_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!._*
👉🏻1⃣
*Matsanan cigar* hayaniyar dake tashi agidan ce taja hankalina, cikeda bak'in ciki natashi daga barcin safen dana koma, fitinar gidanmu dabance data kowane family House dana Sani kona ta6a jin labarinsa a rayuwata, haka gidan namu yake kullum tamkar kasuwar 'yan danbe, daga matan gidan zuwa 'yan mata da yara tamkar muna ganin hanjin juna, saika rantse badaga tsatso d'aya muka fitoba.
Kururuwar danaji maman Safara'u ta kurma yasani kuma jan dogon tsaki, sai kuma najiyo muryar gwaggon haleema Na fad'in “kai amma wannan lamari baiyi dad'iba, kekuwa maman biyu ya kamata ki canja wannan halin naki, dan tabbas inba wani abu kikayiba babu yanda za'ayi yaronan Sadeequ yadage shi cikinsu *MUNAYA* yakeso, duka yaushe aka gama maganar nan akan shafi'u amma shine zaki koma kan Sadeequ kuma yanzu?”.
gaba nane ya fad'i, cikin zaro idanu waje nace, “ashema mu akanmu fitinar take yau?”. yink'urin sakko nake daga gadon Munubiya tashigo tana share kwalla, binta nayi da kallo harta fad'a saman gadon ta kwanta rufda ciki tareda fashewa da kuka mai ban tausayi. Hakan Yakuma tabbatar min lallai mud'inne dai ake hargowar akanmu. a fusace Na dirgo daga gadon na nufi k'ofar fita, (ko kad'an banida hak'uri, musamman akan cin zarafin mahaifiyarmu da akeyi agidan lokuta da dama idan irin hakan ta taso), taku biyu nayi naji an damk'oni, najiyo cikin masifa dan nasan Munubiya ce.
“wlhy ki sakeni kafin nafara huce haushina akanki munu! yau saina gyarama kowacce 'yar iskar mata zama agidannan dan kutu.....
Bankai ga k'arasawa ba Munubiya tai saurin rufe bakina da tafin hannunta.
Kici-kicin kwacewa nafarayi amma nakasa, dan bak'aramin ruk'o taminba, raina yak'ara 6aci ainun danjin irin rashin kunyar da Safara'u ke zubama innarmu a tsakar gida, bansan na wancakalar da Munubiya gefe ba nafice da gudu.
Babu Wanda yaga fitowata sai dai saukar sautin marin dana zubama Safara'u a farar fuskarta sukaji.
Hakan yaja gidan yay tsit na wucin gadi, sai kuma hayaniya takuma 6allewa, Safara'u da mamarsu sukayo kaina danufin duka....
Tsawar da baba k'arami ya bugace tasaka kowa dakatawa tsakanin ni dasu, hakama matan gidan sai suka fara jan k'afafu danufin barin wajen.
A tsawace yace, “kar wadda tabar wajen!!”.
Tsitt kakeji gidan yayi, tamkar bashi bane d'azun ya cakud'e da hayaniya tamkar ana biki ko suna.
Jarabar gidanmu ba bak'on Abu bane a anguwarmu, danta rigada tazama tamkar ajininmu take (yo ajininmu mana zance) tunda kullumne babu fashi sai anyi hayaniya, kodai matan gidan kokuma mu 'ya'yan gidan. Babu mai d'agama wani k'afa koda na second d'ayane kuwa, yanzun zakaji gidan shiru, anjima k'ad'an kaji an doka gangar shaid'an, musamman ma fad'an yara dayafi komai saurin had'a fad'an matan gidan da a kulum, a rana sai ayi fad'a biyar akan yara kawai, innarmu ce kawai da Maman Fauziyya keda k'ok'arin K'aucewa irin wannan fitintunun dasuka zama tamkar shan ruwa acikin gidanmu.
Baba k'arami yafara fad'a tamkar zai ari baki, inda yake shiga bata nan yake fitaba, kowa yayi tsit yana saurarensa, (saboda kasancewar masifaffe shima) sai da yayi mai isarsa sannan yajuya yafita yana fad'in nida Safara'u mu sameshi falonsa. harda iyayenmu mata.
Duk abinnan da akeyi innarmu na kicin tana had'a Karin kumallon safe, kuma kalma d'aya bata tofaba a zancen nasu, datasan ma zan fito bazata barniba nima.
A falon baba jafaru yanemi jin ba'asin tushen fitinar, cikin d'aga muryar da hargowa maman Safara'u tafara fad'in “Alhaji wlhy kashiga tsakanina da maman biyu a gidannan, idanfa tanama sauran matan gidannan Yanda taske so, suna barinta nibazan bartaba, tasanni tasan waye ubana ehe, kum.......
Hannu yay saurin d'aga mata, “kinga Suwaiba nifa ba wannan ne yasani kiranku ba, sonake naji minene ya kawo hayaniyar?”.
Cikin jin haushin an tareta tace, “Alhaji akan yaronnan Sadeequ ne, kowa yasan wajen Safara'u yake zuwa a unguwarnan, amma jiya da yamma sai ya aiko kiran Munaya, dayake ALLAH yatashi tonon asirinsu sabida bayaune na farko ba sai d'an Aiken ya kwatsa maganar a tsakar gida, babu dai Wanda yace komai, dan azatonmu ba Sadeeq d'in Safara'u baneba, goshin magriba saiga Safara'u tashigo tana kuka. Na tsareta da tambaya da k'yar tacemin cikinsu 'yan biyu tagani da Sadeeq a zauren gidan Malam halilu suna hira da dariya, kuma hardama mata gwalo akayi. Saboda na gaskata zancenta na sake aiken Rahma taganomin da idonta, harma taji Sadeeq d'in nafad'in ai koma miza'ayi bazai auri Safara'u ba, cikin wad'an nan munafukan yaran daba ganesu akeba zai aura, saboda darene yasani d'inne maganar a raina har safiyar yau d'inan, amma wlhy Alhaji da k'yar na iya barci nida Safara'u jiya.
“hummm” kawai nafad'a ina dafe kaina, saboda jin Yanda aka canja maganar.
Babak'arami ya kalleni yace, “Munubiya ce ko Munaya?” (dan basa ganemu saboda tsananin kamata da hassana ta).
Zuciyata cikeda bak'in ciki nace, “Baba Munaya ce”.
“yauwa Munaya, ina 'yar uwarki?”.
“Tana ciki baba”.
Baba ya kalli Safara'u daketa matse kwallan munafurci tun d'azun yace, “k! Safara'u tashi kiramin Munubiya ”.
Batareda ta amsaba tatashi tafita, mintuna kad'an saigata sun dawo tareda Munubiya datasha kuka idanu sukayi luhu-luhu. tsaki naja a raina ina hararta ta gefen ido, rashin jarumtar ta na bani haushi, ta cika hak'uri da sanyin hali tamkar innarmu.......
Maganar baba ce tadawo dani daga tunanin dana tafi. nad'ago ina kallonsa saboda kiran sunana dayayi, muryar a dake na amsa da “na'am baba”. kallonsa ya maida kan Safara'u yana fad'in “wacece acikinsu kika gani tareda Saddik'un?”.
Binmu da kallo Safara'u tayi, cikin matse kwalla tace, “baba niba ganesu nakeba, sai sun banbanta min Kansu sannan”.
Baice komaiba dan shima yasan da hakan, (ta hallaya ne kawai kowa ke banbantamu agidan, hatta da innarmu kuwa). Baba yabimu da kallo alamar son sanin wacece acikinmu.
Da sauri Munubiya tace, “baba nice”.
Nima na kar6e da fad'in “baba k'arya takeyi nice jiya Sadeeq ya aiko kira, kuma babu wata alak'a dake tsakaninmu, hasalima ya kirani ne akan Safara'un, sune dai suka maida zancen haka”.
Daga Safara'u har mamanta harara suka ballamin, babu ragi nima na rama kuwa.
Baba ne yakatsemu da fad'in “miya faru to Munaya?”.
Janye idona nayi daga Kansu na maida gareshi, kaina ak'asa Nace,
“baba ya kirani ne yana tambayata minene abinda Safara'u tafiso a rayuwarta, dan yanason yabata gift na birthday d'inta, kuma soyake yayi mata bazata. shinefa nake lissafa masa muna dariya saboda ina cewa ya had'o mata da gyad'a soyayya dan ita mayyarta ce, a dai-dai lokacinne kuma na hangota zata shigo gida, nifa dama tsokana namata gwalon, Ashe ita ta d'aukeshi wani Abu. Kuma wlhy Rahma k'arya takeyi, lokacin data fito tareda yaa Hameed ta ganni yana bani kayansa nakai masa ciki shi zai shiga masallaci salla. Wannan shinefa abinda yafaru, shine suke cewa nakwace mata Sadeeq, har ana cin zarafin innarmu da farar safiyar nan”.
Ajiyar zuciya innarmu ta sauke a hankali, taji dad'i daba abinda suke zargin baneba.
Wata uwar harara baba jafaru ya watsama maman Safara'u, “kai Suwaiba kedai ALLAH ya gyaraki, dan ALLAH kuringa bincike akan Abu idan yara sun fad'a muku, tokinji dai abinda yafaru, kekuma Safara'u dayake bakida tarbiyya har bakinki yana iyama Ai'sha rashin kunya ko, ki tabbatar saina saka Abdulhameed yacimin ubanku keda Rahama yau a gidannan. Ai'sha kiyi hak'uri dan ALLAH ”.
Innarmu ta yink'ura zata mik'e tana fad'in babu komai babansu, ALLAH ya kauda fitinar gaba”.
“Amin” muka fad'a muma muna mik'ewa mukabi innarmu a baya.
Koda muka fito, sai matan gidan suka zubo mana ido suna kallo tamkar yau suka fara ganinmu, a raina nace munafukai, haka zaku k'are.
Ran innarmu ya6aci matuk'a a wannan karon, amma kasancewarta mutum mai hak'uri da shanye damuwa sai bata nunaba.
Nida Munubiya kam kasa shanye 6acin ranmu mukayi, munsan koma wace irin wulak'antawa za ai mana agidan *KAKARMU* ce taja mana, itace tabada kowacce iriyar k'ofar tozartamu, idan kaga abubuwan da ake mana saika d'auka ba jinin gidan baneba, tunda muka taso a haka muka tsinci kanmu, hakama mahaifiyarmu a wannan halin muka risketa tana fuskantar k'ask'anci da wulak'anci daga Kakarmu da matan Abban mu, harma da matan k'annensa, bamuda 'yanci irin na 'ya'ya, mahaifiyarmu batada kima irinta matar gida (Uwargida), hakan yasamo asaline dalilin................✍🏼
👎🏻
Tofa masu karatu dalilin mi? Dani daku duk muna buk'atar jin wannan dalili a bakin MUNAYA!, saiku kasance dani danjin Yanda wannan labari mai d'unbin harmutsi da tsalle-tsalle zai kaya, miye manufarsa? ina kuma ya dosa?.
Amsa d'aya zan iya baku.👇🏻
*_LABARIN MAI TSAWONE_*
saikun kasance dani a hankali zancigaba da warware muku lauje cikin nad'i.
ALLAH yasa zaku bani had'in kai, tabbatarwata shine yanda zaku kar6i wannan labarin.
Dan haka kumuje zuwa🥺✍🏼✍🏼
Zamu cigaba Monday insha ALLAH, wannan d'and'anone.
Sannan wannan karon zandinga typing ne Monday to Friday kawai insha ALLAH, kunga banda weekend kenan😊.
One luv🥰
*_ALLAH ka gafartama mahaifanmu😭👏🏻._*
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_Ban yarda wani yaymin amfani da labarin nanba tako wace irin hanya, idan hakan tafaru ban yafeba gsky, ALLAH yabani ikon fad'ar abinda zai amfanar dani da Ku, ya tsare harshena daga fad'ar abinda zai cutar damu baki d'aya._
*_ALLAH ka gafartama mahaifina da dukkan sauran musulmai dasuka kwanta dama, kabama marasa lafiyarmu lafiya👏🏻._*
👉🏻2⃣
...........Zan iya ce muku fitinar gidanmu ta farone daga tushe, dan kuwa ginannen abune tun zamanin k'uruciyar iyayenmu...
Malam Faruku shine kakanmu, matarsa d'aya Marwa'natu (Innaro), 'ya'ya hud'u suka Haifa a duniya, maza uku mace 1. Auwal, Hameesu, Saffiya, Jafaru.
ALLAH yayi Innaro mace mai mugun son abin duniya, arayuwarta tanason ace komai daga gareta aka fara ganinsa, kokuma wajen 'ya'yanta, sun tsayama 'ya'yansu duk sunyi karatun addini dana boko, sai dai Safiya iyakarta primary aka mata aure. Sukuma mazan duk sunkai matakin babar makaranta (jami'a). wannan yasaka Innaro d'aukar burin duniya ta d'ora akan 'ya'yan, harma matan dazasu aura.
Auwal shine yafara kammala karatunsa, dan haka Malam faruku mahaifinsu yace ya fiddo matar Aure.
Bai wani tsaya Jan rai ba ya gabatar da Ai'sha amatsayin wadda yakeso.
Kai tsaye innaro tace sam bata aminceba, d'anta bazai auri d'iyar buzayeba kuma 'Yar iska, Auwal yayi lallashin yayi rok'on akan fahimtar da ita sonda sukema juna shi da Ai'sha, amma Sam tak'i saurarensa balle ta fahimcesa.
Da farko Malam faruku yasaka musu ido, azatonsa innaro zata sakko cikin sauk'i, amma ganin yanda ta kafe akan bakanta saiya sanya baki da tambayarta dalilin k'in amincewar.
Kai tsaye tace batason su Ai'shar ne, Dan ba'asan asalin suba, sannan kuma 'Yar iskace, shima kuma yasani ai. cikin hikima Malam yaso fahimtar da ita halin k'addara kowa da irin tasa, itama Aishar bayin kanta bane ba, amma tak'i saurarensa shima. ganin abin zai tasamma rashin mutumci yace to aure tsakanin Auwalu da Ai'sha kamar anyi an gama. A wannan lokacin ba k'aramin birkicewa innaro tayi musuba, amma Malam faruku yace tayi tagama, dan hujjarta batada muhimmancin dazai haramta auren Auwal da Ai'sha. babu 6ata lokaci kuma aka fara shirin bikin.
*Wacece Ai'sha?*
Ai'sha d'iyace gawasu buzaye 'yan k'asar Niger wad'anda k'addarar rayuwa ta jawosu zuwa k'asar Nigeria, su biyu kacal iyayensu suka Haifa, Aisha itace babba, sai k'anwarta Rabi'atu, wurjanjan suka shigo k'asar Nigeria, sun fara rayuwane awata tashar mota, inda anan tsautsayi ya fad'ama Ai'sha wani mara imani yamata fyad'e anan cikin tasha da daddare, randa abin yafaru Malam faruku yaje tashar zai bada sak'o akaima wani d'an uwansa dake garin Maiduguri, ya taras anata cecekuce atashar, yayinda Ai'sha da iyayenta ke rungume da d'iyarsu sunata kuka da kururuwa.
Malam faruku yatambayi abinda ke faruwa daga wajen mutanen dasuka zagayesu suna kallo, babu 6ata lokaci matashin saurayi yafad'a masa komai.
Hankalin Malam faruku yayi matuk'ar tashi, danshi mutumne mai kishin al'umma, anan ya d'auki Ai'sha da iyayenta suka nufi asibiti, saboda jinin daketa zuba daga jikinta (Dan bazata wuce 15 ba sannan), duk wata kulawar da yakamata anbama Ai'sha a asibitin, har tsawon kwanaki hud'u tasamu lafiya sarai, kamarma komai bai faruba, sai dai tabo Na zuciya da aka bar mata itada iyayenta. tun suna zaman asibiti Malam faruku ya fiskanci iyayen Aisha basuda wajen zama, dan haka yak'udiri niyyar taimakonsu.
Akwai wani d'aki k'arami ciki da falo dake gidansa, saiya zagaye musu shi da Katanga yamasa gyara.
Tunda aka fara aikin innaro ta tada hankalinta, duk zatonta aure zai k'ara, ganin tana neman tara masa k'asa ya zaunar da ita yamata bayani dallah-dallah, maimakon ta kwantar da hankalinta tunda ba kishiyar bace saima takuma tadashi, tace bazata zauna da iyayen Aisha ba.
Malam faruku yace bata isaba, Dan gidansane babu mai hanashi ajiye Wanda yakeso akuma lokacin dayaso.
Dole badan innaro tasoba su maman Aisha suka zauna agidan, sai dai ko kad'an basajin dad'in zama da ita, kullum gori da cin mutunci take musu, su Aisha kam basuda sakat awajenta, saita koma sakasu aiki tamkar boyi-boyinta. Malam faruku ne ya koyama mahaifin su Aisha sana'a, har shima yasamu rufin asirin rik'e iyalensa dai-dai gwargwado, amma ko kama k'afar Malam faruku baiyiba, lokuta da fama ma shine ke taimakonsa dawasu abubuwan Na rayuwa, musamman d'inkin sitturar su Aisha da wasu matsaloli Na yau da kullum dasukan taso. tun zuwansu gidan Auwal yafara k'aunar Aisha, duk da mahaifinsu ya Sanar musu da komai akan k'addarar da ta fad'ama Aishan kuwa, shekararsu biyu suna soyayya, tun Aisha Na d'ari-d'ari dashi saboda tsoron abinda aka aikata mata har tazo tasaki jikinta dashi, sai dai babu Wanda yasan suna soyayyar sai Rabi'a k'anwarta.
Ana haka kuma Auwal yazo da zancen Aisha zai aura.
To haka dai akayi auren Auwal da Aisha badan innaro tasoba.
Wannan kuma yasakata d'aukar Karen tsana ta d'orama Aisha, kullum cikin zagi da cin mutuncin Aisha take, sosai tazamar mata Uwar miji mai kishi da sarakuwa, ga gorin datake mata akan ita 'Yar iskace, babu wani fyad'e da'aka mata, taje tayi iskancinta an fake da fyad'e an dawo an lik'ema d'anta da asiri, tujara dai iri-iri dai ta innaro.
Aisha tanada hak'uri, ko kad'an abinda innaro kemata bai hanata girmamata ba da bata matsayi irinna uwa, amma innaro bata gani.
Watan aurensu 7 kacal innaro ta samoma Auwal wata yarinya mai suna Mero, mero d'iyace ga wani matashin d'an kasuwa, tun alokacinma ana lissafashi a masu kud'in yankin balle yanzu daya zama shahararre, Auwal bayason Mairo, amma dolensa ya aura saboda innaro tace zata tsine masa.
Shigowar Mairo Yakuma k'untata Aisha a gidan, dan tunkan ta shigo innaro tagama 6ata sunan Aisha dana iyayenta awajensu mairo, shigowar mairo da wata 1 kacal kuma tasamu ciki, wannan fa yakuma k'ara ta6ar6arewar al'amura, gashi sannan ALLAH ya yalwatama Auwal d'in babu laifi, harma yasayi wasu filaye uku shida 'yan uwansa anan cikin anguwar kusada su innaro, amma ba'a ginaba, dan babu kud'in ginin lokacin.
A wannan lokacinne kuma k'addara ta afkama iyayen Aisha, ranar wata alhamis da daddare aka maka ruwa Na tashin hankali, Wanda yay sanadin fad'awar d'akin dasuke ciki suka rasu.
Aisha da Rabi'a sunshiga matuk'ar tashin hankali, hakama Malam faruku, innaro kam ko'a jikinta.
Rasuwar iyayen Aisha yasaka rabi'a k'anwarta dawowa hannunta da zama, akuma lokacinne Hameesu shima yace Rabi'a yakeso da aure. tashin farko innaro ta taka masa birki da kukarin zata tsine masa kuwa. dole yabar maganar auren Rabi'ar yasamo wata Ruk'ayya ya aura.
A lokacinne Mairo ta haihu namiji, zokaga murna wajen innaro da mairo, Malam ma yayi murna, hakama Aisha, dukda innaro tace Na munafurcine. ranar suna yaro yaci Abdulhameed, koda wasa mairo bata ta6a yarda Aisha ta d'auki hameed ba, dan innaro tahana, Auwal yayi fad'an shida Malam harsun gaji.
Rayuwa tacigaba da tafiya tsawon shekaru, zuwa sannan su Auwal sun had'a hannu sun gina filinsu, kowa da 6angarensa, gidanmu yafara yawaita da 'ya'ya, dan matar Hameesu ma ta haihu Namiji Shafi'u, hakama matan gidanmu sun k'aru, dan jafaru ma yayi aure, hakama Hameesu yak'ara aure shima, ga iyayenmu sun kuma bunk'asa, dansu wuce buk'atun yau da gobe, dai-dai gwargwado akwai rufin asiri agaresu, alokacin kuma sai Auwal yakuma auro ta uku, auren iyayenmu yakoma tamkar gasa wajen za6o 'ya'yan manya, dan kuwa Aisha ce kawai d'iyan talakawa acikinsu, tana zaunene kawai da k'arfin ALLAH dakuma Na Malam faruku, saikuma soyayyar mijinta Auwal, amma da dan ta innaro ne da tuni Auwal ya saketa.
Akwaima randa fada ya had'a mairo da Aisha akan Rabi'a ta doki hameed saboda yamata rashin kunya, dukan da mairo taima Rabi'a saiya sa Aisha kasa hak'uri a ranar ta tanka mata, nankuwa mairo tafara zuba mata gori da cin zarafi, da innaro tazo danjin ba'asin rigimar saitace dole Auwal yasaki Aisha, dukda kuma mairo ce mai laifi, Auwal yayta magiya amma innaro tace yaza6a ko ita ko Aishan, babu yanda zaiyi yasaki Aisha saki d'aya alokacin. Hankalin Aisha yatashi matuk'a, dan batasan inda zasu dosaba, tunda basuda kowa a Nigeria, ga innaro tsaye akanta tace atake saita bar mata gidan d'a.
ALLAH ya tak'aita abunne dai-dai sanda Aisha ke fitowa rik'eda hannun Rabi'a kuma saiga Malam faruku yadawo daga kasuwa, nanfa ya tambayi ba'asi, Aisha tasanar masa komai, maidata yayi gidan, yakuma saka Auwal ya maida aurensu atake awajen, sannan ya tabbatar masa ko bayan babu ransa yasake sakin Aysha bai yafeba, kuma inhar innaro tasake sakashi ya saketa itama abakin aurenta.
Wannan shine dalilin dayasa auren Aisha da Auwal bai sake rawaba. rayuwa kuma tacigaba da shurawa. Matan gidanmu 7.
Auwal matansa uku, Aisha (innarmu) Mairo (mama) Sadiya (gwaggon haleema)
Hameesu nada biyu, Ruk'ayya (umma) Hadiza (momy)
Jafaru Nada biyu shima, Suwaiba (maman safara'u) Hafsatu (maman Fauziyya).
Kowacce ta haihu acikinsu, amma banda Aisha, wadda saida sukayi shekara 20 da aure itada Auwal sannan ALLAH yabata ciki, zokiga murna wajen Auwal da ahalinsa, saidai banda matan gidanmu da innaro, dan aganinsu duk sunfi Aisha matsayi, (maman fauziyya) Ce kawai babu ruwanta, dan suna d'asawa da Aisha sosai, ita kad'aice bata raina innarmu ba, dan Yaya ma take cemata.
Babu irin wahalar da Aisha batasha agidanba acikin shekarunan, kullum cikin mata gorin haihuwa dana talauci ake, harma dana batada asali, tundaga kishiyoyinta har matan k'annen mijinta basu raga mataba, kowacce jitake ina wuta tasaka innarmu a gidan, dama ga d'aurin gidi daga innaro suna samu. innarmu bata cemusu komai, saidai tashiga d'aki tasha kukanta, 'ya'yan maman fauziyya ne kad'ai ke shigowa d'akinta, amma sauran duk an hanasu, gashi ta aurar da Rabi'a tuni, itama harta haihu uku ma.
to saikuma ga Aisha da ciki rana tsaka, bayan tagama fidda ran haihuwarma gaba d'ayanta. cikin ikon ALLAH cikinta yakai haihuwa, ranar data haihu saiga 'yan biyu k'yawawa kamarta duk mata, A zahiri matan gidanmu suna k'untatama innarmu ne saboda yanda innaro tagama 6ata Aisha awajensu, a bad'ini kuma suna k'in Aishane saboda tafisu k'yau da komaima Na halittar jiki, (dan cikakkiyar buzuwa Ce) mai k'yawu Na asali, dirarriyar macece doguwa, fara tas, gashin kai, idanu da komai ALLAH yabatasu. Sa6anin su daba haka sukeba. cikin ikon ALLAH kuma saigashi ta haifo 'ya'yanta masu tsananin kama da ita.
Hassana (Munubiya) da Hussaina (Munaya) wad'anda suke matuk'ar kama da juna, kamar Munaya da Munubiya ta 6aci matuk'a, ko Aisha saitayi da gaske take banbancesu, saida suka fara girmanema ake d'an banbantasu tawajen halayya shima ba kowaba, amma Aisha ita tana ganesu kai tsaye a sanan.
Munubiya tanada hak'uri tamkar Aisha, duk wahalar dasukesha wajen yaran gidan bata iya ramawa, saidai tasha kukanta tashare hawaye. sa6anin Munaya da take fitinanniya, bata bari a cuceta, koda anfi k'arfinta saitabi tawata hanyar tarama kuwa, wannan yasaka matan gidan da yara sukafi tsanarta, sai dai kuma basa iya banbancesu itada Munubiya, sometimes Munaya takanyi laifi akama Munubiya a daka, itakuma Munubiya bazata ta6a fad'in ba itaceba.
Ganin hakan yasaka Aisha yima Munubiya shaida saboda aringa banbantasu, amma Munaya Na k'yalla ido tagani sai itama tayima kanta irin ta Munubiya komai da komai, idan sau dubu akama Munubiya shaida ajiki Munaya ma zataje taima kanta, hakama Munubiya takanyi idan anyima munaya, hakan yasa Aisha ta hak'ura kawai harma suka Shiga makaranta, nanma rikicin Munaya bai k'areba, dan saima abinda yay gaba, tajawo fad'a akama Munubiya adaka, hakan kuma bazaisa gobe ta fasaba.
Shekarar su goma Aisha takuma haihuwar 'yan biyu duk maza, Aryaan da Aiyyaan, tundaga lokacin kuma bata sakeba.
Sai dai Munaya da Munubiya suna matuk'ar k'aunar junansu over abinma har saiya Baka mamaki, sannan suna k'aunar mahaifiyarsu da k'annensu, Munaya ce kan shiga idan ana cin zarafin mamansu, amma ita Munubiya saidai taita kuka.
Yanzu haka zancen danake muku shekarunmu 19 nida Munubiya, muna matakin farko a jami'a, munzama 'yan mata, k'yawunmu da tsananin kamarmu da innarmu yasake fitowa, mun fita daban a gidanmu, dan mukad'aine kamarmu daban, Ayyan da Aryan ma duk Abbanmu suka kwaso, wannan yasaka suke kama da 'yan gidanmu.
Tabbas bamajin dad'in zaman gidanmu, saboda k'unci da hantara damuke fuskanta muda mahaifiyarmu awajen Innaro da matan gidan, harma dawasu yaran gidan 'yan uwanmu, amma wasu muna shiri dasu sosai, musamman ma mazan yayyenmu manya, dansu babu ruwansu da gutsiri tsomar cikin gidan.
Gidanmu gidane tamkar gidan hayar daya had'a k'abilu daban-daban saboda yawan rikici, kullum cikin fad'a muke, ba iyayenba ba yaranba, kai kace muna ganin hanjin junane.
Gwargwadon iko akwai hali a gidanmu, dan iyayenmu sun rik'e gidanmu sosai da buk'atinmu, dukda yawa da ALLAH yabamu, bamu rasa ci da sha ba da situra, hakama matsalolin karatunmu, dan kai tsaye zance gidanmu gidan 'yan bokone, kullum cikin gasa da juna ake, burin kowa ace shine gaba, batun ilimin addinima kam Alhmdllh, dan tsaye iyayenmu suke akanmu, har gobe yaa hameed bai daina zama gaban malamai ba balle mu 'yan baya-baya. ak'alla yaran gidanmu munkai mu 43 kuma.
ALLAH yayma Malam jafaru kakanmu rasuwa shekara biyu kenan, innaro Ce dai tana nan daram, al'amuranta sai abinda yay gaba, dan har gobe bata k'aunar innarmu, kuma bata daina cin zarafinta ba agaban kowa da mata gorin rashin dangi.
Hakan yasa kullum cikin buri da k'udirin binciko dangin Innarmu nake, ko itama zata samu 'yancin kanta kamar kowa😢.
Wannan shine labarin gidanmu, sai ahankali zaku cigaba da fuskantar ainahin halayen jama'ar gidanmu da aiyukansu, harma da sunayensu😊.............✍🏼
To masu karatu, sai nace yanzufa za'a fara, saiku kasance dani danjin labarin *_RAINA KAMA.... kaga gayya_* dan akwai babban al'amari a gaba, bawai gidan su Munaya kawai labarin ya shafaba, akwai wani lauje cikin Nad'i daga d'ayan 6angaren labarin Na Raina kama.....😉 suga gayya ba👎🏻😄.
One luv🥰
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu😭👏🏻_*
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻3⃣
.........Fad'a sosai innarmu tamin akan Marin Safara'u danayi, sannan ta d'ora da nasiha kamar yanda tasaba, wani kam yashiga kunnena, wani kuwa tabaya yabi, dan harga ALLAH Na daina zama kowa yana taka mana mahaifiya a gidan.
Innarmu tace, “ku shirya gobe idan ALLAH ya kaimu Ku tafi gidan mamanku Rabi'a Ku k'arasa hutunku, banason zamanku a gidan nan tunda fitina yake kawowa”.
A sanyaye Munubiya ta amsa da “to innarmu”.
Amma ni saina tunzuro baki gaba ina k'unk'uni, dan banason tafiya ko ina, canma saboda d'an mama Rabi'a d'inne Marwan, ko kad'an bama shiri dashi, saboda masifarsa. “kai innarmu, yanzu dan ALLAH saboda wasu can bazamu mik'e kafa yanda mukeso ba agidanmu, duka fa hutun sati biyu ne kacal, amma saimunje wani waje?, ni wlhy inkika barni babu mai k'ara mana koda kallon banza a gidannan, harma innaro bazan bartaba.........”
Maficin danaga innarmu tajawo yasani tashi da sauri nabar gurin, Na tabbata shirin bugamin takeyi. Munubiya ta saka dariya tana kallona, “ke ga rashin arzik'i ga tsoron tsiya, dukan maficin kikema wannan gudun?”.
Harara Na balla mata, “yo k'ya fad'i haka mana tunda ba jikinki baneba, tsoro kam kinsan waye matsoraci acikinmu ai”.
Munubiya ta ta6e baki “naji dai, koma mizaki ce kije kiyita cewa, inama kayana dakika saka jiya? na wanke, dan dasu zanje”.
Wayar innarmu Na d'auka ina dannawa, batareda na bata amsaba Na nuna mata laundry basket d'inmu.
Innarmu tace, “to Aljanar waya ajiyemin kafin ki k'ararmin kud'in ciki, ina taki?”.
“kai innarmu, please mana, zan kira Ayusher nefa nasanar mata muna zuwa gobe, ALLAH wayata babu ko nera aciki Munu ta cinye min jiya”.
“kiji tsoron ALLAH munaya, Nina cinye mini kud'in waya? bake kika kira Balkisu ba da kanki?”.
“to dana kirata sai nace kuyita surutu har kud'ina ya k'are”
innarmu Na shirin yin magana muka jiyo kururuwar kukan Safara'u da Rahama. dariya Na k'yalk'yale da ita, ina fad'in “o, ALLAH ga yaa hameed can yana gwajin kwanji a jikin gayu”.
Harara innarmu ta ballamin, saikuma tamik'e tana shirin fita, nasan kar6arsu zataje, nai saurin fad'in “kai innarmu, kid'an barsu su lallasu mana”.
Dakk'uwa ta watsomin tareda fad'in “K'aniyarki Munaya”.
Dagani har Munubiya dariya muka sanya harda tafawa kuwa.
Ba'a rufa mintuna 3 da fitar innarmu ba muka fara jiyo hargowar Maman safara'u (dama ita bata magana a hankali) Yaa hameed takema masifa akan dukansu safara'u dayakeyi, maman su yaa hameed babu hak'uri, itama tafito suka fara cacar baki, yaa hameed kam ficewarsa yayi bayan innarmu ta kwaci su Rahama a hannunsa da k'yar. kafin kace mi gidan yakuma kaurewa.
Munubiya tace, “kai jama'a ko breakfast ba'ayi agidanba har antafi wrestling zagaye na biyu”.
Na fad'a saman gado ina Dariya, danni mamaki 'yan gidanmu nakeyi da bala'insu. wayar Innarmu tayi ringing, da Sauri Na duba sainaga Abbanmu ne, cikeda d'oki Na amsa tareda masa sallama sannan Na gaidashi.
Yace, “Munubiya ina maman takune?”.
“Abba ba munu bace, nicefa”.
“to to munaya ce? hayaniyar mi nakeji haka agidanne Munaya?”.
K'yafta min ido da zungurina Munubiya tashiga yi wai karna fad'a masa (dayake a Hans free nasaka wayar, tana jin komai) amma saina harareta da murgud'a baki nace, “Abba Mama Ce da maman safara'u suke fad'a”.
Tsaki yaja da fad'in “ALLAH ya shiryesu to, ina maman taku ne?”.
“Amin Abba, Innarmu tana can wajen rabon fad'an ai”.
“shike Nan, idan tashigo kice takirani muyi magana”.
“to Abba bye”.
Yace, “ok dear bye”. Sannan ya yanke wayar.
Ina yanke wayar Munubiya ta kaimin bugu, Na kauce ina dariya “yo da bakina a hanani fad'ar gaskiya”.
“ba hanaki akayiba, amma kinsan idan Allura ta tono garma mune tushen fad'an ai, kinkuma san halin Abba da d'aukar zafi kamar baba k'arami”.
“tab, ta k'are musu dai suda suka takalo wlhy, jarababbu dangin masifa”.
“kina ciki kenan tunda kema dangin kine ai”.
Dariya muka Sanya nida munubiya.
*washe gari*
Tafiyar mu gidan mama Rabi bai yuwuba, saboda dawowar Abbanmu, da innarmu ta sanar masa a waya zamuje can muk'arasa Hutu sai yace a'a muyi hak'uri mu zauna, Dan akwai bak'in da zaiyi a k'arshen sati (weekend), kuma yanason dukkan yaran mukasance muna nan.
Innarmu tace shikenan.
Wannan dalilinne ya hanamu tafiya Hutu, dama ni ba so nakeba, Munubiya ce keta zakwad'in tafiyar.
Yau ta kasance alhamis, tunda safe muka tashi da himmar wanki nida Munubiya, ina sharar sashenmu Munubiya na fidda kayan wankin, yayinda Aryan da Aiyan keta tara mana ruwa daga fanfo zuwa banbu.
Ina gama sharar na wanke hannuna na k'arasa bakin fanfo inda Munubiya ke k'ok'arin jik'a kayan. zama nayi bisa d'an dakali da akayi wajen saboda irin hakan, wanki ko wanke-wanke da sauransu, waya nake latsawa ina nemo mana wak'a, dan muji dad'in wankin, maganar aunty khaleesa kawai mukji a kanmu tana fad'in,
“k! Munaya tashi kije ki gyaramin d'akinmu, akwai wani zanina nan ki d'akkosa ku wankemin”.
Banza namata ban d'agoba, sai Munubiya ce tace, “to aunty khaleesa”.
Shirun danayi ina kuma tamke fuska yasata gane nice munaya, Dan haka ta kalli Munubiya dahar tatafi, “k Munubiya!... dawo, bakece zakiyiba, k! Dan uwarku Munaya tashi kije kimin”.
Da sauri Munubiya tace, "Aunty khaleesa ai nice munaya, waccan Munubiya ce”.
Hararta tayi, “mai dani 'yar iska to, ko kina tunanin ban ganeku nima d'in?”.
Banyi niyyar d'agowa ba, amma jin abinda tafad'a yasani sakin guntun murmushi, nasan k'arya takeyi tace tana ganemu kai tsaye, yanzu ma dan kawai na nunu halin nawane shiyyasa tagane nice, kawai tafad'ane dai, mai da kaina nayi nacigaba da abinda nakeyi.......
Wata ashar ta lailayo ta makamin, tareda zaburowa tamkar zata dakeni, dai dai nan sallamar innaro ta karad'e tsakar gidan. mu duka kallonta mukayi, nikam kallo d'aya namata na d'auke kaina, (dan nikam natsani kakarnan tamu) Munubiya da aunty khaleesa suka gaidata, nikam a d'age nace “ina kwana”.
“kin yima uwarki Ai'sha dan Ubanki”, cewar innaro ta na nunani da d'anyatsanta manuniya👉🏻, tacigaba da fad'in “ni zakima gaisuwa a haka? kamar wata sa'ar uwarki?, aiko Aisha da ubanki basu isa sumin gaisuwa hakaba balle ke haihuwar yanzun”.
Baki na la6e, ba tareda na kalleta ba natashi nahau wankin, Munubiya kuma tawuce danta gyarama su aunty khaleesa d'akinsu. abinda nayi na nuna halin ko in kula saiya kuma tunzura innaro, ta fara hayagaga da matse kwalla wai naci zarafinta.
Wannan yasaka matan gidanmu da yara fara fitowa d'ai-d'ai suna kallonmu (dan al'adar gidanmu ce hakan, da anji kaya-kaya kowa zaiyo waje yaganema idonsa abinda ke faruwa).
Dady ya k'araso da sauri yana fad'in “Inna miya farune haka da kuka? Keda waye?”.
“wannan shed'aniyar yarinyar mana” tayi maganar tana nunani “waini yarinyar nan zataima d'ibar albarka saboda uwarsu kullum tana aibantani a gurinsu, shiyyasa duk sun rainani....”
Baki bud'e nake kallon innaro da sherinta. wlhy wannan tsohuwar bazataga Annabi ba........
Maganar Dady ta dawo dani daga mamakin innaro. Yace, “Munaya ce ko Munubiya? miya farune keda inna?”.
Dady yanada sauk'i, ba kamar Abbanmu da baba k'arami ba sun fishi zafi.
Nace, “dady Munaya ce. wlhy babu abinda namata, kawaifa daga shigowarta duk muka gaidata, shine kawai ta hau zagina wai ban gaidata da k'yauba.......”
“amma ai gaisuwar rashin tarbiya kikai mata”. ‘cewar Aunty khaleesa’.
Dady zaiyi magana Aunty Ramlah tace, “wlhy Dady ba haka bane, duk abinda yafaru akan idona yafaru, dan nafito zan d'iba ruwa a fanfo”.
Dakuwa Innaro ta mata, “kinci uwarki hadiza, kema ashe munafukace ban saniba, to ko hadizar ta haifama Ai'sha ne ke?”.
Fakar idon Dady aunty Ramlah tayi ta dallama innaro harara, sannan tace, “yo daga fad'ar gaskiya, nidai wlhy Dady abinda nagani nakuma ji kenan”.
Girgiza kai Dady yayi, sannan yace, “kiyi hak'uri Inna, Munaya tayi kuskure amma bazata sakeba. Munaya zoki bata hak'uri”.
Ban musaba nazo har gabanta nace tayi hak'uri, bata amsamin ba, saima hararata datayi kawai. nima saina bar wajen nakoma kan wankina.
Dady Yakama hannun innaro suka shiga falonsa, matan gidanmu duk suka bar wajen, basuso wasan yak'are a nanba, sunso ace cin mutuncin innaro yasauka har kan innarmu.
Innarmu dake tsaye daga k'ofar falonta tanajiyo abinda ke faruwa dukda katanga ta shiga tsakiya, ta girgiza kai kawai tana komawa ciki da fad'in ALLAH ya k'yauta.
Ina wanki ina zubda hawaye, sosai raina ya sosu yau akan abinda Innaro tamin, dukda bawai yaune karon farko da hakan ya faruba, sai dai na yau yamin zafi ainun, har inaji natsani zaman gidanmu, a fili na furta ALLAH kabamu miji muyi aurenmu mubar gidannan”.
Munubiya dabansan tazo wajenba naji ta amsa da Amin sweetheart, wlhy koni yanzu addu'ar danake mana kenan, sai dai banason mutafi mubar innarmu a wannan halin dasu Aryaan”.
“hakane Munu..., karki damu, insha ALLAH munayin aure d'auke innarmu zamuyi ko Abbah ya yarda kobai yardaba wlhy!!”. ‘ta k'arashe maganar a harzuk'e’.
Murmushi Munubiya tayi, dan tasan ran 'yar uwar tata yakai k'ololuwar 6aci.
Har muka gama wankin innaro na gidan bata tafiba, bamusan uwarmi takeyiba. dayake girkin gwaggon Haleema nema ranar. ina tsaye a bayan flowers d'in d'akinmu ina goge glass d'in windows naga Abdul yafito d'aukeda tire an jera sabbin kuloli akai, nasan Abbanmu baya gari, dan haka nace, “Abdul wazaka kaima abinci haka?”.
Yace, “Aunty zan kaima innaro tana falon dady”.
Kai na jinjina masa kawai nace jeka, cigaba nayi da aikina ina fad'in “shidai munafurci ai dodone, maishi yakeci”.
Koda na koma ciki sai nake bama Munubiya labari, innarmu dake bayanmu bamu saniba tace, “to ina ruwankine wai Munaya?, nifa banason gutsiri tsoma wlhy, wai sai yaushene zaku daina jamin fitina a gidanan ne?”.
A sanyaye mukace kiyi hak'uri innarmu“.
Batace komaiba tashige d'akinta, muduka da kallon tausayi muka bita, dukda tasan ita ake tauyema hak'i amma bata ta6a nuna itace mara laifi, kullum ta amince itace a k'asan kamar yanda kowa ke kallonta agidan.
★★★★★
Washe gari Abbah yadawo da yamma, duk munyi murnar ganinsa, shima kuma hakan take a garesa.
Sai da daddare suka tara iyayenmu mata meeting shida Dady da baba k'arami.
Abbanmu yay gyaran murya sannan yace, “dama wani abune yasaka muka taraku, maganace akan yaranmu mata, Ramlah da khaleesa da Rahaima da Hauwa'u kowa yasan sun fida mazajen aure harma an tsaida bikinsu nanda bayan salla”.
Duk suka amsa da eh.
“yauwa to Alhmdllh, yanzu munada sauran yara 'yan mata agidanan ak'alla su 8, kuma duk kusan Kansu d'ayane, dukda su Ramlah sun girmemusu, to wani uzirine yataso na tilas zamu had'awa auren wasunsu danasu khaleesa. shin ko akwai wad'anda a cikinsu sukeda tsayayye? domin a fiddasu?”.
Da sauri maman safara'u tace, “Safara'u nadashi, dan harma yanason turo iyayensa, amma nace ta dakatar dashi sai angama na yayyensu”.
“to Alhmdllhi, sai kuma wa?”.
Umma Ruk'ayya ma tace, “Fiddausi tanada tsayayye itama”.
“masha ALLAH, to bayansu fa?”.
“mamansu yaa hameed tace, “ai inaga sukenan kam Abban Hameed”.
“yanzu su 6 kenan suka rage? to dama Alhaji halliru d'an majalissar datta6ai, nasan duk kunsan abokinane shak'ik'i? to shine yanemi alfarmar nemama 'ya'yansa maza biyu auren biyu daga cikin 'ya'yana, d'aya d'ansane na cikinsa, d'aya kuma d'an yayarsane tarasu tabari yacigaba da rik'onsa. to harga ALLAH nasan yaransa sunada tarbiyya dan haka na amince, amma dukda haka saida nasake dogon bincike akan yaran saboda yaron yanzu ka haifeshine baka haifi halinsa ba, to Alhmdllh suma basuda wata matsala, dan haka mun yanke magana dashi akan suzo saisu za6a acikinsu, wannan shine dalilin dayasa muka taraku kenan”.
Hummm yaufa anzo da Sabon al'amari a gidan namu, nanafa iyayenmu mata suka hau tsugunne-tsugunne, kowa burinta ace d'iyarta aka za6a, harma da iyayensu safara'u dakeda mijin a hannu, ganin sunji gidan maik'one kowacce tafara k'ok'arin gani da fatan 'yarta ta kasance acikin gidan, aiko sai shirye-shirye kowa keyi a asirce, aka fara gyara 'ya'ya.
Mudai a 6angarenmu babu abinda innarmu kemana, hasalima inda taji maganar anan ta barta, komu bata sanarma ba, sai abakin Fauziyya mukejin komai.
Yanda ake shirye-shiryen bak'i takowanne 6angare saika d'auka 'ya'ya. Shugaban k'asane zasuzo, ni abinma mamaki yabani dan kowanne d'aki da nasu shirin, dayake kowane d'aki akwai budurwa d'aya, mu 8ne, su shida kowanne d'aki 1 kenan, saimu mu biyu a d'akinmu, 'ya'yan abbanmu mu 4 kenan, na baba k'arami 2 na Dady 2, gashi biyu za'a za6a acikinmu amma saika d'auka mu duka za'a za6a saboda shirye-shiryen da iyayenmu keyi.
Ranar Asabar (Saturday) kenan takama zasuzo, dan haka muduka 'yan Matan 8 baba k'arami yace muhad'u muyi girkin tarbarsu.
Ni Munaya, Munubiya, Safara'u, Fauziyya, Haleematu, Fiddausi, Zarah, Siyama.
A kitchen d'in 6angarenmu muke girkin, dukda dai iyayenmu sun d'an saka mana hannu wajen tsara kalolin abincin daya dace a tanada. Ni abunma haushi yabani, yanda naga 'yan uwana NATA rawar kai, sai wani k'alk'ale-k'alk'ale akema abinci da drinks na gargajiya damuka had'a.
A raina nace Kodai sune iyayen cin tsiya, ai bazasuci ko quarter d'in abincinnan ba, wannanma ai almabazzaranci ne wlhy, mutun biyu kawai amma anmusu abinci wajen kala 6, banda kuma kayan ciye-ciye irinsu snakes da nau'in nama da aka sarrafa zuwa daban-daban. haka dai muka gama aka kai falon baba k'arami aka shirya, sannan kowa takoma 6angarensu danta kimtsa........✍🏼
Anan ne za'ayi kece rainin👌🏻😄🏃🏻♀
Guys kumuje zuwa😉👎🏻
One luv🥰🥰
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*👏🏻😭
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻4⃣
.......Daga ni har Munubiya babu wata kwalliya damukayi, hasalima ni ko mai k'in shafawa nayi, danayo wankanma sainayi kwanciyata na hau barci. sai wajen 1 munubiya ta tadani wai sun iso, dama lokacin duk fashin salla muke nida munu.... (zakusha mamaki idan nace muku dai-dai da prioud yakanzo mana rana d'aya nida hassana ta, kuma musami tsarki tare), tashinai ina yatsine fuska, dan naji haushin tadanin datayi, toilet nashiga domin kimtsa jikina, sama-sama nadinga jiyo maganar Ikram tana fad'in “Aunty wai innaro tace kuzo”.
Cikeda mamaki munubiya ta amsa da to. nima abin yabani mamaki, dan haka nafito da Sauri, “wai Munubiya minake jiyowa ina toilet? ”.
Maganarta d'auke da mamaki tace, “wai innaro ke kiranmu”.
“ni da ke? kokuma mu duka?”.
“wlhy ban saniba munaya, sai dai munje d'in magani”.
Innarmu tashigo d'akin tana cewa “waishin Baku naji innaro ta aiko kira bane?”.
Muka amsa da “eh innarmu, mune”.
“to mi kuke jira, kuwuce kutafi mana”.
Babu Wanda yay magana acikinmu muka fita muna mamakin wannan kira Na innaro.
Tun a k'ofar falon baba k'arami mukaga wasu k'yawawan takalma, ga wani k'amshi yacika wajen, wicewa mukayi batareda mun shigaba, dukda mun hango Zarah da Siyama da Fiddausi natahowa cikin matsanancin gayu, saika rantse fita zasuyi wani gagarumin biki.
A k'ofar gidama munci karo da motoci uku duk bak'ak'e wulik, sai dai ta tsakiyar tafi k'yau da d'aukar hankali, garadan samarine majiya k'arfi kusan su 7 tsaitsaye ajikin motocin, duk suna sanye da bak'ak'en suit, daka gansu kasan babu sauk'i, hakan yasa muka fahimci bodyguards d'in bak'inne.
Gida biyu ne tsakanin gidan innaro da gidanmu, dan haka muka Isa da wuri. a tsakar gida muka isketa tana shanyar lawashin albasa. muka gaidata.
Yanda ta saba haka ta amsa mana, amma tace mushiga ciki tana zuwa.
Kusan mintuna 40 muna falon innaro zaune, amma bata shigoba, hakan yasakani tunanin tabas akwai wani lauje cikin nad'i a kiran namu, tashi nayi nalek'a tsakar gidan ta window, amma bata nan. “Munubiya kinsan Innaro bata gidanan kuwa?”.
Cikeda mamaki tad'ago tana kallona, “kamarya bata nan?”.
“Munu... Wlhy ko rantsuwa nayi babu kaffara aciki, akwai dalilin kawomu nan”.
A sanyaye Munubiya tace, “karki damu Sweetheart, ko mai suke nufi ALLAH ya fisu, dama naga mamansu ya hameed tafito d'azu bayan mungama girki, ai d'an hakkin daka raina shike tsolema ido, *_RAINA KAMA KAGA GAYYAFA_* inji masu iya magana.
Hakane dear.
Daga nan muka zauna shiru kowa da abinda take tunani, har barci ya sace Munubiya, nukuma nahau chart kawai.
A gidanmu kuwa su Siyama ne suka fara Isa falon, tundaga k'ofar falon daddad'an k'amshin turaren bak'in yafara rikitasu, sun shiga da sallama, yayinda sukuma bak'in suka amsa.
Gaskiya masha ALLAH dan kuwa matasan samarine k'yawawa masu aji da gayu, suna kama da juna, hakan zai tabbatar maka da cewa jininsu d'aya. sunci ado cikin wasu rantsatstsun shaddoji gizna, sai maik'o sukeyi, d'aya yafi d'aya sakin fuska.
Su Siyama sun gaidasu cikin shauk'i da zumud'in fatan kowaccensu ta kasance abar za6i.
Sun amsa musu cikeda jan aji da nazartar su, ahaka Fauziyya da Safara'u da Haleematu suka shigo suma, suma dai gaidasun sukayi. Fauziyya da Zarah ne kawai sukayi hankalin tashi su zuba musu ruwa da lemo, sannan suka musu bismillar abinci.
Mai d'an yawan fara'ar ne yamusu godiya, sannan yace, “to ya sunan k'annen namune?”.
Cikeda yanga kowacce tafara gabatar da kanta agaresu, yayinda sukuma suka maida hankali sosai wajen nazartarsu, bayan sun gama suma suka gabatar musu da kansun.
“Ni sunan Sulaiman, brother d'ina kuma Sa'eed, munji dad'i kwarai da gaske Na tarbar damuka samu daga gareku”.
Murmushi duk sukayi suna nuna farin cikinsu suma, sund'an ta6a hira.
Babu Wanda yadamu da rashin ganinmu acikinsu sai Fauziyya, iyayenmu kuma basusan babumu ba, dansu suna falon Abbanmu suna hira.
Kusan awa d'aya sannan duk suka fito suka barsu dan sud'anci abinci.
Suna fita Sa'eed ya kalli Sulaiman a yatsine, “my man nida yaran nan nakula sunada rawar kai, garama mai farin kayannan naga kamar tafisu nutsuwa (Fauziyya)”.
“wlhy gskyarka bro... Amma Kasan dolenefa mucika umarnin dad, tunda yayi rantsuwa akan dolene muza6a acikinsu, kai wlhy mun jama kanmu, ni dama tun maganar farko da dad yamana Na maida hankali naza6o da duk hakan bata faruba gareni”.
Cikin ta6e baki Sa'eed yace, “wannan kuma kaika Sani malam. amma basuma 8 akace manaba?”.
“eh hakane, amma kamanta ance biyu acikinsu sunada samari”.
A nanma bakin Sa'eed Yakuma ta6ewa. sun d'anci abinda aka ajiye musu, sannan su Abba suka shigo suka gaisa, cikeda girmamawa suka gaida su Abba, hakan yayima Dady da baba k'arami dad'i, sun kuma tabbatarwa yaran sunada tarbiyya, dama basa kokwanto akan zance yayan Nasu.
An musu rakkiya duka Sassan gidanmu, sun Haida iyayenmu mata. ganinsu Yakuma rud'ar da iyayenmu, kowacce addau'arta ALLAH yasa d'iyarta aka za6a, yo wad'annan zuk'a-zuk'an samari haka, ga kud'i ga ilimi, kowacce saida suka ajiye mata kud'i suke fitowa, har innarmu ma.
Tun aiko kiranmu Innarmu taji ajikinta da biyu aka turamu can, amma baiwar ALLAH hakan bai dametaba, tasan dai wata bata aurar mijin wani, dan haka ko'a fuska bata nunama wani bama cikin wad'anda suka je wajen bak'inba.
Saida Innaro takusa awa d'aya sannan tashigo gidan, yinai tamkar ban gantaba, Munubiya kam tanata barcinta, itama sai bata kulaniba tashige bedroom d'inta.
Shigarta baifi da mintuna 3 ba mukajiyo sallama a k'ofar d'akin, nice Na amsa, Basheer yafara shigowa, sai kuma Sulaiman da Sa'eed, irin k'amshin damukaji a k'ofar d'akin baba karami yasani d'agowa dan jinsa anan, hakan ya tabbatar min da sune sukazo gaida Innaro.
Tunda suka shigo idonsu ya sauka a kanmu, sun kasa d'auke kai daga kallonmu.
Cikeda jan aji nace, “ina yininku”.
Duk suka amsa da “lafiya big girl”.
Basheer yace, “kai Aunty dama kuna nan Ku?”.
Kallonsa nayi nace, “eh, ana nemanmu ne?”.
“a'a, amma dai ba'asan badaku akaje wajen bak'iba”.
Hararsa nayi, saboda sanin halin shegen surutunsa, “malam kaje ka kira musu Innaro ka zauna kana zubama mutane shegen surutu uwa aku”.
Baki ya zum6ura sannan yanufi bedroom d'in Innaro.
Wanda tunda suka shigo yakasa d'auke kai daga kallona, saima zama dayayi kujeraf dake kallona yace, “ok dan bakwa buk'atar ganinmu kuka gudonan kenan? Sai kuma gashi ALLAH ya kawomu mun ganku, dama ance rabon kwad'o...... koko my man?”.
Murmushi Sulaiman yayi, yace “hakane wlhy bro, hakanma dasukayi yamana dai-dai”.
Magan ganinmu yasaka Munubiya tashi, Sulaiman yace, “sleeping beauty kin tashi?”.
d'an waro idanu Munubiya tayi, sai kuma ta kalleni dan neman k'arin bayani.
Innaro takatsemu da fad'in “toku kuna ganin bak'i basai Ku tashi Ku basu wajeba”.
“cikin tsokana Sulaiman yace, “a'a Granny idan sun tashi wazamu kalla? Sun gudo wajenki dan karmu gansu kuma sai gashi ALLAH ya kawomu har gida”.
Ba k'aramin k'ona ran innaro maganar tayiba (dama an kawomu nanne dankar bak'in su gammu balle su za6emu, amma kuma sai gashi sun gammu anan d'in. Anyi gudun gara kenan.....🤣🙊).
Bamu tsaya sauraren abinda innaro zata ceba mukayi fitowarmu zuwa gida.
Su Sa'eed sun gaida innaro, anan take tambayarsu kosun za6a acikin wad'anda sukaje gaishesu acan gidanmu.
Sa'eed yace, “eh mun za6a Granny, amma wad'annan dasuka fita yanzu”.
Caraf innaro tace, “ai wad'annan anmusu miji shiyyasa su basujeba, sai dai cikin wad'ancan”.
Bahaka sukasoba, amma yazasuyi, sai dai har sukabar gidan basu sanar da wa suka za6aba.
Koda muka sanarma innarmu cewa tayi babu ko mai, karma hakan ya damemu.
★★★★★★★★
Har tsawon kwana 5 babu wata magana data fito akan suwa bak'in suka za6a, su Abba basuce da kowa komaiba.
Hankalin iyayenmu mata duk atashe yake, kowa takasa kunne taji wacece aka za6a, sai dai babu mai iya tunkarar iyayenmu maza da zancen, dan duk ba suga fuskar hakanba.
Satinsu guda da zuwa saiga bak'i sunzo wai an kawo kud'in aure.
Hankalin iyayenmu fa yakuma tashi, dan ganinsu wani munafurcin akayi shiyyasa aketa k'unbiya-k'unbiya. Nanfa suka shiga 'yan tsugunne-tsugunne Na gulma irinta gidan yawa.
Kwana biyu dayin haka su Abba suka sanar da cewa nida Munubiya sukace sun za6a.
Innaro ce tafara k'aryatawa, sannan tace, Sam bata aminceba, ina jikokin talakawa 'ya'yan bak'in haure suka kai matsayin auren 'ya'yan babban mutun irin sanata halliru, ai k'aryane sannan munafuncine, agabanta su Sa'eed sukace Zarah da Siyama suka za6a. (Zarah k'anwar ya hameed Ce, babanmu d'aya, Siyama kuwa d'iyar momy Hadiza Ce d'iyar dady).
Jin wannan zance yasa kowa ya fahimci akwai munafunci a lamarin, kowa yasan yanda mamansu ya hameed suke da momy Hadiza a gidan, kansu had'e yake. aikam matan gidanmu suka harzuk'a sunata yada magana, harma abin yaso yazama fad'a, innarmu ce batace komaiba, ita cewama Abbanmu tayi dan ALLAH amaida zancen auren kansu Siyamar tunda innaro tace dama su suka za6a.
Banza abbanmu yamata dan yasan innaro tayi hakanne danta k'untatama innarmu, amma tabbas dabakin su Sulaiman sukace 'yan biyunnan suka za6a, shin sai yaushene inna zata bar muzgunama Aisha da munanata a gidannan?, shekara kusan Arba'in ana Abu guda babu sassauci, tunda yake baita6a ganin rana d'aya da innarmu tama innaro koda kallon banzaba bare rashin kunya, sa6anin sauran matan gidan da basa kunyar ya6a mata magana koda ta habaicine.
Kwana kusan hud'u ana d'auki ba dad'i akan wannan zance, saboda akawo k'arshen maganar sai Abbanmu yace su Sa'eed suzo su nuna wad'anda suka za6a da kansu.
Hummm bamusan miya faruba, (konace mi innaro dasu momy hadiza suka k'ulla ba) munga dai sunta murnar zuwansu Sa'eed d'in, sai rawarkan had'a abincin tarbarsu sukeyi, dan ranar su biyu kacal sukayi, kuma abin mamaki wannan karon agidan innaro aka saukesu.
Bayan isowarsu dakamar mintuna 20 sunci abinci sai akace duk muje gidan innaro.
Su Haleematu duk sun rigamu tafiya, mune k'arshen zuwa muda Fauziyya, saidai muna shiga gidan Innaro ta samu mukabi ta k'ofar kitchen nida Munubiya kawai, Fauziyya kuma aka barta tashiga ta falo.
Yanda sukaita zumud'in kallonmu wancan karon a yau ba haka bane, gaba d'aya hankalinsu Na kan Siyama da zahra, abin ya bamu mamaki har sauran 'yan uwanmu.
Tunda mukaga haka duksai muka fice muka koma gida, su Haleematu harda kukansu, mukanmu zukatanmu sun sosu, dan harga ALLAH Sa'eed ya kwantamin arai.
Wanan lamari saida yajawo gagarumin fad'a agidanmu irinma wanda ba'a ta6a yiba, dan saida takai matan gidanmu da 'Yar tone-tone asirinsu yanda suke kulle-k'ulle wani lokaci akan innarmu da junansu.
Sosai ranar saida ran kowa ya 6aci, amma mamansu yaa Hameed da momy Hadiza su wasai sukejin kansu, koba komai sune a sama suke gani, 'ya'yansu zasuje gidan Hutu.
Abbanmu yasamu innarmu yayta bata hak'uri, dan tabbas yanada tabbacin akwai lauje cikin nad'i akan lamarin, tunda su Sa'eed da kansune suka Samar masa za6insu, amma gashi a wannan karon since su siyama ne ba 'yan biyu ba.
ALLAH sarki innarmu sarkin hak'uri, cewa tayi babu komai, dama can su Siyamar ne matansu, Dan haka tunran gini tun ran Zane, suma sauran ALLAH yabasu Na kwarai.
Sosai Abba yak'ara jin jinama hak'uri da tawakkali irin Na matar tasa, abin sonsa, wadda yakejin har duniya ta tashi k'aunarta dabance a ransa, yana sonta harma baisan yanda zai fassaraba, kullum cikin mata k'yak'yk'yawar addu'a yake akan ribar hak'urin datakeyi da kowa agidan har mahaifiyarsa. yana ganin Kimar Aisha sosai da girmanta, tunda suke babu rana d'aya dazaice gawani abun aibu data aikata masa, sai dai abinda ba'a rasaba saboda zomu zauna zomu sa6a, balle shekara kusan 40 ba wasabace.
★★★★★★★
An tsaida bikin Siyama da Zarah dai-dai danasu aunty Hauwa'u, komai kuma ankawo, saura lefe da sadaki kawai.
Ahaka muka koma makaranta inata yak'in fidda Sa'eed daga raina, ALLAH ma ya taimakeni dama bawai yashiga irin cancikin nan baneba.
******
Yau lectures d'in safe garemu, dan haka mukayi shiri da wuri nida Munubiya, a tsaitsaye mukasha kunun da innarmu ta dama mana, Dan yau girkin mamansu ya Hameed ne, idan bata gadama ba sai takai 8 bata kammala ba, har yara saisun makara,
Aiyaan yashigo d'auke da lunch boxs nasu yana tura baki gaba. “kai kuma lafiya kake cuno baki uwa na agwagwa?”.
6ata fuska yakuma yi tamkar zai fasa kuka, ya zube lunch boxs d'in saman kujera “Aunty ba mama bace tace wai yau batayi abincin dazamuje dashi makaranta ba, hakama fa jiya abincin dare ta d'umama ta zuba mana, amma damukaje school saigashi a kulan Haneep Indomi ne da kwai”.
Aryaan ya kar6e da cewar “ALLAH kuma aunty namu tsami yayi kafinma muci, haka mukadawo da yunwa”.
tausayi yaran suka bani, Munubiya tace, “kuyi hak'uri kunji 2 d'in inna, watarana sai labari ai”.
Kansu suka jinjina mata sukace “to aunty”.
innarmu tana jinmu amma uffan bataceba.
Fita nayi batareda nacema kowa komaiba, wani shago dake can k'asan layinmu naje, nasiyo musu yoghurt da cake k'ananu, nahad'o musu da biscuits.
A harabar gidan Na iskesu harsun fito, sauran yaran sunata shiga school bos d'insu da ake kaisu makaranta. School bag d'insu nabud'e Na saka ma kowa nasa, sannan nace ayi karatu da k'yau kunji babys d'inmu”.
Cikeda jin dad'i suka amsa min da fad'in “to auntynmu”.
Kumatunsu Na sumbata sannan na taimaka musu suka shiga motar suma.
Ina shigowa munubiya tamik'e tana fad'in “wai ina kikaje? kinsanfa jarababben lecturer d'inanne zai shigar mana yau”.
“sorry sweetheart tashi muje”.
Dubu 1 innarmu tamik'o mana, kar6a mukai muna mata godiya, muka fito tana binmu da addu'oin fatan alkairi.
Mun lek'ama su Siyama, kowacce sai tace batada lectures d'in safe, fauziyya da Feedausi ce kawai muka tafi, dansu duk department d'inmu d'ayane..........✍🏼
One luv🥰🥰
*_ALLAH ka gafartama iyayrnmu👏🏻😭_*
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻5⃣
...........Wajen 4pm muka fito daga cikin makaranta, mu 6 ne yanzu, sa6anin d'azu damukazo mu hud'u, bayan tahowarmu Safara'u da Haleematu suka taho suma, duk da mun rigasu gama lectures sai muka jirasu suka fito muka rankayo tare domin tafiya gida, bamu samu school bos ba, dan haka muka da6o sayyadarmu har zuwa babban gate, muna tsaitsaye abakin titi, tareda wasu daga cikin tsirarun d'alibai irinmu, tundaga nesa muka hango tahowar motocin da uban gudu, saika d'auka sukad'aine akan titin saboda gudun dasuke tsulawa tamkar zasu tashi sama. duk baya muka matsa, dan tabbas wad'annan suka sameka babu abinda zai hanasu takeka su wuce batareda sun damuba.
Tamkar wucewar iska haka suka dinga gittamu, jikake shuuuu!! shuuu!! shuuu!!.
Furicin wani mayshin saurayi dake jingine jikin motarsa yazo d'aukar wasu 'yan mata biyu dake gefenmu 'yan matan sunada jin kan masifa, ko'a makarantar bakowa sukema maganaba, department d'inmu d'aya dasu amma ko kallo basu isheniba, dan ko sallama bata ta6a had'ani dasuba..
Saurayin yabi motocin da kallo yana fad'in “tab ashe *_GALADIMA!_* yashigo gari kenan?”.
“Da gaske yaa Usman?”. ‘d'aya acikin 'yan Matan tafad'a cikin matuk'ar zumud'i’.
Yace, “da gaske mana baby, baga motocinsa kuna ganin sun wuceba”.
Dan danan suka shiga murna, kai kace an musu albishir da aljanna ne.
Baki na ta6e inajan k'aramin tsaki. Fiddausi tace, “to waye shi galadima d'in?”.
“oho musu”, ‘cewar Munubiya’.
Budurwar dake tsaye d'ayan gefenmu itada saurayinta suna jiran abin hawa suma tace, “Galadima d'an Sarki kenan, *Yarima Sameer!”*.
“humm lallai kuce manyane, shiyyasa suke gudun da kosunbi takan talaka babu abinda za'ayi”. ‘cikeda 6acin rai nake maganar’.
Dariya su siyama sukayi suna fad'in “toke ina ruwanki?, k'asarfa tasuce, sai yanda sukayi da ita, tsakaninmu dasu saidai mu hangesu cikin mota ko ranar hawan salla”.
Dogon tsaki nakuma ja tareda kauda kaina daga garesu na maida hankalina wajen tare wata taxi dake gabatomu.
A motama firar dasu Haleematu sukaitayi kenan, ta Galadima ne ko uwarmi ne ma Na manta. nidai uffan ban kuma tofawaba, hasalima haushi hirar tasu takoma bani, dan mai taxi d'in yasaki baki sai wani basu labarin Galadima d'in yakeyi dakuma kwarzan tashi, earphone na jayo a cikin lady's bag d'ina na manna a kunne danma nabar jinsu gaba d'aya.
Saida muka iso gida sannan Fauziyya dake kusa dani ta zungureni, d'agowa nayi Na kalleta sainaga duk sun fice, bance komaiba nafito nima.
Mun iske innarmu bata nan, saisu Aiyaan kawai zaune a falo suna kallo, shigowarmu yasasu tasowa da gudu suna mana oyoyo, muma mun taryesu da murnarmu, Munubiya tace, “Aryaan miyasa baku cire Uniform ba kukayi wanka?”.
“yo aunty mun dawo munga Innarmu bata nanane”.
Nace “innarmu bata nan? to ina taje?”.
“muma bamu saniba aunty, munje kuma kitchen bamuga abinci ba, kuma yunwa mukeji”.
Munubiya tace, “ya salam, kujira ina zuwa”.
Fita tayi, babu dad'ewa sai gata tadawo cikin damuwa, ina cirema su Aryaan Uniform, Na kalleta ina fad'in “mike faruwa Munu...? Ina abincinne?”.
Kwallar idonta ta share, ta zauna bisa kujera sannan tace, “naje mama tace wai innarmu ta d'auka abinci tatafi dashi hospital, dan haka shine rabonmu”.
Raina a 6ace na mik'e zan fita, da sauri munubiya ta ruk'oni, “please Munaya, kibarta kawai, yakamata mu kira innarmu muji waye a hospital? Inaga wannan yafi komai muhimmanci nake gani akan abinda mamar tamana”.
“Haba Munubiya, wannan wane irin rashin mutunci ne, wai mi Matan gidannan suke tak'ama dashine? Idan suna tak'ama da Ubanninsu muma ai nan gidan Ubanmune ko, yanzu ace yarannan kamar su Aryaan su dawo school tun 3 amma ahanasu abinci, wannan wane irin zaluncine? Kisakeni kawai naje naci kutumar uban matarnan munubiya, wlhy sai dai yau Abba yace nabar masa gidansa”.
“A'a munaya, duk hakama bata tasoba, idan hankali ya6ata hankali ke nemosa, bai kamata mutaru muzama d'ayaba mu da su. bara kawai naje kicin d'in Na dafa mana wani abun mai sauk'i, kiyi hak'uri dan ALLAH, kinga innarmu bazataji dad'iba idan tatarar da faruwar hakan”.
Badan raina yaso ba Na hak'ura, saman kujera nakoma Na zauna ina huci, nikad'ai nasan minakeji a zuciyata.
Munubiya tafita dan nema mana abinda zamuci, nikuma Na d'auki waya domin Kiran innarmu naji abinda tajeyi asibiti.
Harta katse bata d'agaba, nakuma kira akaro Na biyu sannan ta d'auka, gaisheta nayi da tambayar mitajeyi asibiti?.
Daga can tace min Nafisar mama Rabi'a Ce jikinta ya motsa yanzu hakama jini ake buk'ata amma an Gaza samu, gashi yaa marwan dayakan bata jinin baya nan yayi tafiya shida Abbansu.
Hankalina a tashe nace “innarmu ganinan zuwa yanzunnan insha ALLAH, kuna general hospital ne?”.
“eh muna nan”.
“ok insha ALLAHU ganina zuwa”.
'Dakinmu nashiga da Sauri nad'an watsa ruwa a tsaitsaye saboda naji dad'in jikina, komai ban tsaya shafawaba Na zira doguwar Riga jallabiya Na fice da hanzari. A k'ofar fita falo naci karo da munubiya d'auke da babban faranti tazubo spaghetti tanata turiri.
namatsa baya da Sauri INA fad'in sorry, munubiya bara naje asibitin wajensu innarmu, wai jikin feena ne ya motsa kuma ana buk'atar jini, gashi yaa marwan sunyi tafiya da abba”. Munubiya tace, “toko Na juye mana abincin a kula mu tafi gaba d'aya?”.
Nace, “a'a munu... Ki zauna dasu Aiyaan bara naje ni kad'ai, baikamata mubar wajen ba kowaba”.
“to shikenan, yanda akayi ki ta6oni awaya, amma in kunkai dare zakuganmu muma, abincinfa?”.
“humm munu bar abincinnan, banida wata nutsuwar cinsa, saina dawo”.
Ban jira amsarta ba nafice. ALLAH ya taimakeni INA fita nasamu napep. Mintuna kad'an muka isa hospital d'in, kud'insa na biyashi nashige da hanzari ina k'ok'arin kiran innarmu.
Babu dad'ewa kuwa ta d'aga, nace mata gani acikin asibitin. Kwatance tamin na inda aka kwantar dasu 6angaren masu sikila.
A rikice na iske innarmu da mama Rabi'a, saboda jikin feena ya motsa mata sosai a wannan karon.
Nace, “mama yanzu mi ake cikine?”.
“Rashin jininne matsala yanzu Munaya, sunce kuma anemoshi da gaggawa, to dama can jinin Fadeel baya yimata shiyyasama ko gwadasa ba ayiba, Marwan dake bata kuma sunyi tafiya da abbansu”.
“mama ina zuwa, bani takardar da suka baku”.
Mik'omin tayi nafita da saurina. dukna rikice inata kai kawo dan ganin ansami jinin, amma har magriba ta rufa ba a samuba, saboda jinin feena yanada wuyar samu, ana cikin kiraye-kirayen sallar isha'i saiga Ayusher ta iso itama, dama an barta a gidane saboda babu kowa, to takasa hak'uri tabiyo sahu, da ita muka cigaba da shiga da fita, saida aka fito sallar isha'i ALLAH yasa aka dace da samun leda 1, saura 1, dama biyu suke buk'ata. ana cikin d'aura mata saiga Munubiya ita dasu Aryaan da kulolin abinci.
Koda aka gama sakawa sai muka koma Neman d'ayar ledar data rage, yanzu harda munubiya muke tare.
Muna a lab d'inne muna shawarar ko a d'iba namu jinin idan zaiyi babu damuwa. Takun takalman damuka jiyo yasamu juyawa harda likitan da maganarsa takatse bisa k'ok'arin bamu amsa dayakeyi. wani ni'imtaccen k'amshine ya iso hancinanmu tunkan mamallakin turarenma yakai ga isowa inda muke. d'auke kaina nayi na maida ga mai d'ibar jinin.
Likitan naga yafara gyara kujera yana fad'in “dama yalla6ai ya shigo gari yau? Ni nama manta yaune ranar dayake bada jini”.
Bai samu mai bashi amsaba a cikinmu har tawagar Wanda yakira yalla6ai suka iso wajen.
Munubiya da Ayusher suka matsa gefe saboda wata uwar tsawa da masu take masa baya suka daka mana, nikam koma motsawa banyiba bare nasan ALLAH yayi ruwansu awajen, saima baki dana ta6e na d'auke kaina daga saitin dasuke.
Bulala d'aya daga masu jajayen rigunan ya d'aga da nufin zubamun.
“Wanda suke kira Yalla6ai dake zaune a kujerar da doctor ya ajiye masa ya d'agamasa hannu da Sauri, alamar karya dakeni”.
Cikeda girmamawa yace, “angama zaki s.........”.
Hannu Yakuma d'aga masa alamar baya buk'atar kirarin.
Baki nakuma ta6ewa sannan na ra6a ta gefensu nafice, banga fuskar Yalla6ai d'in nasuba, saboda ya juyamin bayane ni, sananan shima tunda yashigo bai kalli kowaba a lab d'in, yanata aikin danna wayarsa, kuma baiyi magana ba, ko doctor da Norse's d'in da suka gaidashi hannu kawai ya d'aga musu, kuma ko d'agowa baiyiba yanata aikin danna waya kai kace zai danno hanyar zuwa aljannane aciki.
Waje na dawo nayi zamana ina cigaba da game a waya, su Munubuya dai suna cikin, bansan uwarmi suka tsaya yiba awajen.
Kusan mintuna 40 saigasu sunfito, takun takalmansu kawai naji, amma ban d'agoba, sai k'amshin turarensa daya cika illahirin wajen, saikuma gaisuwar da mutane keta faman zubewa sunayi masa, ko sau d'aya banji ya amsaba.
Tsaki naja inamaijin haushin wannan mutumin, to wayema shine? dayakema mutane wannan jinkan., motsooww aikin banza kawai.
Tabbas yaji tsakin da akayi, hakanne yasakashi d'ago k'yawawan idanunsa yakai duba saitin Inda yajiyo tsakin, akan *munaya* dake zaune bisa kujerun dake Jere awajen ya sauke su, sai dai baya ganin fuskanta sosai, saboda ta duk'ar da kai tana danna waya, kuma gyalen jallabiyarta yarufe mata Rabin fuska, ita kad'aice zatayi wani motsi awajen suji, dan tafi kusanci da Inda suke tsaye.
Janye idanunsa yayi kawai daga gareta, yay saurin d'agama bayin dake k'ok'arin tafowa gareni hannu. Cikin Wata tattausar murya mai aji dake cike da k'asaitar masu isa najiyo yana fad'in “Bayta kawai”.
Cikeda girmamawa bawan yace, “ya shugaba tsaki tayi fa”.
Shiru yay kamar bazai tankaba, saikuma najiyo yace, “kasan dawa take?”.
Bawan girgiza kai yayi alamar a'a.
Bai sake cewa komaiba yay gaba suka bishi a baya.
'Dago ido nai nabi bayansu da kallo, sainaga sun nufi 6angaren mata masu haihuwa.
janye idona nayi ina fad'in “kadaiji dashi Malam, kana fama da Girman kai kamar wani Sarki? Abinma dariya ko (R) bai iyaba, wai bayta”.
Dai dai nan su Ayusher suka iso cikeda farinci, hannunsu d'auke da ledar jinin
Cikeda jin haushi nace, “wai uwarmi kuka tsaya yi acikin lab d'inne?”.
“Uwarmu ta gode”. ‘ cewar Ayusher’.
Munubiya kuma tace, “zaman namu aiko yayi amfani, tunda gashi mun samo sauran jinin ko”.
Na kallesu da mamaki, “ina kuka samo jinin kuma to?”.
“Galadima ya bayar”.
Cikin ta6e baki nace, “miye kuma Galadima? A inama kukaga wani Galadima kome ma kukace?”.
“wanda yashigo muna cikifa, ai Galadima ne (Yareema Sameer d'an sarki)”.
Ido na waro waje, “wai kuna nufin wannan mai shegen girman kai d'in dama shine Galadiman? kenan munu.... shine yawucemu d'azu munfito makaranta?”.
“kwarai kuwa sweetheart shine, kuma wlhy bashida Girman kai kamar yanda kike zato ko Sis.. Ayusher? ”.
“Wlhy kuwa hakane Munu..., ashe duk k'arshen ko wane wata saiyazo asibitinan yabada jininsa gamasu buk'ata, gashi jinin nasa mai irin wahalar samu d'inanne irinna feena, kai mutuminnan yayi wlhy, Sarauta ba karya baceba, danyau naga tsantsar sarauta da mulki da k'asaita ajikin Galadima, yanzu haka zai zagayane yaduba marasa lafiya”.
Harara na ballama Ayusher daketa zabga surutu uwa aku, na warce jinin daga hannun munubiya ina fad'in “idan kun gama shirmen kwa taho”.
Kallo suka bini dashi, Ayusher tace, “Anya yarinyarnan batada aljanu?, ke kowama bai mikiba?, yanzu nan duk had'uwar Galadima Munaya tana nufin bai burgeta ba kenan?”.
Dariya Munubiya tayi, sis... Ayusher har yanzu baki gama fahimtar Munaya ba na lura, kyagama abinda yafi haka indai daga wajentane. Yanzu hakama tunda kikaji tace haka ko sau d'aya bata kalleshiba wlhy bare tasanma kalarsa. kinga muje kinji.
“humm aiko wlhy inabata kalleshiba anyi babu ita kuwa, ruwa ta shata kuma, yo kobabu komai aina bada koda labarine nace nata6a ganinsa ido da ido ko”. ‘cewar Ayusher’.
Dariya kawai Munubiya tayi, taja hannunta suka tafi.
Sanda suka iso harma an fara k'ok'arin sakama feena jinin, dama wancan yak'are.
Duk muna zaune a k'ofar d'akin bisa kujerun wajen, Aryaan da Aiyaan duk suna jikin mama Rabi'a barci ya d'aukesu, fadeel na kusada innarmu yanacin abincin dasu Munubiya suka kawo, zama nayi kusada fadeel d'in na saka hannu nad'au cokalin dayake cin abincin ina fad'in bro... nimafa yunwarnan nakeji, rabona da abinci tun kusan 1 danaci a kafteriya na makaranta”.
Kallona yayi yana cewa “sannu da k'ok'ari sis...., shiyyasa gakinan tsula guda bak'ya gaba bakya baya keda munu....”.
Cokalin nakai zan kwala masa a kai ya kauce yana dariya, nima dariyar nayi na d'auki kular abincin na k'ara mana.
Muna cikin ci Ayusher ma tamatso tace zataci, munci mun k'oshi sannan muka gyara wajen, mama da innarmu ma sukaci, dan zuwa yanzu duk mun sami 'Yar nutsuwa.
Kusan 10pm saiga Abbanmu shida baba k'arami, duk muka gaidasu suka tambayi mai jiki, innarmu da mama Rabi'a suka amasa musu da sauk'i.
Har d'akin suka shiga, suka duba feena daketa barcinta, sannan sukace muzo mu tafi gida, za'a bar innarmu da mama Rabi'a su kwana.
Saida safe mukai musu muka fito, Fadeel ya d'akko Aryaan, baba k'arami ya d'akko Aiyaan.
Saida muka fara sauke Ayusher da Fadeel gida sannan mukuma muka wuce.
Mun tarar gidan tsitt alamun duk anyi barci, saidai masu wayar dare da samari irinsu aunty Ramla, saikuma masu charts.
Abbanmu da baba k'arami suka d'auki su Aiyaan, har d'akinsu suka kaisu sannan suka fita.
Muma shirin barci mukayi muka kwanta cikeda kewar Innarmu, muna kwanciya muka kirasu da k'arajin mai jikin sannan muka tafi duniyar barci muma, dagani har Munubiya babu mai wani saurayin da zamu 6ata lokaci wajen yin hirar dare...............✍🏼
Kumuje zuwa my guys🤩👎🏻
Gobe idan ALLAH ya kaimu baza kujiniba, inada wani d'an uziri, sai Monday idan ALLAH ya kaimu kuma.
https://chat.whatsapp.com/K1qwmMusX7ILDLATGSvfHJ
*_RAINA KAMA........ FANS CLUB_*
_Duk Wanda yasan yana karanta wannan buk d'in ya garzaya yanemi link Na RAINA KAMA FANS CLUB, a wannan gidan kawai zan dinga posting a halin yanzun, awannan karon bazan turama kowa buk ta PC ba, narigada nayi rantsuwa. Amma annan zaka iya samu da faro, sannan inhar ba'a tattaunawa akan novel d'in zanyi waje da mutum babu ruwana, kuma kar a turomin kowanne novels acikinsa Dan ALLAH, inba hakaba zan fidda mutum ko Yaya nake dashi🙅🏻, nabud'e gidanne saboda anan kawai zan dinga posting yanzu, sai wasu groups dabasu wuce 3 ba._
Ina fata zaku bani had'in kai please, inba hakaba ALLAH zai koma Na kud'ine saboda tsaro ba tsoroba😎🤣
One luv🥰🥰
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu👏🏻😭_*
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_____________
*_ASSALAMU ALAIKUM_*
_Jiya da daddare akaita kirana mutane Na tanbayata Yaya jiki, tun ban fahimci maganarba hardai nafara tsarguwa nayi tambaya. Dan sai kira kan kira ake jeramin, wata take sanar dani taga wani posting ne yana yawo wai za'amin CS. babu shiri nabud'e data naga mike faruwa, group d'in farko dana bud'e sainaci karo da wannan posting d'in mutane nata comments, nabud'e nabiyu ma hakan dai._
*_Assalamualaikum Alaikum,Dan Allah kuyiwa billyn Abdul(ma rubuciyan RAINA KAMA. Adua'baby ya mutu a cikin ta zaa cire Mata Shi yanzu_*
_sai daga baya nakejin Bily galadanci ce batada lfyar, amma wata ta maida zancen haka saboda sunan namu yazo d'aya, to ALLAH yabata lfy itama._
_sannan ina shawartar jama'a Dan ALLAH kuringa nutsuwa wajen tantance Abu kafin Ku yad'ashi, domin wadda tayi wancan write up d'in ta zaunane ta tsara nata son zuciyar, wadda tayi posting d'in farko akan ciwon Bily galadanci sunan Bily tasaka ba nawaba, itakuma ta canja nata tsarin tashiga ya d'awa, ALLAH ya shiryar damu, yakuma bama marasa lfyarmu lafiya._
*banyi niyar posting ba yau, amma ganin wancan write up d'in yana cigaba da yad'uwa yasani dole yi Dan na warware muku zancen.*
______________________________
👉🏻6⃣
.......Bamusan abinda yafaruba, mukaji 'yan gidanmu suna k'ananun magana da safe, wai girkin jiya na dare da mamansu yaa hameed tayi sai asararsa akayi, girkin yay d'anye yak'i dahuwa, kuma a gas tayi girkin bare ace iccen yabata matsala, gashi kuma normal gas d'in yake aiki.
Muna cikin yima su Aiyaan shirin school muka fara jiyo hayaniya, sai da muka gama musu shirin sannan muka fito, cirko-cirko muka iske 'yan gidanmu, yayinda mamansu yaa hameed keta zabga masifa. tana fad'ama abbanmu wai mune muka mata kwari shiyyasa jiya abinci yay mata d'anye danta hanamu abinci, kuma gashi yanzuma tasaka doya amai tak'i soyuwa.
Ni dariyama taso bani wlhy, wai mune muka mata kwari, to miye kwarinne ma datake magana a kai? danni bamma sanshiba.....
Maganar Abbanmu ta katsemin tunanina.
“ 'Yan biyuna kuzo nan naji kunji”.
K'arasowa mukayi kusada abbanmu harsu Aiyaan, ya kallemu cikeda kulawa, “haba 'yan albarka mike faruwa haka?”.
Cikeda rashin fahimta nace, “Abba a ina?”.
“haba twins d'in Abba, bakuji mi mamanku take fad'aba? abinci yamata d'anye jiya da yau”.
“amma Abba Dan abinci yayi d'anye kuma sai ace mune? Kagafa jiya munama asibiti bamuci abincin dareba agida, darana ma mama hanamu tayi tace innarmu tatafi da kasonmu asibiti, haka muka dawo muka iske su Aryaan sunajin yunwa, sai Munubiya Ce tamana girki, kuma tayi takai mana wani asibitin, ni wlhy Abba bammasan wani kwari dasuke maganaba akai, wannan ai canfine, tunkuma zamanin da aka barsa”.
“canfin uwarki, kujimin munafukar yarinya, inbakune kukayi muguntarba uwarwaye yayi, to wlhy ahir d'inku, ba 'yan biyu ba ko 'yan gomane ni ubanku zanci a gidannan.......”
Afusace Abba yace, “to ai gani, saikizo kici ko, ai gaskiyama yarinyarnan tafad'a, wannan canfine kawai, dan abinci yayi d'anye saikuma a fassarashi dawani Abu daban, haba Dan ALLAH, saikace wata mara ilimin addini? Karna sake jin wannan maganar, inba hakaba rankowa zai 6acine a gidannan”.
Yana gama fad'a yabar wajen. muma ganin haka muka tasa su Aiyaan gaba muka koma 6angarenmu. duk da nakasa fassara mi mama ke fad'i hakan yamun dad'i, koba komai dai ai ALLAH yamana sakayya da hanamu abinci datayi muda wad'anan k'ananun yaran da basu da alhakin kowa.
Yanzuma munubiya Ce ta dafo mana indomi mukaci, sanan ta zubama su Aiyaan a kulolinsu Na makaranta, suna tafiya muma mukayi shirin tafiya School.
Bamu tsaya jiran sauranba mukayi gaba saboda zamu biya ta asibiti, kuma munsan acikinsu babu mai binmu, harmun fita saiga Fauziyya tabiyomu, itama zataje taduba feena d'in.
Alhmdllh munma tarar an sallamesu sunata shirin tafiya gida, mukaima feena sannu, ta amsa tana fara'a da tambayarmu ya makaranta?. mukace gatanan zamu tafi.
Bamufi mintuna 30 ba muka fito, Fadeel ya d'aukesu, mukuma muka wuce school.
A mota Munubiya take bama Fauziyya labarin ganin Galadima damukayi jiya a asibiti, ko sau d'aya ban saka musu bakiba har muka sauka.
★★★★★
A wannan karon har mamansu yaa hameed tagama girkinta Na kwana biyu asarar abinci akaitayi, Dan kullum d'anye yake mata. hakan yasa taita sakin habaici agidan itada muk'arrabanta irinsu momy hadiza,.
Maman Fauziyya ta sanar ma innarmu komai tun randa taje duba feena agidan mama Rabi'a, Dan haka Innarmu tayi kunnen uwar shegu dasu, tamkarma batasan da ita sukeba balle ta nuna tama fahimci zancen nasu.
Innaro ma tazo tayi tata tsiyar San rai, tabi duk ta zagemu dacin mutuncin innarmu, koma fitowa innarmu hanamu yi tayi, har Innaro tagama tafice. Matan gida najin dad'i.
★★★★★★
Haka rayuwar tacigaba da tafiya, yau da gobe kayan ALLAH har gashi azumi ya rage saura kwanaki uku kacal a fara, Dan haka musulmai NATA shirin tarbar wannan wata mai tarin albarka da falala.
Kasuwanni sun cushe saboda yawan hada-hada, duk da 'yan kasuwa sunyi taiyar tasu ta k'arama abinci kud'i, maimakon su sassauto bayin ALLAH su sami sauk'i (ALLAH ka shirya 'yan kasuwarmu subar wannan hali dai).
A 6angaren gidanmu ma iyayenmu maza duk sunyi shirin, Dan dukkan wani abun buk'ata an tanadeshi, sai abinda ba'a rasaba dazai iya lalacewa idan an ajiye, wannan anbarsa yayunmu maza su ringayo cefanensa kullum kamar yanda aka saba.
Itama Innaro an ajiye mata dukkan abinda zata buk'ata, dukda kullum daga gidanmu ake kaimata abinci, safe yamma da dare, kuma dolene kowane 6angare sai sunkai nasu.
Muma a 6angarnmu munyi dukkan namu shirin, dukda abin zai had'e mana da zuwa makaranta, hakan yasa nake tausaya mana, gashi ana tsula rana mai zafi kuma.
Alhmdllh yau ta kasance Alhamis, kuma yaune ake saka ran ganin wata atashi da azumi washe garin juma'a.
Har zuwa 9pm kunnen kowa naga redio da talabijin, jira kawai Muke muji sanarwa daga sarkin musulmai. sai wajen 9:30pm sanan aka Sanar da ganin wata, duk wani Muslim yana cikeda d'okin fara azumin watan Ramadan da zamu Shiga goma ta marmari (inji hausawa😂).
Tun alokacin duk muka d'auki niyya, kasancewar girkin innarmu ne tayi shirin tafiya d'akin Abbanmu, muma tace mu kashe TV muje mu kwanta kar atadamu da asuba kuma muzo muna k'unk'uni.
Badan mun soba muka kashe mukaje mukai shirin barci muka kwanta da addu'ar abakunanmu.
Aiko da asuba dak'yar innarmu ta iya tashinmu mukai sahur, tea kawai muka shama, dama mu bama sahur da abinci nida munubiya, garama ita wani lokacin takan had'a da kunu ko fura.
Bamu kwantaba saida akayi sallar asubahi, still kwanciya muka kumayi, sai 8 innarmu ta tadamu, kasancewar yau saima 10 mukeda lecture, kuma zamu fito 12 ne.
Tunkan aje da nisa azumin yafara garani, dak'yar Na daure aka kammala lecture muka fito, amma badan Na fahimci komaiba nidai yau.
Su Munubiya sai dariya suke mini wai Raguwa, nidai ban kulasuba, Burina kawai naga mun Isa gida Na kwanta.
Tunda muka dawo school nazube a falo k'asan carpet, ban sake Sanin duniyar danake cikiba saida munubiya ta tadani nayi salla, Ashe harsu Aryaan sun sako masallacima inata barci, sallarma dak'yar nayita atsaye, INA kammalawa nakuma kwanciya.
“oh ni Aisha, wai Munaya mikikeson maida kankine? yanzu azumin kikema langa6e haka? saikace yau kika fara azumi a rayuwarki?”.
“ALLAH innarmu bazaki ganeba, nidai ALLAH yasa akira salla da wuri”.
Munubiya dasu Aiyaan suka sakamin dariya. “Aunty yanzufa k'arfe 2 ma, sauran kusan awa 5 dawani Abu asha ruwa”. ‘Aryaan yafad'a yana dariya’.
Harara Na Dalla masa INA fad'in “ALLAH inbaka rife wannan bakin naka mai gajerarrun hak'oraba zaka dakune, Dan k'aniyarka kaiba yanzu kagama lodama cikinka abinciba?”.
Aunty nimafa Dan innarmu bata tadamu baneba kawai, amma insha ALLAHU gobe zamuyi ko Aiyaan?”.
cikin zumud'i Aiyaan yace, “eh mana, muma zamuyi bro”.
“kuma wlhy yaro bai Isa karyashiba, garama karku d'auka”.
Munubiya tamik'e tana dariya, “imm innarmu bara kiga naje nafara rage aikin, miza'ayi?”.
“ki fere doya kafin Na fito, Munaya tashi maza kuje, kekuma ki gyara kayan miya”.
“wayyo innarmu ki tausaya min mana”.
“mukuma mu kashe kanmu tunda bama azumin ko?”. ‘cikeda gatse tayi maganar’.
“a'a innarmu, bara naje kodaga zaune sainayi”.
“kimayi daga kwance, raguwar banza kawai, ai mijinki yashiga uku, wataran sai yadawo aiki baki gama abinciba”.
Baki Na tura gaba sannan nafita.
Mun rage aiki sosai kafin la'asar, sai bayan sallar la'asar d'in 'yan Matan gidanmu suka shishshigo kitchen d'in kamar yanda aka saba, dama duk shekara gaba d'aya muke had'uwa a kitchen d'in 6angarenmu ayi abincin bud'a Baki, saidai saboda munada yawa akanyi time table saboda a rarrabu kowa da ranar da Zai taya mai aikin ranar.
Da yake aikin yawane dandanan muka kammala kafin 6, a can tsakar gida aka shinfid'a manyan tabarmi bayan an tsaftace wajen, duk azumi gaba d'aya muke had'uwa asha ruwa dama anan, kafin matar ya hameed ta rasu har itama anan suke zuwa suyi bud'a Baki.
Bayan mun had'u mun gama shirya komai kowa yanufi 6angarensu ya watsa ruwa kafin akira salla, dolene kaga jama'ar gidanmu aranar mu burgeka, babu fad'a babu hantarar juna, (yo kowa azumi yagama cin k'aniyarsa🤣🤪).
Kasan cewar babu wuta ya kamal yazuba fetur a Gen... Ya tada, kowa yayi wanka saiyayi shirinsa da alwala yadawo tsakar gida ana jiran kiran salla, yara dabasuyi azumi baneba suketa shargallensu a tsakar gidan.
Yanda na zube a tabarman tamkar mara kashi yasaka yaa Shafi'u fad'in “kai kekam anyi raguwar yarinya wlhy, nasan dai Munaya Ce, Dan Munubiya tafiki jarumta”.
Dariya wad'anda ke wajen sukayi, yaa Naseer yace, “gaskiya mijinki yaga banu, yo idan yayi wasa dai bazai dinga cin abincin bud'a bakiba a gidansa”.
Cikin dariya Aunty Hauwa'u ke fad'in “sai ya d'auka mata 'Yar aiki ai”.
Caraf maman Safara'u ta amshe zance... “yo basai idan mai halin d'aukar 'Yar aikin bane, ana fama da masarar tuwo da shinkafa a jajibo mai aiki?”.
Gurin tsit yayi kamar ruwa ya cinyemu, da alama kowa baiji dad'in furucin Na maman safara'u ba, sai mamansu yaa hameed ce tayi dariya itada momy Hadiza.
Ganin abin zai koma cin zarafin juna sai maman fauziyya ta d'ako wani zance, daga nan aka koma hirar d'inkin salla. babu dad'ewa ma aka kira sallar magriba, cikeda d'oki kowa yafara k'ok'arin cin dabino. tab aini kam bandani, tuni Na d'ebi ruwa mai sanyi nafara sha, Dan shine babban burina. a gida mukayi jam'i, baba k'arami yajamana limanci. da ganan kuma kowa ya maida hankalinsa wajen bud'a baki, harda su hajiya innaro😕, tayi kane-kane ita masu gidan 'ya'ya😏, koda wasa dagamu har innarmu babu Wanda yashiga sabgarta gudun gwalasa, har aka gama lafiya muka gabatar da sallar isha'i da asham. daga nan aka d'an ta6a hira kowa yahad'a kan 'ya'yansa zuwa 6angarensa.
haka muka cigaba da gudanar da ibadar azumin watan ramadan, tun ina ragwan taka harna fara daurewa, an gama goman farko aka shiga ta biyu (goma ta wuya🙊 ).
Gaskiya nad'an wahaltu a tsakanin, ga makaranta ga aikin gidanmu dabaya k'arewa, ko wanke-wankema ya isheka, dukda had'uwa akeyi anayi kuwa.
Azumi yana 13 aka kawo kayan sallarmu, an bajesu tsakar gida kowa ya za6a, kala uku-uku ne dama duk shekara, atanfa, shadda, les, saikuma iyayenmu mata su k'ara mana gwargwadon abinda ALLAH ya hore musu.
Munada telolinnmu masu mana d'inki iya 'yan gidanmu kawai, shiyyasa bamuda matsala. Washe gari kuwa sukazo suka gwadamu, kowa aka saka sunansa ajikin kayansa da style d'in data za6a.
Innarmu ma sun saya mana itada mama Rabi'a, dan tunma kan azumi an kammala mana d'unkunanmu mudasu feena, (innarmu tana business itada mama Rabi'a) shiyyasa duk wani abun kwalliya Na 'yan mata bama rasashi, duk da dai 'yan gidanmu suna mana d'agawar sun fimu komai, saboda danginsu masu kud'ine, suna ganin kayansu sunfi namu tsada. hakan baita6a damunmu ba, dan aganina duk sutura sunanta sutura, yawan kud'in nawani bai d'ad'ani da k'asaba, to barema Munubiya da babu ruwanta.
Ana cikin haka muka shiga goman k'arshe Na azumi (goma ta d'okin sallah🤪😂).
Ranar wata weekend yayyanmu maza suka kwashemu domin za6o takalma da sauran tarkace Na kwalliya, dama duk ankai yaran suma kowa ya za6o, mu matasan 'yan matan muka rage dakuma yayyenmu su Aunty khaleesa.
Plaza ce babba mai k'yau da burgewa, kayansu Na manyane, amma yayyenmu dayake sunaso mufito suka kaimu can, sa6anin da da ake kaimu kasuwa kamar sauran yaran, su aunty khaleesa ne kawai ake kawowa nan saboda sune manyan 'yan mata, to yanzu muma mun shigo layi💃🏻.
Sosai muka rikice da tsarin wajen, takalmane 'yan waje wad'anda duk inda kayi taku sai an kalleka ansan kagama Isa. Harda bags, kayan makeup, turarurruka da dogayen ruguna irinsu Arabia's gowns, gyalilla da kayan 'yan kunne, kananun Maya Na garari Na mata da maza, kai inaga babu abinda zakazo Baja sameshi awannan PLAZA d'inba kam”.
Lallai an narka dukiya a wannan waje, ko plazan wanene? oho. munga dai sunan plaza d'in *BIRNIN GAYU!!*
“Lallai kuwa taci sunanta birnin gayu”. ‘ cewar Anty Ramlah’.
Haleematu tace, “wlhy wannan ace plaza d'in mijinace to bazan maimaita kaya sau uku ba, hakama waya duk wata za a dinga canjamin”.
Dariya tabamu, dan haka muka shiga darawa kuwa. kowa yad'auki abunda yakeso gwargwadon iko, yayyanmu suka biya da kud'in dasu Abba suka basu, sannan suka cika mana danasu kud'in, kowa yafito cikin farin ciki muna jera musu godiya, mun d'auki picture's sosai awajen kuwa. muna tafiya a mota nake cewa yaa Anas dan ALLAH wai Plaza d'in waye wannan?”.
“ai plaza d'in ta babban kwaroce k'anwata, plaza d'in *GALADIMA* ce”.
shiru nai kamar banjishiba, danjin sunan wanda ya ambata, inada tabbacin kuma wannan mai girman kan tsiyar yake nufi kenan, yayinda 'yan uwana suka rud'e da firar galadiman.
d'an tsaki naja nace, “ashema Na mai shegen girman kai d'innan ne”.
Kusan atare sukace ke a ina kika sanshi? dahar kikasan yanada girman kai”.
Shiru namusu, sai Munubiya ce tashiga basu labarinsa da had'uwar damukayi a asibiti da shi, aikam duk sai sukabi suka rikice, harda masu fatan yazame musu mijin aure.
bansan miyasa duk hirar tasu ta k'untataniba, tabani haushi, saina maida hankalina ga kallace-kallacen jama'ar daketa kai kawo akan titi.
Har mukaje gida suna hirar Galadima sudasu yaa hameed dake basu labarin halayen kirki Na Galadima d'in, wai kuma bashida girman kai kamar yanda Na fad'a, kawai dai dan ban fahimcesa bane nima.
Nidai jinsu kawai nakeyi, amma badan Na yarda baida girman kai ba, tunda da idona Nagani ba labari aka baniba.😏ehe
Innarmu tayi mamakin wad'annan kanya, dan haka takasa hak'uri, har 6angaren samarin gidanmu taje tamusu godiya da fad'an d'awainiyar tayi yawa ai, ga hidimar biki Na tunkarosu.
Sunji dad'i sosai akan hakan da innarmu tayi, koba dad'i kowa yayi aikairi yanaso anuna jindad'i kuma amasa godiya.
Sukace tayi hak'uri, ai k'annensu ne, idan basu mana ba wazai mana, da samari suzo suna mana hidima su lalata mana rayuwa ai garasu sumana su kare mutuncinmu.
Sosai innarmu ma taji dad'in furicinsu, dan hakan ya nuna cewa su basu d'auki halayen iyayensu mataba Na raba d'aya biyu.
Salla nata gabatomu, yayinda aka fara 'yan kimtse-kimtse Na shirin bikin sallar, masallatai nata rufe tafseer, hakama gidajen redio dana talabijin..............✍🏼
*Kusaka yayan mahaifiyata a addu'arku, ALLAH yamasa rasuwa ranar alhamis😭👏🏻, ALLAH ya gafarta masa, ya raya abinda yabari.*
_Bansan makaranta Raina kama.... kunada yawa hakaba wlhy, nazata ki rabin group bazaku kaiba🙆🏻, gashi yacika wasu basu sami wajeba kuma._
Na gaisheku k'yauta, ina fatan duk kuna cikin k'oshin lafiya kuda iyalanku🤝🏻😊?.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*.👏🏻😭
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻7⃣
.......Yau ake saka ran ganin wata, dan haka kowane gida zaka iya jiyo kamshin miya dana nama, harma da kayan snacks.
Muma agidanmu kusan hakanne ta kasance, dan kowanne 6angare sunata hidimarsu, yau ko bud'a baki bakowa yasamu zaman yinsa ba.
Muma muna namu 6angare muna taya innarmu ayyukanta, dayake kowa yana miyarsane, da safe ahad'u ayi tuwo da masa da shinkafa, haka muke had'a kalolin abinci iri-iri saboda yawan jama'a da gidanmu kan tara a ranar salla, abokan yayunmu maza, abokan su abbanmu dawasu dangin iyayenmu mata.
Har wajen 10 munata aiki, sai kuma a lokacinne mukaji ana sanar da ganin wata.
Nannafa yara suka shiga murna gobe salla, Muma kanmu manyan murnar mukeyi. badan mun kammala aikiba muka kwanta.
Washe gari tun kiran sallar farko aka tadamu muka fara aiki, sai wajen 7am muka samu kanmu, a gurguje muka fara wanka da shirin tafiya idi, duk shekara dama 'yan gidanmu a masallacin da sarki yake salla muma mukeyi.
A gurguje duk mukaita fitowa saboda horn da yayyenmu suketa mana, yara an d'urasu a school bos d'insu Na makaranta, yayinda mukuma muka rarrabu a motar yayinmu datasu Abba dasuka bayar, tunda bakowa keda motarna acikin yayyen namu.
Dagani har Munubiya cikin shigarmu muke iri d'aya tamkar yanda muka saba a koda yaushe, dai-dai da kwalliyama iri d'ayace a fuskarmu, komai namu mukayishi iri d'ayane, wannan yasaka ake gaza banbancemu akoda yaushe.
Mun Isa filin idi, inda muka taddashi dank'am da jama'a maza da mata, wasu harda iyalansu, kamar yanda muma muka taho baki d'aya harsu innarmu, mu mata muna 6angaren mata, yayinda mazan sukayi nasu 6angare.
Khud'ubar da aka gabatar tazamo mana mai ratsa jiki da 6argo, Malam yayita cikin tsantsar larabci, yayinda wani malamin ya fassara acikin harshen Hausa, saboda marasa jin larabcin irinsu o e🙊.
Daga nan aka gudanar da sallar idi kamar yanda addini ya koyar.
Had'a kan yaran muka shigayi gudin karsuyi wani waje, sai dai hakan bata samuba, dan annemi Kamal da Haneep an rasa, nannafa muka shiga bulayin nemansu, duk mun rikice, gashi baba k'arami da Abbah sai fad'a suke wai sakacinmu ne.
Tamkar zan kifa haka nake tafiya da sassarfa ina kalle-kalle. ban ankaraba naji naci karo da Abu, tunkan inkai idona kansa k'amshin turarensa yabigi hancina. da sauri na ware manyan idanuna bisa kamilalliyar fuskarsa dake d'aure babu alamar yasan miyema dariya, janye idona nayi cikin fargaba da fad'awa kogin tunani, inban mantaba irin wannan k'amshin naji a asibiti wajen Wanda aka kira galadima a wacan ranar da feena batada lafiya.
Cikin yanayin tantama Na maida idona nad'an saci kallonsa...
Tsaye yake kyam tamkar dutshin da aka dasa waje d'aya, idonsa akan wayarsa dake k'asa a tarwatse, Wanda inada tabbacin karon damukacine yasaka wayar fad'uwa.
A rikice nace “ya Salam” tareda duk'usawa nafara harhad'a wayar.
A hankali ya durk'usa kamar yanda nima nayi, ya d'ora hannunsa akan wayar dana ke k'ok'arin sakama battery ya zareta daga cikin hannuna. bugun zuciyata yak'aru saboda tsoro gashi yak'i cewa uffan, nasan nice da laifi, kafin Na ankara ya sake d'oramin wayar bisa hannuna yamik'e yabar wajen.
Sororo nabisa da kallon mamaki da al'ajabi, sanye yake cikin farar shadda k'al, wando da riga harda malun-malun, ya murza hularnan da ake kira Minister bak'a a kansa, takalminsa da agogonsa duk bak'ak'e, duk da bawani k'are masa kallo nayiba fuska da fuska nasan tabbas yayi k'yau, kayan sun maidashi wani babban mutum. Ajiyar zuciya Na sauke saboda ya 6acema ganina, nabi wayar daya barni da ita a hannu da kallo, tomi yake nufi da hakan?.
Banida mai bani amsa, dan haka nacigaba da had'a wayar, sai alokacin Na lura da sim card d'insa dake kan wayar yacire d'azun lokacin daya kar6a kenan.
Jujjuya wayar nashigayi cikin tafin hannuna, wayace mai azabar k'yau ga k'amshin turarensa ya manne jikin wayar tamkar itama ana fesa matane. 'Yar tsagewane tayi kad'an daga gefe, amma daga hakan ni banga wata matsalaba, kenan yana nufin koyaya waya ta tsage a hannunsa tatashi aiki a garesa?. Nanma babu mai bani amsata. Cikin mak'oshi Na furta to wanene wannan d'in shikuma?”.
“Galadima!”. ‘naji wata murya tafad'a abayana’.
Cikin hanzari najuyon dan inga mai bani amsar tawa. wayam naga babu kowa, sai alamar gittawar mutum mai jajayen kaya.
Goshina Na dafe inamai runtse idanuna, cikeda mamaki nace, “kenan shine wanda yabama feena jini? Galadima!”.
Nafad'a cikin bud'e idanuna inabin inda yabi da kallo tamkar zan sake ganinsa, a hankali nakuma furta _“Galadima!”_.
“galadima kuma?”.
Najiyo muryar Safara'u a bayana, da sauri a cusa wayar cikin hijjabina Na mik'e, kallonta nayi cikin basarwa nace, “ya angansu ne”.
Tace “eh mana an gansu tun d'azun, saikuma aka koma nemanki, miya faru naji kina kiran sunan galadima?”.
d'an guntun tsaki naja “naji wasu 'yan matane suna fad'in wai INA zasuga Galadima, tunda ance yazo sallar idi. shine nikuma nake maimaita sunan Galadiman saboda takaicinsu”.
Dariya Safara'u tayi, ke 'Yar uwa karkiga laifinsu wlhy, koni zan sameshi saina bar Sadeeq wlhy, yanzu fa Nima ake nunaminshi, dama haka yahad'u? Wayyo ALLAH yau naga tsantsar gwanzartakar sarauta ajikin bawan ALLAH nan, tafiyarsama kawai abin kalloce, inaga kuma yayi magana?, kai ALLAH yakai damo ga harawa...... kedai kawai........
Baki kawai Na ta6e, batareda nagamajin k'arshen zancen nataba nayi gaba abuna da mamakinta a raina, wai zata iya Barin sadeeq?, saikace ba'akan sadeeq d'in bane akaso cin zarafina da innarmu, amma yanzu saboda taga Wanda ya fishi bakinta yake furta haka.
Da gudu Safara'u tabiyoni. Kusan a tare muka k'arasa Inda motarmu ta tsaya, yaa hameed yafara zagina akan INA kuma naje Na tsaya?, hak'uri nabashi muka Shiga mota kawai, dan nasan shima d'in masifafene kamar su abbanmu.
Amotar ana fira amma ni tunanina yanakan had'uwarmu da Galadima ta yau, ga mamakin wayarsa daya bari yatafi a hannuna batareda yace min uffanba, kai wannan Bawa yanaji da k'asaita da mulki.
Har muka Isa gida bakina bai iya furta komaiba acikin hirar tasu. Mun tatar su innarmu ma harsun huta su, yara kan summa fara cin abinci.
Ban zauna faloba kamar yanda munubiya tayi, saina zarce bedroom d'inmu Na 6oye wayar sannan nacire hijjab d'ina nashiga bathroom Na wanke hannuna gudun kar wani yaji k'amshin turaren saina dawo falon.
Tuni gidanmu ya kacame da hayaniya, munubiya tazubo mana masa da fankasu zamu faraci Ayusher da Feena suka shigo da gudu, juna muka rungume muna murnar ganinsu, Yaa Fadeel & yaa Marwan suma suka shigo, sai mama Rabi'a dake take musu baya tana rik'e da hannun Ahmad.
Nan muma muka kacame da farin cikin ganin 'yan uwanmu wad'anda bamuda kamarsu, innarmu ta baje mana abinci da kayayyaki da dama dansu duk ta tanadesu, sai makwafta dasuke gaisawar arzik'i suma duk tabada ankakkai musu.
Bamusan hidimar da kowa keyi anasa 6angarenba, mudai namu muka sani.
Ayusher takawo bakinta saitin kunnena, ahankali ta rad'amin sweet sis.... Wlhy k'amshin turaren Galadima kikeyi, kinsan har abada bazan mance k'amshi nan ba”.
Cikin dakiya Na d'ago kai Na kalleta tareda balla mata harara, “Ayusher wlhy ki kiyayeni, a'a k'amshin turaren sarki kikaji bana Galadima ba k'arewa”.
dariya ta sanya harda rik'e ciki, nikuma Na tashi Na canja waje ina mamakin Ayusher mai gani har hanji, duk dawanke hannuna danayi sosai amma ace wai har yanzun anajin k'amshin turaren?, kai shikam wannan dawane mayen turare yake aiki haka?”.
Wajen 12 muka fito domin zuwa kallon sarki dazai wice yima governor barka da salla.
A wannan karan tafiyarmu daban data 'yan gidanmu, dan mafi yawancinsu duk sun fice gidajen kakanninsu, tacan masu ra'ayin zuwan suma zasuje.
Mukuwa mudasu yaa marwan muka tafi.
Acikin gari duk inda ka kalla jama'a ne keta kai kawo, musamman yara da 'yanmata da samari, kowa yaci kwalliya ta kece raini da garari (yo dama ai ance ba'a za6ar budurwa ran salla, saboda duk k'azantar mutum ranar saika sameshi cikin tsafta da gayu😂).
Dukda akwai rana hakan bai hanamu jeruwaba domin kallon wucewar mai martaba sarkinmu da jama'arsa.
Masu busa algaita da kid'an taushine suka fara wucewa, sai kuma ga tawagar sarki Na biye.
tawagar saiki Na wucewa sai ta Galadima, kamar yanda mukaji wasu gungun samari Na fad'ar cewa ga Galadima nan.
Kowa yasan dama tsarin haka yake, daga sarki sai shi.
'Daga idanuna nayin donson sake ganinsa a karo na biyu. yanzu kam ya canja shigarsa zuwa milk coulor d'in janfa da wando Na lallausan yadi, Wanda aka k'awatashi da d'inkin surfani Na ainahin gidan masu sarauta, ya d'ora Brown Na alk'yabba mai kwalliyar Milk Color, hakama rawaninsa daya zagaye fuskarsa ya kasance milk ne, takalmansa heir cover masu lankwasa daga gaba irinna sarauta, sukuma Brown. yanzun kam fuskarsa d'auke take da k'asaitaccen murmushi mai kama da anmasa dole, hannunsa d'aya dayake d'agama mutane yana d'aureda farin agogon azurfa, sai zabba biyu a yatsunsa Na tsakkiya Wanda nake k'yautata zaton azurfane suma.
Nanfa su Ayusher suka fara d'aukarsa hotonsa a wayoyinsu.
Tsaki naja ina hararsu, “mtsoww wahalallu kawai, dama kanku kuka d'auka yafi Ku k'are wajen d'ura hotunan Wanda baisanma da zamankuba a wayarku”.
Kafin cikin su Ayusher wata tabani amsa, wasu 'yan mata dake kusadamu d'aya ta kar6e da fad'in “k 'yan mata kama kanki, kodai kema son nasa ne yakaiki ga kishinsa?”.
Wata wawuyar harara Na buga mata, “kekuma shasha waya sako bakinki?, kajimin ballagaza kawai, uwarmiye abin so a jikinsa dahar ya isa ayi kishinsa? Ke dai dabakisan inda ke miki k'aik'ayiba ita dakon wahala, dan nakula ke amatanma suffar mata maza ALLAH yayiki....”
Gaba d'aya suka taso min da masifa tamkar zasu cinyeni d'anya itada k'awayenta..
Yaa marwan dake zaune saman mota a bayanmu duk yana saurarenmu yad'ago kai ya kalleni, yasan tabas Munaya ce, baya buk'atar k'arin bayani kuma ko tambayar wacece ita, tunda Na nuna halin nawa, yace, “K munaya zoki shige mota”.
Nasan halinsa sarai baya wasa damu, cikin tunzura baki gaba nazo nashige motar Na zauna, amma saina bar k'ofar abud'e k'afafuna awaje, banida buk'atar cigaba da kallon kuma, dan haka nabud'e data nashiga chart kawai ina cika ina batsewa masifa nacin raina, gashi kuma an hanani amayar da'ita,. sai antayama yaa Marwan harara nakeyi ta gefen ido baima San inayiba, gaba d'ayama sainaji dama banzo kallon hawanba.
Koda muka bar nan ba gida muka komaba, yawo yaa Marwan yaytayi damu gidajen dangin babansu, bamune muka dawo gidaba sai magriba, kowa yayi ti6is da gajiya.
Mun tarar innarmu da mama Rabi'a sunata shan hirarsu ta zuminci.
Sai kusan 10 suka bar gidan.
★★★★
Washe gari muma agidansu mama Rabu'a muka yini har innarmu, koda yakema fitarmu mukayi nida Munubiya, Feena, Ayusher, mukabar su mama agida dasu Aryaan.
Yauma mun zaga gari sosai, dan Ayusher takira mana wani saurayinta yazo ya kwashemu, yauma munje munga hawan sarki da la'asar, saidai yau babu Galadima a tawagar, hakan bai dameniba, dan nama manta da lamarinsa ni.
Kwanaki kusan biyar zuwa 7 munashan shagalin salla, munsha yawo tamkar bamuda mafad'i mudasu Ayusher, sai Fauziyya dakan bimu wani lokacin idan basu fitaba da mamarsu suma.
'Yan matan gidanmu kowa sabgar gabansa yayi, rana d'ayane muka fita gaba d'aya domin gaida danginsu Abbanmu da Innaro takafa ta tsare akan sai munje wai su Anty Ramla sunyo musu sallamar aure.
Kwanaki 10 cif dagama bikin salla muka koma makaranta.
Haka rayuwa tacigaba da shud'ayawa, yayinda 'yan gidanmu keta shirin bikin 'ya'yansu, shiri akeyi babu kama hannun yaro, kowa burinsa ace 'ya'yan d'akinsa sune Star's, kuma sunfi kowa komai.
Sati uku kacal bikin yarage, an kawo lefe daga gidan senator halliru, akwatina 24, siyama 12 Zarah 12.
Humm ai ranar munsha kallo Na al'ajabi wajen mamansu yaa Hameed da momy Hadiza, habaici da gugar zana da burga, kowa yashashi, har dai abin yak'ure mamansu haleematu da maman Safara'u suka tanka musu, kafin kice mi gida yagama kacamewa da hayaniya, kowa yana ya6ama kowa magana, saida suka gama cin zarafin junansu sannan sukayi shiru bisa tsawatarwar baba k'arami, dayake yana gida a lokacin.
An bar maganarne kawai amma badan ta k'areba, mudai a 6angarenmu ma innarmu hana kowa fitowa tayi, dayake weekend ne.
Suma sauran duk an kawo nasu lefan, Aunty Rahaima, Ramlah, Hauwa'u sai aunty khaleesa, suma dai Alhmdllh, komai sai dai mak'iyi, duk da basukai nasu siyama ba gaskiya. a wannan karonma dai saida akayi 'yan gulmace-gulmace a gidanmu, amma basu bari tafito sarariba.
Suma su yaa Hameed aka kai nasu lefan gidajen matan dazasu aura shida Ya shafi'u da yaa Nasser. suma iyayenmu sunyi k'ok'ari wajen had'a musu lefen girma, ankai kuma kowa Na sambarka.
Tun bayan gama kai lefe gidanmu yakuma d'inkewa da k'us-k'us na gutsiri tsomar gidan yawa, kowa yana gulmar kowa akan aga wace rawa zaka taka, su 5 masu aurar da 'ya'yan.
Mamansu yaa hameed zata aurar da 3, yaa hameed, aunty khaleesa da Zarah.
Sai maman Haleematu zata aurar da aunty Hauwa'u.
Sai Momy Hadiza zata aurar da Siyama da aunty Raihan.
Mama Ruk'ayya kuma zata aurar da yaa Shafi'u da yaa Naseer.
Maman Safara'u kuma Aunty Ramlah.
Innarmu da maman Fauziyya ne kawai bazasu aurar da kowa ba, dan haka suka zama 'yan kallo, sai idan mazajensu sun saka su acikin shawarane.............✍🏼
*_Ya Rabbi ka gafarta iyayenmu😭👏🏻_*
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_________________________
_Happy marriage life *SANNA S MATAZU* ALLAH ya sanya alkairi da albarka a wannan aure, yabaku zaman lafiya na har Abadan da zuria d'ayyiba, bad'i muzo cin rangam💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻😄👌🏻._
__________________________
👉🏻8⃣
.......Hidimar biki ta kankama gadan-gadan, dan har bak'in nesa sun fara isowa, a ranar alhamis aka gudanar da sister's and brother's day Wanda mune k'annensu muka shirya musu da yayinmu maza. da farko a tsakar gidan innaro aka shirya, saboda su Abba bazasu barmu mu saka kid'aba a gidanmu, gashi mun gayyato k'awayenmu ne, sai abokan su yaa Nasser danasu Anas. daga baya kuma sai muka canja shawara saboda samun wani fili damukayi can k'asan layinmu, filin a zagaye yake da katanga an saka gate. Tunda safe suka fara shirye-shiryen gyara wajen, kasancewar sai 4pm za'a fara, mudai makaranta muka tafi nida fauziyya da Munubiya, dan munada lectures, amma sauran duk k'in zuwa sukayi, barema su Siyama amare.
Around 3pm muka dawo gida, yauma kam da alama wasu bak'in sun iso, dan gidan Yakuma cika da yara da 'Yar hayaniya.
Mun tarrar innarmu tana d'akin abbanmu, dan haka mukayi wanka muka fara shirin tafiya wajen taron, ko abinci bamu nemaba, dagani har munubiya mun iya makeup, kasancewar mama Rabi'a tasakamu wajen koya muda Ayusher lokacin damuka gama secondary, a d'an tsakanin kafin fitowar results d'inmu, taga damuyi zaman banza gamma muje mukoya wata 'Yar sana'ar, tunda bamusan inda rayuwa zata kaimuba. Ko gama shiryawa bamuyiba Rahma tashigo kiranmu inji su Aunty Rahaima, dan mune zamu musu kwalliya.
Mun tarar dasu duk sunyi wanka dama mu suke jira, zaman musu kwalliyar mukayi, ni nafarama Aunty Hauwa'u, yayinda Munubiya takema aunty Ramlah.
Kiran Ayusher yashigo wayar munu...., ta d'aga tana fad'in “kin isone?”.
Bansan mitace mataba daga can, naji tace, “kizo muna 6angaren su Aunty Ramlah”.
Babu dad'ewa saiga Ayusher itama, ta gaggada su Aunty's d'in, sannan muma tabamu hannu muka gaggaisa cikina musabaha.
“lah dear nifa harna fidda ran zakizo ALLAH”.
Ayusher tace “kibari kawai, wancan jarabbaben ne yasakani aiki, tuwo mama tayi da rana, kinsan kuma bayaci shi, shinefa ya tsareni wai saina masa sakwara, harfa nayi shirin tahowa”.
“uhm ai lamarin yaa marwan saishi, matarsa dai taga banu wlhy, shi anya ma yata6a budurwa kuwa?”.
Dariya duk muka sanya a d'akin, aunty Hauwa'u tace, “ai marwan akwai miskilanci wlhy shima, nifa zan iya cewa mun ta6a magana dashi kuwa?”.
Ayusher tace, “yo aunty ai wannan kowama haka yake masa, komu muka gaidashi sai yaso yake amsawa, kullum mama cikin masa fad'a take amma abanza wlhy?”.
Nann dai hira Yakoma kan yaa Marwan da mutane masu muskilanci irinsa, Munubiya ce mai kareshi, (dama ita suna d'an d'asawa, nice dai kamar muna ganin hanjin juna dashi danma ina tsoronsa ).
Kasan cewar mu uku ne sai kwalliyar tai sauri, dan danan muka kammala, nida munubiya mukayi tamu muma, simple makeup mukayi, amma komai iri d'aya, dama haka mukeyi, komai namu kullmun iri d'ayane.
Munyi k'yau, 6angarenmu muka koma mukayi shiri cikin blue d'in skirt da pink d'in Riga kamar yanda aka tsara sai veil shima blue.
Na jujjuya ina kallon kaina a mirror, “kai jama'a nikam bazan iya fita hakaba gaskiya”.
Ayusher dake kwance tana danna wata tad'ago ta kalleni, “kai amma kuma wlhy kayan sun miki k'yau, kinganki kuwa? dan ALLAH ki barsu, kiyi rolling veil naki kawai”.
“kai ba munaya kad'aibafa, nima bazan iyaba, after dress zan d'ora wlhy”.
Dariya Ayusher tayi, ta tashi zaune tana ajiye wayar, “waiku miyasa k'auyawane sister's, naga a ke6antaccen waje za'ayi?”.
“amma kuma dai ai akwai maza kema kin sani”.
“to alaranmiya, Ku saka, amma kafin Ku saka d'in nidai kuzo miyi hotuna”.
Gaskiya koni nasan munyi k'yau, kasancewar mud'in fararene, kalolin duk sai suka kar6i jikinmu blue & pink. Wanda bai saniba saiya ce mu 'yan uku ne har Ayusher, dan muna matuk'ar kama da juna, sai dai Ayusher tafimu haske da d'an jiki.
Sai da mukad'anyi hotuna sannan muka fito. Innarmu tace kunyi k'yau, amma dan ALLAH kar inji wani yayi abinda za'ace gashi-gashi, Ku kama kanku da mutuncinku kunga dai acikin anguwane, idon kowa akanku yake”.
Mukace to innarmu insha ALLAH. mun fita tana binmu da addu'a.
A k'afa muka taka har wajen taron, tunkan mu k'arasa muke jiyo tashin kid'a. wajen dank'am yake da 'yanmata da samari, k'awayen amare da namu muma, sai 'yan uwa kuma da abokan su yaa Nasser, dama shi ya Hameed bai gayyaci kowaba, yace ya bar mana mu k'anne (shidama ba auren farko bane).
Tunda muka shigo akai mana caa da idanu, wasu tsantsar kamarmu ce tajawo hankalinsu kanmu, wasukuma burgesu mukayi, wasu kuma gulmarmu sukeyi da zaginmu, to dama shi taro ya gaji hakan, ballemu da ake ganinmu k'ask'antattu agidanmu, kamar kowama yafimu komai.
Amare suma duk sunyi k'yau cikin tasu shigar ta Riga da wando pink gaba d'aya, sai suka d'aure k'ugunsu da blue d'in belt, suka d'aura jacket blue.
Snacks ne kawai akad'anci a wajen da drinks, sai pictures da'aka d'auka da video, 'yan mata sunata casar rawarsu da samari, mudai muna daga gefe zaune muna shan kallo. mun rarraba gifts d'in damuka tanada, bawani Abu bane masu tsada. silifas d'in wankane sai brush, MacLean, soson wanka da sabulu d'ad'd'aya aciki, gifts d'in nan mun shiryashine kawai dan tsokana dama. gabda magriba taro yatashi lfy, kowa ya kama gabansa. muma gida muka koma.
★★★★★
Washe garima saida mukaje makaranta, sai dai 11:30 muka fito lecture, ALLAH ya taimakemu muka samu taxi da wuri.
Sanda muka dawo har 'yan jere sun dawo, kowa dangin mamarsa sukaje jerensa, shiyyasa mukaji tsitt babu gutsiri tsoma.
Muna dawowa ko wanka bamu tsaya yiba mukaci abinci muka tafi shagon auntynmu data koyar damu makeup domin yin k'unshi da saloons.
Cikin farin ciki ta tarbemu, dan mun rabu da ita cikin mutunci bayan mun iya aiki, Aunty salamah batada damuwa, inkaga tana maka fad'a to baka fahimtar abinda take koyar dakai ne, kwazon damuka nuna alokacin yasa takeji damu over. Tana kiranmu 'yan ukun ta.
K'unshi aka mana mai k'yau da gyaran kai, (dan d'aurema k'arya gindi irinnan aunty salamah harda mana gyaran jiki😊, wai tanaso muma musamo mazajen aure🙈).
Kowa ya gammu yasan munyi k'yau sosai.
Amakare mukaje gida, dan mun tarar amare nata jiranmu mu musu kwalliya, 'yan gidanmu harsun fara k'ananun magana, wai wulak'ancine yasa muka fita ai, kuma muna kallon lokaci yana k'urewa mukak'i dawowa. hakan da innarmu taji yasata kiranmu tana mana fad'a, hak'uri muka bata dacewa gamunan a hanya.
Masifa mukaitayi nida Ayusher, munubiya na bamu hak'uri, wlhy badan innarmu ba da bazanyi kwalliyar nanba yau.
Babu zancen mu huta muka hau musu kwalliyar. aikam ranar k'in fita wajen kamun nayi da akayi a tsakar gidanmu, kwanciyata nayi, innarmu taitamin fad'a kuwa.😕
Washe garin asabar d'aurin aure, dakam gidanmu yacika tab, 6angarenmu dai da sauk'in mutane, sai mama Rabi'a kawai da matan abokan Abbanmu.
K'arfe goma aka d'auro auren yaa Hameed da amaryarsa, sai yaa Nasser shima da yaa Shafi'u.
Na 'yan matan kuwa sai k'arfe 1:30pm. K'ofar gidanmu yacika dank'am da jama'a ta ko'ina, 'yan siyasa tawagar senator halliru da abokan su Sa'eed, hakama mijin aunty Rahaima d'an siyasane, dan haka harda governor a mahalarta taron d'aurin auren.
Har aka gama d'aura aurarrakin ina d'akinmu kwance, ko wanka banyiba, garama munubiya da Feena da Ayusher su duk sunyi, amma suna d'akin basu fitaba, sai balkisu k'awarmu da itama tazo mana.
Hira suketayi, nikam dai ina kwance kaina namin ciwo.
Gidanmu babu masaka tsinke, tako ina jama'ane, amare ansha k'yau, su siyama baki har k'anne an auri 'ya'yan sanata, hakama iyayensu sai burga sukeyi, ranar munga gasar dressing wajen iyayenmu mata kam, kowacce so take ace itace uwar amarya datafi kowa fita.
Innarmu kam babu ruwanta, shiga d'aya tayi ta atanfar da Abbanmu yamusu Na fitar biki, sai da yamma ta canja da less.
Aranar kowaccensu tayi yini. Baza'a kai amareba sai washe gari, saboda anason agudanar da dinner waje d'aya, amma an kawo nasu yaa Shafi'u sudai.
Yau d'inma dai mune muka musu kwalliyar su dukansu, kafin k'arfe 8pm afara kwasar mutane zuwa wajen daza'a gudanar da dinner d'in.
Gurin yayi k'yau sosai, yayinda aka shirya ma amare da anguna hi table.
Sai dai kuma wata sabuwa, ba duk angunan bane suka halarci wajen dinner d'in, nan fa aka fara 'yan gulmace-gulmace tsakanin dangin iyayenmu mata, tuni labari harya kai kunnuwan iyayenmu mata dasuke zaune a gida.
Amaren da babu angunansu sunsha kuka, wad'anda kuma dama sukasan angunan nasu ustazaine bazasu zoba basu damuba.
Haka dai aka gudanar da dinner d'in zukatan wasu babu dad'i, tunkan agama ma wasu sukaita tafiya gida abinsu. K'arfe 11 aka tashi.
A wajen dinner kam nayo saurayi mai suna Fu'aad, hakama munubiya da Ayusher dun sunyi, Fu'aad k'yak'yk'yawa dashi masha ALLAH, duk da dai bawani sake masa nayiba ya burgeni.
Su Ayusher sunata tsokanata, nidai ban kula suba.
Washe gari da safe kuwa saida abin yazama fad'a, wai ankama wasu suna gulma akan rashin zuwan sauran anguna, kuma dangin momy Hadiza ne, aikam sosai aka zuba rikici, har saida abbanmu ya tsawatar.
Aranar aka shirya kai amare, dole sai dai a rarrabu, tun la'asar aka fara kawo motoci, baba k'aramine yabada shawarar ahad'a tafiyar kawai gaba d'aya, su aunty Hauwa'u suma su siyama rakiya, sannan suma haka.
Haka kuwa yayima wasu iyayenmu mata dad'i, dan kobabu komai saji yanda gidan kowacce ya kasance.
mun fara kai su Siyama da Zarah, wad'anda babu alamun kuka a idanunsu, gidajensu jere da juna, sunyi k'yau masha ALLAH, kayan gado dai duksu Abba sukayi, kuma kud'insu d'aya, saidai kowa da za6insa, kayan kitchen ne kowa uwarsa tayi da sauran tarkace, ananne kowa ya ware ido dan aga kwazon uwar mutum, nidai agareni babu makusa, gidansu Zarah duk yayi.
Mun ajiyesu tareda k'awayensu, mukuma muka tafi kai sauran.
Daga Nan sai gidan aunty Rahaima, itama masha ALLAHU wlhy, saidai mak'iyi, gidanta yayi k'yau, sai dai tanada kishiya.
Saikuma gidan aunty khaleesa, itama dai d'in zamm zamm wlhy, daga nan sai aunty Ramlah, wlhy itama yayi d'as, itama tanada kishiya. Aunty Hauwa'u ce k'arshe dan itace babba, itama gidanta yayi k'yau sosai.
Nidai aganina babu wadda mahaifiyarta batayi k'ok'ari ba wlhy, amma hakan bai hana sauran gumtso gulmarmakiba aka taho da ita.
Kasancewar duk babu Inda muka zauna aka taho gida da wuri, harzamu wuce Fu'aad daya d'akkomu yace bari yashiga Birnin gayu plaza damu.
Nace a'a muwuce gida kawai, kar aga kowa yadawo mu bandamu, gashi lokacin har 8:30pm ya wuce.
Ayusher ce tace indai bazamu dad'eba ashiga, saimuce muna gidajen su siyama mu, mun zauna jiran anguna.
Kamar dai nace a'a amma nayi shiru, saboda naji munubiya da feena suma sun bada goyon bayan mu Shiga, sannan Fu'aad yace bazamu dad'eba.
Ya kalleni murya k'asa-k'asa yace, “ginbiya bakice komaiba?”.
Murya a sanyaye nace, “indai bazamu wuce 1hour ba muje”.
“insha ALLAHU my luv bazama mu kaiba”.
A kasalance Na d'aga masa kai saboda agajiye make ti6is.
Haka yashiga wajen nidai zuciyata Na dukan uku-uku daban San Na miyeba.
Munshiga cikin plaza d'in, bansan takamaimai miyasa Fu'aad yace mushigo wajenba, tunda dai bawani abin ci ake saidawa a wajenba.
Mun shiga 6angaren kayan kwalliya, yace kowa yaza6i abinda yakeso.
Nidai nace masa a'a mun Gode.
6ata fuska yayi yana hararata, ya maida kallonsa gasu munubiya dake tsaye “please dan ALLAH karku biye mata, kuje Ku d'auka”.
Badan suma sunasoba suka amsa da to.
Ya kalleni yana fad'in “mujeto ni na d'ebar miki”. bance masa komaiba nabi bayansa ganin kamar yayi fushi, wayarsa aka kira, ya zaro daga aljihu, saida yad'an saci kallona yaga hankalina baya kansa sannan ya d'aga, murya k'asa-k'asa tamkar mai gulma yace, “nagama aikina”.
Dawowa yayi wajena bayan ya katse wayar, da kansa yake za6ar mini duk abinda yadace.
Su munubiya ma sunacan suna d'auka, kamar ance munubiya ta bar wajen saita zagaya tabaya, a dai-dai wannan lokacinne shikuma yake tunkarowa shida wasu matasan samari guda biyu, da alama yana zagayene kowani abun daban. tafiya yake cikeda nutsuwa da sarauta, sai sautin takunsa dakakeji, tunkan su iso gareta k'amshin turarensa ya iso.
Waige-waige munubiya tafara, tanason tuno mai wannan k'amshin. bata ankaraba saijinta tayi tatafi suuuu santsi ya kwasheta.
Shi mutumne mai yawan tausayi da taimako, da sauri yayo kanta kafin taje k'asan, Dan yasan fad'uwarta a wajen babban had'arine, yakai hannu zai rik'eta itakuma ALLAH yabata ikon dafe wasu tarin baskets dake wajen. Cikin runtse ido da sauke ajiyar zuciya ta furta “Alhmdllh”.
Janyewa yayi daga rankwatowar dayay kanta tamkar zai rungumeta, batareda yace uffanba yafar wajen.
Muduka akan idonmu komai ya faru, wad'anda suke tare dashine sukaima munubiya sannu, mukuma muka k'araso da sauri gareta muna tanbayarta babudai wata damuwa ko?.
“babu komai Alhmdllh”. ‘tafad'a tana gyara tsayuwarta’.
Nace, “kunga kuzo mu tafi hakanan, wlhy inajin tsoron agane bama gidansu siyama”.
Duk suka amsa da gsky mu tafi, da k'yar muka yarda mukaje wajen biyan kud'in. yabiya sannan muka tafi.
ALLAH ya taimakemu ba'a mana fad'aba.
Duk cikinmu babu Wanda yakuma maida hankali akan abinda yafaru a birnin gayu plaza, saidai abin yakasa barin raina, kamar zuciyata tana cikin fargaba, amma bansan ta miyeba, ita kanta Munubiya wani sukuku nake ganinta, bandai tanbayeta ba Na share.
Washe gari Monday, muka tashi da shirin makaranta, saida muka gama gyara gidan tsaf sannan muka tafi harsu Ayusher, dayake lectures d'inmu Na yau sai 1:30pm ne. yauma sauran 'yan uwanmu bakowa yaje school d'inba ma har fauziyya.
Tun muna tsaye abakin titi muna jiran taxi naga wasu tsirarun mutane nabinmu da kallo. ban kawo komai arainaba muka samu taxi.
Driver ma yana tuk'i yana kallonmu ta madubi, sainaga kuma ya kalli takardar dake saman cinyarsa. d'an fara tsarguwa nayi, amma saina dake ina zaton irin dirobobin nanne masu shegen kallon tsiya.
Da muka sauka cikin makaranta ma bata sauya zaniba, kallonmu akeyi har ana nunamu, wasu da jaridu a hannu wasu kuma waya.
Munubiya tace, “Manaya bakiga abinda ke faruwaba tundaga fitowarmu gida zuwa nan ne?”.
“nagani wlhy Munubiya, bansan miyakawo wannan kallon k'urilla d'inba, dama bakiga kallon da direban can yake manaba ni da ke harya saukemu, ko sanda muke sallama dasu Ayusher idonsa Na kanmu kyam kuma yana kallon wata jarida dake cinyarsa”.
Muduka kallon jikin junanmu mukeyi, babu wanda shigarsa tazama aibu acikinmu, sannan bama tareda wani abin kallo,
Hannun juna muka kama muka cigaba da tafiya cikin tsantseni da nazartar kallonda 'yan uwanmu d'alibai suke mana.
Tunda muka shigo cikin class sai duk aka zubo mana idanu, kuma anata k'us-k'us. yanzu kam hankalinmu yatashi sosai, wai mike faruwane? saikace yau mutane suka fara ganinmu? shin yaune muka fara shigowa makaranta?.
Bamu da mai bamu amsar tanbayarmu, muka nufi Bilkisu dake zaune itama tazubo mana idanu, ga jarida agabanta, kamar yanda muka gani wajen sauran 'yan department d'inmu, wasu narik'e da jaridu wasu wayoyi, sunyi group group kuma suna k'us-k'us.
Da sauri Na k'arasa zan d'auki jaridar gaban Bilkisu amma saitayi saurin d'aukewa............✍🏼
Babbar magana, shin mike faruwane? kallonmi jama'a kema su Munubiya? Sannan mi ake kallo a jikin jaridar da wayoyin kuma?🤦🏻♀.
Nasan masu karatu ma wannan amsar suke son sani🤔
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻9⃣
.......K'yaleta nayi najuya sit d'in bayanmu Na fusge ta hannun wani guy, rubutun farko dage jikin jaridar a shafin farko na tsirama idanu.
*_BABBAR MAGANA, GALADIMA SAMEER RUNGUME DA MATASHIYAR BUDURWA A PLAZA 'DINSA SUNA SUMBATAR JUNA!!_*
sai kuma hoton dake k'asan rubutun shima har kala biyu, Na farko abinda yafarune na fad'uwar Munubiya a birnin gayu plaza, har Galadima yay yink'urin taimakonta amma tadafe baskets ko ta6ata ma baikai gayiba, amma abin mamaki da al'ajabi a hoton galadima ya rungume munubiya ne bakinsa akan nata.
Hoto nabiyu kuma ni da shi ne afilin idi lokacin damukayi karo har wayarsa ta fad'i, ko kad'an bai ta6aniba, ko waya daya kar6a a hannuna hannuna danashi basu had'uba, amma anan an nuna hoton yana rik'e da hannuna duka biyu muna kallon juna.
“Innalillahi” nafara maimaita jikina har yana rawa, gawata uwar jufa data fara jik'a sassan jikina, lallai dolene duk inda muka gitta abimu da kallo.
Ju yowa nayi na kallo munubiya dake tsaye a bayana, itakam hawayema takeyi.
Jikina a sanyaye nakama hannuta muka fita daga cikin hall d'in, kallon da ake Manama ayanzu yafi na d'azun, Dan labarin sai kuma yad'uwa yakeyi yanzun.
Muna fitowa muka samu taxi sai gida.
Tunda muka sauka naga wasu gungun samarin dake layinmu a majalissarsu sun zubo mana idanu gaba d'aya, tuni zuciyata tafara tsitstsinkewa, kenan labarin harya iso nan?. Dagani har Munubiya jamukai muka tsaya, saboda ganin dukkan ahalin gidanmu tsaye cirko-cirko a tsakar gida, hardasu yaa hameed anguna, ga bak'i dabasu gama tafiyaba, innarmu kwance akan tabarma maman fauziyya namata fifita, ga Abbanmu kusada ita tsugunne yana shafa mata ruwa.
Jaridar dake hannun baba k'arami mukabi da kallo, bansan sanda wani kuka yatahominba nima, sa6anin da munubiya kawai keyin kukan.
Da gudu mukayi kan innarmu, amma sai yaa hameed ya daka mana tsawa, “karku sake Ku ta6ata wlhy, idan bahakaba jikinku kuwa saiya fad'a muku”.
Babu shiri mukaja burki, amma sai muka durk'ushe ak'asa muka fashe da kuka.
Innro tace, “kwayi kuka kuwa munafukai, ahiyyasa ai ANNABI yace a auri mace tagari, Dan 'ya'ya susami uwa tagari, yo wannan aimu ba sabon abu baneba agaremu, tunda dama halin uwarku kenan, itama saida tagama tambad'arta a titi aka k'ak'abama d'ana”.
Rintse idanu nayi saboda yanda maganganun innaro ke sukar zuciyata. Dady yakatseta da fad'in “dan ALLAH inna kiyi hak'uri kibar maganarnan”.
“hameesu barni nafad'i gaskiya, wannan abin kunya har ina, wai jikokinane yau aka buga ajikin jarida namiji rungume da d'ayarsu a titi” ta face hanci tana share hawaye da bakin zani, “ALLAH ya wadaran irin wannan rayuwa taku kuda uwarku, kun jawo mana abunkunya, yanzu dawane ido duniya zata cigaba da kallonmu” feeet, takuma fyace majina”.
Mudai ni da munubiya muna durk'ushe rungume da juna Luna rairai kuka maiban tausayi dacin zuciya, yayinda 'yan gidanmu da sauran 'yan biki suketa k'us-k'us a tsakaninsu.
Isowar likita yasa aka kama innarmu aka maida falon Abba, a sank'ame take tamkar gawa....
★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★
*_GAGARA BADAU PLACE_*
Shirye-shiryen komawa India yakeyi hankalinsa kwance, Dan yau zai koma ga mahaifansa da 'yan uwansa dake can, jirgin k'arfe 8pm zaibi.
Yana gama had'a 'yan abubuwan dazai iya buk'ata yadawo falo ya zauna, sanye yake cikin farare k'al d'in kayan Adidas na training, dogon wando da Riga mai dogon hannu, yasaki hular abaya, kayan sun masa k'yau sosai.
Kallo d'aya yayma abincin dake kan center table d'in ya d'auke kansa, cikin k'asaitacciyar muryarsa mai cikeda isar masu mulki naji ya furta “Saykin k'ofa”.
Kai kace anmasa dolene saiyayi maganar.
Da hanzari sarkin k'ofa yashigo falon, ya zube a k'asa “barka da hutawa ya shugabana”.
Kansa kawai ya jinjina, sannan yace, “waye yakawo abinci nan ne?”.
“ya shugabana bansan daga ainahin wane 6angare bane, amma bayin dasuka kawo daga 6angaren sarauniya Zulfah ne”.
Baice komaiba ya d'aga masa hannu alamun yatafi.
Sai da yad'an rissinar da kansa alamar girmamawa sannan yamik'e, dokace agareshi shi bayason kirarin da akema 'yan gidan sarautar. dan haka basa yimasa shi, Saboda gudun 6acin ransa.
zamewa yayi yay kwanciyarsa akan doguwar kujerar ya lumshe idanunsa batareda yabi takan abincinba.
Sallamar sarkin k'ofa tasakashi bud'e idanunsa akansa, ya amsa sallamar bisa la66ansa, sarkin k'ofa yazube agabansa, cikeda girmamawa yace, “ya shugabana yalla6ai Muftahu yace amasa iso gareka”.
Alama yamasa akan yabada izinin ya shigo.
Fita sarkin k'ofa yayi. babu dad'ewa saiga Muftahu yashigo da sallama, Galadima yabud'e idonsa yana kallonsa tareda amsawa.
Zama yayi kujerar dake kallon Galadima, yace, “yalla6ai barka da hantsi”.
Murmushi Galadima yayi, ya tashi zaune sosai yana fad'in “my man daga ina haka naganka ayikice? bakaje aikibane?”.
Ajiyar zuciya Muftahu ya sauke, yacije le6ensa na k'asa yana mik'ama Galadima jaridar dake hannunasa, “nafita wlhy sainaci karo da wannan jaridar data fito a safiyar yau”.
Cikin halin ko inkula Galadima yace, “Miye had'ina da jayidan to?”.
“Kayi hak'uri ka kar6a ka duba”.
A shafin farko yay karo da abinda yasakashi sake kallon Muftahu, kai Muftahu ya d'aga masa alamar yacigaba.
*_ANYI WALK'IYA...., GALADIMA DA AIKA-AIKA A FILIN IDI_*
cikin hanzari yabud'e shafin farko, nankuma an saka.
*_BABBAR MAGANA, GALADIMA SAMEER RUNGUME DA MATASHIYAR BUDURWA A PLAZA 'DINSA SUNA SUMBATAR JUNA!!_*
sai hoton farko dana biyu, wad'anda suka d'aure kansa, danshi gaba d'ayama ya manta daduk abinda yafaru, tundaga na birnin gayu plaza harna filin idi d'in. d'agowa yay yakalli Muftahu sannan ya maida kallonsa ga dogon rubutun da akai akan sharhin hotunan. bazai iya karanta rubutun ahakaba, saiya fara waige-waigen neman medical glasses d'insa.
Fahimtar haka da Muftahu yayi yace, “ina yake in d'auka maka?”.
Da hannu ya nuna bedroom d'insa ba tare da yace komai ba.
Mik'ewa Muftahu yayi yanufi bedroom d'in, babu dad'ewa saigashi yadawo, ya mik'a masa sannan yakoma inda yake da ya zauna yana fad'in “ko ka kawo na karanta maka”.
Nanma baice uffanba yamik'a masa jaridar, kansa ya maida jikin kujerar ya jingina ya lumshe idanunsa.
Tiryan-tiryan Muftahu yafara karanto k'aryar da aka jera jikin jaridar, ko sau d'aya bai motsaba, amma yana saurarensa.
Muftahu yagama cikin sauke ajiyar zuciya, Amma tabbas wannan wata k'ullaliyace, ai ba abinda yafaru kenanba jiya a birnin gayu, ni nama rasa mizan cema wannan gidan jaridar wlhy”.
Galadima ya bud'e idonsa dake a lumshe, ya kad'a yay jajur saboda 6acin rai, akan Muftahu ya saukesu batareda yace komaiba, tuno abinda yafaru a filin idi yayi kusan sati 4 kenan, tabbas sunyi karo da yarinya, wadda ayanzu haka ko fuskarta bazai iya tunawaba, dan ko'a waccan ranar kallo d'aya yamata, a jiya kuma ko ta6a yarinyar baiyiba ALLAH ya kareta daga fad'uwar dazatayi. jinjina kansa yayi cikeda 6acin rai da mamaki.
Muryarsa a sark'e yace, “Muftahu imason bayanai akan yayannan najikin jayiday su duka”.
“ok yalla6ai, amma ai yarinya d'ayace duba kagani”.
Kar6ar jaridar yayi yakuma kallon hotunan, tabbas duk yarinya d'ayace, wannan ya sake tabbatar masa da an shirya masa hakanne.
Mik'ewa yayi yazari mukullin mota batareda yace ma Muftahu komaiba, ganin haka shima Muftahu saiya mik'e yabi bayansa.
Cikin sauri dogaren dake binsa inhar zai fita suka taso gareshi, amma saiya d'aga musu hannu.
yana k'ok'arin bud'e motarne Jakadiyya ta iso inda yake...
Cikin rissinawa tace, “barka da hantsi galadima”.
Bai iya amsa mataba, sai hannu daya d'aga mata kawai.
Kuma rissinawa tayi tace, “Galadima takawane yabani izinin in kirayeka”.
Kallonta yayi zaiyi magana saikuma yay shiru ya maida motar yarufe tareda cillama Muftahu dake bayansa kyes d'in.
Muftahu ya cafe.
Komawa yayi 6angarensa yashiga wanka, kusan mintina 40 sannan yafito sanye da bathrobe fara k'al, bai wani d'au dogon lokaciba yay shiri cikin k'ananun kaya, yayi k'yau sosai, ya feshe jikinsa da turarensa masu matuk'ar k'amshi.
Wayarsa ce tashiga ringing, baibi takantaba yacigaba da hidimarsa, dama tun yana bathroom yakejin ana kiransa.
ta baya yabi inda bayi bazasu isheshi da gaisuwa gaisuwa d'innanba, dayake sarki yana gida, yau ana hutun zaman fada saboda tunawa da abinda yafaru da tsohon sarki (mahaifin Galadima Sameer) duk ranar litinin tana zama ranar daba'a zaman fadane...
★.★.★.★.★.★.★.★.★.★
Kowa ya ganmu yasan muna cikin rud'ani, da k'yar aka samu innarmu ta farfad'o, sai dai an hanamu mushiga mu ganta.
Gidanmu kam abin nema yasamu, hakama cikin anguwa, saboda yad'uwar labarin a social Media.
Muna zaune a falo duk mun zabga uban tagumi dagani har munubiya, idanunmu duksun kunbura saboda kuka, Ni ba abinda yafaru a jaridar ne yafi damunaba, halin da mahaifiyarmu ke ciki shine babbar matsalata, bamuda kamarta duk duniya, bazanso wani Abu ya sameta asanadinmu ba, bayan bak'incikin datake k'unsa agidanmu kuma.
Kamar anjeho mama Rabi'a itada ya Marwan suka shigo falon. mun tsorata kwarai da gaske, cikin daka tsawa mama Rabi'a take tambayarmu innarmu.
Hakanne ya tabbatar mana da suma labarin yaje musu. munubiya ce tabata amsa cikin kuka, sannan tace “wlhy mama sharrine, ba abinda yafaruba kenan n......”.
Saukar marin datajine yasakata rufe bakinta 6am, kafin na tantance mai Marin nima naji saukar nawa.
Ko kad'an yaa Marwan baiji tausayinmu ba, saida yamana lik'is da duka, dak'yar Dady ya kar6emu a hannunsa, amma baba k'arami da Abbanmu casukai yama k'ara mana.
'Yan gidanmu duk sunfito cirko-cirko a tsakar gida, kowa na tofa albarkacin bakinsa, gashi akwai sauran 'yan biki dabasu gama tafiyaba.
Iyayenmu da yayinmu duksun taru akanmu, ana tambayarmu wacece daga cikinmu.
Kafin Munubiya tayi magana nayi saurin cewa “kuyi hak'uri iyayena, nice munaya a gaba d'aya hotunan, wlhy kuma tsautsayine, amma ba ainahin abinda yafaruba kenan”.
Munubiya zatayi magana nayi sarin rik'e hannunta alamar kartace komai, “karki d'aurama kanki abinda ba laifinkiba Munubiya, nice Munaya na aikata....”
Itama cikin kuka tace “wlhy bake baceba, nice, wlhy nice”.
Nima nace “wlhy nice”.. ....
Tsawa Abbanmu yadaka mana, atare mukayi shiru yace “nasan dama Munaya kece, Munubiya bazata aikata wad'annan abubuwan ba, dukda kema d'in nayarda da tarbiyyar dana baki, amma bansan miya kaiki ga aikata hakanba, shiyyasa ranar idi mukaita nemanki, Ashe kinacan kina d'akko mana magana, tunda aure kikeso zan miki, nabaki nanda sati 2 kacal, inbaki kawomin mijiba zan had'aki dadu Wanda nayi niya”.
Yana gama fad'ar haka yatashi ya fice, baba k'arami ma ficewarsa yayi.
Wani kuka mai tsuma rai muka kuma fashewa da shi, musamman ma ni danasan nasaka kaina a tarko, amma hakan shine dai-dai, bazan amince naga 'Yar uwata cikin bak'in cikiba, insha ALLAH koma minene zan jureshi, muniya tanada hak'urin dazai iya cutar da ita akan wannan lamarin, gashi baba yafurta in ban fiddo da mijiba zai auramin Wanda yaso, to idan hakan ta kasance kan Munubiya wane hali kuke tunanin zata shiga? Musamna dabamusan gidan dazamu iya fad'awaba tunda nasan abinda Abba yafad'a tabbataccene, dan shi baya magana biyu.
Dady ne yashiga lallashinmu, tareda mana nasiha da nuna mana illar abinda muka aikata, musaman ma ni. ya Marwan kam sai antayamin harara yakeyi shida yaa hameed.
Yinin yau kam kuka muncishi harmun godema ALLAH, mu duka kwance muke rijif da zazza6i, har akayi isha'i bamu kumajin motsin kowaba, mukuma muna d'aki kwance mu duka k'udundune a bargo.
Su Aryaan sunacan nanuk'e da innarmu dake 6angaren Abbanmu har yanzun, dan haka 6angarenmu saiya kasance tsitt. a ranar dai haka muka kwana babu lafiya nida Munubiya, babu mai iya taimakon wani acikinmu, ga yunwa ga damuwa ga ciwo.
Zuwa asubahi ko salla kasa gashi muyita mukayi, dan k'arfinmu yagama k'arewa...😭
★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★
Ya isa sassan mai martaba, bayan masu tsaron k'ofa sun gama kwasar gaisuwa suka masa iso.
Izinin shiga mai martaba yabashi.
Falone k'aton gaske, Wanda nikaina banmasan yanda zan musalta k'yansa da girmansaba, ga kujeru rukuni-rukuni, ko ina yagama d'umamewa da sanyin AC, gawani k'amshi na musamman.
daga can gefe na hango mai martaba kishingid'e bisa wani lallausan carpet da aka k'awata da tarin tum-tum, gabansa tirene dake d'auke da jug na glass cikeda zo6o, sai wani k'aramin kwano na tangaram Wanda bansan miye acikiba, saikuma k'aramar butar shayi awani tiren daban, da mug guda d'aya.
Fuskarsa d'aure take tamau alamar yana cikin 6acin rai, ga jarida a hannunsa.
Cikeda girmamawa Galadima ya zauna a gefen dardumar, ya tankwashe k'afafunsa sannan ya risina yana fad'in “barka da rana ranka ya dad'e”.
Mai martaba bai amsaba, sai ma cilla masa jaridar hannunsa dayayi.
Galadima yabi jaridar da kallo batareda ya d'aukaba.
“ka d'auka ka duba mana, dan inason sanin gaskiyar zancen”.
Kan galadima a k'asa yace, “takawa nima yanzu Muftahu yakawo min nagani, nama fito zanje ga gidan jayidayne kiyanka ya isomin, amma wlhy Abba ba gaskiya baneba, ka.......”
Da sauri mai martaba ya d'aga masa hannu cikin 6acin rai “mi kakeson fad'amin? kana nufin zasu buga abinda baka aikata bane? ai sunsan gidan daka fito, haka kawai bazasu maka sharri ba kodan gudun abinda zaije ya dawo. Sameer yanzun nan da mutuncinmu kaje ka aikata wannan son zuciyar domin ka 6atama wannan masarautar suna? Lallai kacika d'an halak, kuma kayi dai-dai, tabbas ka kafa tarihin dawani bai ta6a yin irinsaba a wannan masarautar, Dama Ashe kabud'e waccan plaza d'inne domin son zuciyarka? Yanzu da ace lafiyar Yaya k'alau wane irin hali kake tunanin zai tsinci kansa? Ina ganinka shiru-shiru Ashe kaid'in shaid'anine”.
Runtse idanu Galadima yayi zuciyarsa na k'una da kalaman mai martaba k'anin mahaifin nasa, amma yagaza furta komai, sai idanunsa daketa k'are rinewa zuwa jajazur.
Har mai martaba yak'araci fad'ansa yagama Galadima bai iya furta komaiba, kansa ak'asa ko motsi baiyiba.
“katashi kabani waje, k'arfe 8:30pm akwai meeting, saika jira hukunci daga mama Fulani ”.
Rissinar da kai Galadima yayi yace, “ALLAH ya huci zuciyayka, na bayka lafiya”.
Banza mai martaba yay masa, yatashi yafice shikuma cikin k'unar zuciya.
Yana fita wayarsa ta fara ringing, ransa adagule yacirota da nufin kashewa gaba d'aya, saiyaga *_My dear Momma_* rintse idanunsa yayi ransa nakuma suya, yasan tabbas labari ya Isa gareta kenan, wannan wace irin masiface, mahaifiyarsa dake wata k'asa har ankirata an Sanar mata, ko halin datake ciki baza'a kallaba?. Kasa d'aga wayar yayi harta tsinke.
Tabbas duk Wanda yake gidan jaridarnan saiyayi Dana sanin saninsa arayuwa.
Kiran Momma ne yakuma shigowa, yanzuma bai d'agaba harya k'arasa sashinsa.
Sai da ya zauna sannan yafara k'ok'arin nemanta cikin suyar zuciya data ruhi...............✍🏼
To masu karatu, ko wanene da wannan aika-aikar? tabbas yau Munaya tabani matuk'ar tausayi daga ita har munubiya, kai harma Galadima.🤦🏻♀
Kumuje zuwa danjin Yaya kuma zata kasance🙆🏻?.
Yanzufa aka fara wasan👌🏻⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀🤾🏻♀
*_YA ALLAH ka gafartama iyayenmu😭👏🏻_*
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻🔟
.......Maman Fauziyya ce taga shirun yayi yawa narashin gittawarmu ta aiko Kamal yagani muna nan, dan ita azatonta ko mama Rabi'a tawuce damu gidanta ne.
Da gudu yakoma ya sanar mata gamucan babu lafiya a d'akinmu.
ai bata tsaya jin k'arshen zancenba ta garzayo, halin data iskemu aciki itama hankalinta yakai k'ololuwar tashi, takira baba k'arami a waya tana Sanar masa, duk da haushinmu dayakeji hakan bai hanashi shiga tashin hankaliba shima. atare suka shigo da dady, shima abbanmu sai gashi yashigo.
Duk kuma jikinsu sai yayi sanyi, aganinsu yakamata su sauraremu ajiyan, amma duk da haka babu iyayen dazasuga wannan abun hankalinsu bai tsashiba, garashi d'an manyan mutanene, nashi mai sauk'ine, amma mune awahale.
Haka aka kira doctor yaduba mu, yace damuwace ta haddasa mana zazza6in, sai kuma yunwa.
Da k'yar maman fauziyya ta taimaka mana mukayi wanka da ruwa mai d'umi, sannan mukayi sallar asubahi. tea ma dak'yar muka shashi sannan mukasha magani, still kwanciya muka k'arayi, nan barci ya kwashemu.
Dadyne ya kalli 'yan uwansa, cikin damuwa yace, “yaya Auwal yanzu bazamuyi wani yunk'urin bincike akan lamarinnan ba? ni dai sainake ganin kamar yarannan bazasu aikata hakaba, tsawon shekaru muna tare dasu, bamu ta6a jin makamancin abinan ba daga garesu, sainake ganin bai kamata mu yanke hunci ba akan abinda bamuda tabbas kuma cikin fushi”.
“Hameesu karka goyi bayansu akan wannan lamarin, babu yanda za'ayi abuga labarinan alhalin bai faruba, kaduba fa shi yaron d'ane ga Sarki, shinema Galadima, kodan tsoron abinda zaije yadawo ai nasan gidan jaridarnan saji tsoron buga labarin”.
“hakane yaya, amma baka ganin mak'iyanshi zasu iya amfani da wannan damar domin 6ata sunansa? maybe kuma su yaranmu tsautsayine ya gitta akansu”.
“maganarka gaskiyane Jafaru, nima wlhy hakan nake tunani, amma yakamata mujira muji daga gidan Sarki, Dan inhar Dan 6ata sunan yaron akayi nasan bazasu k'yaleba, kuma zasu nememu”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke yace, “nidai koma minene gsky aure yakamata ayima Munaya, Dan nikam banta6a cin karo da abinda ya rud'ar daniba irin wannan, mahaifiyar yarannan wlhy batayi barciba jiya, kwana tayi kuka, kuna ganin dai irin cin zarafin da inna tadinga mata jiya a tsakar gida gaban kowa, shin minene laifin A'isha akan wannan lamarin? zata aiki su Munubiya ne akan suje su aikata hakan?”.
“kayi hak'uri yaya, lamarin inna sai hak'uri, kasan dai halinta ai”.
Haka sukaita tattauna yanda zasu 6ulloma lamarin.
★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★
Jiki a sanyaye ya danna kiran Momma, bugu biyu ta d'aga, cikin girmamawa ya gaidata, ta amsa itama cikeda kulawa kamar yanda ta saba. hakanne yad'an sakashi jin sanyi a zuciya, ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in “Momma ya jikin Abie?”.
“Alhmdllh Moh'd. wani mummunan labari yanzu Ummu Erfaan takirani take sanarmin?, sai kuma ga mama Fulani ma takira tanata fad'a. yanzu kuma Sauban ya nunamin wasu pictures wai an turo masane”.
Rintse idanunsa yayi cikin k'unar zuciya, murya a sark'e yace, “Momma nima haka kawai nagani”.
“ban gane kaima haka kaganiba Moh'd, kagayamin gaskiya please, wannan ba k'aramin Abu bane bafa”.
Da k'arfi ya cije lips d'insa tamkar zai hudashi da hak'ori, cikin wata murya dake nuna k'ololuwar 6acin ransa yace, “Momma wlhy bansan komaiba, yanay idi tabbas munyi kayo da wata yayinya hay wayata tafad'i ta fashe, jiya kuma yayinya takusan fad'uwa a plaza nayi yink'uyin taimakon ta saima ALLAH yasa bata fad'iba, kuma ko ta6a banyiba, shine kawai yau gidan jayiday nan suka maida pictures d'in haka fa”.
Ajiyar zuciya Momma ta sauke, (dan tarigada tasan halin d'an NATA, duk da ba'a shaidar d'an yau musamman idan yabar gaban idonka) “Muh'd tabbas wannan k'ulline, amma kuma yarinya d'ayace ai”.
“haka nagani nima Momma”.
“yanzu mi sarki yace?”.
“Momma wlhy maganay babu dad'inji, hayma sun shiyya meeting a kaina”.
“Humm Muh'd wannan maganace mai girma, kuma tabbas domin 6ata sunanka ne da namu akayi, akwai kuma dalilinsu nayin hakan, ita wannan yarinyar kodai da saninta kokuma an shigo da itane saboda cikar manufarsu”.
“Momma su waye to?”.
“Masusan ganin bayanmu mana, sun biyo wannan hanyarne domin dak'ileka da ragema kaifi”.
Wani naushi ya kaima k'aramin teble d'in gabansa na glass, nan take ya tarwatse. bai damu da ciwon dayajiba, cikin k'araji yace, “tabbas kafin suga bayana nizanga nasu!!! rayuwar mahaifina bazata salwanta abanzaba!! Saina wulak'anta dukkan masu hannu aciki kosu waye su wlhy billahi Momma! numfashina fansa akan mahaifina!!”.
Dole Momma tacire wayar daga kunnenta saboda yanda Galadima ke magana cikin matsananciyar tsawa.
Saman kujera ya wurga wayar, batareda ya katse kiranba, afusace yafito daga 6angaren nasa, tsawa ya dakama dogaransa.
Gaba d'ayansu cikin rawar jiki suka nufi motocin da ke fake a wajen, ko jira abud'e masa baiyiba yabud'e yashiga.
Hankalinsu a tashe yake daganin yanayin shugaban nasu, sunsan tabbas ran 'yan maza ya 6aci yau, Dan kowa yasan rashin son hayaniya irinta Galadima a masarautar nan.
Saida suka fito daga masarautar a d'arare sarkin mota yace, “ranka ya dad'e ina muka dosa?”.
Tamkar bazai tankaba, sai kuma can afusace yace, “plaza!”.
“angama Ranka ya dad'e, ALLAH ya huci zuciyarka ya shugabana”.
Banza yamasa bai tanka masaba, sai huci yakeyi yanna karkad'a k'afafu da taunar lips, idonsa yayi zajur saboda masifar 6acin rai.
A plaza ma tunda yashigo kowa ya fahimci yanda cikin 6acin rai, Dan ko kallon masu gaisheshi bayayi, mutane masu siyayya sai kallonshi sukeyi, dama wasu gulmace takawosu dansu k'ara ganema idonsu akan labarin da ayau yazaga ko'ina da ina. kai tsaye wani Office yashiga.
Cikin hanzari Wanda yake a office d'in yamik'e domin kwasar gaisuwa, sai dai yanayin ogan NASA yayi masifar rikitashi.
Bai saurari gaisuwarba yace, “inason ganin abinda yafayu a CCTV tundaga safiyay jiya hay daye”.
Jiki Na rawa guy d'in yace “angama ranka ya dad'e”.
Kujera ya jawoma Galadima ya zauna, sannan yagyra zaman computers d'in wajen sosai, tariyo wa yafarayi cikin nutsuwa, saida yadawo Sunday morning 6pm sannan ya saki, tundaga bud'e plaza har zuwa masu share-share da goge-goge dasukayi aikinsu, har lokacin da masu sayayya suka fara Shiga da fita a plaza d'in, har an wuce yace “dawo baya kad'an”.
A slowly yadawo bayan kad'an, har zuwa kan wasu samari biyu d'aya sanye da jallabiya d'ayan wandon Jeans da farar t-shirt.
“kayo zooming d'in yayannan dake tsaye sunan waige-waige”.
Zooming d'insu yayi, sannan yasanya play yanna tafiya a slow.
Samarin sunata 'yan kalle-kallene, saikuma zuwa can d'aya yasaka waya a kunne yana magana da kallon cctv camera d'in dake hasko tsakkiyar plaza d'in Inda motoci ke Parking, saikuma ya janye idonsa ya maida kan motocin dakeJere a wajen. da ganin Kasan yana maganane, Dan d'ayan dasuke tare yanata gyad'a Kansa alamar gamsuwa da abinda d'an uwansa yake fad'a.
Galadima Na zaune shiru, idonsa nakan computers d'in yana nazarin gayun har aka wuce Kansu, baice uffanba yacigaba da kallon shigi da ficin jama har zuwa 8:11pm, daga nan Computer tayi d'iff.
Da Sauri Galadima ya kalli sarayin “mi yake fayuwane?”.
“Ranka ya dad'e wlhy nima ban saniba, amma bara Na duba”.
Danne danne saurayin yafara da 'yan dube-dube, babu wata matsala daga nan.
Kallon Galadima yayi yace “ranka ya dad'e babu wata Matsala daga nan, sai dai Idan daga cameras d'inne”.
A tsawace yace “bangane mikake nufi daga cameyas d'inne ba!? Kenan hay shigowata jiya babu kenan!? kuma kana zaune a office amma bakayi complain ba tun ajiyan? mika aikata!!? mi suka baka ne domin tozarta ni!!? nace nawa suka baka Saleem!!!!?”.
Kusan duk Wanda ke cikin plaza d'inan a yau yaji wannan hargagin Na Galadima.
Jikin matashin saurayin ne yafara rawa, ya zube a k'asa gaban Galadima saboda tsabar tsoratar dayayi da yanayinsa, tunda yake aiki a k'ark'ashinsa baita6a ganinsa cikin wannan yanayin irin Na yau d'inna ba, duk da labarin abinda yafaru yazo kunanensu, sunkuma ganin a jarida da social media baiyi zaton lamarin zaiyi zafi hakaba.
“wlhy yalla6ai babu Wanda yakeda abinda zai sayeni na cutar dakai, Kaine ka ceci rayuwata daga garari, ka tallafi maraicina a lokacin da nake Neman lalacewa saboda rashin matallafi, kazama gatana nida mahaifiyata da k'annena, mizaisa nabiyema rud'in wasu akan 6ata maka suna....”
“ya Isa haka!!”. ‘galadima yafad'a cikin tsawa’.
Gaba d'aya Galadima ya birkice musu a plaza, yasa securitys d'in wajen da dogaransa sun kori dukkan masu sayya dake ciki, ya tartare ma'aikatan wajen a d'aya, ya tabbatar musu da in har munafukan cikinsu da aka had'a baki dasu basu fidda kansuba gaba d'aya sai sunyi dana sanin saninsa.
Kaf d'insu sun rud'e, sai rantse-rantse da k'ok'arin kare Kansu sukeyi, amma yak'i saurarensu, ganin zasu kuma dagula masa lissafi saiya basu suspension kawai aka rufe plaza d'in baki d'aya.
Motocinsa Na k'ok'arin barin wajen motar Muftahu tashigo.
Muftahu ya faka motarsa waje d'aya suka fito shida Harun, (shima Harun abokin Galadima ne makusanci, Dan zan iya cewama yafi sanin sirrin Galadima fiye da kowa a abokansa gaba d'aya, shi d'an waziri ne).
Tunkan su k'araso Galadima ya sauke glass d'in motar da kansa. kallo d'aya sukai masa duk suka tsorata, Dan basu ta6a ganinsa a irin wannan 6acin ranba, baice uffanba, sai nuni daya musu akan su shigo motar.
Basu musaba suka bud'e suka shiga, Muftahu a gaba, Harun yashiga baya kusada Galadima.
Bayan gaisuwa dasukayi garesa babu Wanda Yakuma cewa komai, Dan ko gaisuwar bai amsa musuba, hannu kawai ya d'aga musu.
Sun hau titi sarkin mota yace “Ranka ya dad'e ina muka dosa?”. ‘cikin girmamawa da taka tsantsan yay maganar”.
Murya a shak'e yace “gidan Jayiday”.
Sarkin mota bai fahimtaba, amma yana tsoron tanbaya, murya k'asa-k'asa ya tambayi Muftahu ”.
Murmushi kawai Muftahu yayi yana girgiza kai, shiya shiga yima sarkin mota kwatance har suka Isa.....
★.★.★.★.★.★.★.★.★.★
Muna tsaka da barci saboda allurar da doctor yamana Innaro tafad'o d'akin, babu ko tausayi tashiga tashinmu cikin d'ad'd'aka mana duka a baya da cinyoyinmu.
Dagani har Munubiya a firgice muka tashi zaune.
“kutashi munafukai, Ashe abin ba a iya runguma da kama hannu ya tsayaba harda ciki kuka kwaso mana?, tsinannun gayyar tsiya, wlhy dagaku har uwarku yau saikin bar gidanan, a yau d'inan idan ubanku bai saki uwarkuba kun tattara kun tafi saina tsine masa albarka, yazo yaza6a ko Ku ko ni yau agidanan. sai kuma tafashe dakuka, takama bakin zaninta datayo lullu6i tana sharar hawaye, “kai ni dai Malam ya cutar dani akan had'a wannan aure da d'iyar marasa asali, ai gashinan ta Haifa mana bala'i da masifa, shikuma yatafi yabarni da kunyata, Malam kacuceni katafi kabar mana baya da k'ura. Wlhy yau sai A'isha tabar gidanan itada gayyar tsiyar 'ya'yanta, natsaneku daduk wandama zai soki A'isha, natsaneku wlhy, takuma fashewa da kuka.
Tuni matan gidanmu kowa yafito, wasu harsun shigo falonmu, wasu kuma Na daga k'ofar d'aki, harda tsirarin 'yan biki da sukak'i tafiya domin tsayawa kallon kwaf.
Cikin matan gidanmu ne wata taje tasanarma innaro wai bamuda lafiya munata amai duk abinda mukaci, anakiran likita ya dubamu yace duk munada ciki wata uku-uku.
Ni da Munubiya mun had'e kai muna kuka mai tsuma rai saboda tozarcin da innaro kemana muda mahaifiyarmu agaban bainar jama'a.
Dady da Abba k'aramine suka shigo sunama innaro magana akan bafa haka zancen yakeba, babu Wanda yace munada ciki.
Hayayyak'o musu tayi tana zaginsu, wai k'aryane suna kare Innarmu ne, aida likitan bai fad'aba baza'aje a sanar mata ba.
Cikin 6acin rai baba k'arami yace, “inna waye yaje yafad'a miki wannan maganar to?”.
“cikin matan gidanan mana, kuma daga bakin wadda nasan bazataimin k'aryaba”.
Ran Dady ma a wannan karon ya 6aci, afusace yace, “inna wacece acikinsu? Wace 'Yar isakar matace”.
Nanafa matan gidanan mu suka shiga raba idanu akan juna.
Innaro tace “karka kuma zaginta, idaba ayiba bazatace anyinba, kuma koma wacece bazan fad'aba, idan kuma ni kake zagi sainaji?”.
“ALLAH ya huci zuciyarki inna, ni yaza'ayi Na zageki”.
“kai dai kasani sakarai”.
Duk abinda ke faruwa Abbanmu da Innarmu Na saurare daga d'akinsa amma acikinsu babu Wanda yayi yunk'urin fitowa.
Kayanmu innaro tafara kwasa tana watsowa waje, wai saimun bar gidan.
“Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, wannan wane irin tashin hankaline?”. ‘innarmu tafad'a cikin matsanancin kuka’.
Rungumeta Abbanmu yayi shima yana k'ok'arin maida kwallar data cika masa idanu.
Ganin abin yana Neman wuce gona da iri baba k'arami yafita da hanzari, wani tsoho dake can k'asan layinmu yaje ya d'akko, tsohon abokin Malam faruku ne na k'ut da k'ut, shika d'aine zai iya takama Innaro burki kuma.
Aiko hakance ta kasance, tunda yashigo yay magana Innaro ta dakata da abinda takeyi tana huci da fidda numfashi.
Tsoho Malam Labaran yace, “haba innar jafaru, da hankalinki da girmanki kike aikata wannan abin Na yara a gaban sirikanki da 'ya'yanki da jikokinki? Shin babu mai fad'a miki kijine wai kekam?”.
Cikin sassauta murya tace, “malam mai kanwa nasan bakasan ainahin abinda yafaru bane kaima, amma wlhy da dakanka zakace Auwalu yasaki marar asalinnan sukama gabansu itada 'ya'yanta am.....”
Hannu ya d'aga mata, yagyara tsayuwarsa jikin sandarsa dake taimaka masa tafiya, naji komai innar jafaru, amma wannan hanyar da kuka biyo ba wai itace mai 6illewa ba, bincike yakamata ayi domin asan gaskiyar lamarin. dan haka zoki wuce gida, zuwa gobe zamu tattauna akan lamarin sannan kowa ya nutsu, mukuma jira abinda zai fito daga can gidan Sarkin”.
Badan innaro tasoba tafice, hakama matan gidanan mu basuso wasan yak'are iya nanba, sunso a yau Innarmu tabar gidan da saki, sannan mukuma mahaifinmu ya koremu. Kowa taja k'afa takoma d'akinta cikeda takaici da addu'ar ALLAH yasa daga gidan sarkin suma su d'auki mummunan mataki akanmu.....
Maman fauziyya Ce kawai ta nuna damuwarta akan lamarin
★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★
Su Galadima ma sun isa gidan jaridar *Manuniya* tun sanarwar isowarsa ta kad'a hantar cikin ma'aikatan wajen, musamman wad'anda basuda laifi akan lamarin, tirsasu akayi.
Shi kansa manaja d'in wajen a kid'ime yake, dukya rikice yarasa matsugunni har Galadima da gayyarsa suka iso office d'in bisa jagorancin sakatare d'insa.
K'asa yazube kawai yana kwasar gaisuwa wajen Galadima, ko kallo bai ishi Galadima ba, cikin daka tsawa yafara magana...........✍🏼
Tofa masu karatu, ko manajan jaridar MANUNIYA zai amsa laifinsa? Kokuwa zai fad'i wad'anda suka sanyashine inba laifinsa bane shima? to koma dai shima da had'in bakinsa?. Wane mataki masarautar su Galadima kuke ganin zata d'auka akansa? Shin ina ma maganganun Momma suka dosa ne? Miya faru da mahaifin Galadima har suka koma k'asar India da zama?.😕
Kumuje zuwa my guys danjin yanda zata kaya. da amsoshin d'unbin tambayoyinkun nan.
0 comments:
Post a Comment