Hausa novels 2023

  • Home
  • Ciwon Idanuna
    • Internet
    • Market
    • Stock
  • Agola
    • Dvd
    • Games
    • Software
      • Office
  • Mijin Biza
    • Child Category 1
      • Sub Child Category 1
      • Sub Child Category 2
      • Sub Child Category 3
    • Child Category 2
    • Child Category 3
    • Child Category 4
  • Kwarata
  • Health
    • Childcare
    • Doctors
  • Inda Ranka

Monday, November 27, 2017

AGOLA Page 41-50 (The end)

 November 27, 2017     AGOLA 1-END     No comments   

AGOLA Page 41-50 (the end)

.

Suna zuwa aka nufi labour room da ita, shi kuma Saleem yashiga da Jalila su Bilkisu suna binshi abaya, itama daki aka nufa da ita domin adubata. Sameer gurin su Baba Mairo yanufa, koda yaje ya iske har ansaka gawar Jidda ambulance, za,a kaita gida, Baba Mairo tace lafiya Sameer naganka arude? Alh wanda fuskar shi take jike da hawaye, ya goge idon shi yace lafiya de Sameer? Yace bakomai dama Falak ce zata haihu tana dakin haihuwa.


Alh, yace to ina Jalilan kotana gidanta? Kai yasosa yace a,a nabarta ita da Saleem inaji befada mata ba, yauwa kada kufada mata kawai yadauketa yakaita gida. Baba Mairo kikoma gurin Falak din mucemu wuce da gawar, tunda Halima tana gurin Zarah.

.

Goge kwallan idon ta tayi tace a,a Alh muje inaso inyima Jidda wanka da kaina, kai Sameer kasamu Halima tunda dazu akayi ma Zarah allurar bacci kace taje gurin Falak din, nizanje can gidan. Yace to nima yanzu zanzo kafin agama shiryata tunda ance yau za,a kaita tunda dare beyi ba.


Haka suka nufi gida da ita kowa yana cikin damuwa. Babu bata lokaci Falak ta haifi kyawawan yaranta guda biyu, Mace da namiji, cikin koshin lafiya, bayan angama shiryasu aka fada masu Sameer, Bakaramin murna Sameer yayi ba, dan betaba tunanin samun yan biyu ba. Wayarshi ce tayi kara, yana dubawa yaga Saleem.


Dauka yayi yace Saleem ya Jalilan ta farfado? Yace E amma haryanzu kamar bata gama dawowa hayyacinta ba, amma likitan yace zeyi mata allurar baccin dazata kaita har gobe dan tasamu ta huta. Sameer yace toshikenan yanzu itama Falak ta haihu, ansami twins, fito muhadu semuwuce can gidan.


Saleem yayi farin cikin ganin jariran masu kyau dasu, bayan ankai Falak dakin hutu, itama haryanzu kuka takeyi, suka dubata da jiki, suka ce zasuje sukai Jidda, Falak tace Allah sarki Yaya Jidda Allah yajikanta, naso ace nakara ganinta. Sameer yace se hkr addu,a zamu cigaba dayi mata, bara muje semun dawo, nasan se gobe za,a sallameki gara kizauna ana ku huta, tace tosekun dawo ina Jalilafa? Anan suka fada mata abinda yafaru, tace to Allah yabata lafiya, haka suka fita suka bar Umman Sameer agurinta.

.

Gida mata se kuka sukeyi, Baba Mairo da Matar Kawan Alh, su sukayima Jidda wanka, suka shiryata, babu bata lokaci aka fiddota, akayi mata sallah,aka nufi gidanta na gaskiya da ita.

     Koda sukaje Alh, kasa sakata kabari yayi, sbd kukan dayakeyi, sede su Kawu ne da Baba na Zariya da Kawun Sameer suka sakata, Alh, yabama kowa tausayi agurin, haka aka gama sakata akabarinta aka rufeta, suka dawo.


Aranar haka kowa yazauna masu bacci kadan ne, dan Alh, tunda yashiga daki, yayi wanka yayi alwala yayita nafila da karatun Qur'ani har seda aka kira sallah sannan yanufi masallaci. Bayan sunadawo ne, yake tambayar Sameer yabega Jalila ba, anan yake fada mashi halin datake ciki, da kuma abinda Falak tasamu, yayi murna sosai, yace tobai bazama zamuyi ba, muwuce muga jikin nasu.


Lokacin dasukaje asibitin har Falak tayi wanka Anyima jariran wanka suma, sunyi gwanin kyau, sede daka kalli Falak kasan tana cikin damuwa. Baba Miaro tana kusa da ita dan agurinta ta kwana, ita kuma Umman Sameer ta kwana agurin Jalila ita dasu Bilkisu.


Jalila kuwa tafarka, tunda tayi sallah itama take kuka, se lallashinta sukeyi, haka Alh, yasameta, yana ganinta shima yaji wani sabon kukan yazo mashi, da kyar yasamu yadedeta kanshi yashiga, shima lallashinta yashiga yi, sannan suka nufi gurin Falak, acan ma du lallashin ne, daga can yawuce gurin Zarah.


Zaune suka sameta duk ta kwance bandage din da aka rufe mata ciwon tana ta wasa dashi, cikin sauri Saleem yaje yajira nurse, ana suka riketa aka sake mata wani sabon dressing din. Tagumi Alh, yayi, yana kallonta, yarasa neke mashi dadi aranshi, addu,a kawai yakeyi itace take kara sanyaya mashi ranshi. Fita yayi yace bara yatafi tunda gari yayi haske sbd masu zuwa gaisuwa.


Karfe 10 aka sallami Falak da Jalila, Baba Mairo tace awuce da Falak gidansu Jalila, idan kunje se a bude part dinsu nada tazauna aciki, sbd asamu saukin zirga zirgar. Sameer yace hakan ma yayi, tace nima anjima zanzo sbd nasan babu wanda ze zauna agurinta, idan yaso se Halima tazauna agurin Zarah, anjima se indawo.

.

Sunzo tafiya, su Bilkisu sukace bara suwuce gida anjima zasu dawo, godiya sukayi masu, Saleem yabasu kudi suka tafi, sun fito kenan suka hadu da Al,amin, Jalila yagane, hakan yasa ya tsaya suka gaisa, kallonta yayi tana kuka yace ina fatan kunshedani? Al,amin ne, yame jikin? Falak tashare idont tace Allah yayi mata rasuwa jiya da dare. Kiyayi kamar ansara mashi icce akanshi, wasu irin zafafan hawaye ne suka zubo mashi. Yace shikenan Jidda ciwo ya warke, darabon mugana ashe, sallama yayi masu yace zeje yadauko Ameerah suzo tare.


An gyara part din su Falak na da dama kuma babu abinda aka cire aciki, tunda Hajjo tarasu da aka kulle shi ba,a kara amfani dashi ba, share shi akayi aka goge, sannan Falak da Jalila suka shiga ciki, amma Falak cewa tayi adakinta na da zata zauna bazata shiga dakin Ummanta ba, Sameer yaje yadauko mata duk kayan dazasuyi amfani dasu yakawo, Baba mairo ta dora ruwa takara yima yaran wanka, tasa Falak itama takara yi.


Saleem ne zaune afalo shida Jalila, haka yayita lallashinta da kyar yasamu taci abinci shima kadan taci, yace Jalila inaso ki kwantar da hankalinki yanzu babu abinda Yaya Jidda take bukata daga gurinmu se addu,a. Kirika yawan ambaton Allah da addu,oi zaki samu sauki aranki, nasan dole kiyi kuka amma hakuri zakiyi. Allah yaji kanta, yabama Ummi lafiya, tashi yayi yace zeje waje. Itama shiga gurin Falak tayi, dan batason zuwa bangarensu.

.

Haka aka cigaba dazaman gaisuwa, Al,amin da Ameerah sunzo gaisuwa, itama tasha kuka, Al,amin yakira Jalila yace yadauki nauyin ginama Jidda rijiya amakarantar almajirai kamar yanda taroka, kuma zeginata ne da sunan ta, amatsayin sadakar daze bata. Sosai Jalila tayi mashi godiya, seda suka jera kwana 7 suna zuwa gaisuwa, ranar da akayi sadakar 7 aranar akayi sunan Falak, bawani taro akayi ba, bayan sadakar 7 akayi radin suna.


Namijin aka samashi sunan Alh, wato Abba, ana kiranshi da Ameer, dan Falak tace tana son sunan, Macen kuma Aka samata sunan Hajjo, Zainab, ana kiranta da Ameerah. Falak tayi mamaki sosai da Sameer besa sunan babanshi ba, har seda tayi mashi magana, murmushi yayi yace haba Dear, Alh, shine mutumin da yayi sanadiyar haduwata dake, kuma ya cancanci abinda yafi haka agurina dake baki daya. Umma kuma dana sa sunanta, kinga tarasu kuma saka sunanta zesa murika tunawa da ita, jawota yayi yace kada kidamu nasan nan da shekara 2 zaki kara sama mana wasu babies din. Murmushi tayi tace nagode.


Ayau ne, Jalila zata koma gidanta, dan Alh, yace sutafi gida zatafi samun sakewa idan tana kusa da mijinta, sauran mutane ma, duk sun watse se yan uwa kawai suka rage, yan Zariya ma yau zasu tafi, Alh, yasa aka kira kowa yace yana son magana dasu, anan falonshi suka taru, hada Kawunshi, da Kawun Sameer, da Mal. Garba dasauran mutanen.

.

Bayan anbude taro da addu,a, aka kara yima Jidda addu,a sannn Alh, yafara magana, hakuri yakara bama kowa, sannan yace Jalila,Falak, ayau nakeson kowa takoma gidanta, wanda yarasu yariga da yarasu, dan haka addu,a kawai zamu cigaba dayi mata, banaso insamu labarin acan kun kasa sakin jikinku, kowa hkr yakeyi arayuwa, kuma dama dan Adam baya zama haka, har se Allah ya Jarabceshi, dan haka murika daukar kowace kaddara tazo mana da hannu 2, Allah yayi maku Albarka.


Kuma itama Zarah munyi magana da Malam, yace gobe Malaminshi zezo yafara yimata rukiya, dan haka nayima Dr, magana zamu maidota gida yau, idan yaso se arika zuwa gida ana mata dressing, tunda yanzu yakoma bayan kwana 2. Kallon Kawaunshi yayi yace Kawu ko akwai abinda zakace?.


Gyara zama yayi yace hakane, duk abinda kafada yayi dede, sede abu 1 nakeso inkara, Baba Mairo mungode kwarai da irin abunda ku kai mana, daga ke har Halima, tabbas kunzama yan uwa, sede ina rokonki wata alfarma, daga ke har Halima, duk da bata nan, amma ga malam nan, muna neman alfarmar daka barsu sudawo gidan nan dazama, kaga akwai marar lfy, kuma yanzu Zarah ba matsayi matar Abba take ba, asali ma, babu sauran igiyar aure atsakaninsu, idan har kayarda mun rokon alfarmar dasu dawo nan dazama, hakan zeyima Abba sauki dan baze yuwu ace mubama shi mal. Garba ita yatafi da ita ba, duk da tayi mana laifi amma ba,a kallon abinda yawuce, idan ka kalli alherin da mutum yayi maka zaka iya temaka mashi dashi.


Kaima Abba dole kayi hkr da duk abinda Zarah tayi maka, tabbas tacutar da kai da kowa naka amma, ka kalli darajar yaranku kayi hkr, inaso tacigaba dazama agidan nan har Allah yabata lafiya, daga nan kuma seta zaba ma kanta abinda taga zefi mata.

   Amma inaso inji daga bakinka ka amince zata cigaba dazama agidanka harta samu lafiya?.

      

       Se kunjini a next page dina wadda insha Allah shine last page. Nagode da kaunarku gareni.


.


Shiru Alh, yayi nawani lokaci, sannan yace shikenan Kawu duk abinda kace yayi dede, Allah yabata lfy. Kuma nagode da abinda kuka yi mani, Allah yasaka da alkhairi. Kawu yace Alhmdll, anjima malamin ze iso, dan haka se kuje kudauko ta. Haka suka tashi kowa yafara shirin tafiya.


Bayan andauko Zarah daga asibiti duk wanda yaganta seya tausaya mata, takoma kamar skeleton ne aka sama fata, tayi baki, ga kafarta da aka yanke tundaga cinyarta har kasan kafar sun shanye tazama siririya, ta yanda bazata kara amfanuwa ba, sede ciwon dake jiki yayi sauki, sbd Kawu yabada ruwan addu,a ana shafa mata akan ciwon, hakan yasa yadena fitar da ruwan dayakeyi, kuma dama aljanun jikinta ne suke sakashi zuba.


Jalila da tunda ta kalli Zarah take kuka, a part dinsu Falak Alh, yace akaita, awani daki dayake farkon shiga daga gefen falon, anan aka saka mata katifa, dayake akwai bandaki aciki, sede dakin bawani girma gareshi ba, bayan su Baba Mairo sunyi mata wanka, suka gyarata aka daureta tana kwanciya tayi bacci.


Saleem ne yazo daukar Jalila, tana kuka haka suka tafi su Baba Mairo se hkr suke bata, Falak ma seda tayi mata kuka, Sameer yace kema shiryawa zakiyi anjima zamu tafi, Baba Mairo tace gsky bazaku tafi ba, dama inaso inga Alh, muyi magana, dama ace yaro daya gareta se kutafi, amma yara har biyu, sannan kai kuma aikinku idan kafita wani lokacin har dare kake kawai, yazatayi da yaran? Kuma kaga muduka muna nan bare ma ace ni inje inzauna mata. Sameer yayi murmushi yace haba Baba yanzu dan Allah so kuke inzama gauron karfi da yaji? Inde haka ne, nima sede indawo nan. Baba Mairo tace nidama ai bance zan hanaka ganin matarka ba, sekaje ka kullo gidan kaima kadawo nan idan sukayi ko wata daya ne, sunyi kwari se ku koma gidanku. Yace shikenan nagode, tace yauwa zanje insamu Alh.


Da misalin karfe , Kawun Sameer suka iso da Malamin dazeyima Zarah karatu, Alokacin shima Sameer ya iso gidan da akwatinshi, dan Alh, yace shima yadawo, a dakin Falak yasauka, su kuma su Baba Mairo suna dakin Hajjo, Alh, shi kadai a part dinsu.


Afalo akayimata shinfida bayan sunyi mata alwala, malamin yazo yafara yi mata karatu, yadade yana karatu amma sunkiyin magana, sbd manyan aljanune, kuma bakake, yasha wahala sosai, kafin suka fara magana.


Wayyo Malam, ya isa zamuyi magana wlh, zufar goshin shi yagoge yace inajinku..... nide sunana Zurkum, kuma nine shugaban bakaken aljanu, wannan matar bata da kirki, sunyi da megidanmu akan duk lokacin da mijinta yagane halin datake ciki, akwai abinda ze sameta, amma haka ta amince, mu kuma dama mune yasa muke mata aiki, kuma dama duk wanda ya kasance yana maka aiki duk ranar daka dena biya mashi bukata, to kanka ze dawo, hakan yasa tundaga ranar da asirinta yatonu muka shiga jikinta.

.

Mune nan muka fado mata da durowa akafarta, kuma muka shanye jinin jikin kafar da bargon kafar, hakan yasa bazata kara amfani da kafar taba, tabbas wannan mata tayi sa,a tasamu masu yimata addu,a amma munso semun bi duk wani jini dayake jikinta munshanyeshi duka sannan daga karshe mukasheta, amma karfin addu,ar da akeyi mata yasa muka kasa aikata abinda mukayi niya. Amma kusani wannan mata bazata kara ganin haske arywarta ba, sbd tasamu mun cuci mutane, aciki harda karamin yaro wanda besan komai ba.


Dan haka kada ka konamu zamu tafi amma duk lokacin data kara shiga gonarmu tabbas takira ajalinta. Malam yace kuyi mani alkawarin bazaku kara shiga jikinta ba, idan kun fita. E munyi alkawari, amma itama ta gyara rayuwarta, takuma koma ga Allah wanda take bautamawa, hakanne ze kareta daga shrrinmu. To nagode.


Wata irin kara Zarah tasaki tare da atishawa, har so 3 sannan takoma ta kwanta, bacci yadauketa. Malam yace Alhmdllh, insha Allahu data farka zata dawo hankalinta, sede ina tunanin zata iya kaiwa gobe, dan haka zantafi gobe da safe zandawo. Ga wannan asamu wani ya zauna kusa da ita, aduk lokacin data farka abata wannan ruwan addu,ar tasha. Allah yakara sauki, kome kenan sauran bayanin idan nazo gobe zakuji.


Godiya sosai, sukayi mashi, yatashi yatafi. Falak, tana gefe se kuka takeyi, Baba Mairo tace banga amfanin asarar hawayen da kikeyi ba Falak, ace kuka yaki karewa, haba dan Allah, so kike kijama kanki wata cutar. Umman Sameer tace gsky Falak ya isa haka, kin sande kuka baya maganin komai, nasan akwai abubuwa da yawa dakike tunawa, amma kiyi hkr kisama kanki dangana, kinga kinrasa mutane dayawa arayuwarki, kuma duk da haka numfashinki bedena tafiya ba, dan haka kimanta da duk abinda yafaru dake arayuwa, Allah yana tare dake.

.

Idan kika kalli baiwar da Allah yayi maki ta yara 2 ya isa ki godema Allah, ada kinkasance ke daya, yabaki miji nagari, sannan yazo ya azurtaki da yara, Allah kadai yasan iyakar abinda zaki haifa, kinga wannan ma wata rahama ce daga Allah. Falak tagoge idonta tace nagode, da irin kulawarku gareni, kuma insha Allah, nadena saka damuwa araina. Baba Mairo tace yauwa kokefa, tashi ki kaima mijinki abinci kije daki kidauko yan biyu ki maidasu dakinku.


Bangaren Amarya da Ango kuwa, da kyar Saleem ya lallashi Jalila, taci abinci tayi wanka, yasa sukayi sallah, yajata zuwa gado yacigaba da lallashinta yana kara kwantar mata da hankli, taji dadin irin kalaman dayake fada mata sosai, cikin lokaci kankani taji zuciyarta tayi haske, duk wata damuwa ta gushe, daga lallashi shima ango ya canza tasha, naja masu kofa nace seda safenku.


Washe gari da safe har 8 tayi amma Zarah bata farka ba, mutanen gidan harsun gama karyawa, sunyi wanka, suna jiran tashinta, Baba na Zariya kuwa har yagama shiryawa dan yace shima yau zetafi, jiran tashinta kawai yakeyi da kuma jawabin da malam yace zeyi, se wajen 8:30 sannan ta farka cike da firgici, Baba Mairo tayi saurin riketa tana tofa mata addu,a Umman Sameer tamiko maganin da malam yabasu aka bata, kallonsu kawai takeyi Babanta yace kintsaya kina kalon mutane bazaki bude baki kisha maganin ba? Baki ta daga tasha maganin, sannan tamaida kallonta zuwa cikin Falon, akan Alh, tasauke idonta, suna hada ido yayi saurin dauke kanshi tare da kara daure fuska. Juyawa tayi tana kallon Baba Mairo da Falak, wacce take rike da Ameerah, dan Ameer yana bacci.


Sauke kanta kasa tayi dasauri takara kallon Alh, idanunta suka ciko da hawaye ganin kafarta datayi anyanke, kuma ta koma siririya. Haka falon yayi shiru kowa yana kallonta. Sallamar su Kawu da Malam sukaji, anan Alh, yafita domin ya shigo dasu. Bayan sun shigo aka gaggaisa, suka samu guri kowa yazauna, Sallamar Saleem da Jalila sukaji, dan Alh, yayi ma Saleem waya akan suzo. Falak da tunda taga yanda Jalila ke tafiya tafara dariya ciki ciki, suna hada ido da ita Jalila ta maka mata harara. Sameer ya zunguri Falak ahankali yace kede kincika sa ido. Zama sukayi suka gaida kowa, Jalila se kallon Zarah takeyi wadda kanta yake akasa tana kuka.

.

    Bayan kowa yayi shiru Kawun Alh, wanda shima yana cikin falon, yayi gyaran murya yafara magana...... to Alhmdllh Allah mungode maka da ka kawo mana karshen wannan iftila'i da muke cike, wanda bakowa bane yayi sanadiyar shigarmu cikinshi seke, Zarah, tabbas kincutar da mutane dayawa arayuwarki, ki godema Allah daya barki harzuwa yanzu da ranki, wanda yabaki damar neman gafarar wadanda kika cuta, sauran kuma da kika kashe, sede ince tsakaninki da Allanki ne, kuma ki kara godema tsohon mijinki,,,, saurin dago kai tayi jin abinda Kawu yafada, wai tsohon mijinta.


E tsohon mijinki, dan yanzu haka babu igiyoyin aurenshi akanki, duka ya sauke maki su, kuma duk da irin abinda kika yimashi besa yayi watsi dake ba, ya tsaya akanki ganin baki wulakanta ba, duk da ke burinki kenan inda Allah yabaki dama, kiga kin wulakanta shi, sede ahi azuciyarshi ba haka bane, asali ma, yahanaki fita kije ki gogu da sauran yan'uwanki mahaukata, kuyi yawo aduniya kuna bin bola, yara suna jifarku, wasu marasa imani kuma suna binku suna maku fyade, kuna haihuwa akan titi, duk wadan nan abubuwan babu wanda Abba yabari kikayi, asalima acikin unguwar nan, bakowa yasan halin dakike ciki ba. Sannan wadan da kike da burin ganin bayansu, sune suka zama gatanki, alokacin da kika rasa wadanda zasu zauna dake,  Falak, yarinyar da kika tsana, kinso ki lalata mata rayuwa, Allah yatsare abinshi, kin kashe mata Uwa, kaninta ma baki barshi ba, amma duk da haka ta tsaya domin ganin kinsamu lafiya,

.

Baba Mairo dattijuwa me kirki, wadda ahaife ta haifeki, bake bama, Abba kanshi ta haifeshi amma bata isa ki daraja taba, sbd kawai tana aiki a karkashinki, segashi yau tayi maki abinda Mahaifiyarkice kadai zata iya yi maka shi, tazauna dake acikin halin hauka, na tsawon kwanaki, tayi jinyar diyar cikinki, wadda ayanzu bata duniyar. Harma wata daban wadda baki sani ba, kawai ta dalilin yarinyar da kika tsana itama ta amfaneki, kinga kenan kinci darajar Falak, sirikarta gatanan azaune, sbd ke take zaune gidan nan, kuma ita tayi jinyar Jidda.


Saboda haka yanzu shawara tarage naki, dama ni naroki Abba akan yabarki kizauna agidanshi harki samu sauki sannan sekizabama kanki rayuwar data yimaki, mahaifinki ma nine na tsaidashi, sbd baki daukeshi da muhimmanci ba, bare kuma yan 'uwanki, wadan da tunda sukazo bikin Jalila sukace bazasu dubaki ba, sbd kema kin manta dasu, dan haka yarage naki ki gyara rayuwarki, duk wanda ya yarda zumunci to wata rana seyayi dana sani.


Shiru falon yayi inbanda kukan Zarah bakajin komai, sauran masu tausayi sede hawaye, Jalila, kam idanunta harsun kumbura, azuciyarta tana tirrr da irin halin Umminta, yanzu agaban kowa harda mijinta kalli yanda ake fada mata bakaken maganganu, jitake kamar tabar falon.


Malam yayi gyaran murya yace to Zarah, kinji de da kunnenki irin abubuwan da kika aikata, ace wai musulmi ne, da kanshi ya aikata wannan abun, sbd son zuciya da kuma kwadayin abun duniya, gashi nan ta sanadiyar abinda kikayi kalli irin abinda kika jama kanki, yanzu bakida saura daraja agurin kowa, sede idan har kin tuba kuma kin gyara halinki, abinda nakeso dake, idan har kinyarda zaki canza halinki, to dole sekin koma baya kin gyara rayuwarki daga farko, dan kinada karancin addini, kuma dole sekin gyara ibadarki, sannan zaki samu damar neman gafara agurin ubangijinki, sauran mutanen da kika cutar kuma gaki gasu, zaki iya neman gafararsu, saura kuma sede ince Allah ya gafarta maki,amma tabbas kina da kalubale agabanki, kuma duk wanda yayi niyar tuba, to dole seya bar duk wani abu najin dadin duniya sannan ze iya samun lokacin ibada. Daga karshe kuma ina maki ta,aziyar mutuwar diyarki, tare da fatan alkhairi na auren diyarki Jalila.

.

Kuka sosai Zarah takeyi, jitake dama Allah yadauki ranta, da irin wannan rana daya gwada mata, jan jiki tayi ta matsa kusa da Babanta, wanda shima kanshi yake kasa yana kuka, kafarshi takama tana kuka tana fadin Baba kaine mutum na farko daya kamata infara neman gafararka, tabbas na cuceka, na wulakantaka, ban baka darajarka ta Uba agareni ba, kai cona, daban zama 'ya tagari ba,nahada kai da makiyiyarka munzalunceka.  Dan girman Allah Baba kayi hrk kayafemun, nasan idan baka yafemun ba, raywata bata da amfani, wlh ko haka Allah yabarni naga rayuwa kayafemun ko naga haske arayuwata. Kamota yayi yana kuka yace, ya isa haka Zarah, nayafe maki, duniya da Lahira, idan kina da laifi nima inadashi danayi sakaci da addu,a har wata tasamu galaba akaina, tazo taruguje tarbiyar dana baki afarko, tabbas, yanzu kam naga falalar addu,ar iyaye akan 'ya'yansu. Allah yagafarta mana gaba daya. Kije kinemi gafarar mijinki, shine yafi can canta daya yafe maki.


Matsawa tayi kusa da Alh, wanda shima yake kuka kamar karamin yaro, zata kama kafarshi yayi saurin janyewa, tace nasan banida bakin dazan nemi gafararka, na cutar da kai, na wulakanta ka, naci amanarka, na ha'inceka, nakasa bama yaranmu tarbiya mekyau, amma dan Allah kada kadubi laifukan dana yi maka, ka kalli girman Allah da darajar yaranmu ka yafemun, kaima Allah ze saka maka da mafificin alkhairinsa, kayi hkr da duk abinda nayi maka.


Shiru Alh, yayi yana kuka, Jalila ta matsa kusa dashi tarike kafarshi tana kuka tace, Dady dan Allah kayi hkr ka yafema Umminmu, nasan ta cutar da kai amma idan baka yafe mata ba, zata shiga wata irin rayuwa, dan Allah Dady. Goge idonshi yayi yace shikenan Jalila nayafe mata, ko alahira wani yanacin arzikin wani, haihuwa me rana, kigodema yarki kinci darajarta, nayafe maki.

.

Komawa gurin Falak tayi tana kuka tama kasa magana, dan muryarta harta dashe, Falak ta tashi ta aje Ameerah, tadawo takama Zarah tana goge mata kwallan idonta, itama tana kuka tace haba Ummi, kintaba ganin inda uwa tadurkusama yarta? Kamar yanda bazaki durkusama Jalila ba, haka nima agurina na daukeki Uwa, kada ki wahalar da bakinki gurin neman gafarata, ni 'yarkice, na dade dayafe maki, kuma har cikin zuciyata nayafe maki, Allah ya yafe mana gaba daya, Zarah jitayi gaba daya kunyar Falak da sauran mutanen falon takama ta, kallon Baba Mairo tayi tace Baba Mairo dan Allah kiyafemun abinda nayi maki, tabbas ke Uwa tagari ce dayakamata ace narikeki amatsayin Uwa, amma sena wulakantaki narike wadda tayi silar shigata wannan rayuwar amatsayin Uwa, gashi ta dalilinki nasamu alkhairi inbadan keba, dayanzu nakarama kaina zunubi me yawa,amma se bakibi son zuciyarki ba, kika kareni daga fadawa halaka. Nagode da irin zaman da kikayi dani da yarana. Baba Mairo tace ai bakomai Hjya. Zarah tace zanso kidena kirana da wannan sunan, dan yanzu nazama diyarki, narasa gatana Uwa, inaso kimayemun wannan gurbin dan Allah.


Kwalla Baba Mairo tagoge tace bakomai Zarah dama can ni amatsayi diya na daukeki, Allah yayi maki albarka,kuma Allah yajikan jidda, kallon Umman Sameer tayi tace Umma duk da bansanki ba, amma kinmun alkhairi, nagode maki sosai, Allah yasaka maki da gidan Aljannah. Tace Kawu kaima nagode kayi sanadiyar samun lafiyata.


Sameer kaima bansan dawane baki zan nemi yafiyarka ba, amma dan Allah kayi hkr da duk abinda namaka, kuma kayafemun, nagode sosai da dawainiyar da kukayi mana kaida Saleem, Allah yabiya ku. Suka ce amin. Zarah tace Allah sarki Jidda Allah yaji kanki, banida rabon neman gafararki, nasan banzamo Uwa tagari agareku ba, amma ina rokon Allah ya yafe maki laifukanki, kema Jalila kiyafemun. Kuka tasaka, kowa seda yatausaya mata.

.

Malam yace to Alhmdllh naji dadi sosai da kuka zamo mutane masu yafiya ga junanku, kuma dama haka Allah yakeson bayinsa masu saurin yafiya akan laifin da,akayi masu, dan duk mutumin da,aka cuta, yana da ikon daukar mataki amma yayi hkr ya yafe tabbas wannan mutumi Allah zesaka mashi da mafificin alkhairinsa. Allah yakara yafemana laifukanmu, yashiryar damu da iyalanmu, Allah yasa mufi karfin zuciyarmu. Daga karshe Alh, inason inroki wata alfarma agareka, inaso kamar yanda su Baba Mairo zasu zauna agidanka, inaso itama Zarah kayi hkr kabarta tazauna agurinsu, tunda zatafi samun matemaka, akan idan takoma gidansu, tunda shima babanta ba aure gareshi ba, kaga idan Allah yakawo mata miji setayi aure hakan zetemaka mata tasamu saukin damuwar datake ranta.


Kawun Alh, yace tabbas Malam karigani, nima abinda ke raina kenan, kaima Alh, bazeyuwu kazauna haka ba, amma kome kenan, nan da kwana 2 zanzo akwai maganar dazamuyi. Zarah jitayi kamar ta kurma ihu, wai agabanta ake maganar mijinta zeyi aure, ita kuma gata ta nakasa, kilama bazata kara aure ba. Goge idonta tayi aranta tace kaicona. Jalila ma hakanan bataji dadin abinda Kawu yafada ba, taso ace ba saki 3 Dadynta yayi ma Umminta ba, da tasashi ya maidata.

.

Malam yace to ai semu rufe taro da addu,a ko? Anan yayi masu addu,a yayi masu sallam Alh yabashi kudi masu yawa, yace baze karba ba, Kawu yace a,a ai ba biyanka mukayi ba, kyauta ce yayi maka, anan ya amsa yayi masu godiya yatafi tare da Kawun Sameer. Alh, da Kawu da Mal. Garba suka fito suka nufi part din Alh, Kawu yace kaima Mal. Garba yakama kasamu kayi aure zama babu mata bakaramin matsala bane, sbd akwai lalurar ciwo kuma ga al,amuran rayuwa.


Murmushi yayi yace wlh Alh, ni tsoron ma matan nakeyi, dariya Kawu yayi yace kada kasamu damuwa, idan har kabani dama nizan zaba maka. Yace haba ai yanzu munzama daya, duk wacce kazaba mun nikuma na amince. Yace dama akwai wata diyar kanina da mijnta yarasu yabarta da yara 2 mace da namiji, yanzu haka tana gidana anan take zaune, idan har ka amince zaka aureta, amma kuma da yaranta zata zauna, to? Malam. Garba yace ai babu damuwa, yaro ai nakowa ne, wlh na amince, sede bansani ba ko ita. Kawu yace kamar yanda mukayi maganan nan da kai itama haka tacemun inzaba mata, nikuma gsky nayaba da kai, shiyasa kuma idan bazaka damuba, zanso kabani dama inmaka gyaran gidanka.

.

Alh, yace a,a kawu kabarni nizanyi wannan aiki, Kawu yace ai ni narigaka, dan haka kaima seka samu wani abun kayi mashi. Har kuka seda mal. Garba yayi, yace babu abinda zance maku se godiya. Alh, yace shikenan nikuma zanbude mashi babban shago wanda zerika kula dashi. Kawu yace yauwa, dan haka bawani daukar lokaci abun zeyi ba. Yace nagode sosai. Kawu yace kaima kashirya kilama tare za,ayi bikinka dashi. Alh, yayi dariya yace haba Kawu niyanzu ai nagama kallon wata mace ince inasonta, inama zan tsaya kallonsu. Kawu yace ato aini harna kallo maka. Dariya suka sa gaba daya.


Baba mairo se lallashin Zarah sukeyi, tace tashi muje kiyi wanka kici abinci, inaso kisaki ranki kada wata cuta tadameki, kidauka kamar ba,ayi komai ba, Jidda kuma addu,a yakamata kirika yimata. Haka suka kamata suka kaita bandaki dan tayi wanka.

.

Falak taja Jalila daki tana tayi mata tsiya, Jalila tace wlh ke muguwa ce, koma kimun sannu shine daga shigowata ina kallonki kinamun dariya, wai dan Allah ya akayi kika gane? Falak tace yo daga tafiyarki mana. Jalila tace nashiga 3 yanzo kowa yasan abinda yafaru dani, har Dady ko? Falak tana dariya tace ke kwantar da hankalinki ai babu wanda ya kula dake, kinsan hankalin kowa yana gurin Ummi. Jalila tace wash, harnaji dadi, Falak tace to Allah yasa nan da wata 9 musami yan biyu. Jalila ta kaimata duka tace wlh yan biyu su tsaya akanki, Falak tace toshikenan zamu gani ai. Baba Mairo tashigo tace to meza,a dafa ne agidan yau? Jalila tace a,a Baba kibari tunda ina gida indora, tace a,a Jalila daga ganinki bakijin dadi, kawai kibarshi kizauna kihuta. Dariya Falak tayi tace Baba kawai kidafa komai medadi, Jalila tajuya tana gungunai, Baba Mairo tace waini menace ne? Falak tace rabu da ita Baba, Jalila tadauko pillow tana dukanta dashi, baba mairo tayi waje tana dariya.


Bayan kwana 2 komai yafara dedeta, sede haryanzu Zarah takasa sakin jikinta agidan, duk da Baba Mairo tana kokarin ganin tana janta ajiki, gaba daya sunkwaso kayansu sun maido gidan, zamansu gwanin ban sha,awa Umman Sameer da Baba Mairo sune suke girkin gidan, Zarah kuwa ansama mata sanda hartafara amfani da ita, kuma kafarta tana kara samun sauki, sede aje ayi mata dressing, kuma jikinta yafara haske. Kullum tana cikin jan carbi tana istigifari, sallah akai akai takeyinta. Sameer yace ze kawo mata malamin daze rika kara mata karatu.


Bayan kwana 2, Kawun Alh, yazo, kai tsaye gurin Baba Mairo yawuce, waje suka fito, wata magana suka gamayi, sannan nga sunnufi bangaren Alh, Bayan sungama gaisawa Kawu yace dama nace maka zanzo bayan kwana 2 togashi nan nazo, kuma tare muke da Baba mairo dan ina ganin maganar zefi ayita tana nan.


Bawani abu bane akan maganar auren danayi maka ne, akwai wadda nagani kuma na yaba da hankalinta, bakowa bace se sirukarka, Zaro ido Alh, yayi yace bangane ba. Yace E sirukarka nace, wato mahaifiyar Sameer mijin Falak, tabbas tana da halin kirki inaso kayi hkr ka karbi zabin damuka yimaka nasan bazakayi dana sanin abun ba.


Shiru yayi Baba Mairo tace gsky Alh, nima ina maka sha,awar auren Halima, nina zauna da ita kuma kasan bazan zaba maka abinda ze cutar da kai ba. Amma me kace? Alh, ya sosa keya yana murmushi. Kawu yace shikenan nagane, kuma naji dadi daka amince, insha Allahu kasamu wadda zata share maka hawayenka, Allah yabada zaman lafiya, kuma insha Allahu nan da asabar mezuwa za,a hada dana mal. Garba, kaga tsohon sirukinka da kai zaku Angwance arana daya. Dariya Alh, yayi yace kai kawu. Godiya yayi masu.

.

Haka Baba mairo tasamu Umman Sameer da maganar, amma da kyar ta amince, dan cewa tayi tana jin kunyar Zarah, Baba Mairo tace bakomai zanyi mata bayani kuma nasan zata amince. Zarah wadda take jin duk abinda suke fada dan tazo zata shiga falonsu taji suna magana. Kuka kawai takeyi tana kara tsanar Asabe da kuma irin halinta, share idonta tayi, tayi sallama tashiga, bayan tazauna tace Baba Mairo kuyi hkr naji duk abinda kukace, nazo shigowa naji kuna magana amma wlh ba labe nayi maku ba. Umma kada kidamu babu komai, koma menene nina jama kaina, kuma zanfi son ace kece kika auri Alh, akan yaje waje yasamo wata, Allah yabaku zaman lafiya. Fita tayi tana kuka. Baba mairo tace tokinji abinda tace, Halima tace shikenan, Allah yazaba mana abinda yafi zama alkhairi.

     Baba Mairo tace amin, dan haka kinga saura kwana 5 daurin auren kuma da an daura zaki tare, dan haka dole ingyaraki dan bawai tsufa kikayi ba, kawai rashin gyarane, murmushi tayi ta tashi tafita. Kowa yaji dadin wannan hadi da akayi, duk da Jalila bataji dadi ba, amma kuma taji dadin da akace Umma Alh, ze aura dan tasan halinta.


Haka akayita shirye shirye Umman Sameer cikin kwana 5 tayi kyau sosai tafito mace me kyau, dan komai yana son gyara. Sameer se tsokanarta yakeyi yana cewa dama Ummanshi tana da kyau amma batason yin kwalliya, itade sede tayi ta murmushi. Sameer yazo gurin baba Mairo shida saleem yace gsky Baba ana daura auren su Umma nima zandau matata mukoma gida, dan gsky abun da kunya. Saleem yace hakane Baba dan Allah kibarsu su koma. Tace to ai shikenan, dama ita nake tausaya mawa, tunda kace ku koma se kutafi amma wlh karika dawowa dawuri, yace angama Baba Mairota. Dariya tayi, sukayi mata godiya.

.

Ayau asabar aka daura auren Alh, Abba Bala da Halima kan sadaki dubu 30, se Mal. Garba da Samiyya suma sadaki dubu 30, kuma aranar aka kai kowa gidanta, Kawu yayi kokari na gyran gidan Mal. Garba, gashi Alh, yabude mashi babban provision store, haka aka kai amarya Samiyya sede ance yaranta sedaga baya za,a kawosu.


Halima ma Alh, yasa mata kaya adakin Zarah, ita kuma aka maida mata kayanta can part dinsu, akace idan su Falak suntafi seta koma dakin falak, aranar zarah ko abinci bata ciba, tana dakinta takasa fitowa, kuka kawai takeyi, seda tabama kowa tausayi, amma kuma ita tajama kanta.


Bayan kwana 2 da biki Sameer yadauki matarshi suka koma gidansu, wanda yakara shan gyara kamar wata sabuwar amarya, tayi mamaki sosai ganin irin gyran da yayima gidan, haka suka bude sabuwar rayuwa.

.

Haka rayuwa tacigaba da tafiya cike da jindadi Alh, yanajin dadin zama da Halima, shikanshi yasan yanzu yana cikin kwanciyar hankali, har mantawa yakeyi dawata Zarah, dan koyaje gaida baba Mairo bata barin su hadu, shima baya nemanta, yana bama Baba Mairo girma sosai kamar ita ta haifeshi, kuma yahanata yimasu girki, yacika masu store da komai na abinci yace suyi iyakar nasu, bayaso ta wahala. Jikin Zarah kam ya warke, har ancire daurin kafar tazama dungulmi, sede haryanzu bata maida jikinta ba, dan kullum cikin kuka take, da tunani, sede kawai bakin datayi ne yaragu amma duk wanda yasanta ada yanzu baze iya gane taba. Malamin da Sameer yasama mata yana zuwa yana mata kari kullum, tamaida hankali sosai gurin koyon karatu.


Bayan shekara daya Jalila tahaifi yaronta me kyau aka samashi sunan Mahaifin Saleem, suna kiranshi da WALEED.Taro yayi kyau, yaran Falak sunyi wayau sosai, kamar sunfi shekara daya, kuma alokacin ne tafara laulayi, bayan suna sukaje asibiti, likita yace bakomai zata iya cigaba dabasu nono, amma tafara basu abinci, idan cikin yayi girma seta ciresu.


Halima ma tasamu ciki wanda haryayi girma, Alh, bakaramin farin ciki yayi ba, ganin zekara samun haihuwa. Zarah ma jiki yayi kyau, tafara dangana, har tafara kiba, kullum Baba mairo cikin kulawa da ita takeyi.

.

Ayau Halima ta tashi da nakuda sede har Alh, yafita bata fada mashi ba, sede takira Baba mairo, tana zuwa ta temaka mata, cikin lokaci kankani tahaifi danta namiji, Baba mairo tayi mashi wanka ta gyara gurin itama tayi wanka sannan aka kira Alh, akace yazo an haihu, lokacin dayazo yaga abinda aka haifar mashi seda yayi sujada yagodema Allah, har kwallan farin ciki seda yayi. Zarah ma tayi farin ciki, kuma tazo tayi mata barka, dan bata shigowa gidan idan Alh, yana nan.


Bayan kwana 2 da haihuwarta Samiyya matar Mal. Garba ma ta haifi mace, zarah bakaramin jin dadi tayi ba, haka tashirya ita dasu Jalila da Falak sukaje barka, Aranar sunan halima bakaramin kashe kudi Alh, yayi ba, seda ya yanka manyan raguna Biyar, taro yayi taro, yaro yaci sunan Alh, Abba, dan yace sunanshi zesama yaron za,a kirashi da KARAMEE. Bayan kwana 2 akayi sunan Samiyya, itama tasamu alkhairi sosai.

.

Cikin Falak yana wata 6 ta yaye yan biyu, aka kaisu gurin Baba mairo, haka suka cigaba darenon cikin Falak, harya kai lokacin haihuwarshi, da dare suka nufi asibiti, suna zuwa ta haifi yaronta me cike da lafiya, nan Sameer yarika kiran waya yana fadama mutane, bayan ta huta aka sallameta, suka dawo gida.


Ranar suna yaro yaci sunan mahaifin Sameer Abdullahi ana kiranshi da SUDAIS, Falak ansha kyau sosai, dan takara zama babbar mace, haka taro yatashi cike da farin ciki.


     Bayan shekara 2 an maido su Ameer da Ameerah gida, har ansasu makaranta, kowa yagansu yana sha,awarsu, domin suna matukar kama, gasu kyawawa, Jalila takara haihuwa tasamu mace, aka samata Zarah, suna kiranta da AMAL, shima   Waleed an saka shi makaranta, hada Karami ma Alhn yasashi makaranta, dan itama Halima wani cikin gareta.

.

Haka rayuwar Zarah tacigaba da tafiya agidan Alh, kullum jinta takeyi kamar tana kurkutu, idan tayi tunanin komawa gidan ubanta setaga gara tayi zamanta, dan batada daki agidan, gashi de tana cin abinci mekyau, amma kullum kamar ana dibarta, Baba Mairo harta gaji da lalllashi tasa mata ido, shiyasa yanzu idan zatayi kuka seta shige daki sannan, amma duk da haka da baba Mairo ta ganta seta gane tayi kuka sede kawai ta kyaleta. Ga Son Alh, dayake hanata bacci, batason tana sonshi dayawa hakaba seda tarasashi, kuma taga yayi aure, wani lokacin har labewa takeyi idan yashigo tayi ta kallonshi. Zama tayi bisa gado tace Oni zarah, yanzu wai nice haka, lallai rayuwa ta koyamun hankali, Danasani nayi hkr da Hajjo munyi zaman mu Da yanzu nasan nazama wata babbar Hajiya.


Danasani banyima Alh, asiri ba, dayanzu ina nan da kafata lafiya lau, Danasani ban dauki shawarar Asabe ba, dayanzu bnshiga wannan kangin ba. Ya Allah kaji tausayina ka kawomun karshen wannan zaman danakeyi.

   Allah kashirya duk masu irin halina ya Allah. Kwanciya tayi tana kuka me tsuma rai.


     Nikam dariya nayi nace Zarah ada kenan, dama ai Danasani keya ce.


Wata bakar jaka Falak tadauko taciro wani abun hannu, tadawo

kusa da sameer tazauna, yana kallonta, tace Ameerah zonan, hannunta takama tasaka mata abun hannun, Ameerah tace lah, Momy ke kika siyomun? Kwallan idonta tagoge tace a,a Grandmother dinki ce tace inbaki, Ameerah tace toyaushe zan ganta? Sameer yajawota yace kin kusa ganinta kinji. Ameer yace Dady nito ina nawa? Tashi yayi yadauko wani karamin agogo yace kaima ga naka, yace toni wayace abani? Murmushi yayi yace kaima GrandFather dinka yace abaka, tashi sukayi suna tsalle, sukace Thank you Momy and Dady, waje suka nufa suna murna.

.

Jawo Falak yayi yace haba my dear kin manta kince bazaki kara kuka ba, tace dole inyi kuka my Luv.


Kawai natuna wani abune, wai yau nida ake kira AGOLAH, nice nake zaune da yarana har 3, suke kirana momy, agaskiya ina tausaya ma duk wata AGOLAH datake AGOLANCI awani gida, Allah yajikanku Umma da Abba, badan narasa kuba da babu wanda ze kirani da AGOLAH, har yau idan natuna sunan nan yanamun ciwo.


Sameer yace banaso kina rike abu aranki, kinmanta kince kinyafe masu? To kibar tuna abun, komade menene yanzu gashi kin daukaka, ayanzu kina sama da ita kuma ita tana kasa dake, kuma kinmata nisa, sosai. Yanzu albishirinki. Tace goro, yace hajjin bana tare za,ayi damu. Tsalle tayi ta rungumeshi tana murna tace wow amma gsky kayimun babban albishir, bansan ma dame zan gode maka ba. Dariya yayi yace ni ai nasan da abinda zaki godemun, kuma Falaka, kinfi haka agurina, kece farin cikina, kin bani kyautar yara har 3 kina kula dani yanda yakamata, nine zance bansan dame zan gode maki ba. Amma yanzu tashi mushiga ciki kibani goron albishir. Tashi tayi tana dariya tashige daki.


ALHAMDULILLAH

.

Ina mika godiyata ga Allah daya bani ikon kammala wannan littafi nawa mesuna AGOLAH. 

   Kuma ina mika sakon gaisuwa meyawa ga dukkanin masoyana nagode da irin kulawarku gareni. Allah yabar zumunci, abinda nafada da kuskure sekuyi hkr dan dan Adam ajizine.


Nasadaukar da wannan littafi ga mahaifina, ALLAH YAJI KANSHI DA RAHAMA AMIN, ALLAH YAJIKAN DUKKANIN MUSULMAI BAKI DAYA, MUKUMA IDAN TAMU TAZO ALLAH YABAMU GUZURIN TADDASU.


ALLAH YAKAREMU DAKA SHARRIN ZUCIYA YASA MUFI KARFINTA AMIN.


..

CALL or SMS

07066508080


.

Whatsapp

07066656752


Read More

Share this

WhatsApp

AGOLA Page 41-50 (The end)

 November 27, 2017     AGOLA 1-END     No comments   

AGOLA Page 41-50 (the end)
.
Suna zuwa aka nufi labour room da ita, shi kuma Saleem yashiga da Jalila su Bilkisu suna binshi abaya, itama daki aka nufa da ita domin adubata. Sameer gurin su Baba Mairo yanufa, koda yaje ya iske har ansaka gawar Jidda ambulance, za,a kaita gida, Baba Mairo tace lafiya Sameer naganka arude? Alh wanda fuskar shi take jike da hawaye, ya goge idon shi yace lafiya de Sameer? Yace bakomai dama Falak ce zata haihu tana dakin haihuwa.

Alh, yace to ina Jalilan kotana gidanta? Kai yasosa yace a,a nabarta ita da Saleem inaji befada mata ba, yauwa kada kufada mata kawai yadauketa yakaita gida. Baba Mairo kikoma gurin Falak din mucemu wuce da gawar, tunda Halima tana gurin Zarah.
.
Goge kwallan idon ta tayi tace a,a Alh muje inaso inyima Jidda wanka da kaina, kai Sameer kasamu Halima tunda dazu akayi ma Zarah allurar bacci kace taje gurin Falak din, nizanje can gidan. Yace to nima yanzu zanzo kafin agama shiryata tunda ance yau za,a kaita tunda dare beyi ba.

Haka suka nufi gida da ita kowa yana cikin damuwa. Babu bata lokaci Falak ta haifi kyawawan yaranta guda biyu, Mace da namiji, cikin koshin lafiya, bayan angama shiryasu aka fada masu Sameer, Bakaramin murna Sameer yayi ba, dan betaba tunanin samun yan biyu ba. Wayarshi ce tayi kara, yana dubawa yaga Saleem.

Dauka yayi yace Saleem ya Jalilan ta farfado? Yace E amma haryanzu kamar bata gama dawowa hayyacinta ba, amma likitan yace zeyi mata allurar baccin dazata kaita har gobe dan tasamu ta huta. Sameer yace toshikenan yanzu itama Falak ta haihu, ansami twins, fito muhadu semuwuce can gidan.

Saleem yayi farin cikin ganin jariran masu kyau dasu, bayan ankai Falak dakin hutu, itama haryanzu kuka takeyi, suka dubata da jiki, suka ce zasuje sukai Jidda, Falak tace Allah sarki Yaya Jidda Allah yajikanta, naso ace nakara ganinta. Sameer yace se hkr addu,a zamu cigaba dayi mata, bara muje semun dawo, nasan se gobe za,a sallameki gara kizauna ana ku huta, tace tosekun dawo ina Jalilafa? Anan suka fada mata abinda yafaru, tace to Allah yabata lafiya, haka suka fita suka bar Umman Sameer agurinta.
.
Gida mata se kuka sukeyi, Baba Mairo da Matar Kawan Alh, su sukayima Jidda wanka, suka shiryata, babu bata lokaci aka fiddota, akayi mata sallah,aka nufi gidanta na gaskiya da ita.
     Koda sukaje Alh, kasa sakata kabari yayi, sbd kukan dayakeyi, sede su Kawu ne da Baba na Zariya da Kawun Sameer suka sakata, Alh, yabama kowa tausayi agurin, haka aka gama sakata akabarinta aka rufeta, suka dawo.

Aranar haka kowa yazauna masu bacci kadan ne, dan Alh, tunda yashiga daki, yayi wanka yayi alwala yayita nafila da karatun Qur'ani har seda aka kira sallah sannan yanufi masallaci. Bayan sunadawo ne, yake tambayar Sameer yabega Jalila ba, anan yake fada mashi halin datake ciki, da kuma abinda Falak tasamu, yayi murna sosai, yace tobai bazama zamuyi ba, muwuce muga jikin nasu.

Lokacin dasukaje asibitin har Falak tayi wanka Anyima jariran wanka suma, sunyi gwanin kyau, sede daka kalli Falak kasan tana cikin damuwa. Baba Miaro tana kusa da ita dan agurinta ta kwana, ita kuma Umman Sameer ta kwana agurin Jalila ita dasu Bilkisu.

Jalila kuwa tafarka, tunda tayi sallah itama take kuka, se lallashinta sukeyi, haka Alh, yasameta, yana ganinta shima yaji wani sabon kukan yazo mashi, da kyar yasamu yadedeta kanshi yashiga, shima lallashinta yashiga yi, sannan suka nufi gurin Falak, acan ma du lallashin ne, daga can yawuce gurin Zarah.

Zaune suka sameta duk ta kwance bandage din da aka rufe mata ciwon tana ta wasa dashi, cikin sauri Saleem yaje yajira nurse, ana suka riketa aka sake mata wani sabon dressing din. Tagumi Alh, yayi, yana kallonta, yarasa neke mashi dadi aranshi, addu,a kawai yakeyi itace take kara sanyaya mashi ranshi. Fita yayi yace bara yatafi tunda gari yayi haske sbd masu zuwa gaisuwa.

Karfe 10 aka sallami Falak da Jalila, Baba Mairo tace awuce da Falak gidansu Jalila, idan kunje se a bude part dinsu nada tazauna aciki, sbd asamu saukin zirga zirgar. Sameer yace hakan ma yayi, tace nima anjima zanzo sbd nasan babu wanda ze zauna agurinta, idan yaso se Halima tazauna agurin Zarah, anjima se indawo.
.
Sunzo tafiya, su Bilkisu sukace bara suwuce gida anjima zasu dawo, godiya sukayi masu, Saleem yabasu kudi suka tafi, sun fito kenan suka hadu da Al,amin, Jalila yagane, hakan yasa ya tsaya suka gaisa, kallonta yayi tana kuka yace ina fatan kunshedani? Al,amin ne, yame jikin? Falak tashare idont tace Allah yayi mata rasuwa jiya da dare. Kiyayi kamar ansara mashi icce akanshi, wasu irin zafafan hawaye ne suka zubo mashi. Yace shikenan Jidda ciwo ya warke, darabon mugana ashe, sallama yayi masu yace zeje yadauko Ameerah suzo tare.

An gyara part din su Falak na da dama kuma babu abinda aka cire aciki, tunda Hajjo tarasu da aka kulle shi ba,a kara amfani dashi ba, share shi akayi aka goge, sannan Falak da Jalila suka shiga ciki, amma Falak cewa tayi adakinta na da zata zauna bazata shiga dakin Ummanta ba, Sameer yaje yadauko mata duk kayan dazasuyi amfani dasu yakawo, Baba mairo ta dora ruwa takara yima yaran wanka, tasa Falak itama takara yi.

Saleem ne zaune afalo shida Jalila, haka yayita lallashinta da kyar yasamu taci abinci shima kadan taci, yace Jalila inaso ki kwantar da hankalinki yanzu babu abinda Yaya Jidda take bukata daga gurinmu se addu,a. Kirika yawan ambaton Allah da addu,oi zaki samu sauki aranki, nasan dole kiyi kuka amma hakuri zakiyi. Allah yaji kanta, yabama Ummi lafiya, tashi yayi yace zeje waje. Itama shiga gurin Falak tayi, dan batason zuwa bangarensu.
.
Haka aka cigaba dazaman gaisuwa, Al,amin da Ameerah sunzo gaisuwa, itama tasha kuka, Al,amin yakira Jalila yace yadauki nauyin ginama Jidda rijiya amakarantar almajirai kamar yanda taroka, kuma zeginata ne da sunan ta, amatsayin sadakar daze bata. Sosai Jalila tayi mashi godiya, seda suka jera kwana 7 suna zuwa gaisuwa, ranar da akayi sadakar 7 aranar akayi sunan Falak, bawani taro akayi ba, bayan sadakar 7 akayi radin suna.

Namijin aka samashi sunan Alh, wato Abba, ana kiranshi da Ameer, dan Falak tace tana son sunan, Macen kuma Aka samata sunan Hajjo, Zainab, ana kiranta da Ameerah. Falak tayi mamaki sosai da Sameer besa sunan babanshi ba, har seda tayi mashi magana, murmushi yayi yace haba Dear, Alh, shine mutumin da yayi sanadiyar haduwata dake, kuma ya cancanci abinda yafi haka agurina dake baki daya. Umma kuma dana sa sunanta, kinga tarasu kuma saka sunanta zesa murika tunawa da ita, jawota yayi yace kada kidamu nasan nan da shekara 2 zaki kara sama mana wasu babies din. Murmushi tayi tace nagode.

Ayau ne, Jalila zata koma gidanta, dan Alh, yace sutafi gida zatafi samun sakewa idan tana kusa da mijinta, sauran mutane ma, duk sun watse se yan uwa kawai suka rage, yan Zariya ma yau zasu tafi, Alh, yasa aka kira kowa yace yana son magana dasu, anan falonshi suka taru, hada Kawunshi, da Kawun Sameer, da Mal. Garba dasauran mutanen.
.
Bayan anbude taro da addu,a, aka kara yima Jidda addu,a sannn Alh, yafara magana, hakuri yakara bama kowa, sannan yace Jalila,Falak, ayau nakeson kowa takoma gidanta, wanda yarasu yariga da yarasu, dan haka addu,a kawai zamu cigaba dayi mata, banaso insamu labarin acan kun kasa sakin jikinku, kowa hkr yakeyi arayuwa, kuma dama dan Adam baya zama haka, har se Allah ya Jarabceshi, dan haka murika daukar kowace kaddara tazo mana da hannu 2, Allah yayi maku Albarka.

Kuma itama Zarah munyi magana da Malam, yace gobe Malaminshi zezo yafara yimata rukiya, dan haka nayima Dr, magana zamu maidota gida yau, idan yaso se arika zuwa gida ana mata dressing, tunda yanzu yakoma bayan kwana 2. Kallon Kawaunshi yayi yace Kawu ko akwai abinda zakace?.

Gyara zama yayi yace hakane, duk abinda kafada yayi dede, sede abu 1 nakeso inkara, Baba Mairo mungode kwarai da irin abunda ku kai mana, daga ke har Halima, tabbas kunzama yan uwa, sede ina rokonki wata alfarma, daga ke har Halima, duk da bata nan, amma ga malam nan, muna neman alfarmar daka barsu sudawo gidan nan dazama, kaga akwai marar lfy, kuma yanzu Zarah ba matsayi matar Abba take ba, asali ma, babu sauran igiyar aure atsakaninsu, idan har kayarda mun rokon alfarmar dasu dawo nan dazama, hakan zeyima Abba sauki dan baze yuwu ace mubama shi mal. Garba ita yatafi da ita ba, duk da tayi mana laifi amma ba,a kallon abinda yawuce, idan ka kalli alherin da mutum yayi maka zaka iya temaka mashi dashi.

Kaima Abba dole kayi hkr da duk abinda Zarah tayi maka, tabbas tacutar da kai da kowa naka amma, ka kalli darajar yaranku kayi hkr, inaso tacigaba dazama agidan nan har Allah yabata lafiya, daga nan kuma seta zaba ma kanta abinda taga zefi mata.
   Amma inaso inji daga bakinka ka amince zata cigaba dazama agidanka harta samu lafiya?.
      
       Se kunjini a next page dina wadda insha Allah shine last page. Nagode da kaunarku gareni.

.

Shiru Alh, yayi nawani lokaci, sannan yace shikenan Kawu duk abinda kace yayi dede, Allah yabata lfy. Kuma nagode da abinda kuka yi mani, Allah yasaka da alkhairi. Kawu yace Alhmdll, anjima malamin ze iso, dan haka se kuje kudauko ta. Haka suka tashi kowa yafara shirin tafiya.

Bayan andauko Zarah daga asibiti duk wanda yaganta seya tausaya mata, takoma kamar skeleton ne aka sama fata, tayi baki, ga kafarta da aka yanke tundaga cinyarta har kasan kafar sun shanye tazama siririya, ta yanda bazata kara amfanuwa ba, sede ciwon dake jiki yayi sauki, sbd Kawu yabada ruwan addu,a ana shafa mata akan ciwon, hakan yasa yadena fitar da ruwan dayakeyi, kuma dama aljanun jikinta ne suke sakashi zuba.

Jalila da tunda ta kalli Zarah take kuka, a part dinsu Falak Alh, yace akaita, awani daki dayake farkon shiga daga gefen falon, anan aka saka mata katifa, dayake akwai bandaki aciki, sede dakin bawani girma gareshi ba, bayan su Baba Mairo sunyi mata wanka, suka gyarata aka daureta tana kwanciya tayi bacci.

Saleem ne yazo daukar Jalila, tana kuka haka suka tafi su Baba Mairo se hkr suke bata, Falak ma seda tayi mata kuka, Sameer yace kema shiryawa zakiyi anjima zamu tafi, Baba Mairo tace gsky bazaku tafi ba, dama inaso inga Alh, muyi magana, dama ace yaro daya gareta se kutafi, amma yara har biyu, sannan kai kuma aikinku idan kafita wani lokacin har dare kake kawai, yazatayi da yaran? Kuma kaga muduka muna nan bare ma ace ni inje inzauna mata. Sameer yayi murmushi yace haba Baba yanzu dan Allah so kuke inzama gauron karfi da yaji? Inde haka ne, nima sede indawo nan. Baba Mairo tace nidama ai bance zan hanaka ganin matarka ba, sekaje ka kullo gidan kaima kadawo nan idan sukayi ko wata daya ne, sunyi kwari se ku koma gidanku. Yace shikenan nagode, tace yauwa zanje insamu Alh.

Da misalin karfe , Kawun Sameer suka iso da Malamin dazeyima Zarah karatu, Alokacin shima Sameer ya iso gidan da akwatinshi, dan Alh, yace shima yadawo, a dakin Falak yasauka, su kuma su Baba Mairo suna dakin Hajjo, Alh, shi kadai a part dinsu.

Afalo akayimata shinfida bayan sunyi mata alwala, malamin yazo yafara yi mata karatu, yadade yana karatu amma sunkiyin magana, sbd manyan aljanune, kuma bakake, yasha wahala sosai, kafin suka fara magana.

Wayyo Malam, ya isa zamuyi magana wlh, zufar goshin shi yagoge yace inajinku..... nide sunana Zurkum, kuma nine shugaban bakaken aljanu, wannan matar bata da kirki, sunyi da megidanmu akan duk lokacin da mijinta yagane halin datake ciki, akwai abinda ze sameta, amma haka ta amince, mu kuma dama mune yasa muke mata aiki, kuma dama duk wanda ya kasance yana maka aiki duk ranar daka dena biya mashi bukata, to kanka ze dawo, hakan yasa tundaga ranar da asirinta yatonu muka shiga jikinta.
.
Mune nan muka fado mata da durowa akafarta, kuma muka shanye jinin jikin kafar da bargon kafar, hakan yasa bazata kara amfani da kafar taba, tabbas wannan mata tayi sa,a tasamu masu yimata addu,a amma munso semun bi duk wani jini dayake jikinta munshanyeshi duka sannan daga karshe mukasheta, amma karfin addu,ar da akeyi mata yasa muka kasa aikata abinda mukayi niya. Amma kusani wannan mata bazata kara ganin haske arywarta ba, sbd tasamu mun cuci mutane, aciki harda karamin yaro wanda besan komai ba.

Dan haka kada ka konamu zamu tafi amma duk lokacin data kara shiga gonarmu tabbas takira ajalinta. Malam yace kuyi mani alkawarin bazaku kara shiga jikinta ba, idan kun fita. E munyi alkawari, amma itama ta gyara rayuwarta, takuma koma ga Allah wanda take bautamawa, hakanne ze kareta daga shrrinmu. To nagode.

Wata irin kara Zarah tasaki tare da atishawa, har so 3 sannan takoma ta kwanta, bacci yadauketa. Malam yace Alhmdllh, insha Allahu data farka zata dawo hankalinta, sede ina tunanin zata iya kaiwa gobe, dan haka zantafi gobe da safe zandawo. Ga wannan asamu wani ya zauna kusa da ita, aduk lokacin data farka abata wannan ruwan addu,ar tasha. Allah yakara sauki, kome kenan sauran bayanin idan nazo gobe zakuji.

Godiya sosai, sukayi mashi, yatashi yatafi. Falak, tana gefe se kuka takeyi, Baba Mairo tace banga amfanin asarar hawayen da kikeyi ba Falak, ace kuka yaki karewa, haba dan Allah, so kike kijama kanki wata cutar. Umman Sameer tace gsky Falak ya isa haka, kin sande kuka baya maganin komai, nasan akwai abubuwa da yawa dakike tunawa, amma kiyi hkr kisama kanki dangana, kinga kinrasa mutane dayawa arayuwarki, kuma duk da haka numfashinki bedena tafiya ba, dan haka kimanta da duk abinda yafaru dake arayuwa, Allah yana tare dake.
.
Idan kika kalli baiwar da Allah yayi maki ta yara 2 ya isa ki godema Allah, ada kinkasance ke daya, yabaki miji nagari, sannan yazo ya azurtaki da yara, Allah kadai yasan iyakar abinda zaki haifa, kinga wannan ma wata rahama ce daga Allah. Falak tagoge idonta tace nagode, da irin kulawarku gareni, kuma insha Allah, nadena saka damuwa araina. Baba Mairo tace yauwa kokefa, tashi ki kaima mijinki abinci kije daki kidauko yan biyu ki maidasu dakinku.

Bangaren Amarya da Ango kuwa, da kyar Saleem ya lallashi Jalila, taci abinci tayi wanka, yasa sukayi sallah, yajata zuwa gado yacigaba da lallashinta yana kara kwantar mata da hankli, taji dadin irin kalaman dayake fada mata sosai, cikin lokaci kankani taji zuciyarta tayi haske, duk wata damuwa ta gushe, daga lallashi shima ango ya canza tasha, naja masu kofa nace seda safenku.

Washe gari da safe har 8 tayi amma Zarah bata farka ba, mutanen gidan harsun gama karyawa, sunyi wanka, suna jiran tashinta, Baba na Zariya kuwa har yagama shiryawa dan yace shima yau zetafi, jiran tashinta kawai yakeyi da kuma jawabin da malam yace zeyi, se wajen 8:30 sannan ta farka cike da firgici, Baba Mairo tayi saurin riketa tana tofa mata addu,a Umman Sameer tamiko maganin da malam yabasu aka bata, kallonsu kawai takeyi Babanta yace kintsaya kina kalon mutane bazaki bude baki kisha maganin ba? Baki ta daga tasha maganin, sannan tamaida kallonta zuwa cikin Falon, akan Alh, tasauke idonta, suna hada ido yayi saurin dauke kanshi tare da kara daure fuska. Juyawa tayi tana kallon Baba Mairo da Falak, wacce take rike da Ameerah, dan Ameer yana bacci.

Sauke kanta kasa tayi dasauri takara kallon Alh, idanunta suka ciko da hawaye ganin kafarta datayi anyanke, kuma ta koma siririya. Haka falon yayi shiru kowa yana kallonta. Sallamar su Kawu da Malam sukaji, anan Alh, yafita domin ya shigo dasu. Bayan sun shigo aka gaggaisa, suka samu guri kowa yazauna, Sallamar Saleem da Jalila sukaji, dan Alh, yayi ma Saleem waya akan suzo. Falak da tunda taga yanda Jalila ke tafiya tafara dariya ciki ciki, suna hada ido da ita Jalila ta maka mata harara. Sameer ya zunguri Falak ahankali yace kede kincika sa ido. Zama sukayi suka gaida kowa, Jalila se kallon Zarah takeyi wadda kanta yake akasa tana kuka.
.
    Bayan kowa yayi shiru Kawun Alh, wanda shima yana cikin falon, yayi gyaran murya yafara magana...... to Alhmdllh Allah mungode maka da ka kawo mana karshen wannan iftila'i da muke cike, wanda bakowa bane yayi sanadiyar shigarmu cikinshi seke, Zarah, tabbas kincutar da mutane dayawa arayuwarki, ki godema Allah daya barki harzuwa yanzu da ranki, wanda yabaki damar neman gafarar wadanda kika cuta, sauran kuma da kika kashe, sede ince tsakaninki da Allanki ne, kuma ki kara godema tsohon mijinki,,,, saurin dago kai tayi jin abinda Kawu yafada, wai tsohon mijinta.

E tsohon mijinki, dan yanzu haka babu igiyoyin aurenshi akanki, duka ya sauke maki su, kuma duk da irin abinda kika yimashi besa yayi watsi dake ba, ya tsaya akanki ganin baki wulakanta ba, duk da ke burinki kenan inda Allah yabaki dama, kiga kin wulakanta shi, sede ahi azuciyarshi ba haka bane, asali ma, yahanaki fita kije ki gogu da sauran yan'uwanki mahaukata, kuyi yawo aduniya kuna bin bola, yara suna jifarku, wasu marasa imani kuma suna binku suna maku fyade, kuna haihuwa akan titi, duk wadan nan abubuwan babu wanda Abba yabari kikayi, asalima acikin unguwar nan, bakowa yasan halin dakike ciki ba. Sannan wadan da kike da burin ganin bayansu, sune suka zama gatanki, alokacin da kika rasa wadanda zasu zauna dake,  Falak, yarinyar da kika tsana, kinso ki lalata mata rayuwa, Allah yatsare abinshi, kin kashe mata Uwa, kaninta ma baki barshi ba, amma duk da haka ta tsaya domin ganin kinsamu lafiya,
.
Baba Mairo dattijuwa me kirki, wadda ahaife ta haifeki, bake bama, Abba kanshi ta haifeshi amma bata isa ki daraja taba, sbd kawai tana aiki a karkashinki, segashi yau tayi maki abinda Mahaifiyarkice kadai zata iya yi maka shi, tazauna dake acikin halin hauka, na tsawon kwanaki, tayi jinyar diyar cikinki, wadda ayanzu bata duniyar. Harma wata daban wadda baki sani ba, kawai ta dalilin yarinyar da kika tsana itama ta amfaneki, kinga kenan kinci darajar Falak, sirikarta gatanan azaune, sbd ke take zaune gidan nan, kuma ita tayi jinyar Jidda.

Saboda haka yanzu shawara tarage naki, dama ni naroki Abba akan yabarki kizauna agidanshi harki samu sauki sannan sekizabama kanki rayuwar data yimaki, mahaifinki ma nine na tsaidashi, sbd baki daukeshi da muhimmanci ba, bare kuma yan 'uwanki, wadan da tunda sukazo bikin Jalila sukace bazasu dubaki ba, sbd kema kin manta dasu, dan haka yarage naki ki gyara rayuwarki, duk wanda ya yarda zumunci to wata rana seyayi dana sani.

Shiru falon yayi inbanda kukan Zarah bakajin komai, sauran masu tausayi sede hawaye, Jalila, kam idanunta harsun kumbura, azuciyarta tana tirrr da irin halin Umminta, yanzu agaban kowa harda mijinta kalli yanda ake fada mata bakaken maganganu, jitake kamar tabar falon.

Malam yayi gyaran murya yace to Zarah, kinji de da kunnenki irin abubuwan da kika aikata, ace wai musulmi ne, da kanshi ya aikata wannan abun, sbd son zuciya da kuma kwadayin abun duniya, gashi nan ta sanadiyar abinda kikayi kalli irin abinda kika jama kanki, yanzu bakida saura daraja agurin kowa, sede idan har kin tuba kuma kin gyara halinki, abinda nakeso dake, idan har kinyarda zaki canza halinki, to dole sekin koma baya kin gyara rayuwarki daga farko, dan kinada karancin addini, kuma dole sekin gyara ibadarki, sannan zaki samu damar neman gafara agurin ubangijinki, sauran mutanen da kika cutar kuma gaki gasu, zaki iya neman gafararsu, saura kuma sede ince Allah ya gafarta maki,amma tabbas kina da kalubale agabanki, kuma duk wanda yayi niyar tuba, to dole seya bar duk wani abu najin dadin duniya sannan ze iya samun lokacin ibada. Daga karshe kuma ina maki ta,aziyar mutuwar diyarki, tare da fatan alkhairi na auren diyarki Jalila.
.
Kuka sosai Zarah takeyi, jitake dama Allah yadauki ranta, da irin wannan rana daya gwada mata, jan jiki tayi ta matsa kusa da Babanta, wanda shima kanshi yake kasa yana kuka, kafarshi takama tana kuka tana fadin Baba kaine mutum na farko daya kamata infara neman gafararka, tabbas na cuceka, na wulakantaka, ban baka darajarka ta Uba agareni ba, kai cona, daban zama 'ya tagari ba,nahada kai da makiyiyarka munzalunceka.  Dan girman Allah Baba kayi hrk kayafemun, nasan idan baka yafemun ba, raywata bata da amfani, wlh ko haka Allah yabarni naga rayuwa kayafemun ko naga haske arayuwata. Kamota yayi yana kuka yace, ya isa haka Zarah, nayafe maki, duniya da Lahira, idan kina da laifi nima inadashi danayi sakaci da addu,a har wata tasamu galaba akaina, tazo taruguje tarbiyar dana baki afarko, tabbas, yanzu kam naga falalar addu,ar iyaye akan 'ya'yansu. Allah yagafarta mana gaba daya. Kije kinemi gafarar mijinki, shine yafi can canta daya yafe maki.

Matsawa tayi kusa da Alh, wanda shima yake kuka kamar karamin yaro, zata kama kafarshi yayi saurin janyewa, tace nasan banida bakin dazan nemi gafararka, na cutar da kai, na wulakanta ka, naci amanarka, na ha'inceka, nakasa bama yaranmu tarbiya mekyau, amma dan Allah kada kadubi laifukan dana yi maka, ka kalli girman Allah da darajar yaranmu ka yafemun, kaima Allah ze saka maka da mafificin alkhairinsa, kayi hkr da duk abinda nayi maka.

Shiru Alh, yayi yana kuka, Jalila ta matsa kusa dashi tarike kafarshi tana kuka tace, Dady dan Allah kayi hkr ka yafema Umminmu, nasan ta cutar da kai amma idan baka yafe mata ba, zata shiga wata irin rayuwa, dan Allah Dady. Goge idonshi yayi yace shikenan Jalila nayafe mata, ko alahira wani yanacin arzikin wani, haihuwa me rana, kigodema yarki kinci darajarta, nayafe maki.
.
Komawa gurin Falak tayi tana kuka tama kasa magana, dan muryarta harta dashe, Falak ta tashi ta aje Ameerah, tadawo takama Zarah tana goge mata kwallan idonta, itama tana kuka tace haba Ummi, kintaba ganin inda uwa tadurkusama yarta? Kamar yanda bazaki durkusama Jalila ba, haka nima agurina na daukeki Uwa, kada ki wahalar da bakinki gurin neman gafarata, ni 'yarkice, na dade dayafe maki, kuma har cikin zuciyata nayafe maki, Allah ya yafe mana gaba daya, Zarah jitayi gaba daya kunyar Falak da sauran mutanen falon takama ta, kallon Baba Mairo tayi tace Baba Mairo dan Allah kiyafemun abinda nayi maki, tabbas ke Uwa tagari ce dayakamata ace narikeki amatsayin Uwa, amma sena wulakantaki narike wadda tayi silar shigata wannan rayuwar amatsayin Uwa, gashi ta dalilinki nasamu alkhairi inbadan keba, dayanzu nakarama kaina zunubi me yawa,amma se bakibi son zuciyarki ba, kika kareni daga fadawa halaka. Nagode da irin zaman da kikayi dani da yarana. Baba Mairo tace ai bakomai Hjya. Zarah tace zanso kidena kirana da wannan sunan, dan yanzu nazama diyarki, narasa gatana Uwa, inaso kimayemun wannan gurbin dan Allah.

Kwalla Baba Mairo tagoge tace bakomai Zarah dama can ni amatsayi diya na daukeki, Allah yayi maki albarka,kuma Allah yajikan jidda, kallon Umman Sameer tayi tace Umma duk da bansanki ba, amma kinmun alkhairi, nagode maki sosai, Allah yasaka maki da gidan Aljannah. Tace Kawu kaima nagode kayi sanadiyar samun lafiyata.

Sameer kaima bansan dawane baki zan nemi yafiyarka ba, amma dan Allah kayi hkr da duk abinda namaka, kuma kayafemun, nagode sosai da dawainiyar da kukayi mana kaida Saleem, Allah yabiya ku. Suka ce amin. Zarah tace Allah sarki Jidda Allah yaji kanki, banida rabon neman gafararki, nasan banzamo Uwa tagari agareku ba, amma ina rokon Allah ya yafe maki laifukanki, kema Jalila kiyafemun. Kuka tasaka, kowa seda yatausaya mata.
.
Malam yace to Alhmdllh naji dadi sosai da kuka zamo mutane masu yafiya ga junanku, kuma dama haka Allah yakeson bayinsa masu saurin yafiya akan laifin da,akayi masu, dan duk mutumin da,aka cuta, yana da ikon daukar mataki amma yayi hkr ya yafe tabbas wannan mutumi Allah zesaka mashi da mafificin alkhairinsa. Allah yakara yafemana laifukanmu, yashiryar damu da iyalanmu, Allah yasa mufi karfin zuciyarmu. Daga karshe Alh, inason inroki wata alfarma agareka, inaso kamar yanda su Baba Mairo zasu zauna agidanka, inaso itama Zarah kayi hkr kabarta tazauna agurinsu, tunda zatafi samun matemaka, akan idan takoma gidansu, tunda shima babanta ba aure gareshi ba, kaga idan Allah yakawo mata miji setayi aure hakan zetemaka mata tasamu saukin damuwar datake ranta.

Kawun Alh, yace tabbas Malam karigani, nima abinda ke raina kenan, kaima Alh, bazeyuwu kazauna haka ba, amma kome kenan, nan da kwana 2 zanzo akwai maganar dazamuyi. Zarah jitayi kamar ta kurma ihu, wai agabanta ake maganar mijinta zeyi aure, ita kuma gata ta nakasa, kilama bazata kara aure ba. Goge idonta tayi aranta tace kaicona. Jalila ma hakanan bataji dadin abinda Kawu yafada ba, taso ace ba saki 3 Dadynta yayi ma Umminta ba, da tasashi ya maidata.
.
Malam yace to ai semu rufe taro da addu,a ko? Anan yayi masu addu,a yayi masu sallam Alh yabashi kudi masu yawa, yace baze karba ba, Kawu yace a,a ai ba biyanka mukayi ba, kyauta ce yayi maka, anan ya amsa yayi masu godiya yatafi tare da Kawun Sameer. Alh, da Kawu da Mal. Garba suka fito suka nufi part din Alh, Kawu yace kaima Mal. Garba yakama kasamu kayi aure zama babu mata bakaramin matsala bane, sbd akwai lalurar ciwo kuma ga al,amuran rayuwa.

Murmushi yayi yace wlh Alh, ni tsoron ma matan nakeyi, dariya Kawu yayi yace kada kasamu damuwa, idan har kabani dama nizan zaba maka. Yace haba ai yanzu munzama daya, duk wacce kazaba mun nikuma na amince. Yace dama akwai wata diyar kanina da mijnta yarasu yabarta da yara 2 mace da namiji, yanzu haka tana gidana anan take zaune, idan har ka amince zaka aureta, amma kuma da yaranta zata zauna, to? Malam. Garba yace ai babu damuwa, yaro ai nakowa ne, wlh na amince, sede bansani ba ko ita. Kawu yace kamar yanda mukayi maganan nan da kai itama haka tacemun inzaba mata, nikuma gsky nayaba da kai, shiyasa kuma idan bazaka damuba, zanso kabani dama inmaka gyaran gidanka.
.
Alh, yace a,a kawu kabarni nizanyi wannan aiki, Kawu yace ai ni narigaka, dan haka kaima seka samu wani abun kayi mashi. Har kuka seda mal. Garba yayi, yace babu abinda zance maku se godiya. Alh, yace shikenan nikuma zanbude mashi babban shago wanda zerika kula dashi. Kawu yace yauwa, dan haka bawani daukar lokaci abun zeyi ba. Yace nagode sosai. Kawu yace kaima kashirya kilama tare za,ayi bikinka dashi. Alh, yayi dariya yace haba Kawu niyanzu ai nagama kallon wata mace ince inasonta, inama zan tsaya kallonsu. Kawu yace ato aini harna kallo maka. Dariya suka sa gaba daya.

Baba mairo se lallashin Zarah sukeyi, tace tashi muje kiyi wanka kici abinci, inaso kisaki ranki kada wata cuta tadameki, kidauka kamar ba,ayi komai ba, Jidda kuma addu,a yakamata kirika yimata. Haka suka kamata suka kaita bandaki dan tayi wanka.
.
Falak taja Jalila daki tana tayi mata tsiya, Jalila tace wlh ke muguwa ce, koma kimun sannu shine daga shigowata ina kallonki kinamun dariya, wai dan Allah ya akayi kika gane? Falak tace yo daga tafiyarki mana. Jalila tace nashiga 3 yanzo kowa yasan abinda yafaru dani, har Dady ko? Falak tana dariya tace ke kwantar da hankalinki ai babu wanda ya kula dake, kinsan hankalin kowa yana gurin Ummi. Jalila tace wash, harnaji dadi, Falak tace to Allah yasa nan da wata 9 musami yan biyu. Jalila ta kaimata duka tace wlh yan biyu su tsaya akanki, Falak tace toshikenan zamu gani ai. Baba Mairo tashigo tace to meza,a dafa ne agidan yau? Jalila tace a,a Baba kibari tunda ina gida indora, tace a,a Jalila daga ganinki bakijin dadi, kawai kibarshi kizauna kihuta. Dariya Falak tayi tace Baba kawai kidafa komai medadi, Jalila tajuya tana gungunai, Baba Mairo tace waini menace ne? Falak tace rabu da ita Baba, Jalila tadauko pillow tana dukanta dashi, baba mairo tayi waje tana dariya.

Bayan kwana 2 komai yafara dedeta, sede haryanzu Zarah takasa sakin jikinta agidan, duk da Baba Mairo tana kokarin ganin tana janta ajiki, gaba daya sunkwaso kayansu sun maido gidan, zamansu gwanin ban sha,awa Umman Sameer da Baba Mairo sune suke girkin gidan, Zarah kuwa ansama mata sanda hartafara amfani da ita, kuma kafarta tana kara samun sauki, sede aje ayi mata dressing, kuma jikinta yafara haske. Kullum tana cikin jan carbi tana istigifari, sallah akai akai takeyinta. Sameer yace ze kawo mata malamin daze rika kara mata karatu.

Bayan kwana 2, Kawun Alh, yazo, kai tsaye gurin Baba Mairo yawuce, waje suka fito, wata magana suka gamayi, sannan nga sunnufi bangaren Alh, Bayan sungama gaisawa Kawu yace dama nace maka zanzo bayan kwana 2 togashi nan nazo, kuma tare muke da Baba mairo dan ina ganin maganar zefi ayita tana nan.

Bawani abu bane akan maganar auren danayi maka ne, akwai wadda nagani kuma na yaba da hankalinta, bakowa bace se sirukarka, Zaro ido Alh, yayi yace bangane ba. Yace E sirukarka nace, wato mahaifiyar Sameer mijin Falak, tabbas tana da halin kirki inaso kayi hkr ka karbi zabin damuka yimaka nasan bazakayi dana sanin abun ba.

Shiru yayi Baba Mairo tace gsky Alh, nima ina maka sha,awar auren Halima, nina zauna da ita kuma kasan bazan zaba maka abinda ze cutar da kai ba. Amma me kace? Alh, ya sosa keya yana murmushi. Kawu yace shikenan nagane, kuma naji dadi daka amince, insha Allahu kasamu wadda zata share maka hawayenka, Allah yabada zaman lafiya, kuma insha Allahu nan da asabar mezuwa za,a hada dana mal. Garba, kaga tsohon sirukinka da kai zaku Angwance arana daya. Dariya Alh, yayi yace kai kawu. Godiya yayi masu.
.
Haka Baba mairo tasamu Umman Sameer da maganar, amma da kyar ta amince, dan cewa tayi tana jin kunyar Zarah, Baba Mairo tace bakomai zanyi mata bayani kuma nasan zata amince. Zarah wadda take jin duk abinda suke fada dan tazo zata shiga falonsu taji suna magana. Kuka kawai takeyi tana kara tsanar Asabe da kuma irin halinta, share idonta tayi, tayi sallama tashiga, bayan tazauna tace Baba Mairo kuyi hkr naji duk abinda kukace, nazo shigowa naji kuna magana amma wlh ba labe nayi maku ba. Umma kada kidamu babu komai, koma menene nina jama kaina, kuma zanfi son ace kece kika auri Alh, akan yaje waje yasamo wata, Allah yabaku zaman lafiya. Fita tayi tana kuka. Baba mairo tace tokinji abinda tace, Halima tace shikenan, Allah yazaba mana abinda yafi zama alkhairi.
     Baba Mairo tace amin, dan haka kinga saura kwana 5 daurin auren kuma da an daura zaki tare, dan haka dole ingyaraki dan bawai tsufa kikayi ba, kawai rashin gyarane, murmushi tayi ta tashi tafita. Kowa yaji dadin wannan hadi da akayi, duk da Jalila bataji dadi ba, amma kuma taji dadin da akace Umma Alh, ze aura dan tasan halinta.

Haka akayita shirye shirye Umman Sameer cikin kwana 5 tayi kyau sosai tafito mace me kyau, dan komai yana son gyara. Sameer se tsokanarta yakeyi yana cewa dama Ummanshi tana da kyau amma batason yin kwalliya, itade sede tayi ta murmushi. Sameer yazo gurin baba Mairo shida saleem yace gsky Baba ana daura auren su Umma nima zandau matata mukoma gida, dan gsky abun da kunya. Saleem yace hakane Baba dan Allah kibarsu su koma. Tace to ai shikenan, dama ita nake tausaya mawa, tunda kace ku koma se kutafi amma wlh karika dawowa dawuri, yace angama Baba Mairota. Dariya tayi, sukayi mata godiya.
.
Ayau asabar aka daura auren Alh, Abba Bala da Halima kan sadaki dubu 30, se Mal. Garba da Samiyya suma sadaki dubu 30, kuma aranar aka kai kowa gidanta, Kawu yayi kokari na gyran gidan Mal. Garba, gashi Alh, yabude mashi babban provision store, haka aka kai amarya Samiyya sede ance yaranta sedaga baya za,a kawosu.

Halima ma Alh, yasa mata kaya adakin Zarah, ita kuma aka maida mata kayanta can part dinsu, akace idan su Falak suntafi seta koma dakin falak, aranar zarah ko abinci bata ciba, tana dakinta takasa fitowa, kuka kawai takeyi, seda tabama kowa tausayi, amma kuma ita tajama kanta.

Bayan kwana 2 da biki Sameer yadauki matarshi suka koma gidansu, wanda yakara shan gyara kamar wata sabuwar amarya, tayi mamaki sosai ganin irin gyran da yayima gidan, haka suka bude sabuwar rayuwa.
.
Haka rayuwa tacigaba da tafiya cike da jindadi Alh, yanajin dadin zama da Halima, shikanshi yasan yanzu yana cikin kwanciyar hankali, har mantawa yakeyi dawata Zarah, dan koyaje gaida baba Mairo bata barin su hadu, shima baya nemanta, yana bama Baba Mairo girma sosai kamar ita ta haifeshi, kuma yahanata yimasu girki, yacika masu store da komai na abinci yace suyi iyakar nasu, bayaso ta wahala. Jikin Zarah kam ya warke, har ancire daurin kafar tazama dungulmi, sede haryanzu bata maida jikinta ba, dan kullum cikin kuka take, da tunani, sede kawai bakin datayi ne yaragu amma duk wanda yasanta ada yanzu baze iya gane taba. Malamin da Sameer yasama mata yana zuwa yana mata kari kullum, tamaida hankali sosai gurin koyon karatu.

Bayan shekara daya Jalila tahaifi yaronta me kyau aka samashi sunan Mahaifin Saleem, suna kiranshi da WALEED.Taro yayi kyau, yaran Falak sunyi wayau sosai, kamar sunfi shekara daya, kuma alokacin ne tafara laulayi, bayan suna sukaje asibiti, likita yace bakomai zata iya cigaba dabasu nono, amma tafara basu abinci, idan cikin yayi girma seta ciresu.

Halima ma tasamu ciki wanda haryayi girma, Alh, bakaramin farin ciki yayi ba, ganin zekara samun haihuwa. Zarah ma jiki yayi kyau, tafara dangana, har tafara kiba, kullum Baba mairo cikin kulawa da ita takeyi.
.
Ayau Halima ta tashi da nakuda sede har Alh, yafita bata fada mashi ba, sede takira Baba mairo, tana zuwa ta temaka mata, cikin lokaci kankani tahaifi danta namiji, Baba mairo tayi mashi wanka ta gyara gurin itama tayi wanka sannan aka kira Alh, akace yazo an haihu, lokacin dayazo yaga abinda aka haifar mashi seda yayi sujada yagodema Allah, har kwallan farin ciki seda yayi. Zarah ma tayi farin ciki, kuma tazo tayi mata barka, dan bata shigowa gidan idan Alh, yana nan.

Bayan kwana 2 da haihuwarta Samiyya matar Mal. Garba ma ta haifi mace, zarah bakaramin jin dadi tayi ba, haka tashirya ita dasu Jalila da Falak sukaje barka, Aranar sunan halima bakaramin kashe kudi Alh, yayi ba, seda ya yanka manyan raguna Biyar, taro yayi taro, yaro yaci sunan Alh, Abba, dan yace sunanshi zesama yaron za,a kirashi da KARAMEE. Bayan kwana 2 akayi sunan Samiyya, itama tasamu alkhairi sosai.
.
Cikin Falak yana wata 6 ta yaye yan biyu, aka kaisu gurin Baba mairo, haka suka cigaba darenon cikin Falak, harya kai lokacin haihuwarshi, da dare suka nufi asibiti, suna zuwa ta haifi yaronta me cike da lafiya, nan Sameer yarika kiran waya yana fadama mutane, bayan ta huta aka sallameta, suka dawo gida.

Ranar suna yaro yaci sunan mahaifin Sameer Abdullahi ana kiranshi da SUDAIS, Falak ansha kyau sosai, dan takara zama babbar mace, haka taro yatashi cike da farin ciki.

     Bayan shekara 2 an maido su Ameer da Ameerah gida, har ansasu makaranta, kowa yagansu yana sha,awarsu, domin suna matukar kama, gasu kyawawa, Jalila takara haihuwa tasamu mace, aka samata Zarah, suna kiranta da AMAL, shima   Waleed an saka shi makaranta, hada Karami ma Alhn yasashi makaranta, dan itama Halima wani cikin gareta.
.
Haka rayuwar Zarah tacigaba da tafiya agidan Alh, kullum jinta takeyi kamar tana kurkutu, idan tayi tunanin komawa gidan ubanta setaga gara tayi zamanta, dan batada daki agidan, gashi de tana cin abinci mekyau, amma kullum kamar ana dibarta, Baba Mairo harta gaji da lalllashi tasa mata ido, shiyasa yanzu idan zatayi kuka seta shige daki sannan, amma duk da haka da baba Mairo ta ganta seta gane tayi kuka sede kawai ta kyaleta. Ga Son Alh, dayake hanata bacci, batason tana sonshi dayawa hakaba seda tarasashi, kuma taga yayi aure, wani lokacin har labewa takeyi idan yashigo tayi ta kallonshi. Zama tayi bisa gado tace Oni zarah, yanzu wai nice haka, lallai rayuwa ta koyamun hankali, Danasani nayi hkr da Hajjo munyi zaman mu Da yanzu nasan nazama wata babbar Hajiya.

Danasani banyima Alh, asiri ba, dayanzu ina nan da kafata lafiya lau, Danasani ban dauki shawarar Asabe ba, dayanzu bnshiga wannan kangin ba. Ya Allah kaji tausayina ka kawomun karshen wannan zaman danakeyi.
   Allah kashirya duk masu irin halina ya Allah. Kwanciya tayi tana kuka me tsuma rai.

     Nikam dariya nayi nace Zarah ada kenan, dama ai Danasani keya ce.

Wata bakar jaka Falak tadauko taciro wani abun hannu, tadawo
kusa da sameer tazauna, yana kallonta, tace Ameerah zonan, hannunta takama tasaka mata abun hannun, Ameerah tace lah, Momy ke kika siyomun? Kwallan idonta tagoge tace a,a Grandmother dinki ce tace inbaki, Ameerah tace toyaushe zan ganta? Sameer yajawota yace kin kusa ganinta kinji. Ameer yace Dady nito ina nawa? Tashi yayi yadauko wani karamin agogo yace kaima ga naka, yace toni wayace abani? Murmushi yayi yace kaima GrandFather dinka yace abaka, tashi sukayi suna tsalle, sukace Thank you Momy and Dady, waje suka nufa suna murna.
.
Jawo Falak yayi yace haba my dear kin manta kince bazaki kara kuka ba, tace dole inyi kuka my Luv.

Kawai natuna wani abune, wai yau nida ake kira AGOLAH, nice nake zaune da yarana har 3, suke kirana momy, agaskiya ina tausaya ma duk wata AGOLAH datake AGOLANCI awani gida, Allah yajikanku Umma da Abba, badan narasa kuba da babu wanda ze kirani da AGOLAH, har yau idan natuna sunan nan yanamun ciwo.

Sameer yace banaso kina rike abu aranki, kinmanta kince kinyafe masu? To kibar tuna abun, komade menene yanzu gashi kin daukaka, ayanzu kina sama da ita kuma ita tana kasa dake, kuma kinmata nisa, sosai. Yanzu albishirinki. Tace goro, yace hajjin bana tare za,ayi damu. Tsalle tayi ta rungumeshi tana murna tace wow amma gsky kayimun babban albishir, bansan ma dame zan gode maka ba. Dariya yayi yace ni ai nasan da abinda zaki godemun, kuma Falaka, kinfi haka agurina, kece farin cikina, kin bani kyautar yara har 3 kina kula dani yanda yakamata, nine zance bansan dame zan gode maki ba. Amma yanzu tashi mushiga ciki kibani goron albishir. Tashi tayi tana dariya tashige daki.

ALHAMDULILLAH
.
Ina mika godiyata ga Allah daya bani ikon kammala wannan littafi nawa mesuna AGOLAH. 
   Kuma ina mika sakon gaisuwa meyawa ga dukkanin masoyana nagode da irin kulawarku gareni. Allah yabar zumunci, abinda nafada da kuskure sekuyi hkr dan dan Adam ajizine.

Nasadaukar da wannan littafi ga mahaifina, ALLAH YAJI KANSHI DA RAHAMA AMIN, ALLAH YAJIKAN DUKKANIN MUSULMAI BAKI DAYA, MUKUMA IDAN TAMU TAZO ALLAH YABAMU GUZURIN TADDASU.

ALLAH YAKAREMU DAKA SHARRIN ZUCIYA YASA MUFI KARFINTA AMIN.

..
CALL or SMS
07066508080

.
Whatsapp
07066656752

Read More

Share this

WhatsApp

AGOLA Page 36-40

 November 27, 2017     AGOLA 1-END     No comments   

AGOLA Page 36-40

.

Hannu bibiyu Alh yasa yadafe kanshi, gabadaya jiyake duniyar tamashi zafi, wani abu ya tsaya mashi a makoshi, wanda daze samu yawuce dayafi jin dadi. Kuka yakeso yayi amma sam hawayen sunki zuwa, tabbas kuka ma rahamane.


Zarah data shigo falo tace a,a Alh yaushe kashigo banji shigowarka ba? Shiru yayi bece komai, dan yanda yakeji idan yabude baki komai ze iya fada mata. Zama tayi kusa tashi tace magana fa nakeyi amma kayi shiru ka kyaleni. Ko baka da lfy? Wani ne ya mutu? Duk tambyr datake mashi hakan besa yadaga kai ya kalleta ba. Cike da masifa tace wai Alh, mekake nufi......


Sallamar da akayi ne, yasata hadiye sauran masifarta. Juyawa tayi tana kallon kofa jin sallamar bata mutum daya bace, baki ta saki ganin mutanen dasuke shigowa. Mamakinta be karuba seda taga Baba Mairo tashigo gata tayi kyau cikin shiga me kyau.


Samun guri sukayi gaba dayansu suka zauna, yaran kuma suka zauna akasa, haryanzu kan Alh aduke yake, guri Zarah tasamu tazauna, gaba daya jikinta yayi sanyi. Wata irin zufa tafara keto mata. Baba Mairo tace Alh ina wuni.


Dago kai yayi cike da mamakin ganinta, ahankali yace Baba Mairo. Tace na,am, dama kina garin nan? Murmushi tayi tace wlh kuwa Alh. Gaisawa sukayi dasu Kawu, Alh ya kalli Jidda wadda taketa kuka har idanuwanta sun kumbura saboda kuka. Yace Mamana lafiya kike kuka?


Kara sakin wani kukan tayi ta tashi tamatso kusa dashi tazube bisa guiwowinta, hankalinshi dana Zarah yatashi ganin irin kukan datakeyi. Jalila da Falak suma duk kuka sukeyi dan sun san abinda Jidda takeyima kuka. Dago kai tayi tace Dady dan Allah kayi hakuri kayafemun, tabbas banzamo diya tagari ba, na cuceka na cuci kaina.


Nasan Allah baze taba yafemun ba idan har baka yafemun ba. Nayi dacen Mahaifi nagari amma rashin samun Uwa tagari yasani nima nazama wadda bata gari ba. Alh, yace Mamana wai mekike fada haka ne? Zarah kuwa da cikinta yafara yamutsawa jitake kamar ta nutse dan kunya, agaban sirikinta Jidda take fada mata wannan maganar, jitayi kamar tashakota.


Alh yace ya isa haka mamana, kidena kuka kifadamun wane irin laifi kikamun haka. Zarah tayi saurin fadin a,a Alh, kabarta tashiga ciki tasamu ta kwanta tayi bacci ta huta kasan batada lafiya. Jidda tace, a,a Ummi ya isa haka, kibarni nafadi abinda aka dade ana boyewa agidan nan, garake Ummi kinada lafiyar dazaki iya tuba zuwa ga Allah, nifa? Ina cikin cuta, wadda ko ayanzu Allah ze iya amsar raina.


Tundaga auran Hajjo da fara shigarta cikin halin banza, da abunda Zarah dasu Asabe sukayima Hajjo da Ameer, harsukayi sanadiyar mutuwarsu, dazuwanta London, da irin hudubar da Zarah takeyi mata, zuwa auren datayima Falak da Sameer, da yanda tabama su Asabe kudi, zuwa yanda Zarah ta temaka ma su Figo har cutar datake dauke da ita seda Jidda tafada masu. Gaba daya falon yayi shiru, kukan Jidda, Jalila da Falak kawai akeji.


Zarah kuwa zama tayi kasa kamar meshirin hawa bori, takasa kuka kuma takasa magana, Alh, kawai ta kurama Ido, hatta da Kawun Sameer seda yafitar ma Jidda da hawaye, su Baba Mairo da Umman Sameer suma Kuka, kawai sukeyi. Sameer da Saleem da dama sun san da labarin amma jin sauran labarin seda yasasu kuka.


Alh da haryanzu yarasa gane wai mafarki yakeyi ko gaske gashi haryanzu hawaye sunkasa zuba a idonshi, zuciyarshi jiyake kamar ansamata wani katon dutse. Tabbas daza,a gwada jininshi babu abinda zesa aga be hau ba.


Zarah yakalla da idanunshi dasuka juye tamkar garwashi, kallonta kawai yake amma yakasa magana, Zunbur Zarah ta mike tace a,a wlh kadena kallona Alh, ka tsaya nida kaina zanyi maka bayanin duk abinda nayi, kai tafara sosawa, da jikinta, can kuma tafashe da dariya, tace.


Yo aike Jidda bakima san komai ba,,,,,, nan itama tashiga fada masu irin abubuwan datayi, komai seda tafada, tanayi tana dariya tace Mairo aike baki iya munafunci bama, gashinan kina ganin AGOLAH hada ciki, ai wlh rantsuwa nayi senaga bayanta. Hauka de tuburan Zarah tafarayi, kowa salati yakeyi yana kallon ikon Allah.


Kawu yace Alh,ai inaganin bekamata abarta haka ba, a kamata ayi mata addu,a Alh daseyanzu yayi magana, yace Malam babu abinda zankara yima wannan azzalumar matar, tsakanina da ita sede alahira. Ta cutar dani, taso tasani inkasa rike amanar marainiyar Allah dana dauki alkawari.


Babu abinda banyi mata ba, amma tarasa abinda zata sakamun dashi se wannan rashin mutuncin da cin amana, tabbas ko hakkin mahaifinta kawai ya isa ya tambayeta, bare kuma na baiwar Allah Hajjo, da karamin yaro wanda ko agurin Allah ba,a bude mashi littafin rubuta lada da zunubi ba. Kai!!! Agaskiya bazan boye maku ba Zarah tacutar dani, Allah shine zemun sakayya, kuma gashi tun aduniya tafara gani, idan da tasamu sa,ata dayanzu nakara zama rakumi da akala. Dan haka ni babu abinda zan mata.


Ke kuma Jidda bazanyi maki baki ba, sbd ba laifinki bane, duk da kema kina da laifi, meyasa Jalila batayi abinda Zarah tasakiba? Yanzu ai kinga karshe da kuma illar bariki ko? Ko ahaka Allah yabarki yahadaki da babban aiki, kuma wannan cuta taki idan har bakisha mata magani ba, zakizamo abin kyama agurin mutane. Abu daya ne zesa nazauna agidan nan, shine auren Jalila, amma iname tabbatar maki ina aurar da ita nima zanbar maku garin, bazan iya zama bakin cikinku yakasheni ba. Tashi yayi yana hada hanya, da kyar yashige dakinshi sbd jirin dayake gani.


Zubewa Jidda tayi agurin tana wani irin kuka me tsuma zuciyar me saurare, Jalila ta matso kusa da ita tariketa itama tana kuka, Falak kuwa jitayi cikinta yawani murda kamar alokacin zata haifi abinda ke ciki, kwantawa tayi tasaki wata irin kara tana kara rike cikinta, dasauri su Baba Mairo dasu Sameer sukayi kanta, jini ne yafara bin kafarta, nan take ta sume.


Cike da tashin hankali Sameer yadauketa Saleem da sauran suna binshi abaya, mota yanufa da ita suna shiga Saleem yaja suka nufi asibiti. Gaba daya hankalin Kawu yagama tashi, su Jalila se kuka sukeyi, Zarah tafito kanta ko dankwali babu, se cizgar gashinta takeyi haka tanufi bakin gate. Jalila tace Kawu kate maka mana......


.


Suna zuwa asibiti aka ansheta aka nufi Emergency room da ita, Sameer hankalinshi bakaramin tashi yayi ba, yakasa zaune yakasa tsaye, Saleem ne yadafashi yace kayi hkrdan Allah, addu,a yakamata muyi mata.


Sameer yace wlh tsoro nakeji kada murasa abinda ke cikin Falak, Saleem yace insha Allah bazamu rasa shiba. Sunfi minti 30 agurin sannan wani likita yafito suka bi bayanshi zuwa office.


Bayan yagama yan rubutunshi yakallesu, murmushi yayi ganin yanda Sameer yayi kamar meshirin yin kuka, yace to alhamdulillahi, munsamu tsayar da jinin dayake zuba, kuma cikin jikinta befita ba. Sede dole ze kara ko sati biyu akan kwanakinshi.


Wani murmushin farin ciki Sameer yayi yace mungode Dr. Yanzu ya jikin nata? Yace dasauki, ansamata karin ruwa tana bacci, zuwa anjima insha Allah zata tashi, sede kada tarika aikin wahala,kuma arika kwantar mata da hankali, magunguna ya basu wanda zasu siyo mata, amsa sukayi suka mashi godiya suka fita.


Zarah kuwa gaba daya tafitar da kayan jikinta, se jan gashinta takeyi, duk tajima kanta ciwo, Jalila se kuka takeyi tarasa yanda zatayi da ita. Kawun Sameer ne yadauko ruwa akofi yayi addu,a ya watsa mata ajiki, nan take tafadi kasa bacci yadauketa. Kamata Jalila tayi takaita dakinta ta kwantar da ita bisa gado.


Wata doguwar riga tasaka mata da kyar, sannan tarufo maka kofar dan kada tafito, dakin Jidda tanufa, dan tunda aka tafi da Falak asibiti bata kara ganinta ba, kwance tasameta ta rufe da zanin gado, numfashinta yana fita dasauri.


Dasauri tahau saman gadon ta budeta, jikinta zafi taji sosai tace Yaya Jidda bakida lfy ne? Kai tadaga mata, sauka tayi taje tadauko mata maganinta, ruwa tadauko mata ta kamata tabata maganin, tana gama sha tayi saurin sauka tanufi bandaki tafara amai, seda tagama Jalila ta temaka mata ta gyara jikinta suka fito, bayan ta kwantar da ita takoma ta gyara bandakin.


Zama tayi tana kallon yanda take fitar da numfashinta kamar zebar jikinta. Wasu zafafan hawayene suka sauko mata, kai ta girgiza tana me tausayin kanta, akan irin rayuwar datake fuskantota, ga Ummi ta haukace, ga Jidda akwance. Ahankali tace Yaya Jidda kozaki shirya muje asibiti? Kai ta girgiza tace konaje asibiti babu abinda zasu mani, kawai kibarni haka. Jalila tace bara inje inkira Dady, hannunta Jidda tarike tace,


A,a Jalila, ayanzu babu abinda Dady yakeso kamar natsuwa, ayanzu yana cikin tashin hankali bekamata kije gurinshi ba, dan yanzu ma Allah kadai yasan cikin halin dayake, Jalila tace haka ne, Jidda tayi murmushi tace kiyi hkr Jalila, zamu barki cikin kuncin rayuwa, Allah yakareki daga sharrin dangin miji, tabbas nida Ummi munbar abin fadi aduniya, amma insha Allahu bazaki tozarta ba, nide ina rokon addu,arki akullum.


Jalila tace bakomai Yaya tunda har Allah yajarabceni da wannan rayuwa yasan zan iya dauka, kuma kema zaki samu rayuwa me kyau, fatana kawai kirika shan maaganinki. Ummi kuma insha Allahu zata samu lafiya. Jidda tace hadomun black tea.


Alh, kuwa tunda yashiga daki jiyayi kamar zuciyarshi zata fito waje, har ya kwanta sekuma yayi saurin tashi yanufi bandaki yadauro alwala yazo yadauki Qur'ani yafara karantawa, yadade yana karatu harseda yaji zuciyarshi tayi dadi sannan yatashi yayi raka,a 2 yayita rokon Allah akan yadora mashi duriya da dangana aduk halin daze shiga.


Jin falon yayi shiru ne, yatashi yafito, akofar kitchen yaci karo da Jalila, wani sabon tausayinta yakara kamashi, kasa kallon idonta yayi yace ina su Falak? Ana tafada mashi abinda yafaru, yace to ina Jidda take fa? Tace tana daki ita zankai ma tea ma, ze kara magana yaji wani sabon kuka yazo mashi kawai yajuya yatafi.


Da kallo Jalila tabishi itama tana kuka, dan taga lokacin da hawaye suka taho mashi.


Awaya yakira Sameer ya tambayeshi jikin Falak, Sameer yace dasauki yafada mashi duka abinda likita yafada. Alh, yace toshikenan idan naji dama dama zanshigo.


Zaune Falak take gefenta Baba Mairo da Umman Sameer ce zaune, sesu Sameer da Saleem zaune abisa kujera, Baba mairo tace sannu Falak, inaso ki kara hkr akan wanda kikeyi, Allah yana kallonki baze bari kishiga wani hali ba, inaso kidauki duk abinda yawuce yazama tarihi. Kada kisaka wani abu aranki yazo yadameki.


Ita kuma Zarah kome tayi dan kanta, gashi nan tun aduniya Allah yafara nuna mata ishara, sede abu daya nakeso kisani, ana barin halak kodan kunya, wlh tausayin Jalila nakeyi saboda zata shiga wata irin rayuwa. Kallon Saleem tayi tace dan Allah kada abinda yafaru yasa wani tunani yashiga ranka, nasan kasan komai akan Jalila tunkafin abaka aurenta, inaso kaji tsoron Allah, kuma kamar yanda wannan abu yafaru acikin gida inaso kabarta agida.


Saleem yayi murmushi yace wlh Baba babu abinda yaragu akan son danake ma Jalila, sema karin tausayinta danaji, kuma insha Allah babu wanda zeji wannan maganar abakina.


Sameer yace bara muje muyi sallah damun dawo zamu tafi gida dan banason ta kwana anan, Ummanshi tace a,a idan bataji sauki ba, babu inda zataje, Baba Mairo tace a,a tunda de komai lfy ai gara mutafi gida zefi, nima banason zaman asibitin.


Bayan mintuna 30 Zarah tafarka daga baccin da takeyi cike da firgici, sauka tayi daga kan gadon tanufi hanyar fita, sede taji kofar arufe,komawa tayi tacigaba da daukar duk wasu kayan bisa dressing mirror dinta tana fasawa, hatta da madubin seda tasa hannunta tafasa shi, duk tajima kanta ciwo, jawo sif dinta tayi cikin tsautsayi tafado mata akafarta ta dama, tundaga kwaurinta, wata irin kara tasaki wadda har megadi seda yaji.


Kasa tafadi, tana ihu, gashi takasa cire kafar daga karkashin sif din. Megadi da driver suka shigo suna sallama, Jalila tafito itama lokacin taji ihun Zarah, suka ce lfy? Wlh nima bansani ba, nade barta tana bacci sede naji ihunta, bayanta sukabi.


Tana bude kofar tasaki salati suduka sukabi bayanta, jini ne kwance akasa, Zahar hartayi shiru sbd azaba, dasauri Jalila takarasa gurinta tana kuka, megadi da driver sukayi saurin daga sif din, ai nan sukaga kafarta ta datsa biyu, kamar ansa gatari an fasa, jikin kaurinta shima harkashin ana gani, kafar se reto takeyi.


Jalila tafita tanufi dakin Dadynsu tana kuka, yana ganinta yace Jalila lafiya de? Cikin kuka tafada mashi abinda yafaru, sosai yaji tausayin Jalila, haryayi niyar kyaleta sekuma yatuna mahaifiyarsu ce, yace shikenan kije kicema driver sukamata sukaita mota inazuwa.


Amotarshi yashiga yace suwauce asibitin, Jalila tana rungume da ita, Zarah tayi shiru se hawaye take fitarwa, suna zuwa asibiti aka karbeta aka nufi accident room da ita, ana akayi mata allura tayi bacci.


Likitan yanufi Alh, yace suje office. Bayan sunzauna yace agaskiya Alh, sede ayanke kafar matarka, sbd kashi kafar yariga daya rabe 2, fata ce kawai tarike sauran rabin kafar, amma shi ciwon kaurin za,a iya mata dressing sbd kashin tsagewa ne kawai yayi. Kuma naga kamar tana da matsalar tabin hankali ko? Alh, yace Dr, inaso kuyi duk abinda zaku iya wanda yadace, babu ruwanka da matsalar haukanta, ita tajama kanta, yanzu haka ba matata bace kawai darajar 'Ya'Yanta zataci. So banason yawan tmby. Dr yamika mashi takarda yace yasa hannu, Alh, yace bara inkira diyarta taji da bakinta, sbd yanzu kome zanyi za,aga kamar nayi da wata manufa ne.


.


Shiru Jalila tayi tana hawaye jin bayanin da Dadynsu yayi mata. Tace shikenan Dady muje insaka hannu. Shiga sukayi Dr, ya mika mata takardar tasaka hannu. Anan Alh, yabiya duka kudin aikin dana magani. Dr, yace zaku iya tafiya dan aikin zedauki lokaci, Alh, yace to mungode, muje Jalila.


Zaune suke afalo Kawu yagama yi masu bayanin abinda Zarah tayi bayan tafiyarsu. Falak tace wlh tausayin Jalila nakeyi, Allah de yabata lfy. Baba Mairo tace ita tajama kanta, kuma gashi duniya tana koya mata hankali, sbd alhaki nawa Zarah tadauka akanta, harna mahaifinta fa, kwata kwata tamanta dashi arayuwarta.

Nide yanzu Malam abu daya nakeso aduba akalli mutunci irin na wannan yarinya Jalila, atemaka ma Zarah da addu,a tasamu lafiya.


Kawu yace bakomai, bawani abu bane yake dawainiya da ita ba, se aljanu, kuma sihirin datayima wasu ne, yanzu aljanun suka dawo kanta. Bakomai insha Allahu zamuyi bakin kokarinmu, babu abinda ya gagari Allah.


Saleem yacema Sameer bara inzo inwuce, Falak Allah yakara sauki, sallama yayi masu suka fita shida Sameer. Saleem yace zanje gida idan na huta zanje indubo Jalila dan tundazu nake kiran wayarta bata dauka ba, nasan tana cikin damuwa. Sameer yace shikenan kayi kokarin kwantar mata da hankali plsssss.


Jalila tana shiga daki tasamu Jidda kwance cikin amai, gashi ta bata jikinta da zawo, cike da tashin hankali ta juya tanufi gurin Dadynsu. Atare suka shigo dakin. Kai Alh, yadafe ganin halin datake ciki. Allahumma Ajirni fi musibatihi haza, Wa aklifini khairan minha.


Itace addu,ar da yarikayi azuciyar shi, yace Jalila kiyi hkr kitemaka mata ta gyara jikinta semutafi asibiti, kada kisa damuwa azuciyarki, kirika addu,a zaki samu sauki. Fita yayi yajirasu afalo. Zama yayi yadafe kanshi, yarasa inda zesa kanshi.


Waya yadauko yakira kanin babanshi yana dauka kawai yasa mashi kuka, se alokacin kukan dayake so yayi yazo mashi jin kamar muryar babanshi. Cike da tashin hankali yace Abba lfyrka meyake faruwa kake kuka? Shiru yayi yacigaba da kukanshi, Kawunshi yace shikenan ya isa haka, koma menene tunda ina gari ganinan zuwa.


Kashe wayar yayi ya kwanta bisa kujera yacigaba da kuka sosai, seda yayi me isarshi sannan yaji dadi azuciyarshi, duk wani nauyi dayakeji ada yanzu yaji sauki, tashi yayi yashiga bandaki yayi wanka, yashirya yasamu su Jalila sun fito suka tafi.


Suna zuwa yanda likita yaga jikin Jidda yace dole abata gado, nan aka kaita wani private room sbd yasan matsalarta. Ruwa aka samata da allurai, nan take bacci yadauketa. Alh, yace Jalila muje gida, tace to.


Suna zuwa yasata tayi masu girki yace tazubo yasata tazauna, atare suka ci abincin yana lallashinta, shima daurewa kawai yakeyi, ahaka suka gama cin abincin Jalila ta kwashe kayan, Alh, yace yauwa idan kinyi wanka semutafi ko, dan dare yayi, tace to.

    Bayan tagama tadauki abincin Umminsu dana Jidda kasancewar asibiti daya suke, suka tafi.

Sadda sukaje har angama ma Zarah aikin ankaita dakin hutu, ana Dr, yafada mashi komai yayi dede amma dole akula da ita sosai sbd karta fama kafar. Godiya yayi mashi yanufi dakin Jidda.


Zaune yasameta Jalila tana bata tea, yace sannu Mamana, kallonshi tayi idonta cike da kwalla, tace yauwa Dady. Zama yayi, Jalila tace Dady ya Ummin take? Yace bacci takeyi kuma komai lafiya angama asa,a zata iya kai gobe bata farka ba, sbd haka kizauna agurun Jidda ku kwana tare. Tace to Dady, yace bara inzo intafi dare yayi kuma Kawu yamun waya yana jirana agida. Sallama yayi masu yakawo kudi yabama Jalila yafita.


Bayan sungama gaisawa Kawu ya kalleshi yace Abba lafiya kuwa nazo gida kuduka bakwanan, gashi kamun waya kana kuka, seyanzu dana ganka nakara tabbatar da babu lafiya dan ayanayin dana ganka nasan bacikin kwanciyar hankali kake ba. Kai Alh ya girgiza yace wlh kawu wani iftila,i ne yasameni alokaci guda, shiyasa narasa yanda zanyi da rai na.............   Anan ya kwashe komai yafada mashi, babu abinda yaboye mashi har labarin Jidda.


Innalillahi Wa inna Ilaihirraji'un. Shine abinda Kawu yaketa fada. Yace lallai Abba ka hadu da wata irin jarabawa wadda bakowa bane ze iya irin wannan dauriya dakayi. Kada kadamu insha Allahu komai ze zama dede, kuma kada kasa abun aranka harya haifar maka da wata matsala, bara inzo intafi dare yayi, kome kenan goben zan sameku asibitin. Yace nagode Kawu, sallama yayi mashi yarakashi bayan yatafi yadawo cikin gida.


.

Washe gari tunda asuba Zarah tacika asibitin da ihu, sbd tafarka kuma babu kowa akusa da ita, gashi allurar da akayi mata tasaketa, hatta daurin da aka yimata na kauri tafara cireshi, hauka sosai takeyi.

.

Duk da zafin datakeji hakan besa ta nutsu ba, abunka da hauka, dakin duk ya baci da jini. Cikin sauri aka shigo dakin, wasu nurse ne guda 2 mata, duk yanda suka so riketa abun ya gagara, nema take taji masu ciwo, daya ce tafita domin kira maza.


Atare suka shigo da wani Dr, tare da wasu maza cleaners 2, kamata sukayi da karfi suka zaunar da ita, Dr, yaduba file dinta, anan yace ma dayar nurse din takawo mashi allura, ko minti 5 ba,ayi ba takawo, amsa yayi tare da zuba ruwan yayi mata, cikin mintuna kadan bacci yadauketa.

.

Dr, yace wannan matar akwai hauka ajikinta, dama kuma jiya Dr, yafada mani kuma dole se ansamu wadan da zasu rika kula da ita sosai idan ba haka ba, wannan kafar zata bamu matsala, yanzu dole kusake mata wani dressing din. Nurse suka ce to. Yace bara na kira mijinta awaya na fada mashi tafarka dan me kula da ita yazo.


Jalila tace sannu Yaya Jidda kitashi in hada maki ko black tea ne kisha kinga tunjiya kike amai, kalli yanda kika koma acikin kwana 1, dan Allah kidaure kici abinci kisha magani kozaki samu sauki, wlh bazan iya daurema wannan rayuwar datake fuskanto ni ba, kinga Ummi tana can kwance kema kuma kice bazakisha magani ba, ai abun seyayi mani yawa, tunda Dady babu ruwanshi da Ummi.


Murmushin karfin hali Jidda tayi tace wlh Jalila nikaina ayanzu inaso in rayu kodan intayaki jinyar Ummi, inaso inrayu kodan nima nayi aure nasamu yarana, inaso inrayu kodan insamu damar neman gafara agurin Ubangijina. Amma nasan namakaro, domin sama tayima yaro nisa, nasan kwanaki na kadan suka ragemun, fatana Allah yakarbi tubata kafin in mutu. Kuka duka suka saka, babu me lallashin wani.


Jidda tace kinyima Baba na Zariya waya kuwa? Jalila tace na masa, yace yau dasafe zetaho. Kai cona, shima wannan bawan Allah ban daukeshi da daraja ba, na dauki hudubar Asabe, wadda itace tayi sanadiyar fadawar Ummin mu cikin wannan halin, duk da hada laifinta amma Asabe ce Babbar me laifi. Jalila tace bakomai insha Allah Ummi zata samu sauki.


Jidda tace gashi yau saura kwana 5 bikinki Jalila kuma ga halin damuke ciki, tabbas mun saka rayuwarki cikin takura. Jalila tace wlh niyanzu auren yafuta arai na, kuma koyanzu baza,a daura ba, harse kunsami lafiya. Jidda tace wlh kada ma kifara, aure kamar anyishi angama ne, bakison inga bikinki kafi Allah yadauki raina?, Shiru Jidda tayi tana kuka, Jalila takara matsowa kusa da ita tace Yaya Jidda dan Allah kibar maganar haka nan, kitashi muje kiyi wanka kiyi brush kisha tea, nasan Dady ze kawo mana abinci sekici.


Jikin Falak yayi sauki dayake agidansu Sameer suka kwana hakan yasa gurin karfe 9 suka shirya su duka suka nufi asibiti, dan Sameer yayi waya da Alh, yafada mashi suna asibiti, tafiya suke ahanya, Baba Mairo tace dole ni nazauna agurin Zarah dan nasan babu kowa agurinta, tunda nasan Jalila tana gurin Jidda, Falak tace toni se nazauna agurin Yaya Jidda. Sameer yace babu inda zaki zauna haka nan kawai ki kwaso mana cuta. Umman Sameer tace gsky kam Falak kiyi hkr zaki rika zuwa dubata amma batun kizauna betaso ba, kema haka nan karfin hali kikeyi amma duka yaushe kika warke.

.

Kawu yace hakane, kiyi hkr idan yaso ke Halima sekiyi masu kara kizauna agurin Jiddan, kema Allah zebaki lada, amma wlh nima ina tausayin Alh, dole kowaye Allah ya jarabta da irin wannan abu yashiga tashin hankali, kuma sbd shi da diyarshi zan nema mata magani, amma da munbarta duniya ta koya mata hnkli, duk da ayanzu ma tafara gane kuranta, tunda ance anyanke mata kafa. Umman Sameer tace ai bakomai yanzu suma sunzama yan uwanmu. Allah yakara basu lfy.


Malam Garba mahaifin Zarah da Alh, ne suka shigo asibitin, kasancewar ya iskeshi agida shine suka taho tare. Mal. Garba yace dan Allah Alh, kayi hkr da irin abinda wannan yarinya tayi maka. Babu irin yanda banyi da ita ba, amma bataji magana taba, tabbas babu abinda zance tsakanina da Asabe sede ince Allah ya isa, duk da kacemun ankashe su, amma bazan yafe mata ba, ita da kawarta, sun cuceni, gashi seda cutar takai harzuwa diyata, duk da itama da laifinta amma Asabe babbar annobace agidana.


Alh, yace bakomai Baba, Allah yakara basu lfy. Yace ameen, kuma hukuncin daka dauka akanta kayi dede, nima dande kawai zuciyar Imani amma da ko zuwa bazanyi ba, to Jalila tayi tamun kuka, kuma ina son Jalila, shiyasa nace zanzo sbd ita. Amma tabbas idan ta warke sede taje wani gurin tayi haukanta amma ba gidana ba. Alh, yace kayi hkr muje de muga jinkin nasu.

.

Suna shiga suka wuce Office, anan Dr, yayi masu bayani. Alh yayi shiru dan yana kunyar mal. Garba, ganin yayi shiru Babanta yace to ai ita tasani, kuyi mata abunda zaku iya kawai ku sallameta. Alh yace a,a Baba baza,ayi haka ba, Dr, inaganin abinda ze faru zansamu wani malami zamuyi maganar dashi dan gsky haukanta bana asibiti bane, kome kenan zanzo mukara magana. Dr, yace gsky dayafi, dan tana cikin wani hali, kome tayi kubarta da halinta amma ceton rai zakuyi kuma kamar jihadi ne, koba komai ai Uwar yaranka ce, kai kuma Baba ai diyarka ce, kasan da mahaifiyarta tana nan kome zata zama bazata iya barma duniya ita ba. Jikin Baba yayi sanyi yace haka ne, likita, kuma nagode da tunatarwar dakamun. Allah yamana jagora. Fita sukayi suka nufi dakin Jidda.


Adakin suka sami su Falak harsunzo, bayan sungama gaisawa, Alh, yace Jalila yajikin nata? Tace to Dady dasauki za,a ce, amma kome taci amai takeyi, yakalli Jidda gaba daya tausayinta yakara kamashi yace sannu Mamana, tace yauwa Dady, kidaure kirika cin abinci maganin baze maki amfani ba, idan baki cin abinci. Kuma banaso kirika saka damuwa akanki, mutane nawa suke dauke da irin cutarki gasunan muna hudda dasu wasu ma harsun fimu lfy da kyan fata, babu wanda ze kallesu yace suna da wata cuta. Meyasa suka zama haka? Sbd suna shan maganinsu, kuma suna cin abinci me kyau, dan haka kicire komai aranki, nide nayafe maki, insha Allahu zaki samu lfy.


Baba Mairo tace yanzu Alh, yajikin Zarah? Yace to banje ma naganta ba, dan Dr, yace mun sunyi mata allurar bacci, dan da asuba data tashi haukan yadawo sabo, duk tajima kanta ciwo, kuma ta fama ciwon kafarta, shiyasa yace dole asamu wanda zerika kula da ita.


Baba Mairo tace bakomai Alh, kome zamuyi, zamuyi ne, dan Allah da kai da kuma yaranta. Nizan zauna agurinta ita kuma Halima zata zauna agurin Jidda, tunda Jalila tayi yarinta ace tayi jinya.  Alh, yace to mungode sosai Allah yasa da alkhairi. Baba Mairo tace, ammade bikinta dagawa za,ayi ko? Alh, yace ina tunanin haka, duk da nariga dana gama gayyatar abokanaina, amma tunda lalura ta gifto dole adaga.


Mal. Garba yace a,a baza,ayi haka ba, wannan yarinya ta dade ana shiga hakkinta, acikinsu babu wanda tacema yashiga rayuwar da yayi, dan haka saboda su baza,a daga bikinta ba, acikinmu waye yasan lokacin dazasu warke? To kuma kawai se ashiga hakkin baiwar Allah ace sesun warke za,ayi bikinta. Shima mijin ai anshiga hakkinshi, yagama fada ma kowa nashi, ai  bikin magaji baya hana na magajiya, dan haka abar bikin nan da kwana 5 kmar yanda akasa, Allah yabasu lfy.


Alh, yace shikenan dama gani nayi kamar Jalilan bataso ayi acikin wannan halin shiyasa zan daga, amma shikenan ke Jalila kiyi hkr, nasan bazakiji dadi ba, ace za,ayi bikinki a irin wannan yanayin komai zezo karshe, ranar asabar za,a daura aurenki kuma aranar za,a kaiki. Kuka Jalila tasaka ta tashi tafita, seda tabama kowa tausayi adakin.


.


Haka suka wuni a asibiti, Falak da Jalila ne, suka koma gida suka yomasu girki, Kawun Sameer kuwa dakin Zarah yaje shida mal, Garba da Alh, anan yafara yimata addu,oi, shiyasa lokacin data farka batayi wani hauka me yawa ba, Baba Mairo tana gefenta ita tarika bata abinci da kyar taci sbd wasan datakeyi.


Lokacin da Saleem yazo shida Sameer bayan yaduba jikin Jidda yakira Jalila suka fita waje, cike da tausayi ya kalleta yace my dear wlh harkin rame. Murmushi tayi tace ba dole ba, yace haka ne, dazu munyi magana da Sameer har nake cemashi koza,a daga bikinmu ne, yace mun a,a Dady yace baza,a daga ba. Jalila tace nima naso adaga amma Baba na Zariya yace a,a.


Saleem yace babu damuwa ki kwantar da hankalinki babu abinda ze gagara insha Allah, fatanmu de Allah yabasu lfy, tace ameen. Yanzu mekike bukata, nasande bawani abu kikace zakiyi ba ko? Tace hakane, walima ce kawai zamuyi da yan islamiyarmu, yace shikenan idan nabaku dubu 100 yayi ko? Murmushi tayi tace basuyi yawa ba? Harararta yayi yace bansani ba, anfada maki bikin wasa zanyi, wasu ma a party kadai suke kashe abinda yafi haka, seni daza,ayi walima zakice wai sunyi yawa. Tace tonaji maida wukar, Allah yasaka da alkhairi, yace yauwa ko kefa.

.

Sameer yafadamun duk abinda yafaru jiya, kuma munyi magana da Abbana sede banfada mashi komai ba, kawaide nace ba,a san abinda yasamu Ummi ba, kuma yakira Dadyn ma sunyi magana, yace zeshigo yadubata se Dady yace a,a yabari tunda saura kwana 4 daurin aure seyayi zuwa daya. Kwallan dasuka zubo mata ta goge, tace nagode, bansan dawane baki zanyi maka godiya ba. Yace bakida bakin yimani godiya sbd kinbiyani dakika amince zaki aure ni. Amma inason inrokeki wani abu 1. Wannan yawan kukan da kikeyi yayi yawa, dan Allah kidena, nasan dole ne, amma inaso kiyawaita fadin Innalillahi wa inna ilaihirraji'un aduk lokacin da kikaji wata damuwa tadameki. Tace shikenan nagode.


Haka suka cigaba da jinyar Zarah da Jidda, jikin Zarah kam ana samun cigaba, amma jikin Jidda ba sauki, duk ta rame tayi baki, idan kaganta bazaka ce Jiddar daka sani bace, haryanzu aljanun jikin Zarah basuyi magana ba, sede haukan dasauki, tana samun sauki aduk lokacin da ake mata addu,a amma idan har bakowa agurinta haka zakaga kafarta tana fitar da wani irin ruwa marar kyau, kuma aranar se ansake wani gyaran dan ta kafarta suke cutar da ita, shiyasa har yanzu kafarta kamar sabon ciwo ne.


Hakan yasa Kawu yace ma Alh, dole zeyima wani abokinshi Babban malami ne, kuma yana da sani sosai akan harkar aljanu, Alh, yace to amma abari bayan biki seyazo.


Kasancewar bawani cikin keanciyar hankali ake ba, hakan yasa Jalila bata samu gyara sosai ba, sede duk da haka Falak tana kawo mata wasu abubuwan sha tana sha, Falak takaita gurin saloon akayi mata, takira wata me kunshi tayi mata, duk da ta rame amma tayi kyau sosai, duk wani shiri da za,ayi na Walima wata kawarta yar ajinsu ta mika ma komai Bilkisu, tare da wata Farida, duk ajinsu daya, malamansu da Sameer sune suka shirya komai, kuna anan makarantarsu za,ayi walimar.


Ana gobe daurin aure ranar juma,a kenan wanda kuma aranar da karfe 4 za,ayi walimar, zaune suke adakin Jidda, tana kishingide tana shan kankana, fuskarta har wasu kuraje sun fara fito mata, kadan kadan tana goge kwallar datake fito mata. Falak tace Yaya Jidda dan Allah kidena wannan kukan, babu ranar dazata zo bakiyi kuka ba. Jidda tace Uhm Falak kenan, nikadai nasan menakeji araina, da jikina. Kamata yayi ace hadani akae wannan hidimar bikinta Jalila, amma sbd son zuciya da biyema rudun duniya kalli yanda nadawo, ina nan kwance za,ayi bikin Jalila, wanda gashi de da raina amma banida ikon halartar bikin, wannan kadai ya isheni ishara.


Kalli Ummi, duk yanda taci buri da bikin nan, amma gashinan son zuciya da rudun duniya itama ya kamata ahannu, har garani nasan me akeyi, amma ita batasan meke faruwa ba, kuma hakan bazesa adaga bikin ba. Lallai mun ishi duk wani me hankali zama abun kwatance. Jalila tana kuka tace Yaya Jidda kiyi hkr Allah yana karbar tubar me tuba, insha Allahu zaki kasance daya daga cikinsu.


Baba Mairo da Umman Sameer ce suka shigo sun dawo daga dakin Zarah sunyi mata wanka, Baba Mairo tace Falak kuzo kutafi kishiryata kinga har 3 tayi, kada ayita jiranku kunsan taro za,ayi sosai bekamata ace ku tsaida mutane ba. Kuma idan kingama kisamu guri kizauna kinsan jikinki yayi nauyi, tace to. Kama Jalila tayi wadda take ta kuka, tace muje, Jalila tace tomuje inga Ummi sannan. Baba Mairo tace kuje taganta seku wuce. Kara kallon Jidda tayi, Allah sarki Jidda kifar da kanta saman cinyarta tayi, tana wani irin kuka me ban tausayi, seda tasaka su kuka. Haka Falak tajata suka nufi dakin Zarah.


Kwance take tana bacci, gaba daya tayi bakikkirin fuskarta kamar an shafa mata bakin tukunya, kafarta meciwo takoma siririya tundaga guiwarta har dungulmin da aka yanke, babu kyan gani, gashi duk tarame, kamar ba ita bace me kiba da jiki me kyau, shiru Jalila tayi tana kallonta, tace Allah yabaki lafiya Ummi. Falak ta kalleta, seta tuna Ummanta, lokacin tana cikin rashin lafiya, zuwa tayi ta taba jikin Zarah, taji babu zafi, kai ta girgiza tace ai dasauki ma tunda ita batajin zafin jikinta. Saurin fita tayi sbd kukan daya taho mata. Jalila tagane me Falak take nufi, duk se tausayinta yakamata, tace kingani ko Ummi, mutanen dakika cuta kika maida banzaye yau gashi sune suke maki rana,

.

Yaugashi Falak da kikaso akashe, itace take amatsayin daya kamata ace kece kikemun abinda takemun. Goge idonta tayi tace Allah yasa kina cikin wadanda Allah ze gafarta ma kura kurensu, sede nasan baze yafe maki laifin bayin dakika cuta ba. Saurin fita tayi tajawo kofar tasamu Falak amota suka tafi.


Jalila tayi kyau sosai tasha hijabinta harkasa, haka tazauna, agefenta Falak ce itama tasha hijabinta da katon cikinta, mutane dayawa sun halarci taron, taro yayi taro sosai aka gayyaci mutane dayawa, kasancewar Jalila tanada kokari amakarantar. Bangaren manyan mutane daban, hatta da Mahaifin Saleem seda yazo shida abokananshi sbd suntaho har daurin aure, Saleem da abokananshi suma sun halarci gurin, Sameer kuwa sune manyan malamai, suna ta hidima da mutane, Alh, da Kawunshi da Mal. Garba dasauran abokananshi daya gayyata duk suna zaune acikin rumfa.


Kanshi yadaga yaga irin mutanen dasuka halarcin gurin kawai seyaji kwalla tacika mashi ido, glass dinshi yaciro yasaka, Kawunshi wanda yana kula dashi yace haba Abba, kayi hkr mana kada kabari mutanen dasuke gurin nan su fahimci halin da kake ciki, nasan kana tunanin babu mahaifiyar Jalila agurin nan, da babu ita akwai wani abu daya ragu? Kalli gefen iyaye mata kagani, ga medakina can da sauran yan uwa waye ze iya cewa babu Zarah agurin? Sede wanda yasanta, kuma kowa ai yasan rashin lafiya ko. Alh, yace shikenan kawu nagode.

.

Haka aka fara bude taro da addu,a sannan aka gabatar da manyan baki, aka kira Jalila domin ta karanta wata sura daga cikin Qur'ani amatsayinta na wadda akema walima, da kyar tafito, seda Falak ta anshi nikaf din wata tabata tasa, sbd tundazu take kuka. Haka tafara karatu cikin dadin murya, sede dakaji muryarta kasan muryar kuka ce, tana cikin karatun tafara kuka, seda ta burge mutane dayawa, sbd sun dauka karatun ne da murna suka sata kuka, wadanda suka san halin datake cike ne kawai suka san dalilin kukanta. Shikanshi Alh, seda yatashi bada sanin kowa ba yanufi cikin motarshi yazauna yarika kuka kamar karamin yaro, seda yaji dadin zuciyarshi sannan yafito, dayake bakin glass yasa babu wanda yake ganin idonshi. Yana zama Kawunshi yagane meyayi, shima kanshi tausayinshi yakeji.


Ganin Jalila tana kuka yasa Sameer yaje ya amshi lasifikar yayi mata godiya duk da shima jikinshi yayi sanyi. Saleem kuwa seda yayi yan kwalla, har abokananshi suna janshi. Gaba daya tausayin Jalila da Sonta suke kara ratsashi.


Haka aka kira Alh, yazo yayi jawabi, dauriya kawai yayi yafito, yana magana shima muryarshi tana rawa, ahaka yasamu yagama, sannan aka cigaba da. Wa,azi. Se karfe 6:00 dede aka tashi, tare da mika ma Jalila kyaututtuka, haka kuma tasamu kyautar kudi daga gurin bakin dasukazo, aka rarraba kayan ciye ciye kowa ya watse.


Adaran ranar su Baba Mairo sukaje suka bada duk wani abinda za,a girka gobe, ita da Hajiya Fatima matar kawaun Alh, dayake anan gidan yace su sauka, sbd itama tasan komai daya faru, ko kayan gara nasiye suka siya sbd lokaci yakure ba,ayi ba, kuma sunje sunyi mata jerenta, dan dama ansayi kayan dakin, sauran abinda ba,a siya ba, na kitchen suka bari se gobe da safe suje su siyo.


Haka suka tsara komai, da sauran yan uwan Alh, dasukazo, abangaran Zarah kam babu wanda yazo se yan uwan Babanta, shima cewa sukayi sbd Jalila da Alh, sukazo dan ita bata yarda suba, amma ko asibitin babu wanda yaleka. Gida kam yacika ba laifi mutane sun taru.


Adaren ranar jikin Jidda yayi tsanani cikin dare tarika suma, haka Umman Sameer da Baba Mairo suke tsaye akanta da sauran nurse, ganin jikin yaki sauki yasa wata nurse tayi ma Dr, waya acikin daren.


.

Se da asuba suka samu jikinta ya dedeta, haka aka samata oxygen har seda numfashinta yadawo dede, duk abinda akeyi su Jalila basu sani ba, dan Baba Mairo tace kada afada masu tunda dare yayi.


Da misalin karfe 6 nasafe Alh, ya iso asibitin anan yakejin abinda yafaru, cike da damuwa yace amma Baba Mairo ai da kunsanar dani, ko dare yayi ai zan iya zuwa, tace hakane Alh, yace sannunku Allah yasaka maku da alkhairinsa, Baba Mairo tace Ameen ai ba komai, duk munzama daya.


Fita yayi yadubo jikin Zarah, tana kwance kamar gawa sbd allurar bacci ake mata idan dare yayi dan kada ta farka tajima kanta ciwo, haryanzu bata farka ba, tausayinta yakara kamashi, yace kaiconki Zarah, kalli yanda kika jama kanki bala,i ana bikin diyarki amma kina kwance cikin hauka, juyawa yayi yafita, yabiya gurin Dr, anan yake kara mashi bayani akan ciwon Jidda. Alh, yace Dr, kode afita da ita waje, ciwonta yana bani tsoro?.


Dr, yace E to hakan ma yana da kyau, amma gsky matsalar Jidda bawani abu bane kawai cutar jikinta ce taci karfin jikinta, kuma da karfi tasamu nasarar karya garkuwar jikinta bawai dan takai lokacin ba, da farko tayi sakaci batazo asibiti dawuri ba, na biyu kuma tafara shan magani tabari. Na ukku kuma yanzu kwata kwata maganin baya yimata amfani ajikinta, sbd kotasha amayar dashi takeyi.

.

Karin ruwan da ake samata ne, kadai yake amfani ajikinta, kuma babbar matsalar bata cin abinci sosai, kotaci ma baya zama. Wadannan sune matsalar Jidda, kuma duk inda kuka kaita, basuda abinda zasu mata. Alh, yace shikenan Dr, nagode. Dr, yace se hkr Alh, Allah ya jarabceka da lalura, amma idan kayi hkr wata rana komai zewuce. Karfe nawa ne daurin auren? Karfe 2 ne, toshikenan Allah ya kaimu. Sallam yayi mashi yafita.


Da misalin karfe 2 dede na rana dubban mutane suka sheda daurin auran Jalila da Saleem, wanda akayi abisa sadaki dubu 50. Adede lokacin su Jalila da Falak suna asibiti, dan Jalila cewa tayi bazata zauna agida ba, tasan anjima babu wanda zebarta tazo asibiti, zaune take agaban Zarah, se kuka takeyi. Zarah kuwa tana kallonta tana dariya tana dariya, Falak tana gefe ta kalli Jalila tace haba Jalila kukan ya isa haka, Jalila tace dole inyi kuka Falak, ace ayau ana daurin aure na, amma Ummina da Yayata suna kwance agadon asibiti, kuma su duka babu me ciwon daza,a fada ta dadi, dukansu su suka jama kansu, yakike so inyi? Kinaji jiya agabanmu wasu suke gulmar Yaya da Ummi, sbd kome kake boyewa dole mutane su sani.


Wlh yafi acema banda Uwa za,ayi bikina hakan zefi mani insan cewar bata raye bazan damu da rashin wanda zemun nasiha ba, amma gata araye kuma cikin halin hauka, wanda zuwa yanzu mutane dayawa sunsan cewar ta hauka ce, kuma qai qayine yakoma kan mashekiya, yakike tunani idan dangin mijina sukaji haka? Nide wlh Ummin kin..... Falak tayi saurin rufe mata baki tace haba Jalila da iliminki, da komai, kinsan fa kome Uwa tazama ba,a canza ta ko? Dan haka inaso kitoshe kunnuwanki da duk wata magana dazakiji daga gurin dangin mijinki, kuma duk wanda yatareki da maganar kiyi banza ki kyaleshi shine kawai abinda ze kwaceki daga gurinsu.

.

Baba Mairo ce tashigo, cak ta tsaya ganin haryanzu basu tafi ba, tace mezan gani haka Falak? Kinsan fa tundazu aka daura auren yakamata ace kuna gida yanzu tasamu takara wanka sannan taci abinci. Falak tace wlh abinda nake fada mata kenan, tonaji kema ai nace kidena yawo dayawa ko, kinsan fa kinshiga watan haihuwarki, dan likita yace zaki iya kara kwanaki ba lallai bane ace kinsan lokacin, kuma wahala ma tanasa mutum ya haihu babu shiri, nide kutashi kutafi.


Jalila tace Baba Mairo yajikin Yaya Jiddan, munje dakin akace antafi da ita za,ayi mata test. A,a jikinta dasauki nabaro Halima agurin suna can gaba yanzu zasu dawo, Falak tace muje driver yana jiranmu.


Fita sukayi suka nufi dakin da aka kai Jidda test, atare suka jero, tana bisa wheel chair ana turata, wasu mata da miji suka wuce su mijin yana dauke da yaronshi, harsun wuce Jidda tace ma Jalila dan kwalama wancan kira kice Al,amin. Jalila tace kinsanshi ne? Tace inaji kamar shine, amma kirashi mugani. Jalila tace Al,amin. Cak ya tsaya atare suka juyo da matarshi, dawowa sukayi da baya, dan danan matar ta bata fuska.

Al,amin yace sannunku yamejiki? Jalila tace dasauki, kuma itace ma tace amaka magana. Kallon Jidda yayi cike da tausayi yace sannu baiwar Allah yajikin? Kuka Jidda tasa, kowa ya tsaya yana kallonta, Matarshi tace dan Allah honey muje kasanfa akwai inda zamu biya ko.


Jidda tace Al,amin, Ameerah, cike da mamaki matar takara kallonta tace ni kuma? A ina kikasanni? Goge kwallan idonta tayi tace lallai duniya kenan, baku ganeni ba? Jidda ce. Gaba dayansu suka zaro ido suka hada baki sukace Jidda Abba Bala? Ta daga kai tace kwarai kuwa. Umman Sameer tace bayin Allah mun tsaya ahanya kumuje dakinta gashi can sekuyi maganar acan.


Al,amin da Ameerah kuka sosai sukeyi dasuka gama jin labarin da Jidda tabasu, tace na cuci kaina, Ameerah kece silar shigata wannan harakar, Al,amin kaine mutumi na farko daka fara sanina 'ya mace amma yau gashi kudayake kunada rabon tsira Allah yatema keku kunshiryu, abun mamaki kuma harkunyi aure hada rabo atsakanin ku.

.

Ameerah tagoge idonta tace tabbas Jidda na cuceki, sbd nice silar shigarki wannan rayuwar,  sede wlh tun bayan damukayi fada dake akan nazo inaso inmaidake ruwa lokacin da kika tuba, mukayi fada tundaga lokacin mukabar unguwar da muke, kuma nasake waya shiyasa bankara nemanki ba, dan naga kinbar harkar danakeyi, haka nacigaba da rayuwar bariki.


Dalilin shiryuwata shine lokacin da Babana yarasu, tundaga ranar naji tsoron Allah, sbd agabana yarasu, nashiga firgici, dama akullum addu,ar Mamana Allah ya shiryeni, segashi Allah ya amshi addu,arta, nashiga damuwa tunbayan mutuwarshi nakara canza layi, duk wasu kawayena seda narabu dasu, sbd malamin dana samu nafada mashi irin rayuwar danayi kuma nace mashi inason intuba, yace abu nafarko dazan farayi shine inrabu da duk wasu kawayena.


Sbd yace mun idan har mutum yana aikata alfasha, kuma yatuba, matukar berabu da abokanan shiba, tamkar be tuba bane, dan wata rana zasu iya dawo dashi ruwa, alokacin hargidanku nazo sede bansamekiba, Umminku tace mun kina zariya, na amshi no ki amma nakiraki bata shiga, alokacin naso mukulla sabon kawance tunda nasan kin tuba.

.

Tundaga ranar nikuma bankara tunanin zuwa gidanku ba, haka nashiga islamiyya wannan malamin yatsaya mun sosai nayi karatu me yawa, wata rana nadawo daga makaranta, nahadu dawani dan unguwarmu tare da wani, na tsaya mugaisa kawai senaga ashe Al,amin ne, anan muka gaisa shima yayi mamakin ganina haka, shine ya amshi no ta yace zezo muyi magana, dan bayason muyi agaban abokinshi.


Naji matukar tausayinki lokacin dayabani labarinki, alokacin yayi kuka shima, dan yacemun shine sanadiyar komawarki ruwa, kuma ya kaiki inda kika hadu da matsala, haryake cemun yaso kuyi aure amma kika kiya, alokacin daya temakeki kuma yace yana zargin kina dauke da cuta, yaso kije kiyi gwaji idan baki da ita kuyi aure amma baki yarda ba.


Ganin nima nashiryu, shima yafadamun irin kallar tubar dayayi kuma yace idan zan amince ze aure ni, dama alokacin mijin aure nake nema ni kuma na amince mashi, yanzu haka yaronmu daya Sultan, kuma haryanzu banwuce karatu ba, dan gani nake gara nayi zamana nayima mijina biyayya yafi dan tsoron yan matan Jami'a nakeyi, keni zan iya cemaki kawata daya yanzu ma kwafciyata, itama tadan girmeni.


Al,amin kuwa kasa cewa komai yayi sbd kuka yakeyi tamkar mace, kowa yakasa lallashin shi. Jidda ma kukan takeyi, da kyar tayi shiru tace bakomai Ameerah wlh nayafe maku, duk da kune silar shigata wannan rayuwar amma babban laifin yana gurina da gurin Ummin mu, mekikace yanzu? Mamanki kullum addu,arta Allah ya shiryeki, toni banda wanda yakemun addu,a se kanwata. Kuma kinsan yanda addu,ar Uwa takeda tasiri akan 'ya'yanta, yakike gani idan da ace Ummina ce takemun addu,ar da Jalila takemun?.


.

Mutum yasamu Uwa tagari ma babban abin alfahari ne, Baban nawa daya kamata shima yatuna dani yamun addu,a bata bari yasan halin danake cikiba, bare yamun addu,a. Asalima tasashi yamanta dani acikin yaranshi.


Wannan Uwa tagari ce? Uhm, nikam ahaka nazo duniyar banci ribar komai ba, kuma gashi zanbarta babu wata riba. Al,amin bakayi laifi ba, dan ka auri Ameerah, laifi nane, fatana kobayan raina kada kumanta dani kurika sakani cikin addu,arku kuma duk wanda zebani sadaka, inarokon daya aje bayan raina agina mun koda rijiyace wadda mutane zasu amfana da ita, koda hakan nasan da kudina nabar abinda wasu zasu amfana dashi, kuma Allah zekai ladar akabarina, amma tabbas ban tara komai na lada ba, wanda zanyi guziri dashi natafiya,,,,,,, kuka ne yaci karfinta.


Shiru dakin yayi sbd gaba daya dakin kowa kuka yakeyi. Al,amin da kyar yace Jidda kiyafemun kiyafemun dan Allah, tashi yayi yadauki Sulta ya aje masu kudi wanda besan yawan suba yafita sbd gaba daya zuciyarshi tayi mashi zafi, Ameerah ta mike tana kuka tamika ma Jidda hannu sukayi musabaha, itama tafita tana kuka, akofar fita suka ga mutum tsaye ya juya baya, da alama shima kuka yakeyi.


Alh, ne yazo tafiya dasu Jalila dan Baba Mairo tace mashi suna nan, tunda yazo zeshiga yaji firarsu kawai ya tsaya akofar dakin. Tausayin Jidda yayi mashi yawa, haka yashiga dakin daka ganshi kasan yasha kuka, bakin glass ne a idonshi amma duk da haka afuskarshi ana ganewa.


Kwance ya iske Jidda tana ta kuka, yace Jalila kumuje kunga har la,asar tayi, Falak kuwuce muje. Jalila ta matsa tarike Jidda sosai, tana kuka, tace Yaya Jidda kiyafemun, zantafi, amma gobe zamuzo, Allah yabaki lfiya. Jidda tace bakitaba yimun komai ba Jalila, nice yakamata inrokeki gafara, na cutar dake, kiyafemun, Falak kema haka dan Allah kiyafemun. Falak tace nadade dayafe maki, Allah yabaki lfiya.


Da kyar aka cire Jalila daga jikin Jidda sunata kukan saurin fita Alh, yayi danshima kukan yakeyi.Jidda kwanciya tayi tana kukan zuci jitake dama Allah yadau ranta yanzu.

.

Da misalin karfe 7 aka gama shirya amarya, tayi kyau, sede fuskarta ko kwalli bata bari anshafa mata ba, bamaze zauna ba ko anshafa, sbd hawayen dasuke zarya afuskarta, afalon Alh, aka kaita suyi sallama, zaune suke da Mal. Garba, da Kawunshi, anan kowa yayi mata nasiha sannan akace Alh, yayi mata nasiha, kasa cewa komai yayi, sede yace Allah yabaki hkr Jalila, saurin tashi yayi yashige daki sbd kuka, daya taho mashi, itama kukan takeyi, haka matar Kawun Alh, ta dagata suka wuce, Falak kuwa dama tundazu Sameer yadauketa yakaita gidan amaryar dan yace baya so tasha wahala, manyan mata 2 ne suka sakata tsakiya, da yan uwan Kakanta, se dangin Dadynsu.


Sauran mutane suka biyo bayansu. Gidanta yayi kyau sosai, haka suka shiga da ita, bayan sunmikata ga dangin mijinta akayi abubuwan al,ada sannan Sameer yashiga yace sufito amaidasu, dan ance manya bazasu kwana ba, Falak ma Sameer ne yace ta kwana sbd Jalila. Da kyar Falak tasata takara yin wanka sbd gidan kowa ya tafi daga Falak se su Bilkisu da Farida, su 3 ne zasu kwana, lallashinta sukayi taci abinci. Suna zaune Jalila tace wlh Falak gabana faduwa yakeyi, Falak tace badole ba, tunda gobe kamar yanzu kina gaban angonki. Tace ke wlh kincika fassara, nikwai inaji ajikina kamar wani ya..... bata karasa fadi ba, Saleem yayi sallama yashigo shida Sameer, daka kalli idanunsu kasan akwai abinda yafaru. Zunbur Jalila tamike tace Ummi ko? Yaya Jidda ce? Kufadamun waye ya mutu acikinsu? Kamota Saleem yayi yace babu wanda ya mutu kawai jikin Yaya Jidda ne yatashi. Murmushi tayi tace wlh banyarda ba, shikenan kawai, nashiga 3 yazakimun haka Yaya Jidda kinsan banda kowa seke, meyasa zakimun haka,,,, kuka tasa masu, Falak taja Sameer tace meya faru, Yaya Jidda tarasu ko? Share hawayen idonshi yayi yadaga mata kai,


Wata irin zufa taji ta taso mata, mararta tawani murda, saurin dafe cikinta tayi ganin halin data shiga yasa Sameer yayi saurin kamata, yace Saleem muje inajin Falak haihuwa zatayi, kadauko Jalila kawai dasu Bilkisu kasa megadi yakulle gidan bari intafi da ita asibiti. Juyawar da Saleem zeyi yayi ma Jalila magana yaganta kwance akasa ta sume.


Read More

Share this

WhatsApp
Newer Posts Older Posts Home

Popular Posts

  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 11 to 20
    Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima.     Casuke A...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 31 to 40
    Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gado...
  • RAINA KAMA Book 1 Page 1 to 10
    RAINA KAMA......!!♦_*                _{Kaga gayya}_          *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!._* 👉🏻1⃣      *Matsanan ...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 21 to 30
    Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”.         Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, murya...
  • BARIKI AUREN SOJA Page 51 to 60
    Motocine guda shida aka ajiye musu sababbi dal suna sheki ta tsakiyar tasha Adon balloon kana gani Kasan motar AMARYA ce ta fito tareda su ...
  • KASUWANCI NA Page 61 to 70
    Ameer kasa jurewa yayi gaba daya jikinsa ya fara rawa,tunawa Meenat tayi ba Muharraminta bane sai ta dan matsa kamar zata fada kasa ta wayan...
  • KASUWANCI NA Page 31 to 40
       A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, d...
  • UMMU AYMANA Part 6
      *UMMU AYMANA PART 6* Suna isa Asibitin likitoci suka rufu akanta,wanda da taimakon Allah bata jimaba ta farfaɗo se kuka takeyi,prince kasa...
  • MIWASMITI Page 31 to 40
    Kuka ta Kuma saki gamida kamo hannushi ta matse a tsakiyar qirjinta Dan jin wani irin suka da yake mata Ga jiri da takeji gaba daya bata gan...
  • KWARATA Part 46,47,48,49,50
    🅿 ------ 46           Tsare Mamy nayi da ido na kasa magana duk saida ta gama buɗemin komai ta ƙare da cewa harma ta gayyato shi zaizo kats...

Categories

  • 'YA'YA DA KUDI 1-END (8)
  • 'YA'YA MATA 1-END (9)
  • 'YAR BOKO 1-END (6)
  • 'YAR FULANI 1-END (14)
  • 'YAR GIDAN TSOHUWA 1-END (6)
  • 'YAR JAMI'A (9)
  • 'YAR MAFIYA 1-END (6)
  • 'YAR TALAKAWA 1-END (7)
  • AGOLA 1-END (17)
  • AKIDATA BOOK 2 Page 45 -End (11)
  • ANAL 1-END (12)
  • ANTIN YARA 1-END (6)
  • AUREN JARI 1-END (9)
  • BAKAR MACE 1-END (3)
  • BARIKI AUREN SOJA 1-End (8)
  • BINTU 1-END (7)
  • CIN AMANA KO FANSA 1-END (10)
  • CIWON IDANUNA 1-END (7)
  • CIWON IDANUNA AUDIO (2)
  • DAGA TAIMAKO 1-END (5)
  • DAKON SO 1-END (4)
  • DAMA TA BIYU 1-END (13)
  • DR BOBBY 1-END (11)
  • DUBU CIKAR MAI CARBI 1-END (7)
  • FULANI 1-END (11)
  • GURBIN IDO 1-END (1)
  • HADIN ALLAH 1-END (8)
  • HIBBAH 1-END (4)
  • INA ZAN GANSHI 1-END (7)
  • INAYA 1-END (9)
  • JIDDARTIL KHAIR 1-End (1)
  • JIHADI 1-END (10)
  • JUWAIRIYYA 1-END (7)
  • JUYAYI PAGE 1-END (6)
  • KASUWANCI NA Page 1-End (1)
  • MACIJINE SHI 1-END (1)
  • MAH NOOR 1-END (5)
  • MAIMOON 1-END (10)
  • MAKARANTAR KWANA 1-END (5)
  • MAKAUNIYAR KADDARA 1-END (10)
  • MATAR ALI 1-END (10)
  • MIWASMITI 1-END (8)
  • MOTAR KWADAYI 1-END (4)
  • NAMIJI BAYA KADAN 1-END (16)
  • NI AYS NAKE SO 1-END (16)
  • RAINA KAMA 1-END (1)
  • RAYUWATA 1-END (6)
  • SHIMFIDAR MIJINA 1-END (3)
  • SONE AJALINA 1-END (5)
  • SURBAJO 1-END (14)
  • TUDUN DAFAWA 1-END (4)
  • TUZURU 1-END (6)
  • UMAR KO FARUUQ 1-END (5)
  • UMMU AYMANA 1-END (8)
  • UMURNIN IYAYE 1-END (7)
  • WAMINAL HOOB 1-END (9)
  • YAN MATAN ZAMANI 1-END (6)
  • ZAYN MALIK 1-END (10)
  • ZUCIYA KOWA DA IRIN TASA 1 (10)
  • ZUMA SAI DA WUTA PAGE 1-END (7)

Social Plugin

  • facebook
  • twitter
  • instagram
  • youtube

Hausa novels 2023

Search This Blog

Powered by Blogger.

Blog Archive

  • July 2023 (7)
  • June 2023 (65)
  • April 2023 (33)
  • March 2023 (132)
  • January 2020 (10)
  • December 2017 (62)
  • November 2017 (33)
  • October 2017 (38)
  • September 2017 (39)
  • August 2017 (75)

Report Abuse

  • Home

Total Pageviews

Copyright © 2023 To Hausa novels 2023 | Powered By WwW.aysnovel.com.ng
Design By Aysha Adam | Theme By WwW.aysnovel.com.ng | Distributed By Aysha Adam