damu yalla6ai zanyo maka tsarabar sweet and biscuit yeah”.
Da sauri yay yunk'urin damk'o hannuna ganin zan gudu. yana rik'owa mukaji ance “hallo”. A bayanmu.
Batareda ya saki hannuna ba duk muka waiga ni da shi.
Matashiyar budurwa fara k'al, kuma k'yak'yk'yawa masha ALLAH.
Dan danan ya tsuke fuska, tamkar ba shine yagama murmushiba yanzun.
Nima bansan murmushi ya gushema tawa fuskarba, baiyi magana ba, sai nice nace “lafiya kuwa?”. yanda nayi maganar cikin rainin hankali yasaka yarinyar rik'e ha6a tana ta6e baki tana fad'in “ke kuma fa?”.
Kamar zanyi magana saikuma Na shareta kawai, galadima Na kalla fuskata a cunkushe alamar fushi, d'ayan hannunsa ya d'agamin yana ta6e fuska alamar shifa babu ruwansa.
Na tura baki tareda juyawa zan bar wajen.
Hannuna dake cikin nasa ya kuma damk'ewa da k'yau, hakan yasani dawowa baya tamkar zan fad'a jikinsa, amma nayi jarumtar tirjewa kodan jama'ar gidanmu.
Dama ajikin wasu motoci muke, sai kawai ya fisgi hannuna muka shige tsakkiyarsu ya mannani jikin mota shikuma yamin rumfa. ban ankaraba naji bawan ALLAHnnan ya ha.......🤥.
Jikina kawai rawa yakamayi saboda tsoro, wlhy ban ta6a tunanin da gaske yake zai iya hukunta bakin nawa a airport d'inba.
Ita kanta budurwarnan idanu ta zaro waje cikin wangale baki.
Nuren dashi kad'ai yake saitin dazai iya ganinmu saikuma wasu tsirarun mutane dake nesa damu, wad'anda ba lallaine ma su fahimci abinda akeba, kaucewa kawai yay daga wajen yana tuntsura dariya.
'Yan gidanmu sunga lokacin da Galadima yaja hannuna muka shige tsakkiyar motocin, amma basa hangomu. tsabar gulma irinta mamansu Yaa Hameed da Momy da Maman Safara'u sai suna shiga k'ok'arin son ganin mi mukeyi a wajen?😱 su duk tunaninsu wata maganar banza nama budurwarnan yake shukamin rashin mutunci Dan duk agaban idonsu tazo wajen har rik'omin hannu da yayi, dukda basa jin mi Muke fad'a Dan muna nesa dasune.
Yaa Sabi'u dabasu lura da abinda ke faruwa ba suka Shiga musu maganar INA zasuje? suzo su ajiyesu gida sufa wajen aiki zasuje.
Ina basu saurareshiba saida sukazo saitin dazasu iya ganinmu.
A tare suka zaro idanu, Baki da hanci, duk sun shiga mamakin ganin Galadima Na kissing d'ina, ai babu shirin suka koma baya zukatansu Na tukuk'i da jifanmu da kalmar 'yan iska fitsararru.
(🤣Yo wayace kuje gani? kazantar dabaka ganiba sunanta tsafta😏😜).
Yana Sakina kunya tasakani fad'awa k'irjinsa Na 6oye fuskata, hannayensa yasaka ya zagaye bayana yana dallama yarinyarnan wata muguwar harara data saka hanjin cikinta kad'awa, babu shirin tabar wajen tana mak'yark'yata da tunanin Galadima ko dai kurmane da gaske.
Driver d'inta dake kallon komai tun d'azun ya tuntsure da dariya yana fad'in ALLAH ya k'ara, bana fad'a miki Shiba Na wasan yara bane ba, banda jaraba kinbi kin nanik'ema bawan ALLAH daga had'uwa a jirgi, kinbi kin addabi rayuwata saina nemo miki number sa, aini nama godema ALLAH da kuma sake had'uwa ya kuma nuna miki ainahin halinsa, saida Na fad'a miki baima dad'e dayin aureba, ke gadararriya kikace aurensa bai damekiba........
Yanda ta daka masa tsawa yasakashi firgita ya russuna yana Neman afuwarta.
Cikeda masifa tace “tada mota mukoma gida”.
“Amma ma'am kin manta jirginku yakusa tashi?”. A tsorace yayi maganar.
Harara ta Dalla masa tace “Ubanka ne ya viyamin kud'in jirgin”.
Wasu yawu masu rad'ad'i driver ya had'iye yana girgiza mata kai, ya bud'e motar ta Shiga sannan ya rufe shima ya zagaya mazauninsa suka koma Inda suka fito😜.
Nasan dai kun fahimci yarinyarnan Ce da suka zauna waje d'aya a jirgi itada Galadima randa zaizo😆🥳.
Ganin tabar wajen Galadima yay murmushi sannan yafara k'ok'arin d'agoni daga k'irjinsa, ban yarda mun had'a idoba na bar wajen.
“Saikin dawo” ya fad'a a hankali.
Kasa daurewa nayi saida Na waigo Dan tabbatar da shine yay maganar kokuwa dai wanine?. Ido muka had'a ya janye nasa cikeda basarwa yana la6e baki.
Nima harara Na watsa masa ina barin wajen.
Tunda Na taho Maman safara'u da mamansu Yaa hameed da Momy suka zubamin ido.
Nikuma fahimtar kallon k'urillar da sukemin saina canja salon tafiya da kuma had'e fuska na nufi zuwa wajen gungun yaran gidanmu masu aure dasuke hira.
Suma duk kallona sukayi, namusu murmushi ina fad'in “lallai munada cin ragunan suna kwannan nan ashe”.
Dariya duk sukayi, Fiddausi tace “yariman namu shikuma da kwad'ayin naman suna yazo?”.
Harara Na zuba mata ina kai mata bugu ta waske itama tana dariya, yayinda su Munubiya ke tayata.
Mun gaggaisa tareda tambayar lafiyar juna, muka d'an ta6a hira kad'an da alk'awarin duk zanje mu gaisa, suma sukace zasuzo tunda ba yanzu zan koma ba. daga nan mukai shirin tafiya, Siyama da Zarah anata mana iyayi su masu motar hawa, (dayake kowacce a motarta tazo).
Ni dai ni da Munubiya Yaa Marwan ya d'aukemu muka tafi.
____________________________
Tunda nabar wajen Nuren yazo ya tasa Galadima da tsiya, wai dama haka yake ashe?, rashin kunyar tasa har agaban surukai?.
Banza Galadima yamasa yay shigewarsa mota yabarsa yana iskancinsa.
Anan suka tafi suka barsa dayake da mota yazo shima.
Galadima na barin airport gidanmu ya nufa shima.
A lokacin 'yan gidanmu suma sun Isa gida, sunata k'ananun magana akan abinda Galadima da munaya sukayi, dan saida suka bama sauran labari, nanfa suka kacame da zancen harda k'arin k'arya akai wai ba kiss kawai sukaiba ('yan gidansu munaya annamimatu🙆🏻😂).
Itadai Maman Fauziyya batace k'alaba, saima dariya da zancen ke bata, Dady kuma bai dawo gidanba, daga nan wajen aiki ya wuce, yaran gidan ma kowa gidanta ta koma basu biyo nanba. Innaro da gwaggo Safiyya kam gida suka shige ana saukesu, dan haka basuji komaiba.
Galadima bai shiga gidan ba, saiya nemi iso gidan Innaro, Habiba ta fito tamasa jagora.
Innaro na falo tana cika da batsewa gwaggo Safiyya na lalla6ata akan ta kwantar da hankalinta.
Koda Galadima ya shigo innaro sai antaya masa harara takeyi, yana kula da ita ta gefen ido, ya murmusa yana zama saman kujera, cikeda tsokana yace “Sweet Granny Yaya dai?”.
Harara innaro ta zuba masa sosai, tana fad'in mikuma kazo min nan?”.
Galadima ya murmusa yana maida hankalinsa ga gwaggo Safiyya, gaisheta yayi ta amsa masa cike da kulawa, sannan ta d'ora da godiya da kwarara masa addu'ar fatan alkairi.
Yaji dad'i sosai, ya amsa cikin fara'a, sannan yace, “Granny ina furar tsufa?”.
“ai bazaka shata ba ”.
Nanma murmushin Galadima yayi yana mamakin wannan rikitacciyar tsohuwa. Yace “tunda bazan shaba Ashe kema kuwa bak'yaje India ba”.
Zabura innaro tayi, ta maida hankalinta ga Galadima tana fad'in “da gaske kake ko shak'iyancine?”.
Mi su Naja'atu zasuyi inba dariya ba, Galadima ma handkerchief ya saka ya rufe bakinsa kawai. Gwaggo Safiyya kanta saida ta dara.
Galadima ya gyara zamansa yana fad'in “karki damu Granny ninmu, insha ALLAH tare dake zamu tafi idan zamu koma”.
Dad'i ya kama innaro ta shiga sakama Galadima albarka.
Shidai murmushi kawai yakeyi. saida yaga sun nutsu sannan yace yazo tafiya dasu Aiyaan ne, babu musu innaro ta mik'e da kanta zuwa gidan danta kawo masa su.
Bayan fitarta gwaggo Safiyya tabama Galadima hak'uri akan darun innaro.
“karki damu gwaggo, ai dama kowa yasan idan sunkai irin wannan age d'in saida lalla6awa, ALLAH dai yaja mana ransu”.
Amin gwaggo Safiyya tafad'a cikin jin dad'i.
Tunda 'yan gidansu Munaya sukaji wai Galadima ne da kansa yazo tafiya dasu Aryaan sai zukatansu suka kuma tunzura, kowa tana ganin hakan salon munafurcine, Maman Fauziyya ta kawoma innaro su, dama suna d'akinta, dan mamansu yaa hameed suna dawowa ta d'auki jakkarsu Aiyaan ta kaimata, wai sai dai su zauna wajenta ita d'akinta babu fili.
Maman Fauziyya batace komai ba ta kar6i su Aiyaan tana jinjina bak'in hali irinnan jama'ar gidan.
Amma kuma yanzu sai gasu sune dajin haushi.
Ita dai innaro ko'a kanta ta jawo hannunsu Zainab ta d'akko jakkar kayansu suka taho.
Koda sukazo ma sai Galadima yace abar kayan nasu su kad'ai yake buk'ata. ya ajiyema Gwaggo Safiyya da innaro alkairi ya fito rik'e da hannun su Aiyaan daketa murna.
Innaro har wajen mota ta rakosu, bata komaba saida taga tafiyarsu. tana komawa gida tahau had'a kayan tafiya, wai gara ta had'a ta huta, duk randa Galadima yazo sai tafiya kawai.
Ita dai gwaggo Safiyya dariya kawai tayi, dan maganar Galadima gaskiyace, lamarin innaro yana buk'atar uziri, ta tsufa sosai, kawai dai ALLAH yabata lafiyane, dan da wuya kaga innaro na kukan wani waje namata ciwo irin na tsufa. (masifarta kam dai kunsan ance abinda kayi a k'uruciya shi kake maimaitawa lokacin tsufa, ALLAH ka azurtamu da k'yak'yk'yawar k'uruciya to🤦🏻♀).
★★★★)(★)(★★★★
A k'ofar sabon matsakaicin gidan motocin biyu suka tsaya, cikin wad'anda suke a motar baya d'aya ya fito ya bud'e motar farko, hamshak'iyar macece mai ji da mulki da kud'i ta fito, kallo d'aya zaka mata ka tabbatar tagama samun duniya, cikin tsantsar tink'aho da homa take zuk'ar iska tareda taku d'ai-d'ai irin na manyan mata.
Cikin sauri aka bud'e mata k'ofar gidan ta shiga guard d'inta na take mata baya.
A tsakkiyar tsakar gidan taja tunga, sai hura hanci takeyi tana harare-harare.
d'aya a cikin guards nata yace, “ ma'am nan shine d'akin da yake”.
Batace uffanba taci gaba da takawa d'ai-dai har zuwa k'ofar d'akin, hannu ta d'aga musu alamar su dakata. Dukkansu baya sukaja domin cika umarninta.
Zaune yake a kujera an d'ad'd'aureshi, kallo d'aya zaka masa ka tabbatar a galabaice yake.
Shigowarta baisa ya d'aga kai ba balle ya motsa, yasan dai bazai wuce k'artan dasuka kawosa wajen baneba. sai dai jin k'amshin turaren mace yabashi mamaki, hakanne ya sakashi d'ago idanu domin tabbatar da yaren hancinsa.
Bakinsa na rawa yace, “Wacece ke?”.
Bata bashi amsaba, saima kujera data ja irin wadda yake kai ta dinning ta zauna, k'afa d'aya ta d'ora akan d'aya tana wani cika da batsewa. “yaro baka isa sanin ni wacece ba, Sai dai cigaba da 6atamin aiki zai sakaka sanina”.
Murmushi Muftahu yayi, ya d'ago idanunsa yana mata kallon rainin wayo, “Saninki dama aikin banzane a gareni, aikin ki kuma da kike ik'irarin ina 6atawa duk da ban sanshi ba, kisa a ranki yanzu ne na fara 6atawa, saiki shirya nunamin ke d'in wacece?”.
“hahaha, yaro baisan wutaba saiya taka”.
“Humm, wuta bata san yaroba saisu k'ulla”.
“karan farauta yaushe uban gidan naka yafara koya maka irin izzarsa haka?”.
“Kinsan zama da mad'aukin kanwa aishi ke kawo farin kai”.
“lallai zan had'a da kanwar da mad'aukin nata duk na koyar dasu darasi. Shi kansa Sameer d'in baikai darajar karen gidana ba balle kai yaronsa”.
Murmushi Muftahu yayi, “ Uhmm sai yanzu na fahimta, sai dai zan tunatar dake abinda kika manta, Wanda kikeyi danshi baima San da zamanki ba, kinga ashe ihu kikeyi bayan hari..........”.
“hhhhhhhh! Abin dariya, inbai fahimta ba ai zai fahimta lokacinda sak'on sunana da gawarka suka isa a gareshi, yanda ban haifi magajin masarautar gagara badauba, zeenah bata isa haihuwar magajinta ba wlhy”.
Idanu Muftahu ya tsura mata, sai yanzu yafara hango kamannin d'aya daga matan tsohon Sarki Abie da suka bar masarauta bayan shekaru biyu da fara jinyarsa, bashida wayau a time d'in, Dan dagasu har Galadima bazasu wuce 7-7 year's ba, saida suntaso sunji labarin bijirewar matan a lokacin da za'a tafi da Abie India, dama shekaru biyun da suka zauna basu ta6a saka hannu a jiyarsa ba, sai Momma keta fama...........
Marin da aka zuba masane ya sakashi dawowa daga dogon tunanin daya tafi....
“tunanin mi kakeyi Karen farauta?”.
Jajayen idanunsa ya zuba mata, sai kuma ya kwashe da dariya, saida yayi mai isarsa sannan ya dakata tareda tsuke fuska, “ina tunano mummunan fuskarkine, in banda abinki miye na kishi da abinda kika bari da kanki? nasan dai Momma ba itace ta hanaki haihuwa ba ai, inason kisan ni ban isa kare Galadima ba dama, amma kulum cikin kariyar Wanda ya haliccesa yake, a tunaninki 6ata sunansa da kikayine ke nufin bazai mulki masarauta mai d'unbin tarihi da girmaba? kinyi kuskure babba wlhy, Dan kinsaka kanki a ramin damisa. duk ranarda Galadima ya gane kece kika saka amasa 6atanci a jarida wlhy saikinyi nadamar rayuwarki..........
Bayan Hannu tasaka ta bugi bakinsa, gefe yay da kansa yana murmushi, ga jini na zuba a gefen bakin, dayake hannunsa a d'ure suke.
Tace, “kafin ni nayi nadamar kai ne da shi zakuyi, Dan yanda kake a tarkona shima yanacan a cikinsa, wawa kawai, kai aboki mai gaskiya ko? zan shayar dakai mamaki, domin saikaga gawar Sameer a gabanka kwance kafin kaima kabishi baya”.
Dawo da kallonsa yayi gareta yana murmushi, “miyasa kika tsorata tunban k'arasaba, Galadima maruci ne, kuma kainuwane, gashi dakalin majina, kina hawansa zamewa zakiyi wlhy, ina tausaya miki yayinda tunaninsa ya waiwayo kanki, Dan yanzu aikin manyanki ne a gabansa ba nakiba, d'ana masa tarkonki kuwa tamakar kin tado damisane daga barci, hakan kuma fitinace babba a gareki da shi kansa Karen farautar taki Harun, tirrr da zuciyarki, ni kaina danasan ma kece bazan 6ata lokacina wajen bibiyar ki ta hanyar Harun ba, amma banyi bak'in cikiba, ko babu komai na ribantu da abubuwa masu yawa, domin ta silar hakan na had'a auren sunna, gashi harda ribar ciki, magajin Galadima Sameer kenan.......
A fusace ta d'aga kofin glass zata kwala masa.
Yace, “relax relax mana giwar mata, ai bangama fad'aba OK?” ba kince zaki kawomin gawar Galadima ba sannan, to miye kuma na fusata haka da wuri?, ni ina kuma tabbatar miki indai Galadima ne zaizo, daga lokacinda yasan ina nan tabbas zai zo, banza karyar farautar wasu, na tabbata k'arya kikeyi ba aikin kanki kikeba kema, sakaki akayi, lallai ke farashinki ya fad'i k'asa, matar sarki mai fad'a aji irin Sarki Saifudden Ce ta k'are ahaka? Abin kaico abin jaje, tirrr”.
Dariya ta kwashe da shi tana tafa hannaye, saikuma ta matsa gabda Muftahu tana magana cikin kunnensa “lallai bayan Sameer akwai magajin sa a gagara badau ashe?”.
“oh sai yanzu kika fahimta ashe?”.
“karen Sameer zaka mutu kaida uban gidan ka, saina saka wannan zuciyar tasa ta buga wannan shine k'udirina”.
“hhhhhhh abin dariya, kudirin wasu dai, danke naki bamai muhimmanci baneba, tunda kuka kasa saka zuciyar Sameer bugawa a lokacin da k'uruciya da rashin sanin kansa ke damunsa, miyasa kuke tunanin zata buga a lokacin da yagama tanadar makaman yak'insa, ranar shiga filin daga kawai yake jira, nagaji da tattaunawa dake please”.
“kaima kace wani Abu yaro, Dan haka mu zuba, kwana uku kawai zakaga gawar Sameer a gabanka!!!!!”.
Bata jira yabata amsaba ta fice daga d'akin, tareda jan k'ofa da k'arfi.
Idanunsa kawai ya rintse. Baya tsoron makircinta, amma yana tsoron na Harun, dan Galadima ya rigada ya yarda da Harun 100%, bazai ta6a kawo zai cutar da Shiba. Waige-waige yashiga yi, yasan babu wani abunda Galadima zai iya bibiya tare dashi.
Da sauri ya girgiza hannunsa saboda tunowa da agogo, jin agogon tare dashi ya sakashi lumshe ido yana ambatar Alhamllh. Matsala d'ayace baya ganin agogon, saboda hannunsa yana a baya ne. Amma dukda haka zai gwada idan za'a dace.
___________________________
Yau na kasance cikin farin ciki, saboda gani tsakkiyar 'yan uwana, dukda ma zazza6ine mai zafi ke nuk'urk'usata, amma kewarsu ta hanani gajiyawa, mun bud'e babin fira a tsakkiyar falon mama Rabi'a, duk abinda akayi bana nan shine ake labarta min, yayinda Nima nake basu labarin India da nuna musu hotuna.
Haka mu kai wannan yini cikin farin ciki da annashuwar kasancewa da junanmu, musamman ma ni da 'Yar uwar tagwaicina da k'addarar aure ta tilasta mana nisantar juna, ji muke tamkar mun shekara ba'a tareba. Kowannenmu k'ok'arin ganin farin cikin d'an uwansa yakeyi.
_____________
Tunda Galadima yabaro gida dasu Aryaan saiya wuce wajen wani hutawa dasu, ya yawata dasu sunata farinciki, yayinda shi kuma yake biyema shirmensu dan d'auke musu kewar mahaifiyarsu, yana son yara, shiyyasa ko yaushe Khaleel d'in aunty Mimi zakigansa manne dashi, sa'annin Khaleel dasu Aiyaan kuwa zai iya zuwa d'aya.
Cikin lokacin k'ank'ani suka saki jikinsu dashi.
Daga nan plaza ya nufa, haka kawai zuciyarsa keta tsikara masa zancen 6atan Muftahu, dukda k'ok'arin wofantar da lamarin da lamarin da ya keyi.
Waya ya d'auka ya shige danne-danne, alamu sun nuna masa wayar Muftahu na cikin masarauta, kenan bai d'auki wayarba, yad'an murmusa kawai yana cije lips, yayinda idonsa ke kansu Aiyaan da Saleem yazo d'auka suje wajensa danya huta.
Bye suka masa, shima ya d'aga musu hannu yana murmushi.
Suna ficewa ya sauke ajiyar zuciya tare da mik'ewa tsaye. zagayen office d'in ya farayi hannunsa goye a baya, a wannan karon bazai ta6a k'yale Muftahu ba, dolene yayi wani Abu akansa, dama yana d'aga masa k'afane domin son ganin gudun ruwansa kawai, yanzu kuma lokacin yayi dazai San mi yake k'ullawa...........✍🏼
*_Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, cakwakiyar network tasani clearing charts d'ina batareda na dubaba, tun around 3:47pm nayi posting amma yak'i tahowa._*
Dan haka ina gayyata kowa gobe a court, zamu shiga shari'a ni da network ne🙄.
Wad'anda suka ga basa ganin posting d'ina gaba d'aya a satinnan duk aikin network ne🙄.
*_ALLAH ya gafartama iyayenmhiyayenmu😭🙏🏻_*
*_typing📲_*
💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._*
*_♦RAINA KAMA.....!!♦_*
_(Kaga gayya)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
~Book 2~ 👉🏻1⃣3⃣
...............Muna tsaka da hira saiga Aunty salamah tazo, daga ni har Munubiya da Ayusher rungumeta mukayi.
Cikin tsokana ta ture Munubiya da Ayusher tana fad'in “ku matsamin, kullum Ku ina ganinku, kewar gambo nakeyi”.
Gwalo na shiga yi musu, mama Rabi'a da Feena namana dariya.
Bayan mun zauna Aunty Salamah ta shiga yaba canjawar danayi tanamin shak'iyanci, nanfa su Munubiya ma suka samu abinyi, sosai suka tasoni gaba sai mama Rabi'a ke kareni.
Can muna tsaka da hira takamo hannuna tana fad'in “zo nabaki wani sirri nan autana”.
Mik'ewa mukayi inamasu Ayusher gwalo, yayinda suma suka tubure basu yardaba sai an bada sirrin dasu. da k'yar muka samu muka shige d'aki muka kulle.
A bakin gado muka zauna Aunty slamah ta sauke ajiyar zuciya tana kamo hannuna cikin nata, serious nima na zama na maida hankalina gareta.
Tace, “Munaya! Aiki yatafi yanda ya kamata, saidaifa labarin ya canja daga yanda kike zato, Muftahu ba munafuki baneba”.
A matuk'ar razane naja baya ina ture hannunta daga cikin nawa, “Aunty kinsan mi kike fad'a kuwa? Anya yaranki Muftahu suka kama?”.
Hannuna ta kamo tana murmushi, kinga zauna, shiyyasa na saka aka d'auki komai dan kema ki gani da idonki”.
Zaman nayi kuwa, ita kuma tayi 'yan latse-latsenta a iPad d'inta ta mik'omin. kar6a nayi cikeda fargaba, da kaina nayi playing d'in video n, tun daga fitowar Aunty salmah daga mota har shiganta cikin gidan zuwa shigarta d'akin, tsayarwa nayi na kalli Aunty ina dariya, “kai Auntynmu kinfa iya Acting wlhy, wanifa saiya d'auka da gaske irin mugayen hamshak'an matan nanne”.
Dariya Aunty Salamah tayi, “wlhy koni dai nayi mamakin dakewata, bakiga sai wani hura hanci nakeba, sukuma su Ameer saikace guards d'in irin manyan mutanan nan”.
Dariya mukayi, sannan nakuma playing na cigaba da kallo.
Shigar Aunty Salamah d'akin da tattaunawarsu da Muftahu. gaba d'aya jikina yayi sanyi, zuciyata sai wani tsitstsinkewa takeyi, idona cike da kwalla nace, “anya gaskiya Muftahu yake fad'a Aunty Salamah?, wlhy da gaske fa shine ya saka mana desire tablets, inhar bada wata manufaba miyasa yay haka?, kumafa ni banta6a ganin wani alamar rashin gaskiya ba ajikin Harun”.
Murmushi Aunty Salamah ta yi, ta dafa kafad'ata tana fad'in, “Munaya mugu bashida kama, Ai Muftahu baisan nid'in ba matar sarkin bace ta gaske, mizaisa ya za6i 6oyemin? yanda yanuna akan k'yamar matar sarkin tabbas akwai mai mugun hali a cikin su da gaske, kinga ai kince bakiga fuskar wanda kika kama yana wayarnanba a bayan window d'inki randa kuka iso”.
“Eh hakane, ban ganiba, maganganun kawai naji”.
“to kin gani, kifa tuna kuma firar da kika ta6aji Galadima nayi a asibiti shida aunty Mimi. wad'annan alamomin sun nuna akwai wata a cikin matan Sarki dakeda hannu a ciki, maganar Harun kuma idanu zamu saka masa tamkar yanda mukaima Muftahu, dan ayanzu idan mun saki Muftahu zakiga sun cigaba da takun sak'ar datafi ta da zafi, dan nariga da nasaka rud'ani a zuciyar Muftahu cewar zamu kashe galadima, tabbas ta wannan hanyar Harun zaizo hannunmu. Maganar Galadima kuma har yanzu karki fara kwantar masa da kai, dan kwantar da kanki zai d'arsa masa rashin aiminci a kanki, ke dai kinsan halin mijinki ai yanzu, kinkuma fi kowa sanin yanda yakamata ki cigaba da tafiya da shi”.
Insha ALLAH Aunty zan cigaba da k'ok'ari nakuma gode da gudunmawarki akanmu, sai dai akwai matsala, dan na lura agogon hannun Muftahu kamar akwai wani sirri a cikinsa, dolene a daren yau a fitar da Muftahu daga gidanan, zanma sarkin mota bayanin yanda zai taimakeku a maidashi masarauta kamar yanda yaymana aikin d'akkoshi, shima Galadima zansa ido akansa saboda tsuntsune shi nai azabar wayo”.
“Hakan yayi Munaya, ALLAH ya cigaba da bamu nasara, insha ALLAH zamu gano komai, ALLAH dai yabama Abba lafiya, yasa mu fahimci komai cikin sauk'i, akan Galadima kuma kici gaba da k'ok'arin da kikeyi Fiyeda da, dan dolene saimun samu had'in kansa kafin musan komai, ALLAH ya ku6tar damu baki d'aya, dan kina dai ganin yanda suka maida Abba”.
Hawayen da suka ziraromin a kumatu na share, cikin Murmushin k'arfin hali nace, “insha ALLAH Aunty Salamah, domin raina da farin cikina fansane akan mahaifina, kuma zuwa yanzu Auren Contract bai damuna, sai dai bazan 6oye mikiba aunty Salamah wannan cikin shine damuwata a yanzu, inaji ina gain zan haifishi na barsa inda yafi k'arfina, bansan wace rayuwa zaiyiba a wannan gidan da kowa zuciyarsa takeda k'arancin imani, Aunty Salamah gidan sarauta tsantsar matsalace kawai, bazaki fahimci hakaba saikin tsinci kanki a ciki, Aunty dan ALLAH ki amince na zuba da cikinnan”.
“munaya waishin miyasa bakida hankaline? to idan baki saniba wannan cikin shine zai zamemiki tsanin mallakar cimma nasara, kuma ta hanyarsane kawai zamu samu had'inkan Galadima domin fidda Abba daga wannan matsalan da Ku kanku ahalinsa, kina tsammanin koda Abba mutuwa yay masu farautar rayuwarsa zasu barku Ku6utane? Dolene saisun samu abinda suke nema koda ace dukkan gidanku zai k'are, bak'ya tunanin aurenku yana cikin abinda yakuma hasala zukatansu, a zatonsu Abbanki yasamu damar had'a kan mijinkine, ya ina jinjinama fik'irarki ke da munubiya kuma zaki 6ata shirin, karma ki bari 'Yar uwarki taji maganar zubda cikinnan, wlhy zaku samu Matsala ne babu ruwana”.
Munaya ta share hawayenta, “shikenan Aunty Salamah nabar maganar insha ALLAH. Amma a yaran nan masu mana aiki bak'ya tsoron wani yaci amanarmu?”.
“komai zai iya faruwa, domin amana tayi k'aranci a rayuwa, tunda yau gashi Harun yafito cikin masu cin dunduniyar Galadima, amma ki kwantar da hankalinki, su duka ukunnan da kike gani amintattunane, kuma Saleem ya saka mana idanu sosai a kansu”.
“to Alhmdllh aunty, ALLAH kamana jagora”.
“amin dai, saikima Munubiya dukkan bayanin da mukayi, ki bata itama ta gani, zuwa gobe zan aiko Bilkisu ta kar6a min, kuma ki fad'a mata yakamata ta koma gidan ta, dan gaskiya aiki bazai cigaba da yuwuwaba tana gidannan, saboda kinga ba ita kad'ai baceba, yanzu haka randa zaku zo da zamu kama Muftahu wlhy nasha wahala wajen nemanta naji kokin iso? dan ta tabbatar min inhar kin iso k'asarnan saitaji a jikinta, amma naita kiranta batayi picking ba, ashe wai wayar na hannun Feena”.
murmushi nayi nace, “sorry sweet auntynmu, insha ALLAH zata koma gobe”.
“shikenan, bara na wuce to”.
“to Aunty ngd sosai, ALLAH ya bada ladan zuminci, ammafa gaskiya kinci zalin muftahu da yawa”.
Dariya tayi sosai, “kibari kawai, nima wlhy ina marinsa tausayinsa Na ratsani, insha ALLAH zan nemi yafiyarsa zuwa nan gaba, ALLAH yasa ya yafemin dai”.
“hhhh zai yafe miki aunty ai duk cikin aikine”.
Mun rakota har tsakar gida, su Munubiya na tsokanarmu wai nad'an sammusu sirrin suma.
Daga ni har aunty Salamah dariya mukayi kawai.
Bayan dawowarmu na turama Munubiya massage akan taje tagani itama.
Sai da taja wasu times sannan tamik'e tana fad'in bara tad'an watsa ruwa. duk muka amsa da to saita fito.
**************************
Su Abba sun isa lafiya, anzo da motar Ambulance d'in asibiti aka d'auki Abba, yayinda Sauban da baba k'arami da inna khumar yazo d'aukarsu su kuma.
Inna da baba k'arami sai baza ido suke suna kallon gari.
Gida suka wuce kai tsaye, yayinda aka wuce da Abba hospital shikuma.
Sun iske jakadiya a gidan, dandanan aka shirya musu abinci, itadai inna sai jinjina k'yawun wannan gida take, yanzu anan gidan jininta ta rayu?. shi kansa baba k'arami ya yaba, Yakuma k'ara tabbatar da manyan k'asarmu Na hutawarsu.
**************************
Babu yanda Muftahu baiyiba dan ya sarrafa agogon hannunsa amma hakan ya gagara, Dan bak'aramin d'auri ya shaba.
Kusan gab da magriba Wanda ke kawo masa abinci ya shigo, ajiye kular abincin yayi sannan ya matsa kusada muftahu zai kwanceshi, cikin murya k'asa-k'asa kamar mai rad'a yace “yalla6ai inhar zaka biyani wlhy zan ku6tar dakai”.
Kallonsa Muftahu yayi sosai nawasu mintuna, “ka tabbatar?”.
“wlhy Oga da gaske nakeyi, Dan wannan matar da kake gani bata wasa bace, duk abinda ta fad'a zata iya aikatashi wlhy”.
Murmushi Muftahu yayi, yace, “nawa kake buk'atar Na baka?”.
“tab aini Oga dubu 100 ma ta wadatar”.
Muftahu yakuma Murmusawa, “zan baka 200”.
Da sauri yaron yaja baya cikin razana, “oga dubu 200 fa? Yo ai sai a d'auka nafara yankan kaine”.
Sosai abin yabama Muftahu dariya, Dan haka ya dara, yo dubu 200 a wajensa ai bata wuce ta siyen agogo ko takalma ba, amma shine shi yake ganin 200k a matsayin wasu kud'in da har za'a iya d'auka yayi yankan kai.
Kallonsa yayi yana murmushi, “karka damu to, amaimakon nabaka kud'in a hannu a zargeka mizai hana Na bud'e maka wata Sana'a da zakabar wannan aikin da kakeyi yanzu”.
“to ai Oga karkaje kasa a kamani wataran, nikuma inhar zan samu Sana'a to zan nutsu”.
“haba abokina, ya zakamin rana nikuma Na maka dare, karka damu kaidai ka aminta dani kawai”.
“to Na amince, yau sai k'arfe 11 zan kawo maka abincin dare, a time d'in sauran sun fita club, insha ALLAH nikuma zan dawo baya nace Na manta da abincinka, daga nan saina ku6tar dakai, sukuma na sanar dasu Na dawo ban gankaba”.
“shikenan babu damuwa, idan zaka dawo kazo da account number, dana koma zan maka transfer insha ALLAH”.
“to Oga Na gode sosai”. Ya fad'a cike da d'oki.
Murmushi kawai Muftahu yayi.
“yauwa Oga bara Na kwanceka kaci abincin to”.
Girgiza kai Muftahu yayi, yace, “a'a ka barsa kawai, banajin ci, in kanaso d'auka kaci kawai”..
“amma Oga ai.......”.
Kai Muftahu ya girgiza masa alamar karyace komai.
Shiru yaron yayi ya d'auki kular ya fice kawai, Muftahu kuma ya bishi da kallo.
**************************
Har akayi isha'i Galadima yana birnin gayu, saida aka kira sallar magriba ne yafita zuwa massalacin dake plaza d'in yay salla tare da ma'aikatan wajen masu salla, daga nan ya gaggaisa da makwaftan wajen dakan zo masallacin yin salla suma, bai fitoba saida akayi sallar isha'i. daga nan yacema saleem yaje dasu Aryaan su za6i dukkan abinda sukeso ya mik'a mass ATM d'insa, shikuma ya kuma shiga office ya kulle kansa ya d'ora tunaninsa daga inda ya tsaya.
Ya dad'e yana zagaye office d'in, yayinda zuciyarsa ke k'ulawa da kwancewa, agogon hannunsa ya kalla, ganin time yayi nisa yasashi furzar da huci, kayansa ya tattaro ya fito, dogaransa duk suka mik'e, suna gaisheshi, amsawa ya shigayi tamkar baya so.
d'aya aciki yace, “zamu tafine ranka ya dad'e?”.
Kansa ya jinjina masa alamar eh, sannan yace “ama saleem magana”.
Da sauri suka amsa da to.
Ficewa yayi, sauran dogaran sukabi bayansa. Mota aka bud'e masa ya shiga, za'a rufe murfin ya hana, idonsa akan k'ofar plaza d'in harsu Aiyaan suka fito tare da saleem, dogarai biyu d'auke da manyan ledoji.
Suna hangoshi suka k'arasa da gudu, murmushi yayi ya d'aukesu d'ai-d'ai da kansa ya saka a motar, sannan aka rufe musu k'ofar.
Sudai dogaransa sai mamakin yanda yake sakema su Aryaan sukeyi.
Har sun fara tafiya ya fad'ama sarkin mota suje zasu taho da Munaya.
A ladabce sarkin mota ya amsa da to.
*****************
Muna tsaka da hirarmu aka kira wayata, sharewa nayi tamkar bazan amsaba, Munubiya ta harareni, ramawa nayi nima sannan Na d'aga.
Ciki-ciki nayi sallama, ya amsa daga can, mamaki ya kamani danjin muryar Galadima, katseni yayi da fad'in “ki fito”. Bai jira cewata ba ya yanke wayar.
Kamar zanyi kuka haka naji, Yaa Marwan ya fito daga d'aki yana saka rigarsa, kallona yayi yana fad'in “k ba jiranki akeba ne?”.
Sai da Na kumbura baki sannan Na mik'e. shikuma ya fice.
Da taimakon feena Na had'a komaina, har abubuwan da mama Rabi'a ta bani, sannan suka rakoni. Mun iske Yaa marwan tsaye jikin motan ya dafa k'ofar suna magana da Galadima dake ciki bai fitoba.
Dogari d'aya ya zagaya ya bud'emin, ido muka had'a da Galadima Na janye da sauri, shima janyewa yay ya maida hankalinsa ga Yaa marwan dake masa magana.
Mamaki ya kamani ganin su Aiyaan, suma cikeda d'oki suka fad'amin a jiki suna dariya da fad'in “Auntynmu!”.
Juyowa Galadima yay yana kallonmu, shima Yaa marwan yay dariya kawai, sannan ya rufe mana murfin yanama Galadima sai da safe.
Su Aryaan sun kacame da bani labari, yayinda nikuma naketa musu dariya da biye musu, mamaki ya kama Galadima, bai ta6a tunanin ina magana hakaba, ya lafe jikin seat yana kallonmu cikeda birgewa.
Nikam nama manta ko gaisheshi banyiba, saida yay gyaran murya sannan Na d'ago Na kallesa, murmushi namasa ina fad'in “yalla6ai barka da dare”.
Shima wani miskilin murmushi ya min yana d'agamin hannu batareda yayi magana ba.
Aiyaan yay saurin fad'a “auntynmu bafa yalla6ai sunansa ba, sunansa Uncle”.
Kamar zan harari yaron sai kuma nad'an murmusa ina kallon Galadima dake kallonmu shima. janye idona nayi daga gareshi Na cema Aryaan to naji zanke fad'a.
Har muka kai gida basu barmu mun hutaba, sai surutu suke da bani labarin abinda yafaru a gida bana nan, danaji zasu kauce hanya kuma sainai saurin waskewa.
★★*★*★★*★*★★
Sarkin mota yana ajiye su munaya ya duba gefen seat d'in data zauna, takarda ya gani ya d'auka, dan sanda zasu shige tamasa wata inkiya da hannu.
Dubawa yay yaga mita rubuta. Sallama yayma sauran 'yan uwansa sallama akan zai shiga gida.
Daga nan ba gidan ya shigaba, saiyay dabarar da yabar masarautar gaba d'aya.
Sun had'u da Saleem a inda suka shirya, saleem Ya bama sarkin mota handkerchief d'in da zasu shak'ama Muftahu.
Sarkin mota ma yaje ya bama Ameer ne, daga nan ya dawo k'ofar fada amma k'aramar k'ofa tacan baya inda keda k'arancin tsaro.
Agaban idonsa su Ameer suka sauke Muftahu a mashin yana cikin yanayin barci saboda abinda suka shak'a masa, saida ya tabbatar sunbar wajen sannan shima ya koma ciki.
Yau dai kam ni kad'ai Na kwanta a d'akina, Galadima ko lek'e bai lek'oba, yana can tare da su Aiyaan a d'akinsa.
Nima kawai saina kira Momma mukasha hirarmu, tana bani labarin yanda jikin Abie yaketa k'yau a tsakaninnan, dukda kar yanzu maganar bata fita amma yakanyi bamai tsawoba, naji dad'i sosai, na masa addau'a mai tsawo tareda fatan alkairi, daga nan muka cigaba da tattaunawa akan maganar Abbana, da zancen su innarmu dasuka k'i yarda su zauna a gidan, innarmu ta dage bazata zaunaba tunda muma anan muke, saida Momma ta saka baki da mata bayanin da zata gamsu sannan ta amince zata zauna. Nasha dariya, dan dama nasan za'ayi hakan, innarmu kawai kunya da kawaici.
Daga nan har muka dawo kan ta Muftahu, dayake tasan komai a kai, da taimakonta nima nake samun k'arfin gwuywa.
Itama tasha mamakin jin Harun a lamarin, ta dad'e tana jinjina maganar nan. ta bama Samha muka d'ora da hira, saida naga time yaja ga zazza6in fama ya rufeni, sallama mukayi nai addu'a Na kwanta.
Masu iya magana since sabo tirken wawa, saina kasa barcin, naji kawai ina kewar Galadima.
Shima kansa yanacan sai juye-juye yakeyi, yakasa barci, bayan sun gama hirarsu dasu Aryaan yay musu shirin barci da kansa suka kwanta, aiki yad'an ta6a yana Neman dabaru akan binciko Muftahu, baiwani dad'eba ya kwanta shima, amma saiya kasa barci, juye-juye yaytayi agadon, ganindai da gaske ya kasa barcinne saiya mik'e yana jan guntun tsaki, kwanciya ya gyarama su Aryaan ya lullu6esu da bargo sannan ya fito da nufin wai zai duba munaya 🤣😜.
Jin shigowarsa yasani k'ara lafewa tamkar nayi barci, ya kunna fitilar d'akin yana kallona, yaja wani dogon lokaci sannan ya kashe ya tako zuwa gadon, “nasan idonki biyu ai, dama kin tashi kinbar wani kumshe-kumshe”.
Shiru nayi nakumak'i motsawa.
Kwanciya yayi a gefena, yaja bargon shima ya lullu6a, tareda juyamin baya, yace “miya hanaki barcine?”.
“farkawa nayi”. Na fad'a batareda ba kalleshi ba.
Murmushi yayi yana fad'inn “ Hummm”.
Daga nan duk mukayi shiru nawani lokaci, kamar an matse bakina nace “yalla6ai na tambayeka please? ”.
Yace, “Uhmm”.
Juyowa nayi ina fuskantar bayansa, a nutse nace, “wai dan ALLAH ina sauran matan Abie yanzu?”.
Da sauri naga ya juyo gareni, ni harma tsoro ya kamani nai baya da sauri, nazata makeni zaiyi, amma sainaji ba hakaba, yace “Munaya mi kika sani a kaina ne?”.
“yalla6ai kamarya mina sani a kanka? daga tambaya?”.
Yace, “Humm yana matsowa gareni, zan matsa ya rik'o hannuna................✍🏼
Kuyi manage da wannan please🤦🏻♀
0 comments:
Post a Comment