Hausa novels 2023

  • Home
  • Ciwon Idanuna
    • Internet
    • Market
    • Stock
  • Agola
    • Dvd
    • Games
    • Software
      • Office
  • Mijin Biza
    • Child Category 1
      • Sub Child Category 1
      • Sub Child Category 2
      • Sub Child Category 3
    • Child Category 2
    • Child Category 3
    • Child Category 4
  • Kwarata
  • Health
    • Childcare
    • Doctors
  • Inda Ranka

Thursday, August 31, 2017

'YAR MAFIYA Part 3

 August 31, 2017     'YAR MAFIYA 1-END     No comments   


Haka Yasiraht ta cigaba da rayuwa tsakanin mafarki da zahiri, a haka suka gama jarrabawar gwajin shiga aji shida sukai hutu suka koma gida.Komawarta gida babu abinda ya ragu tsak'aninta dasu Samar kullum iyayanta na ganinta amma da zarar dare yayi Samar kan zaagayo ya d'auketa.

Tsakanita da Yasar kuwa babu jituwa ko kad'an,shi yana mata kallon azalluma ita kuma kallon ya takura mata.Hakan ya jawo sab'anin ra'ayi sossai tsakaninsu ko gun cin abinci sun dingi fad'a kenan tamkar mage da kare a haka taci hutunta saura sati biyu ta koma wani mummunan lamari ya auku gareta wanda ya tsaya mata arai.

Kwance suke kan makeken gadon da yake mallakinta.Tun dawowarta tare suke kwana da Yasmin, misalin k'arfe biyu na dare Samar ya bayyana a gefan gadon yana murmushi.Gabanta ya tsananta fad'uwa ta aro juriya ta yafa ta kalleshi.Murmushu sukai wa juna cike da tsantsar kulawa.Bai wani d'auki lokaci ba ya dubeta"Yasiraht zuwa nai in gaya miki muna buk'atar jinin Yasmin nan da gobe kiyi tunani".A fusace ta mik'e "ban yadda ba Samar" "ba damuwata bace yardarki ko akasinta".Fu! Ya bar wajan yana huci.

Washegari haka ta yini sukuku da'ita babu abinda take asassawa kanta, Hajiya Nafisa ta lura da yanayinta tai ta janta a jiki amma bata gaya mata damuwarta ba.Yasar ne ya daukesu zuwa shooping bayan magarba suka nufi hanyar zoo road.Cikin nutsuwa yake tuk'in har suka k'arasa, kwata-kwata hankalinsu nakan siyayyar da suke yi sai jin k'arar Yasmin sukai ta fad'i ta kakkafe jini na bin kofiffin hancinta. Karaf ta hangi wulgawar Najwa ta bacewa ganinta, wata giggitafiyar kara ta saki tai kan Yasmin bata ko numfashi take Yasiraht ta zube sumammiya.

Ku biyo mu
[8/8, 8:44 PM] Sanah S Isma'il Matazu:

Yasar yayo kansu cikin rud'ewa ya d'aga Yasmin ganin yanda jini ke zuba wasu mutane ne suka taimaka masa suka d'aukesu sukai mota cikin rudu ya shiga ya ja motar suka nufi T.H ko da sukaje emergency aka shiga da su likitoci sun dad'e akansu kafin babban su ya fito fiskansa ba alamar murmushi, Yasar ya taso da sauri yazo gun Likitan ya ce"Likita ya jikin su jinin da ke zuban ya tsaya?". Cikin sanyin jiki Likita ya dafa Yasar ya ce"Babban ta farfad'o yanzu haka". Yasar ya ce"Alhamdulilah!". Likita ya sake duban Yasar ya ce"kai musulmi ne kuma ko da yaushe ana so musulmi ya kasance mai hakuri da juriya da amsan kaddaransa, sannan Ubangiji yana mana kyauta wanda zamu saba mu shaku da kyautarsa rana d'aya shi da yafi muson abunsa sai ya d'auke".

Likita ya nisa ya cigaba da ce wa"inason kayi hakuri Allah yayi rasuwa ma k'araman...". Take bakin Yasar yasoma b'ari ji yayi duk wani hanyan tafiyan jininsa ya tsaya da aiki kujeran da ke gefen sa ya zauna tare da furta"Innalilahi wa inna ilaihi raji'un ya Allah ka jik'an Yasmin". Sai da ya d'au mintuna likita na kwantar masa da hankali kafin ya ciro waya ya sanar da su Abba suna Asibiti yazo yanzu.

Jikin Yasar a sanyaye ya ce"Doctor zan iya shiga na gansu?". Doctor ya ce"eh ba matsala zaka iya shiga". Da kyar Yasar ya iya d'aga k'afarsa ya shiga d'akin gun Yasmin ya nufa ya sanya kunnesa a k'irjinta yaji ba alamar numfashi ya d'aga hannuta ma haka ya saki jikinsa a sanyaye yana furta"Innalilahi wa inna ilaihi raji'un". Ya juya gadon da Yasiraht ke kwance nan ya ga idonta  a rufe amma tana wasu surutu a hankali wanda sai ka kai kunneka kusa da bakinta ka iya jin mai take fad'a.

Da sauri ya isa gadon ya sunkuya dai-dai bakinta ya ji tana fad'i " bazan tab'a yarda ba ku bada jinin Yasmin d'ina, Najwa kece jagoran d'auko ta har ki yanka ta da hannu ki to tabbas sai na d'au fansa da ga yau ba mutunci a cikin k'ungiya yanda kuka bada jinin Yasmin ma dodon tsafi duk wanda yake da hannu a cikin abun sai yayi na dama sai na fitini kowa a k'ungiyan nan wannan alkawari na d'auka ma.

Abba ne suka shigo Hajiya Nafisatu sai kuka takeyi a asai likita ya musu bayani a waje suna shigowa Yasar ya d'ago da sauri ganin su Abba ne ya niyyan fad'a musu Yasiraht ce tayi sanadin mutuwar Yasmin take bakinsa ya rik'e ya kasa furta komai sai b'arin da bakin ke yi.

Bakinsa ya cigaba da rawa tamkar mazari, tilas ya hakura zuciyarsa na kuna tamkar garwashi a haka aka dauki Yasmin zuwa gida akai mata sallah zuwa makwancinta. Yasiraht kwananta uku a asibiti duk ta kade ta rame tamkar mai cutar wata da watanni.A haka suka koma makaranta zuciyarta cike da kudurin daukar ransa.

Tun komawarsu take neman hanyar fanshewa,kwatsam ranan tana zaune ta nufi kafteriya cin abinci ta tsinkayi muryar Najwa tana bawa Shany labarin daya faranta zuciyarta.
"Walahi shany inason kakus,dole in je jos yau cikin dare in ga lafiyarta, ita kad'ai ta ragemun bani da kowa"."Gaskiya ya dace ki dubota Najwa ko zan rakaki? " "a'a ta fada cikin ci da zuci. Cikin sauri Yasiraht ta yi baya tana murmushin mugunta zuciyarta wasai. Tun daga lokacin take bibbiyar motsin Najwa har dare ya tsala misalin daya taga fitowar wata katuwar tsuntsuwa daga hostel dinsu take tai girgiza ta rikida zuwa suffar tsuntsuwar sama ta lula tabi Najwa.

Cikin tsananin gudu suke keta gajimare,tsafi gaskiyar maishi cikin awa daya zuka isa garin tafiyar awa hudu a awa guda lallai sai tsafin.Yasiraht ta samu waje ta labe a tsakar gidan tana hangen Najwa ta koma ainihin suffarta ta shiga wani kayatacan fallo ta ratsa zuwa bedroom gidan ya kawatu komai akwai can ta hangi Najwa na neman kurewa ganinta saita rikida zuwa suffar wata mage data hanga a harabar gidan tai wuf ta fada dakin baccin ta window ta riga Najwa shiga tai kwance jikin tsohuwar tai linkim.

Da hanzari Najwa ta shiga jin motsi sai dai bata ga komai ba idanunta sukai wani haske walai tauuuu!  Tai jim tana karewa magen kallo ta saki ajiyar zuciya ta shafi kafaffun tsohuawar.
Mikewa Dattijuwar tayi, tana mutsittsika ido tai murmushi"yar Momah kece yanzu a daran nan,ban hanaki tafiyar dare ba? ""Momah so nake in ganki shiyasa nazo amma da safe zan wuce gida koma ki kwanta nima ruwa zan watsa".Komawa tai ta kwanta tace"Pussy na nan da halin ta nanike jikinki?" bata tanka ba ta kwanta Najwa tai waje tana fita harabar fallon gabanta ya fadi, ta dake kawai karaf idonta yakai kan Pussy kwance tana baccinta da yayanta uku.Cikin tashin hankali gabanta ya doka das!  Tai sashin Momah da gudu, turus ta tsaya sakammakon ganin Yasiraht da wuka tana digar da jini ta kyalkkyale da dariya tace "fansa Najwa jinin Yasmin 'yantace ne".

Sama da kasa ta nemi Yasiraht ta rasa,durkushewa tayi tana gunjin kuka kamar mahaukaciya ta mike tai girgiza tana wasu surutai.A firgice ta bayyana tsakiyar dakinsu tana rangaji Shany ta mike tana jijjigata Emeka na gefe tana dariya a ranta tace"ai dama na fada Najwa sai ta fitineku" lallabawa tai ta fice daga dakin ta nufi mahadarsu riskar Najwa tayi tana numfashi ta dafa kafadarta.Bata juyoba itama bata damu ba"sannunki jaruma, ga wannan soban ki saka ko Samar hai isa ja dake ba balle Najwa asalin zoban na kakana ne".Cikin sauri ta warci zoban tasaka wata kara Emeka ta saki Yasiraht na juyawa taga Shany ta dabamata wukar tsafi ta fadi mataciyya "karshan maci amana kenan" Shany ta furta.
Cikin salon tsafi da sihiri Yasiraht tayi gir-giza ta dawo wani irin hallita kamar kada ta tayi kan Shany gadan-gadan, Shany ta ciro sanda tsafinta ta nuna kadar amma ina sai sandan da ya narke ya koma ruwan wuta ya zube a k'asa Yasiraht ta fashe da wani matsanacin dariya bakin ta yana fitar da aman wuta sai hayaki yakeyi ta ce“kee Shany ai kun makara don yanzu sai kun raina kanku sai kunyi nadaman jawoni cikin ku do  zan zame muku k'adangare bakin tulu hahahaha…".

Ta kece da dariya sai da tayi mai isarta ta tun k'aro Shany tana fesa wuta a bakinta Shany ta soma ja da baya Yasirah ta yi wasu surkule ta ke wajan yasoma juyawa Shany tasoma ihu, Yasiraht ta na isowa ta fara fesa mata wuta Shany na ihu sai da ta bata wahala tukun ta kece da dariya ta ce“Shany ba zan kashe ki yanzu ba sai na baki d'an lokaci ki kuma kai ma Najwa labari in har ta kuskura tashiga gonana to sai wata ba ita ba".

Yasiraht na gama fad'an haka ta b'ace bat Shany jiki ba kwari ga shi duk taji ciwo zobenta ta murza take itama ta b'ace sai a gidansu Najwa ta bayyana.

Najwa duk tayi kuka har ta gode ma Allah masu aikin gidan ta kira ta shaida musu mutuwar kakanta a dare aka gyarata aka mata wanka washe gari da safe aka mata sallaha aka kai ta makwancinta Najwa duk ta dawo wani iri ta na tunanin kalan fansan da zata d'auka Shany ta bayyana a hankali ta taka har zuwa kusa da Najwa ta dafata nan ta soma bata hak'uri ta kuma shai da mata abunda ya faru wani gwauro numfashi ta sauk'e a fili Najwa ta furta “tabbas Yasirah ta mana nisa amma ko ta halin k'ak'a sai na rama sai na d'au fansa. A haka akayi kwana bakwai tukun Najwa suka soma shirin komawa makaranta.

Yasirah tana b'acewa bata bayya na ko ina ba sai cikin dajin makarantansu tana dariya nasara wai ita ke da wannan zobe da matsafa da dama duke nimansa sai da ta sai ta kanta tukun ta koma cikin hostel.

Najwa ko da ta dawo tana bibiyan Yasirah amma a b'oye don yanzu Yasirah tsoro take bata ko a gun mitin Samar yanzu yana d'an shakkar Yasirah don yanda take da zoben hannuta.

A haka su Yasirah da Najwa suka fara jarabawansu ta gama makarantar gaba da primary yanzu Yasirah ta samu 'yanci gashi duk ranan mitin sai ta kawo musu tun d'aya ko biyu an shayar da jininsa.

Kwanci tashi suka gama zana jarrabarwarsu masha Allahu komai lafiya aka sallamesu suka koma gidajansu zaman jiran sakammako.
Tsakanin Najwa da Yasiraht kuwa abun yakai intaha domin ta zame musu karfan kafa, tun dawowarta gida samari kemata tururuwar zuwa amma babu wanda take saurara sai Samar shi kadai kawai ta bawa gurbi a zuciyarta.Kwatsam tai karo da soyayyar Muhseen dan aminiyar mahaifiyarta, lokaci daya ya kwanta mata a zuciyarta nan da nan suka amincewa juna ta tattara Samar ta watsar hakan yai bala'in kona ran Samar ya rasa hanyar da zaibi dan kauda Yasiraht ganin babu dama sai ya soma bibbiyar Muhseen.....

Muhseen da daya ne tilo tsoka guda a miya ga Alhaji Lawali mai akwai, asalin mahaifinsa bafulatanin garin Kurfi ne mamansa balarabiyar Egypt hakan yasa Muhseen ya dauko kyau gaba da baya kyakkyane na gaban kwatance.Tun tasowarsa baisan kwaba ba balle harara sangartacan yarone kaf karatunsa a waje yayi hakan yasa ya budi ido da harka da Mata over.Ko kadan mahaifansa basa son laifinsa, yasha yiwa yaran jama a cikkuna da fyade.Tunda Samar ya gama gano waye Muhseen ya cika da farin ciki domin ya samu hanyar gumawa Yasiraht a sadaka.Hanya ta farko daya soma bi neman shiri da Najwa nan da nan suka koma kamar da sannan ya bijiro da bukatarsa dake tayi shirin fansa babu jinkirtawa ta amsa bukatarsa nan da nan ta soma shirin fuskantar matsalar.
Ranar Asabar da yammaci Muhseen ya fito daga Shanawa club, harya gota tarin wasu gun-gun matasan yan Mata ya hangi Najwa a gefe tana taunar cingum daga ganinta babu musu ya tabbatar yan good evening ne in kiya yai mata sarai ta gani sun hada ido ta kanne ta cigaba da hidimar gabanta.Bai yi kasa a guiwa ba ya karasa da fari ta kalleshi ta watsar, daga bisani tabi yarima akasha kida basu wani jimaba ya ribaceta yajata cikin club din ya kama mata daki.

Tsayin kwanaki uku suna tare, Najwa na hillatasa ko kiran Yasiraht bata bashi damar yi ranar kwana na uku ne ta samu suka fita yawo tare, cikin ikon Allah sukaiwa Sahad tsinke anan sukai kici6us da Yasiraht,Najwa ta kalleta ta watsar Muhseen kuwa ko kallonta baiba a haka suka gama siyayyarsu suka fita suna tayar da mota da gudu taiwa motarta key wadda ta aro wajan Yasar ta rufa musu baya.

Tunda Najwa ta hangi tahowar Yasiraht taiwa Muhseen wayau ta amshi tukin, tuki suke na fitar hankali ko gabansu basu duba a haka sukaiwa cikin gari nisa.Najwa ta saki murmushi ganin tarkonta ya kama kurciya.Cikin rashin zato tai ribos motarta tayo baya take motar Yasiraht ta wuntsula ta kife ta kama hayaki bata hakura ba tasake turata tai gaba ta fada rami ta kama da wuta.Tai juyi taja motar  tana kallon Muhseen tana murmushi wanda yakasa hanata kudurinta.Sunyi tafiya mai nisa sun shigo gari ta shammaci Muhseen ta nufi wata katuwar mota cikin hanzari ta danna zobanta ta bace take motar ta murkushe Ammar sai gawa.Tana daga gefe tana kallon mutane kowa na budurunsa, nan da nan tabar wajan.Batai nisaba taji jikinta na shock, tsoro ya shigeta tuni ta bayyana wajan motar Yasiraht.

Gabanta ya tsananta faduwa lokacin da tai arba da Samar,idonsa jajjur yana huci kamun tai wani yunkuri ya kaimata cafka ya dinga azabtar da ita tana ihu, ihuntane ya farkar da Yasiraht daga dogon suman da tayi.

Murmushi ta saki lokacin da tai arba da Najwa nacin azaba wajan Samar kafin su farga ta bace bat, wani hadiminsu tasa ya dauko mata motarta zuwa kofar gida da dingishi ta shiga gidan, nan ta riski tashin hankali labarin mutuwar Muhsun.Kara ta saki ta zube a sume.
Sanah
Rash

Kara ta saki ta zube a gun sumamiya da sauri Yasar sukayi kanta suka zuba mata ruwa ta farfad'o ajiyan zuciya ta saki, sai jin abun take kamar mafarki sai da ta mutsuke idonta taga su Yasar nan ta gaskata abun da ta tarar wani irin kuka mai ban tausayi ta saki tare da tsuma zuciya.

Bayan kwana bakwai duk Yasirah ta dawo shiru-shiru bata son yawan hayaniya mitin ma taki fita haka Samar zai zo yayi ta damunta a satin ne ta fara fita Najwa ko duk a tsorace take don tasan karonsu da Yasirah bazaiyi kyau ba. A haka jarabansu ya fito tare da Admission d'in jami'a batare da b'ata lokaci ba aka mata komai ta fara zuwa makaranta.

'Dabi'u Yasirah sun k'ara canzawa wanda hakan ya k'ara bama S Marafa tsoro sam yanzu Yasirah bata shakkan kowa komai zatayi gabanta gad'i zata yi shi ba tare da tsoro ko shakka ba ga taurin kunne kamar k'ashi.

Kwanaki sun tafi watanni sun wuce shekaru sun shud'e game da halayan Yasirah ko ba abun da ya ragu haka gun tsafi ma tayi nisa sosai don tafi kowa a tsabibanci kuma in taso kawo mutum sai ta kawo ka wanda hakan ya kara mata matsayi a gun matsafa.

S Marafa ganin halim Yasirah ba abunda ya ragu gashi bata kula samaruka hakan yasaka ya yanke shawaran had'ata aure da Yasar d'an uwanta tunda daman sun shaku da ita sosai.

Yasar ya samu aiki cikin ikon Allah yana gudanar da komai a haka ya koma gidan mahaifinsa da zama sabida barazana da tsorata da yake yawan yi.  B'angare guda aka bashi a gidan baya tare dasu don gun kam zamu iya kiransa da gida don basa had'e da Dad d'insa k'ofar su da ban nashi daban sai ya ga dama ya shiga gurinsu.

Yasar yanzu ya gama gane duk abinda Yasirah ke aikatawa amma ba halin fad'a don ko ya zo da niyayar fad'a bakinsa sai ya rik'e gashi hasali Yasar mai wasa a addu'a ne wannan yasa Yasirah ke nasara akansa.

S Marafa ne ya d'aga waya ya kira Yasar ya ce"kazo ka sameni a gida". Ba tare da b'ata lokaci ba Yasar yazo sai da ya gaida Hajiya kafin yaje gun Abbansu ya gaida shi bayan ya zauna Abba ya kira Yasirah nasiha sosai ya fara musu daga k'arshe ya ce“na yanke shawaran had'a ka aure da Yasirah 'yar uwanka kusani ba shawara nake baku ba wannan umarni nane". Yasirah ta d'ago ta fara bama Abba hak'uri tsawan da yadaka mata ne yasata yin shiru take ranta yasoma a zazzala yanayinta yasoma canzawa cikin sauri tafita daga d'akin harda gudunta ta nufi d'akinta. Ko da muka bita nan take d'akin yasoma gir-giza wani wuta ke fita daga bakinta kanta ma naci da wutan kwayar idonta shima wutar yake ci wanna abu ba k'aramin tsoro ya bamu ba na bud'e baki da niyar ihu Sanah tasa hannu ta toshe min baki na.

CI GABAN LABARI....
Yasar an sallame shi a Asibiti tare da garg'ad'in ya kiyaye shan magani da kuma abunda zai janyo makansa mumunan buguwa don zai shafi kwanyansa. Ko da suka dawo gida Ammar shi ya ci gaba da kula dashi har ya warke sosai.

Samar ne ya shigo da motar sa haraban gidan su Yasirah mai gadi ya gaidashi Samar ya amsa cikin sakin fuska mai gadi ya ce“barin kiraka Hajiyar". Mai gadi ya shiga gida ya tarar da Yasira tana shirin fitowa haraban gidan daman ta san da zuwan Samar, mai gadi shi ya sanar mata da sak'on Samar ta ce" gata nan zuwa k'irjinta sai bugawa yake yi don ta san Samar ba zaiyi sassauci akan maganan ba.

Tunda ta fito Samar ya kafeta da ido sai jin zuciyarsa na harba masa da sauri-da-sauri kasa d'auke idonsa yayi daga gareta, tana isowa ta ce"King barka da yamma". Cikin sanyin jiki ya amsa“lafiya ya kk?". Yasirah ta rausaya ta ce“lafiyalau". Shiru gurin yayi sai Samar da yayi dauriya da d'ago ya kalleta cikin so da k'auana. Yasirah ta ce“Samar nayi duk yanda zanyi Abba yaki afasa aure ya ce aure dole ba fashi".

"Yasira gaskiya da sake"cewar Samar dake zaune kan mota fuskarsa babu alamun walwala. Tayi ajiyar zuciya tana dubansa ranta duk a cakud'e hawaye ya ciko ido taf tasa hannu ta share. "Samar bansan ya zamui ba, Abba ya dage kan lamarin sossai.Gashi shugaba kullum cikin gargad'ina take bisa kaucewa dokar k'ungiya".Ta k'arasa maganar cikin raunin murya.

Cikin kaushin murya yace"zanyi hukunci"cikin sauri ta tari hanzarinsa "nasan hukincinka bahagone Samar karkayi pls na rokeka."Bai jira cewarta ba ya kwashi mota da tsananin gudu yabar harabar gidan. Durkushewa tayi  take yanayin halitarta ya soma sauyawa daga yadda take zuwa wata suffar da gudu ta tashi ta shiga cikin gida d'akinta tashiga tasaka ma makulli ta kulle kanta..........

Yasar jiki ya warke kwance ya ke yana tunanin irin had'in da Abba ke shirin yi masa da wannan azzaluman don shi ba wai sonta bane ba yayi a'a sai abunda take aikatawa gashi yakasa sanar da kowa ko yayi yun k'urin hakan bakinsa nauyi keyi ya kasa fad'a. Da wanna tunani aka kira sallah ya fita ya tafi masallaci bai dawo ba sai da yayi sallah isha'i yana zuwa ya samu an kawo masa abinci dining ya je ya zauna ya bud'e kular sai ya manta bai d'auko ruwa ba mik'ewa ya sake yi ya je friza ya d'auko hollandia mai sanyi yazo dining.

Ido ya zaro alamar tsoro don wasu manyan tsutsotsi ya gani suna yawo a rabin abinci da baya yasoma ja sai ganin koyayen d'akin sun d'auke hoton Yasirah dake mak'ale a d'akin ya haska ya tsatstsage wani irin mumunan fuska ya gani a cikin hoton sai ji yayi ana kiran sunansa Ya....sa...r! Ya.....sa...r!! Ya....sa...r!!! Cikin wata irin murya mai ban tsoro ga haske da ke haskashi wal-wal sai ya d'auke gurin yayi duhu tsoro ne ya soma kama shi
nkali yai baya, kansa ya soma juyawa wani abu ya daki kirjinsa.Ya zube kan gado Allah ya bashi sa'a ya soma jan addu'o'i duk wada tazo bakinsa.

Take dakin ya daina girgiza, komai ya koma mazauninsa har abincin tamkar komai bai faruba.Ya yi jim yana tunanin lamarin ture abincin yai ya mike ya dauki mukulin motarsa kai tsaye ya wuce wajan park ya dauki motarsa kirar corrola.Gidansu Nawas abokinsa ya nufa saidai bisa akasi baya nan haka ya dawo gida jiki a sanyayye.

Kwanci tashi maganar biki kara kusantowa take, babu wani jituwa tsakaninsu sai kallon banza da bakakken maganganu in kuwa suka hadu a gaban iyayyansu nunawa suke tamkar babu komai tsakaninsu a haka aketa cudawa.

Yasiraht da Samar hankalinsu yayi mummunan tashi, musamman yadda duk yadda Samar da Najwa sukai kokarin runkarar mahaifan Yasiraht basa nasara saboda karfin addu'a.Har lamarin ya soma taba tsafinsu wanda yake kawo musu koma baya,hankulansu yai matukar tashi sossai.
Yasar ne zaune a office haka kawai yaga office din na girgiza, take kasa ta dare wasu irin hallitu masu kahunhuna suka bayyana suna kawo masa cafka.Ya rintse ido yana ta'awizi wani mashi kakkaifa ya ratso tsakani ya nufoshi gadan-gadan.Take ya runtse yana jiran me aukuwa ta auku jin shiru na lokaci yasa ya bude ido abin mamaki mashin ya gani tsaye dai-dai kirjinsa yana daga ido yaga Yasiraht ce tsaye tana masifa ta tsayar da mashin da karfin tsafinta.

"Shima kasheshi zaki yi Najwa?"
"Tabbas Yasiraht walahi saina illata rayuwarki,ninai sanadin zuwanki kungiya yau gashi kin fini komai".

"Kinyi kuskure Najwa n shirya ja dakowa cikinku, ciki hada daukar rayukan masu neman bibbiyar lamurana".

Take suka soma gumurzun tashin hankali, wanda hakan yaja farfashewar wasu cikin kayan.Can Najwa ta saki kara sakammakon nasarar sokarta da tai da mashin hannunta a gefan kafad'a b'acewa tai tana kuka.

Yasar ya saki ajiyar zuciya, Yasiraht ta gyara office din tas ta dago tana dubansa tai masa murmushi tace.

"Kana musulmi kana sakaci da addu'a ko Yah Yasar?".

Bata tanka ba ta wuce ta rufemasa office din, ya cigaba da jujjuya maganarta a ransa.Shigowar Nawas ya katsemasa tunani, yace "ango! Ango!! ango!!! Dariya kawai yai  suka soma hira.
Sun jima suna hira yai masa sallama ya wuce, haka Yasar ya yini sukuku dashi.
Bata tanka ba ta wuce ta rufemasa office din, ya cigaba da jujjuya maganarta a ransa.Shigowar Nawas ya katsemasa tunani, yace "Ango! Ango!! Ango!!! Dariya kawai yai  suka soma hira.
Sun jima suna hira yai masa sallama ya wuce, haka Yasar ya yini sukuku da shi.

Ana tashi daga aiki ya d'au jakarsa da wayoyinsa ya fita motarsa ya bud'e ya shiga ya tayar ya d'au hanyar gida zuciyarsa cike da tunani kala-kala yana cikin tuk'i sai yaga wata ya rinya cikin fararen kaya ta baza gashinta ba'a ko ganin fuskanta ga ganin haka ya yi shirin taka burki cikin sauri ta juyo garesa tare da ihu ga hak'oranta sun fito, bai san lokacin da ya saki ihu ba ya sake sitiyarin motar ya rutse ido don ya sadak'ar mutuwa zai yi.

Cikin sauri Yasirah ta bayyana gaban motar ta rik'e sitiyarin cikin salon tsafi ta mayar dashi gefen hanya duk abunda yake faruwa idonsa na rufe jin motar ya tsaya ya bud'e idons a hankali dai-dai lokacin Yasirah ta juyo garesa karaf fiskansu ya had'u dana juna hancinsu har na gogan na juna take numfashinsu yasoma fita da sauri-da-sauri kasa d'auke idonsu suka yi daga kallon juna kalon ido-cikin-ido.

Read More

Share this

WhatsApp

'YAR MAFIYA Part 2

 August 31, 2017     'YAR MAFIYA 1-END     No comments   

Wata giggitafiyar k'ara ta saki tana ja baya, a hankali haske ya gauraye komai ya dawo mata dai-dai.A rikice Yasar ya juyo hakan ya haifar da sub'ucewar sitiyarin hannunsa motar ta kaucewa titi ta nufi daji.Wata k'atuwar bishiya ta daka cikin ikon Allah gaban motar ne ya lotsa,da sauri ya fito ya bud'e sashin da take ciki. Sai sauke ajiyar zuciya take, hannunta ya kama jinsa ya yi yayi sanyi k'alau das!Gabansa ya fad'i sakammakon ganin yadda idanunta ya sauya cikin rikicewar murya yace.
"Yasiraht lafiyarki kuwa? ".
Ya fad'a da tsorataciyar murya,

Muryar tace ta sauya tare da bud'ewa, "me ka gani ne?" take ya soma ja da baya a tsorace binsa take launinta ya cigaba da sauyawa wasu hak'ora suka bayyana zak'wazak'wa jini na zuba daga idanunta k'ara ya saki ya yi cikin daji da matsanancin gudu take dajin ya kaure da wata hatsabibbiyar dariya ta cigaba da kuwa da karad'e kunnuwansa. Gaba daya ya rikice can tunanin adu'a ya ziyarci zuciyarsa, take ya soma karanta ayatulkirsiyyu.Wata hajijjiya aka yi dashi ya bugu da bishiya take kansa ya fashe ya fadi babu numfashi.

Shud'ewar rabin awa ya farfado ji yayi kansa ya yi nauyi, ya bude ido a hankali shasshek'ar kukanta ta karade kunnuwansa ya shafa goshinsa babu ciwo sai dai jikinsa ya tsamamma sossai. Ga mamakinsa sai ya riski kansa a bigiran da suka bar motarsu lamarin ya girmi kansa an janyo motar zuwa kusa da hanya. Ya bud'e baki zai yi magana,suna hada idanu wani matsanancin tsoro ya ziyarce shi ji ya yi yaka katabus.
"Tashi mu tafi gida".
Ta fada babu walwala,tayi gaba bin bayanta ya yi tamkar rak'umi suna isa tace "shiga muje".Jiki a sanyaye ya shiga yana tada motar ta tashi suka dauki hanya. Kansa ya yi zafi da yawa, a haka suka karasa gida babu um babu um um.

Ganin yanayin su ya tashi hankalin iyayansu, cikin damuwa suke tambayarsu abinda ya faru haka kawai Yasar ya samu kansa cikin kasa magana Yasiraht ce tayi bayanin cewar hatsari suka yi mamaki ya kashe Yasar amma ya kasa magana saboda fitinan nan kallon da take jefa masa a sace wanda yake hautsina kwanyarsa.Sun jajjanta musu sossai kai tsaye Yasar ya nufi sashinsa bakinsa a nauyayye zuciyarsa cinkushe babu damar magantuwa. Yasiraht taja hannun Yasmin suka nufi sashinta,take akasa masu aiki suka fita da motar bayan an fitar da kayan Yasiraht.

Yasar yana shiga sashinsa ya zube a kan gado, mamakin Yasiraht yake sossai, ji yayi inama ya fad'a abinda ya faru amma daya yi yunkurin hakan sai yaji bakinsa yayi nauyi. Kansa ya sara yana tsananin ciwo.

Tana dawowa daga sallah jakarta ta d'auka ta nufi night prep tana zuwa ajinsu ta zauna ta ciro takardunta tasoma nazarinsu  can zuwa wani lokaci kamar daga sama sai taji wani abu na zagaya k'afarta da sauri ta kalli k'asa bata ga komai ba, a hankali ta d'an matsa da k'afar taci gaba da k'aratu kamar ance juya ki kalli wajen tagan ajin sai ganin wani kujera yana yawo a sama ga kwarangal suna kewaye da gun wani ruwa jini da ke bin ta gefen kujeran yana sauka a kasa sai aka masa hannu da kayukan mutanane a firgice ta mik'e tare da runtse idonta tana hawaye.

Senior da ke ajinne ta daga mata tsawa ta ce"ke Yasiraht lafiyar ki kuwa mai ke damun ki kwana biyu?". Yasiraht ta sunkuyar da kai tare da zubar da hawaye ta ce"Sister nima ban sani ba". Kai Senior ta jin-jina ta ce"zauna to", haka sukayi prep d'in har aka tashi ta nufi hostel tana zuwa ta cire kayanta ta sanya na bacci ta kwanta a gadonta tana tunane tunane kala-kala idonta ta lumshe tana tunano abubuwan da suka faruwa da ita a 'yan kwanakin.

Najwa ne tazo ta dad'e tsaye a kanta tana murmushi Yasiraht da idonta ta d'an rufe sai taga kaman wani irin hallita shi ba cikaken mutum ba sannan shi ba dabba halitta mai ban tsoro cikin sauri ta bud'e idonta sai ta ga Najwa wani sassanyan ajiyar zuciya ta saki tare da mik'ewa ta zauna ta ce"Najwa  ya kike? Ban san shi gowarki". Najwa tayi murmushi ta ce"na dad'e anan ai", nan suka zauna suna hira sai kusan goma Najwa ta mik'e ta ce"barin tafi d'akin mu", Yasiraht ta mik'e ta ce"nagode sosai fa muje na rakaki". Suna tafiya suna hira har ta kai ta d'aki ta dawo.

Kwanaki sun tafi abubuwa da yawa sum faro Yasiraht ce na hango cikin murna tana had'a kayanta a trolley d'inta sabida gobe zasu tafi hutun zango k'arshe na karatu(thirt term) sai da tagama kimtsawa ta hau gadonta ta kwanta tana tunanin Yasir a zuciyarta Najwa ne ta shigo nan ta tashi ta zauna suka fara hiran rabuwa sun dad'e suna hira Najwa ta tazo ta fiya  har sunyi nisa ta juyo ta kalli Yasiraht ta ce" yauwa k'awata ga chocolate(alewa) nan d'azu naje school shop na sai mana". Cike da murna Yasiraht ta amsa tayi godiya da kyar suka rabu.

Washe gari da safe suka gyara hostel sannan suka nufi assembly suka jeru sukayi layi sai zuwa can principal tazo ta ke d'alibai suka mik'e sai da suka gabatar da national anthem kafin suka zauna aka bud'e taro da addu'a bayan sun gama shugaban makaranta tayi bayani tare da cewa hutunsu zai kasance sati shida tana gama jawabi aka sallami d'alibai da murna suna ihu kowa ta fito gate d'im makaranta.

Yasiraht tana fitowa ta sami su Yasar sun zo d'aukarta jikinta a sanyayae ta gai dashi sai da yayi ta tsokana nanta sannan suka shiga mota suka d'au hanya sunyi tafiya mai nisa Yasmin har tayi bacci can ta tuna da chocolate d'in da Najwa ta bata da sauri ta d'auko ta b'are zata saka abakinta Yasar ya ce"abun 'yar haka ne wato rowa zaki min ko", cikin fara'a ta ce"wacce ni na isa na maka rowa..." Fiskansa d'auke da murmushi ya ce" bazaki min dad'in baki na yarda ba", can idon ta ya kai kan ledar chocolate da sauri ta d'auko ta ce"la ga naka ai kai ka fara min rowama ai.

Chocolate d'inta ta saka a baki ta fara taunawa ta had'iye take tafara ganin wani irin walkiya da tsawa tamkar saukar aradu nan ta bar ganin haske sai duhu can ta hango wasu kwarangwal tare da wani irin suffar halittu suna cewa"Yasiraht muna miki murna da shigowa k'ungiyar mu muryoyi ne da yawa nan gashi sai gani abubuwan ban tsoro da firgici.

*9*
Jikinsa ba k'arfi ya mik'e ya nufi d'aki bayi ya shiga ya watsa ruwa tukun ya d'auro alwala yayi sallah ko abinci bai tsaya ci ba kasancewa lokacin bayan sallah azahar ne, kan katifansa ya fad'a ruf da ciki yayi ya baje k'atifansa sai bacci ne ya d'auke sa mai nauyin gaske.

Yasiraht kuwa tana shiga d'aki ta ajiye Yasmin ta rage kayan jikinta ta d'aura towel ta shiga wanka, sai da ta dirje jikinta sosai bayan ta d'auraye sannan ta k'ara yin wankan acewarta yau ta dawo gida dole tayi wanka na musamman, tana gamawa ta d'aura tawul ta fito tana goge jikinta da d'an k'arami tawul sai da ta goge jikinta tukun ta jawo k'aramin kujeran da ke jikin madubin ta zauna, sai da ta shafa mai tukun ta matso sai tin madubin don yin kwaliya.

Wak'an ta takeyi ta had'a kayan gu d'aya ta d'ago da zumar kalo cikin madubi da sauri ta mik'e tawul d'inta har na fad'uwa a kasa hakwara ta gani ta madubi suna zubar da jini tare da dariya, cikin sauri ta juya taga Yasmin na wasanta kalon madubi ta sakeyi bata ga komai ba, fauda ta shafa kawai ta fasa kwaliyan ta d'auko riga da skirt d'inta tasaka suka nufi falo don cin abinci.

Gudu ya ke zuba wa tamkar k'afafunsa zai fita ihu ya keyi yana niman agaji amma ko alaman wani babu a cikin dajin ga wasu manyan hallitu hak'waransu a waje suna gudu suna fisgan naman mutane wasu ko k'ok'on jinine a hannusu suna sha yana zubowa bakinsu sai da yayi gudu duk ya gama galabaita ya iso bakin wani k'aton rami wanda in kafad'a sai dai wani ba kai ba ko k'arshe ramin baya gani wani irin iska yaji mai had'e da guguwa a razane ya juya bayansa.

Hahaha sautin wani dariya da yaji cikin hanzari ya kali sararin samaniya inda yaji dariyan gudan kai ya gani a saman kujera yana yawo ga wani rin hayakin da ya turnuk'e kujeran sai da kujeran ta ju-juya a sararin samani tare da tsawa da walkiya takeyi ta soma matsowa gunsa gani haka yasoma ja da baya ba tare da ya kalli bayansa ba dai-dai lokacin ya kai bakin ramin suuuu ya tafi tare da sakin wani razanane k'ara.
Suuuuu! Yai tafiyar burgu zuwa cikin ramin, wata giggitaciyar kara ya saki daidai lokacin ya farka cikin tsananin firgita yana sambatu.Bakinsa na furta kalmar _"Hasbunallahu wani'imal wakeel"_cikin tsoro ya soma dube-dube sai motsi yake ji tare da alamun tafiya yai ta maza ya duro daga kan gadon jikiinsa yana rawa tamkar mazari.Kai tsaye band'aki ya shiga ya d'auro alwala ya tayar da sallah.

Ya jima zaune kan dardumar yana kaiwa ubangiji kukansa, bai tashi ba sai misalin biyu da rabi zuciyarsa ta yi sanyi sossai ya kwanta.

Washegari da safe dukkansu suka hadu a wajan break, gwanin sha'awa Yasiraht ta kallesu daya bayan daya ta lumshe ido a filli ta furta"gaskiya Daddy i really miss u".Dariya suka sa mata su duka Yasar cikin zolaya yace"rayuwar kwaki da k'arago".Cikin shagwa6a ta cunno baki"Daddy kaji shi ko?" "Kyaleshi diyar Daddy tuzurun kawai"dariya sukai baki daya.
Bayan sun gama bresk fast (karin safe) Yasiraht ta langa6e kai tace"Daddy inason zuwa shooping kace Yah Yas ya kaini",suna hada ido ta kanne ido ta daga gira "yes kai" ta furta da tsona. Ya gimtse fuska"kin raina ni ko? " "Yo raini kuma na nawa? ".Ta fad'a tana yi masa gwalo "to ai saiki nemi mai kai ki"saurin zubewa tayi "pls Yayana na daina"dariya sukai mata yace "ki bari sai zuwa yamma".Da haka sukai sallama Daddy da Yasar suka wuce aiki, Yasmin aka tafi kaita makaranta Hajiya ta nufi sashinta haka ma Yasiraht.

Shiru tana zaune kad'aici ya adabeta, ta juya can ta juya can.Tana zaune taga bangon d'akinta ya dare ta mik'e a tsorace ya cigaba da darewa wata irin fadace ta bayyana mai cike da kayan alatu a tsakiyarta wata kijera ce bisa dukkan alamu ta gwal ce. Gefanta Maza da Mata ne jingim sun kai su d'ari sun zagayeta cikin shiga wasu kaya jajjaye.Gaba d'aya kansu s sunkuye alamun girmamawa kujerar tsakiyar babu kowa,daga wani bango wani kyakkyawan saurayi ya bayyana dogo mai tsayi da cikar fadin k'irji.Fuskarsa doguwa yana da manyan idanu, hannu ya bud'emata "munai miki barka da zuwa Yasiraht zoki zauna"kawai saita samu kanta da rashin musu wa umarninsa gadan-gadan ta nufi fadar......... wata giggitaciyar k'ara aka saki daga gefansu hakan ya dakatar da'ita saboda razanar abinda ta gani.

Sanah
Rash
ku biyo mu
[8/8, 8:44 PM] Sanah S Isma'il Matazu:
💀 *YAR MAFIYA...*💀

Cikin firgita taci gaba da kallon fuskarta ba kowa bace face Najwa, hankalinta ya dugunzuma saboda kalamanta dake ratsa dodon kunnuwanta.
"Walahi Samir baka isa ba, ni zaka yaudara? Dama saboda haka ka matsa in jawota k'ungiya? Kasani kasan halina sarai zan iya kauda Yasiraht a kan ka walahi bana jurar had'aka da wata......."bata k'arasa ba ya kaimata wata muguwar shak'a a zafaffe.

"Ni zakiyiwa iskanci? Kinja mana asara, kinsani sarai dodon tsafi yace mudun ta hau kujerar nan matsayinmu zai hau-hawa a ko'ina saboda baki da mutunci muna dab da cika burinmu na samun *MATSAFIYA* ki wargaza mana shiri".Kakari ta shiga yi aka rasa wanda zai karb'eta.........Turo k'ofar d'akin ya katse hotan komai, Yasiraht ta soma waige-waige karaf suka had'a ido da Uwani mai aikinsu murmushi tayi.....sai dai murmushinta ya kashe sakammakon jiyo sautin muryar Samir a kunnuwanta"Sarauniya ki bamu wannan"ji tayi bakinta ya furta"na baku".Daga nan dif! Sautin ya d'auke Uwani ta ajiye mata abinci ta fita. Shudewar mintuna goma ta soma jiyo koke-koke cikin gidan,da gudu tai waje zuwa sashin da ta jiyo kukan.

Abinda ta gani ya girgizata da sauri ta juya ta koma d'akinta tana shiga ta kulle d'akin nan hoton fadan da ta gani d'azu ya bayyana a gabanta har yanzu suna kan Uwani mai aiki tana ihu suna yankan naman jikinta jiniko wani d'an rami yake taruwa a ciki sai da ya gama taruwa kamar wani iji ko zance cikin salon Sihiri da *TSAFI* wani hanya k'arami ya fito nan jinin uwani ya bi ramin har ya isa zuwa gun wani irin mumunan halitta mai jan ido sannan cikin kwayan idon ruwan ganye yana da dogayen hak'ora jikinsa ba fata sai wani gashi mai tsayi da bai gama rufe jikinba da inda muke muna hango yanda ya ke sanya harshensa yana shan jinin nan.

Yasiraht ganin haka kuma gata a tana kalon ta cikin mutanen sai ta soma ja da baya Samar ne cikin yananyin da ni kaina bazan iya gane ko me ke k'unshe a fuskansa ba ya soma mik'o mata hannu yana kad'a kai alamar k'arta gudu itakuma tana ja da baya al'amari da yaba ma kowa na gun mamaki don Samar yana matuk'ar ji da kansa ga shikuma d'an *SARKIN MATSAFA*  wanda duk ya ke cikin gunyiyan daga maza har mata bai sakar musu fiska bare har suga murmushinsa.
Kafin Yasiraht ta fita har ya tako yazo ida take hannu ya mik'o mata bata iya yin masa musu ba sai ta kama hannu al'amarin da ya ba ma kowa nacikin gurin mamaki, sai da ya janyota k'usa da shi yana kallon kwayar idonta suna iya jin numfashin juna Samar ya kasa d'auke idonsa gada gareta itama haka duk sun shagala da kalon junansu kalon mai d'auke da sak'onni kala-kala a cikinta.

Najwa da ta tsaya zuciyarta na matuk'ar tafarfasa wannan wani irin abu Samar keyi ma Yasiraht duk irin abunda nake masa ai yaci ya gane irin k'aunar da nake masa amma ko sassauta murya bai tab'a min ba irin yanda yayi ma Yasiraht yau tabbas dole na d'au mataki bazai yiwu ta shiga zuciyar da na dad'e ina muradi.

Cikin zafin nama tare da sihiri ta bi iska ta iso gaban su da sauri ta finciko Yasiraht tare da shiga tsakaninsu tana wani irin kalo ma d'auke da alamomin tambaya Samar da har zai yi magana ko me ya tuna sai ya nuna kujeransa da yatsa nan tabi iska ta iso gabansa tayi kasa-kasa tukun cikin isa da mulki ya taka kan matakalar ya zauna a kan kujeran tukun ta tashi da shi sama ta tsaya a sararin samaniya.

Hajiya Nafisatu ganin dare yayi gashi Uwani zata kawo mata ruwan zafi da sauri taje kitchen (madafi) taga ko ruwan bata d'aura ba ga kuma abincinta bata ci ba, gass ta kunna ta d'aura ruwa sai da yayi zafi ta juye ta d'auko zata tafi wata zuciya ta ce"anya Uwani yau lafiya tunda muke da ita bata tab'a mana haka ba barin kai ruwan nan inzo in duba ta.

'Dakin Uwani ta nufa nan ta sameta a k'asa dai-dai k'ofar fita a kwance a k'asa idonunta a sama duk sun kafe, ganin haka ba k'aramin razana tayi ba ta kira sunanta Uwani! Uwani!! Uwani!!! Ido ta zaro tare da d'aga hannuta ta ga ya saki da sauri ta juya tayi d'akin Abba da gudu ta shiga tana fad'in "Alhaji Uwani! uwani!!". Sam bata cikin hayyacinta sai da ya rik'ota ya soma mata addu'a ya ce"lafiya me ya samu Uwanin?.

Hannuta ya kama suka nufi d'akin yana zuwa ya ganta nan ya d'aga hannuta ya ga ya saki nan Abba ya saki salati don ya gane Uwani ta rigamu gidan gaskiya hannu yasa ya rufe mata idanunta tare da d'auko zanin ya rufe ta ya gyara ta a gefe d'aya hannu Hajiya Nafisat ya kama yana bata kalamai masu dad'i da kwantar da hankali ya kai ta d'aki ya fita ya kira Yasar ya masa bayani tare sukaje aka kira Limamin unguwansu tare da wasu makwabta, a dare aka nimi dangin Uwani aka suturta ta tayi kwanan keso.

Yasiraht sai da safe da ta tashi taga gidansu a cike nan ta tambayi hajiyarta me ke faruwa nan ta fad'a mata take taji wani zufa na keto mata ta razana sosai wato jiya ba mafarki takeyi ba asai da gaske abunda jiya ta gani a bacci ya faru nan ta fara hawaye duk wani tsoro tafaraji a haka aka fita da Uwani aka mata sallah aka kai ta gidanta na gaskiya Allahi Akbar rayuwa kenan.
Kwanakin Yasiraht uku a gida gaba d'aya hankalinta ya soma tashi saboda mafarkan da take yi tare da tsoratata da ake yi. Kwata-kwata yanzu kallon mudubi ya gaggareta saboda zahiri in ta kalli mudubi mugayan gane-gane take yi.Ahaka suka cinye kwanakin su suka koma makaranta,sai dai tunda suka koma ta fuskanci canje-canje daga gun Najwa sossai ko harkarta bata shiga balle magana me tsayi ta had'asu.

Kwatsam ranar Juma'a da azahar sun dawo masallaci, taga shigowar k'awayan Najwa su uku bayan su Najwa ce d'aya bayan d'aya ta kallesu Shany ce 'yar asalin garin ebira sai Merry ita kuma Ibadan sai kuma Emeka 'yar Undo bata tanka ba ta cigaba da bibbiyar littafin dake hannunta fizgar littafin yasata d'agowa kafin tai magana Emeka ta tsinkamata mari.Najwa tai murmushi ta jin-jina hannu alamun jin dad'i Yasiraht kasa magana ta yi suka kad'a kai sukai waje, ranar yini ta yi sukukku ko karbar abinci bata je ba.

Wata sabuwa sai Najwa ta tsiri sata aiki hakan yana bata mamaki matuk'a,amma babu yadda zatai ta fahimci hata Malamansu shakarta suke.Kwatsam rana nan tana zaune a labry tana karatu, ta jiyo shewar su Najwa can taji sautin Emeka"ke wai ya kuka yi da prince a kan tsamin yarinyar can?"."Hmm! Kedai bari sisty Samar na neman had'awa kowa jalalla walahi zanyi sanadin tona asirin k'ungiya saboda Yasiraht, shekaruna nawa tare da shi han samu matsayin da yake son d'orata ba sai ita daga zuwanta. Wace wuya ce banci ba wajan kawota duk zatona zan samu matsayin da take kai amma shi ne zai rainamun wayau? ".

"Laifin kine".
Cewar Shany, cikin k'ufula ta furta"kamar ya laifina ban gane ba walahi? ".
"Hmm! Nagaya miki kawai mugama dashi kin wani tsaya ja mana rai, wai ke so ai saiki ci so bagara kui biyu babu ba ko kigama da Yasiraht d'in".
"Keeeee!  Dakata in gama da Samar? Wa zan kama? " Ta fad'a a zafaffe itama cikin zafinta ta maida martani.
"Ki kama sabon zuwa".
Kyakkyawan mari ta shimfid'amata, ta cigaba"saboda baki da mutunci Samar din zan gama da shi? Kin san waye shi a gareni? ".
"Waye fa Najwa?  Banda wanda ya samu a hanyar banza ya cuccuce mu ko kin manta Samar ne yasa kika bada jinnin mahaifanki duka biyun ga doddon tsafi? Kin manta shi yasa kika rasa masoyinki na gaskiya kika bada k'annanki har uku ki gayamun yanzu wa kike dashi a danginki da zaki nuna matsayin jininki duk Samar ya k'arar da su.Shi ne kike so itama Yasiraht ta fad'a, to kisani ada ina tare dake,amma a yanzu nayi d'amarar janye muku zan kasance tare da Yasiraht kun yi galabar kawota cikin ku amma sai nayi sanadin da zata zame muku masifa dalilin marin da kikai mun bana yafiya".

Fuuuu! Tabar wajan, kan Yasiraht yai nauyi tanasan gasgata batun Emeka ta kasa, kawai saita shasshantar da batun ta cigaba da abinda take.Kamar almara Samar ya bayyana yana murmushi,cikin tsoro ta soma da baya amma suna hada ido sai taji wani abu na fuzgar zuciyarta zuwa gareshi matsawa ta

Matsawa tayi kusa dashi Samar kalon yake mata mai cike da so da kauna hannusa ya kalli wani zobuna guda uku a jere manya dasu da kuma rubutu a jiki ta baya kuma alamar kan mutum ne wannan zobe ya danna nan take wani irin hallita ya bayyana a gaban sa tare da rusunawa ya ce"ya shugabana ban umurni na bi". Murmushi Samar yayi cikin k'asaita da mulki ya ce"aljani d'an duguzu ina so ka kai mu dajin k'are dugunka zan huta a gun".

Kafin ka ce mai ta ke gurin ya gauraye da iska nan take Yasiraht ta fara kakkarwa da tsoro nan wata dadduma ta bayyana tare da matasai na alfarma ko da ta duba ta gani d'an duguzu ne ya ke rik'e da dadduman a kansa nan tsoro ya k'ara kamata. Samar ne ya kama hannuta kaman walkiya suka hau kan dadduman nan taga su tsaga bango suka fito gashi tana gani suka wuce mutane amma da alaman su basa ganin su a hankali suka haura sararin samaniya sai keta hazo sukeyi suna tafiya cikin kwanciyar hankali.

Yasiaht ta rasa mai yasa in Samar ya mata magana bata iya masa musu kuma in ta kalli kwayan idonsa yana mata kwarjini bana wasa ba a han kali ta sauk'e sassanya anjiyar zuciya.

Najwa da ta nufo library (gurin karatu) taga wulgawan su Samar nan take wani bak'in ciki ya lulub'eta ga mutane a gun bare ta tanza hallita ta bisu da sauri ta nufi cikin library a girgiza ta dawo wata tsun-tsuwa ta fito daga library ta bisu zuciyar ta na mata k'una sai sake-saken wani irin abu zatayi ma Yasiraht.

Samar suna zuwa dajin nan dadduman ya sauk'o dai-dai bakin ruwa suka sauk'a wani abun ban mamaki ga manyan namun daji suna shawagi a gun ba wanda ya kulasu ko ta inda suke basa bi. Samar ne yasake murza zobe nan wata mata fara da farare kaya ta bayyana ba'a ganin k'afarta sabida fararen kaya ya rufe k’afafunta, ta rusuna ta ce"Ranka shi dad'e 'Dan Sarkin Matsafa jikan matsafa mai kake buk'ata a maka sai da ya d'au lokaci kafin ya ya ce"kayan marmari nake buk'ata". Kafin kace me  wani tire na alfarma kamar na zinari sai kyalli yakeyi tare da d'auke ido kayan mar-mari aciki irinsu Tuffa(Apple), Inabi Ayaba, Abarba, d.s.s.

Yasiraht sam tak'i ci Samar ne ya ce"bazaki ci ba ko sai na baki ya d'auko yankake tufa zai sa mata a baki kawai suka ga wani irin abu ya tun k'aro su da gudu ya buge Yasirah ta fad'i k'asa, nan abun ya fito da wani tsini da niyar zuwa ya cakka ma Yasiraht a cikinta, cikin sauri Samar ya bud'e hannusa sai ga wani sanda ya fito da sauri ya nuna wannan tsun-tsuwar sai ga Najwa ta dawo halittanta na asali ta fad'i a gun tana mai da nufashi. Cike da mamaki Samar ke kallonta a hankali ya tako zuwa inda Yasiraht take ya d'agata tukun ya kalli Najwa nan yaji wani haushinta ya kamasa a hankali yasoma takawa zuwa gun Najwa cikin fushi.

         15
Cikin fushi yake nunata da yatsa, "wato Najwa bakya jin magana ko?  Ina kaucewa sab'amiki kina k'ok'arin k'untatamin to walahi zanyi maganinki".Wata giggitaciyar dariya ta saki, tana hucci mai zafi ta dubeshi.
"Samar ni zaka wulakanta saboda ina bibbiyarka?Walahi kabani mamaki k'warai da gaske, zan nuna maka sharin mace sai kayi nadamar cin amanata".....bata k'arasa ba ya nunata da hannu tuni wani sirririn haske kore ya fito ta tsintsiyar hannunsa ya daki fuskarta take ta saki wata giggitaciyar k'ara data kid'ima dajin.Namun dajin suka dinga gudu suna neman mafaka,yaraf ta zube k'asa babu numfashi.'Daukar Yasiraht ta yi suka bar wajan.

Cikin tsananin gudu suka dinga keta dazzuzuka, a hankali ya sauketa cikin labry d'in ya kama yatsanta yasa mata wani zobe.Zoban yana da tsananin haske in ka kalleshi, jikinsa tambarin kan skelaton ne a jiki daga tsakiya an masa ado da gwal yanata k'yali b'at ya b'ace.A hankali idonta ya soma washewa ta saki ajiyar zuciya kanta yai nauyi sossai a jigace ta nufi hostel saboda gajiya.Turus ta tsaya lokacin data fito, sakammakon ganin d'alibai dandazo guda sun zagaye Najwa cikin galabaitaccen yanayi.

A sanyayye ta karasa wajan tana tambayar abinda ya faru, wata muguwar shak'a Shany ta kawomata wani shock da hannunta ya yi yasa ta sakin Yasiraht bata shirya ba tai baya tana muzurai.Ita dai Yasiraht rakata ta yi da idanu zuciyarta k'war cike mamakin ganin Najwa a wannan yanayi.Take abinda ya faru ya dawo mata, kanta ya sara ras!  Ta dafe ta wuce area d'insu jikinta na rawa.Emeka dake gefe ta kwashe da dariya, cikin gurbataciyyar hausarta tace "yaro bai san wuta ba".

Wani rikitaccen kallo Shany ta aika mata, a daddafe ta wuce hostel  tana zuwa ta zube kan gadonta tana numfarfashi.Ta dafe kanta da yake juya mata sossai, a haka ta yini kwance.Najwa sai da tai kwana biyar kwance sannan ta dawo hayyacinta.

Tun daga lokacin wata gaba ta k'ulu tsakanin Najwa da Yasiraht, kwata-kwata basa ga miciji idan hanya ta had'asu sun dinga hararre-hararre kenan.Abinda yake tada hankalin Najwa yadda duk yadda taso cutar da Yasiraht sai zoban hannunta ya zamo shamaki wajan afkuwar hakan, haka take hakura kiri-kiri kwatsam aka nemesu taron gaggawa a k'ungiya.

Harabar wajan cike take da manyan motoci ababban kalo, abin sai wanda ya gani an kawata fillin ra jajjayan furani da bak'ak'k'e komai na wajan ja da bak'i ne har  kayan jikinsu.A hankali aka soma darewa ana bashi waje yana rik'e da hannunta har suka samu waje suka zauna.Nan aka saki kida sossai taro ya soma gudana, an gama gabatarwa an ci an sha Najwa da Shany na gefe suna kus-kus.Can Samar ya mike ya gabatar da jawabin godiya ga mahallata taron,ya juya yana murmushi ya kali Yasiraht hannunsa ya mika sama yana karanta wasu dalamusan tsafi take wasu kwarre guda biyu suka bayyana kan hannunsa.

Cikin kasaita ya tsareta da ido"karbi kisha" jikinta ko ina rawa yake take ta kafa kai ta hausha wajan ya rude da shewa"kinzama sarauniya!  Kinzama sarauniya!!  Kin zama sarauniya!!! ".Wata giggitaciyar kara Najwa  ta saki tai kanta da wata takobi mai tsananin haske, take Samar ya dakawa Yasiraht tsawa itama tai kanta tana shafa zobanta takobi ta bayyana irin ta Najwa nan da nan wajan ya hautsine sai karar k'arafa kake ji na tashi can Yasiraht tai nasarar yankar Najwa a gefan wuya take ta kwala kara tai lau zata fado kasa. Caraf Samar ya rikota Yasiraht ta diro kan kafafunta tana murmushi ganin Najwa a hannun Samar yasa ta jefa masa wani shu umin kallo ta danna zobanta b'at ta b'ace....

*16*
Ganin Najwa a hannu Samar yasa Yasiraht ta sakar masa wani shu umin kallo ta b'ace, bata bayya na a ko ina ba sai a bayan hostel d'insu  gindin bishiyar d'aurawa ta zauna ta had'a kai da gwiwa tana kuka mai tsuna zuciya sam ta rasa mai yasa take jin wani abu game da Samar duk lokacin da ta gansa da Najwa sai ta ji zuciyarta na mata zafi. Labb'an bakinta ta ciza a fili ta ce"Najwa ni Yasiraht sai na koya miki hankali duk wani hanyan da zanbi na nuna muku kwarewa ta sai nabi kuma sai na fitini kowa a gun sai na zama mai bada umarni abi nice nan zan dawo mai jiran kuren Samar". Murmushin mugunta ta saki sai kuma taci gaba da kuka.

Najwa tana far-fad'owa ta ganta hannu Samar sai taji sanyi a zuciyarta tazo juyawa taji wuyanta ya rik'e sai da ta saki k'ara kad'an Samar cikin sauri ya k'ara rik'e ta tukun ya fara wasu surkulle sai ga kwarya ya bayyana a gabansa nan take ya sanya hannusa ya d'ebi garin magani ya shafa mata tare da wasu sirutai wanda ba musan ko na miye ba take waje ya goge kamar ba ta tab'a jin ciwo ba Najwa sai murmushi takeyi fiskanta d'auke da annuri yau tana jin wani sanyin dad'i ya mamayeta wai ita ce a hannu Samar lalle yau jin kanta take tafi kowa, cikin yanga ta mik'e tare da zuwa kusa da Samar ta tsaya sai da ya aika tama da kalon mai d'auke da tuhuma kafin ya ce"Najwa mai yasa bakiji na ce ki fita a hark'an Yasiraht amma kin k'i ji kinga irin ta nan ko in baki mai da hankali ba zata fara mayar miki da martani kaman yanda tayi yau". Najwa ko ajikinta bata kuma ce da shi k'ala ba sai murmushin da takeyi nan ran Samar ya k'ara b'aci take ya bada umarni da a watse a mitin d'in yana gama fad'a ya bace...

Bai bayya na ko ina ba sai gun da Yasiraht take ta had'a kai da gwiwa tana kuka a hankali Samar yazo ya dafa ta a hankali Yasiraht ta d'ago idonta tab da hawaye cikin sanyin murya Samar ya ce" Yasiraht ki dai na kuka ban son ganin hawayenki na zuba ko kad'an". Cikin fushi ta d'ago dara-daran idonta da sukayi ja ta sauk'esu a kansa da niyar masifa amma sai me kwarjininsa yasa ta fasa Samar ne ya sanya hannusa ya share mata hawaye ya rik'o hannuta suka mik'e tsaye suka nufi hanyan hostel.

Sai da ya kai ta har d'aki ya rarrasheta suna tad'i har tana dariya kafin ya tafi, tun daga wannan rana Yasiraht ta soma canza salo don Najwa bata isa ta tab'ata ba ta share ga salon tsafi da sihirin da Yasiraht takeyi abin har na ba ma Najwa tsoro kuma ko a gun mitin nan danan zakaji ta kawo mutane hakan yasa suka k'ara girmamata.

Ku biyo mu

Read More

Share this

WhatsApp

'YAR MAFIYA Part 1

 August 31, 2017     'YAR MAFIYA 1-END     No comments   

Doguwar Yarinya na hango matashiyan mai ji da jini a jika shekarun ta bazai wuce ishirin da uku zuwa da hud'u ba kallo d'aya zaka mata ka gane tana matuk'ar ji da kanta tamkar 'Yar gidan sarauta, fara ce kuma tana d'an tsayi sannan bata cika kyan d'aga hankali ba amma tana da gizo wanda duk ya kalleta zata na yi masa gizo, tana da idanu manya-manya wanda in ka zuba musu ido na wani d'an lokaci zakaga suna canza kala, ko da mukayi duba zuwa fuskan ta daga gani tana cikin matsanaci b'acin rai take yanayin hallitarta tasoma canza wa, da gudu ta fito daga falo ta nufi d'akin ta da ke can k'arshen d'ankunan k'ofar ta rufe take ta fara wani irin gurnani tamkar namiji zaki wanda yunwa ya dame shi ya fito farauta, cikin tsoro na kalli Sanah na ce"ke kalli yanda takeyi nikam zan gudu don na tsota da ita na fasa kwasan labarin". Wani harara Sanah ta aika min da shi ta ce"dad'i na dake kin fiye tsoro kamar farar kura ba gani a kusa da ke ba? To miye na tsoron?". Hannuna taja mukaje tagar d'akin da ta shiga muka leka, cikin tsoro nake shirin sakin k'ara Sanah ta toshe min baki ko da na k'ara duba wannan Yarinyan ne ke hawaye amma na jini kanta ke firda wuta tamkar an kunan itace da gass, tafin hannuta ma haka yake fitar da wuta kayan jikinta suka canza kala zuwa ja-jazur, cikin murya mai ban tsoro ta ce"Baba mai yasa zakayi haka? Shin kasan had'arin da ke cikin wannan al'amarin kuwa? Kasan halin da Yasar zai shiga kuwa? Ina tsoron Samar in yaji wanan al'amarin shikenan zaku rasa Yasar". Cikin tsoro Sanah ta kalleni"Rash wai mike faruwa ne?", ba tare da na bata amsa ba na kamo hannuta muka nufi falo. Muna daga k'ofa mukaji wani dattijo ya na ce ma Yasar "Allah ya maka albarka tabbas nasan bazaka watsa mana k'asa a ido ba". Wanda aka kira da Yasar kansa na duke a k'asa ya amsa da "Ameen Abba" ya sake rusunawa ya ce"ni zan koma gida naga dare ya soma yi", Tsohon nan ya amsa da"to Yasar ka sauka lafiya ka kula". Cikin girmamawa ya fito yashiga motar sa ya nufi gidan sa ko da ya shiga gida muna biye da shi gate(gareji) ya rufe tare da komawa mota ya ja ya kai gun ajiye motoci ya ajiye motar, ya fito ya fara tafiya irin na gaye wanda ke ji da kansa da kuma boko ya shiga cikin falo tare da mai da k'ofar ya rufe ya nufi hanyar matakala, tass! Tass!!  Tass!!! Kake ji k'arar d'aukewar wuta tare da wani irin walk'iya mai had'e da k'ara tare da tsawa aciki wanda ya samu komawa baya da gudu,  cikin jarumta irin na maza ya soma lalub'en hanya dai-dai k'ofar d'akin ya hango haske wanda ya hango takun sawun k'afa zalla da jini ajiki yana bin hanyar da zai bi, cikin hanzari ya juya zai koma sai ganin yarinya k'arama tana tunk'aroshi ta ware hannuta alamar oyoyo, ga idanun ta yana fitar da hawayen jini bakin ta ma na zubar da jini cikinta yana juyawa da ida mutun yake zai na iya hango zalla jinin da ke juyawa a cikinta, cikin kid'ima yarasa baya zaiyi ko gaba yana juyawa ya ga yarinyar na dariya ta b'ace da gudu yayi hanyar sauk'owa daga matakalar benin, sam ya kasa yin addu'a bare daman shi ba gwanin yin addu'a bane(kira ga 'Yan uwa yana da kyau mu kasance cikin addu'a akullum kar muna mantawa fa Annabi ya koyar mu addu'o'i tun daga kan nashiga bayan gida har da na fita a gida dan Allah mu dage baran yanda zamanin nan ya zama).

    Masu karatu ku biyo 'YA'YAN MUTAN;

Cikin matsanancin tashin hankali ya cigaba da ja da baya. Cigaba tayi da bibbiyarsa bakinta yana hayak'i"kayi kuskure Yasar na shiga komar matsafiya,bazan ragama kaba bana yafiya bana mantuwa saina kassara rayuwarka da duk wanda ya bibbiyi rayuwar god'iyata."Cikin muryar tashin hankali yake fad'in "wacce ce ke? Meye alak'ata da ke? ".

Wata shu'umar dariya tayi,ta huro iska mai tsananin zafi da k'arfi take ta d'agashi sama ta wulwula ta dokashi da bango. Kansa ya tsage, ya soma zubar jini lau ya fad'i k'asa yaraf! 'Dif! Numfashinsa ya d'auke.

Ammar ne ya taho cikin wak'e-wak'ensa kamar an ce dubi can idonsa yakai kan Yasar kwance cikin jini. Wata giggitaciyar k'ara ya saki hakan ya jawo hankalin mutan gidan da gudu sukayo shashin.Ganin halin da yake ciki ya d'aga hankalin kowa, nan da nan aka sashi a mota aka nufi asibiti da shi. Cikin gaggawa aka karb'eshi zuwa emergency (wajan taimakon gaggawa).Likitoci sun duk'ufa a kansa, harzuwa lokacin bai dawo hayyacinsa ba, mahaifiyarsa banda kuka babu abinda take. Saida sa'a uku ta shud'e sannan ya dawo hayyacinsa, an masa k'arin jini sannan aka hana kowa zuwa inda yake saboda suna san auna k'wak'walwarsa.

Cikin tsoro naja hannun Rash cwt muka bar wajan.
Wata shu'umar dariya aka saki, "hahahahahaha! Munyi nasara,munyi nasara".Aka fad'a da wata rikitaciyyar murya gaba daya wajan ya amsa amo suka saki dariya. Sanye suke da jajjayan kaya mazansu da matansu, idanunsu wani irin launi tamkar Rainbow (bakan gizo) akaifarsu zak'o-zak'o tamkar horaye, hak'ora sun zazzago duk gashin kansu ya mimmik'e tsaye dukkansu kayansu jajjayene kowanansu rike da k'ok'on jini suna sha.

Kwanan Yasar uku a asibiti aka sallame shi, saidai an bashi magunguna tare da gargad'i kan ya kiyayye buga kansa saboda saura k'iris yayi loosing memory d'insa.
Duk tsayin kwanakin da ya yi a asibitin babu Yasiraht babu alamunta wajan zuwa dubiya, lamarin daya tunzura zuk'atan 'yan uwa da dama harya haifar da kace nace a ciki.
Tsayin kwanakin yana samun sauk'i sossai, har ya koma wajan aiki.
"Yasira gaskiya da sake"cewar Samir dake zaune kan mota fuskarsa babu alamun walwala. Tayi ajiyar zuciya tana dubansa ranta duk a cakud'e hawaye ya ciko ido taf tasa hannu ta share. "Samir bansan ya zamui ba, Baba ya dage kan lamarin sossai.Gashi shugaba kullum cikin gargad'ina take bisa kaucewa dokar k'ungiya".Ta k'arasa maganar cikin raunin murya.

Cikin kaushin murya yace"zanyi hukunci"cikin sauri ta tari hanzarinsa "nasan hukincinka bahagone Samir karkayi pls na rokeka."Bai jira cewarta ba ya kwashi mota da tsananin gudu yabar harabar gidan. Durkushewa tayi take yanayin halitarta ya soma sauyawa daga yadda take zuwa wata suffar.........

Durk'ushewa tayi take yanayin halitarta ya soma sauyawa daga yadda take zuwa wata suffar......

TUSHEN LABARI......

Alhaji Sani Marafa haifafen d'an garin Bauchi ne, iyayensa fulanin ne gaba da baya, ya kasance d'an boko ne sosai yayi karatun boko amma hakan bai sa ya kauce ma hanyar Allah ba, ya kasance mai zafin nima tun yana matashi duk da aikin k'arfin da yakeyi hakan bai hanasa karatu ba.

Cikin ikon Allah Alhaji Sani Marafa ya kammala degrees d'insa na farko a kan Business Administration yana kammalawa bai dad'e ba ya samu aiki a Ministry of Housing(ma'aikatar kula da gidaje) inda aka bashi Accounter (mai kula da kud'i) na gurin.

Bai dad'e da samun aiki ba yayi aurensa na farko inda ya auri matarsa Nafisatu, Nafisa macece mai kirki da girmama mutunane tana matuk'ar girmama iyayensa da 'Yan uwasa wanda hakan bak'aramin dad'i ya ke masa ba suma 'Yan uwansa suna sonta.

Yau ta kasance safiya da ta sanya iyalan gidan Marafa kuka wanda sukayi rashin 'Yarsa guda d'aya mai Suna Maryam, Maryam ta rasu ta bar Yaro kwaya d'aya mai suna Yasar wanda akala ya kai shekara biyar aduniya, Yasar yaro ne mai shiga rai gashi da hankali amma ya taso cikin gata don duk abunda yakeso shi za'a masa sabida ubansa yana da kud'i dai-dai gwar-gwado.

Bayan zaman bakwai Yasar yak'i zama gun kowa sai Alhaji Sani hakan yasa suka d'aukesa ya dawo hannusu da zama, duk wani gata da mahaifiya zatayi wa d'anta Hajiya Maryam tana k'ok'arin gwada masa sun sanya shi a makaranta *ANSS* makarantar da ake ji dashi a cikin garin bauchi Yasar ya fara karatun sa cikin kwanciyar hankali, amma sam baya son zuwa Islamiya sai da kyar gashi yana da k'ok'ari sosai yana da hazaka da saurin d'auk'an karatu.

Yau Hajiya Nafisatu ta tashi da zazzab'i sosai wanda har sai da aka kai ta Asibiti ko da likita ya gwada ta ya tabbatar ma Alhaji Sani Marafa tana d'auke da juna biyu ohoho masu karatu karkuso kuga murna a gun S Marafa haka sukayita kula da cikinta tare da ta abubuwan da akeso mai ciki tana ci.

BAYAN WATA TAKWAS..

Yau Hajiya Nafisa ta tashi da matsanacin ciwon mara da baya kasancewan Alhaji na gida bai tsaya b'ata lokaci ba sukayi Asibiti, suna zuwa likita ya shaida masa haihuwa ne yake aka shiga da ita labour room (d'akin haihuwa) sai da ta sami kusan awa guda tana nak'uda cikin ikon Allah ta haifo d'iyarta fara sol da ita, ko da aka sanar da S. marafa Hamdala yayi tare da gode ma Allah ko da aka gyarata suka nufo gida, tun da Yasar ya dawo daga makaranta ya samu Hajiya Nafisa haihu Yasar ya tasa 'Yar gaba ko 'Yan barka in sun zo a hannusa suke ganinta dakyar wani zubin ke bada ita a ganta, Hajiya Nafisatu da S Marafa suyi ta ma Yasar dariya don suna jin dad'in yanda yake nuna ma 'Yarsu k'auna.

  

Ranar suna yarinya taci sunan Yasiraht, kulawa sossai Yasir yake bata. Goyo wankinta har kayan kashi tun Hajiya Nafisat na hanashi harta zuba masa ido in yai wani abun sai dai tai murmushi tace "yarinta".

Kwanci tashi Yasiraht ta isa yayye aka yayyeta, ranar ansha kuka da rigima sossai dan Yasir kusan kuka ya yi saboda ganin hawayanta. Shekarun Yasiraht uku cif tayi girma sossai ga kyau ga surutu, dungui-dungui Yasir ke koya mata A B C D.........nan da nan ta iya kamun kace kwabo ta'iya zuwa Z.Hakan yasa Hajiya Nafisat ta shawarci mahaifinta ya sata makarsnta. Makaranta mai tsada ya sakata,boko had'e da islamiyya in an tashi boko sha biyu da rabi, ake shiga tahafiz sai shida. Karatu sossai ake a makarantar, Yasir ya tsaya mata wajan lesson da bitar karatu. Tana primary four ta haddace izuf sha biyar mahaifanta sunji dad'i tare da shirya mata k'ayataciyar walima.

Manyan Malamansu da dama sun hallata, tare da jinjinawa iyayanta. Haka akeso idan yaro yayi kokari a yaba masa basai kin kashe kudiba koda biscuit kikai masa kyauta zai ji dad'i ya samu karfin guiwa. Kwanci tashi al'amura suka cigaba da gudana.

Tunda Yasiraht ta shiga aji biyar Hajiya ta haifi kyakkyawar diya wadda taci sunan Yasmin,ba laifi kyakkyawa ce amma bata kama koda yatsan Yasiraht ba. Shigarta aji biyar ta soma adabar gidansu da batun boarding school, lamarin daya daga hankalin kowa a gidan ssboda basa san nisa da'ita.Tun suna lallab'ata har suka soma yi mata fad'a lamarin daya jawo kukanta sossai. Yasir shi ne sarkin lallashi,  a hakan suka zana jarrabawar gama primary tana da shekaru tara cif, abin kaddara result ya fito Yasiraht taci bording school lamarin daya kawo musayar ra'ayi sossai akan tafiyar. Mahaifinta na ganin tayi kankanta, babu yadda zai yi haka ya barta ta tafi saboda farin cikinta Yasir daya jagoranci tafiyar yafi kowa jigatuwa.
Makaranta Mata da ke garin Kano ta dabo tumbin giwa aka kaita S Marafa da Yasar su sukaje tare da ita aka gama komai aka bata JSS1A su Abba da Yasar basu bar makarantar ba sai da suka tabbatar da an had'ata da Senior (Na sama da ita) kafin suka mata sallama tana hawaye Yasar na hawaye yana rik'e da hannunta da kyar Abba ya raba hannusu suka shiga mota suka bar makaranta.

Rayuwan Yasiraht haka ya cigaba da gudana aciki kwalejin mata da ke garin kano tana karatu dai-dai gwar-gwado sam bata faye yawan kawaye ba sai k'awarta d'aya wato Shukura Adam ita 'Yar cikin garin Kano ne nasu yazo d'aya komai tare sukeyi wasu har suna musu lak'ani da 2stars(taurari biyu) don itama Shukura ba baya bace gurin kyau amma ita bak'a ce.

Seniors da yawa suna kawo musu farmaki akan suna son su da School daughter(d'iyar makaranta) duk wacce ta tsare su sai suce mata a gida an hanasu yin School Mummy(uwar makaranta) wasu daga lokacin da sukak'i amincewa musu zasu fara gallaza musu da zangwama.

Yau take Visiting day (ranar ziyara) duk wani d'alibin da ke makarantar yayi kitso tare da wanke uniform d'insa na makaranta kowa ya fito tsaf sabida zuwan iyaye da yayu/kanne, hakan yake a gun Yasiraht don gayu tayi tana jiran iyayenta can taji wata 'yar ajinsu tazo tana cewa wai ana kiran Yasiraht S Marafa a bakin gate(gareji) yihuhuhu!!! Tayi wani tsalle tare da rawa Shukura sai dariya ta ke mata ta ce"kai Yasiraht irin wanan murna haka?". Yasiraht ta juya ido ta ce"ya bazanyi murna ba yau My Yasar d'ina ya zo tare da Abba na da Ummi na ga swt Yasmin d'ina". Shukura tayi murmushi suka mik'e suka sanya kaya suka fita tare.

Ko da sukaje gunsu Abba da gudu taje gun fa rik'e hannusa tare da fad'i i miss you my Yaya na(nayi kewar ka ko rashin ka)Yasar sai dariya ake mata tukun tazo ta rusuna ta gaida su Abba kayan abinci suka kawomata tare da girki mai dad'i haka sukayita hira har lokacin tafiyansu yayi wanda da kyar sukarabu.

BAYAN SHEKARA UKU.......

Wata kyakwan Yarinya muka hango sanye cikin uniform d'in makaranta  ta fito sai zun b'ure baki takeyi, Yasar ne ya kalleta ya ce"My sisi dole yau ki koma makaranta tunda ke kika zab'a da kanki". Yayi maganar cikin tsokana tare da yi mata gwalo biyo shi tayi da gudu zata kwad'a masa jaka dake hannuta ya tsere, Abba ne ya fito wanda hakan yasa suka nutsu mota suka shiga suka d'au hanyar kano tun a mota take kumbura har suka iso makaranta ko sallamar kirki bata musu ba sabida fushin da takeyi, ta saka junior (na k'asa da ita) suka tayata d'iban kayan ta ta tafi hostel.

Sam yanzu bata jin dad'in makarantar sabida an cire Shukura a makarantar yanzu bata da k'awa sai wata Najwa da ke damunta akan suyi kawance dole ba yanda ta iya ta fara bin Najwa sabida Najwa ta faye naci, wani saran da Yasiraht ta samu sam yanzu bata yawan addu'a komai yinshi take batare da ta nimi kariya daga gun Allah ba.

Wata rana ta kwanta cikin mafarkinta ta ganta a cikin dokar daji sai jin tayi ana kiran suna ta kuma muryan bibbiyu yake fita ga daji ba haske ko tafin hannuta bata gani sai daga can nesa ta hangi wani haske cikin sauri ta k'arasa nan taga wasu irin halita tare da jajayen kaya ajikinsu suna cewa" Yasirah mu na gayyatar ki cikin mu ki zo zamu baki matsayi babba". Muryan mutane dayawa takeji take ta toshe kunnenta aiko sai guri ya fara tsawa rugugugu!!! Tamkar zai zaga kasa ta shiga ciki ko ina na jikinta b'ari yakeyi.

Kasan gurin ne ya fara darewa gida biyu nan tasoma ja da baya tana gudu yana tsagewa ko da ta kalli cikin k'asan da ya tsage ba komai ciki face kogon jini da kwarangwal suna kiranta. Cikin ihu da k'araji ta farka sai gumi takeyi sam ko addu'a ta kasa bare tasamu nutsuwa Sanah ta ce"ni ko anya Yasiraht tana addu'a?". Can na tsaya tunani na ce" ni dai ganina da ita na k'arshe da tayi addu'a tun tana JSS2 aji biyu a zango karatu na farko(first term) Sanah ta jin-jina kai(lalle tana sakaci da addu'a kamar yanda wasu acikin mu suke wasa da addu'a ma kansu bare 'Ya'yansu dan Allah mu kula muringa addu'a don neman kariya Allah ya kare mu da iyalan mu ameen).

Tun daga wannan lokacin aka shiga tsorata Yasirsht, tana gayawa Yasar musamman in yazo mata visiting amma data ayyana hakan sai wani gaggarumin tsoro ya dumfari zuciyarta. Lamarin daya haifar da tarin k'alubale cikin lamuranta na yau da kullum ta soma bak'i da rama ga yawan kad'aici da san kusantar wajan da babu hayanniya musamman dajin cikin makaranta, Lokuta da dama can take tafiya, tai ta shawagi tana yawace-yawacenta.

Abin ya soma ta'azara a gareta, musamman in zata ci abinci ko ruwa sai taga sun sauya launi zuwa jini. Gashi met d'inta sun fara damunta idonta yana tsoratasu saboda rikid'ar da yake yi. Ana haka kwatsam wata rana Yasar ya kawo mata ziyarar bazata shi da Yasmin tayi murna sossai. Suna tsaye suna hira,Yasiraht ta hango abinda yasa ta dinga jan baya..........

Wani k'adangare ta hango suffarsa sake, irin ta mutane ya mik'e yana tafiya zuwa wajan da suke. Dariya yake mata sossai ya bud'e hannayansa yana fad'ar"maraba da mataimakiyar shugaba ki zo garemu zamui miki kyakkyawan masauki".Wasu hallitu masu kawuna suka bayyana gefansa, suna masu biyo bayansa bakunansu biy-biyune wata giggitaciyar k'ara ta saki tai baya. Yasar yai saurin kai mata cafka, lau ta fad'o jikinsa babu numfashi babu alamunsa.
Hankalinsa ya tashi sossai, da sauri ya bude motarsa yana neman ruwan da zai yayyafa mata da kyar ya dai-daita nutsuwarsa ya samo yana zuba mata ta saki  ajiyar zuciya ta dawo hayyacinta.Zuba mata ido ya yi yana nazarinta.

"Lafiya Yasiraht? "
"Babu komai".
Ta bashi amsa tana inda-indar rashin gaskiya kai ya jinjina kawai suka cigaba da hira jikinsa a sanyayye.

Sun dad'e suna hira kafin ya bata sayyya sa suka mata da 'yan kud'ad'e suka mata sallama cike da kewar juna suka tafi, ita kuma ta dawo hostel tana kewan gida kayanta ta jera a locker tana gamawa ta kwanta a kan gado tare da lumshe ido tana tunanin gida don yanzu duk makaranta ya isheta baran ma da Shukura ta bar makarantar sai da lokacin sallah magriba yayi sannan ta tashi tayi alwala ta nufi masallacin makaranta.

Read More

Share this

WhatsApp

Wednesday, August 30, 2017

'YAR TALAKAWA Part 7 (THE END)

 August 30, 2017     'YAR TALAKAWA 1-END     No comments   

'YAR TALAKAWA Part 7
.
Bayan kwana biyu, kullum prince cikin tsokanar neena yake, har abun ya fara koleta, ta kira mum tace a kawo mata ameer yau dan Allah.

Prince na falo a zaune, yana amsa wayar gadon shi, amir ya shigo da gudu cikin falon, yana kiran papa! Papa!...
Prince ya saki baki, yanzun nan yake da niyyar tashi yaje ya dauko shi.
    Inna ladi ce ta shiga falon itam..
   Neena dake daki, tana duba last question pepper din da sukayi, taji karar amir..
   Da gudu ta fito daga dakin..
Tace da karfi, my little. ...!
Amir ya saki papa dinsa, yayi gurin ta da gudu yana dariya..
   Inna ladi tace, a'a gida masha Allah, Allah ya kawo zuri'a tayyaba..
  Prince ya kallo neena, yaga ko a jikinta, tace inna ladi zauna mana na kawo miki juice. ..
  Inna ladi tace a'a barshi, gadai abincin ku na dare nan...inji mamin ku..
  Neena ta amsa basket din tace mun gode, ki gaida min su..

Da daddare, prince yaji su neena shiru, da kamar yanzu tana fitowa kallon wani series, amma yanzu yaji ta shiru..
   Ya mike ya nufi dakin ta...
Yana bude kofa, neena na tullo pillow, pilon ya buge masa fuska..
   Yadan daure fuska, miye haka kukeyi?
  Amir yace, wasa muke papa, ai grany mami tace yanzu anty ta zama momma dina, shine muke celebrating. ..

Prince karaso cikin dakin, yazo dai dai wurin neena, yasa hannun yaja mata kunne kadan...
  Babba dake kike biye wa amir ko, ji yadda koka yamutsa dakin...
   Neena tayi yar kara kadan, zan gyara ai...
  Prince ya saki kunnen ya fice...
  Amir daya kura musu ido yace, a zuciyarsa.
I wil make momma n papa, friends. .ya kalli neena yaga tana luliya kunnen ta...
    Ya turo baki, momma na jin zafi kuma papa ne ya jawo...
  Yazo wurin ta, yaja hannunta, ya zaunar da ita a gado, ya hawo gadon yazo yana luliya mata kunnen, neena taji son yaron ya karu a zuciyarta..ta jawo sa jikin ta, ta rungume shi...tace I will always be wit u my little.

Da sassafe, sunday, amir ya riga su tashi, yaje ya hawo kujera ya bude kofar baya, ya dauki leda, yaje ya samo kyankyaso guda biyu, dama yasan neena da tsoron kyankyaso...

Ya dawo cikin gidan ya shiga toilet, dinta ya ajiye kyankyasan a wurin da take ajiye brush da sabulu..
    Ya dawo dakin prince ya kwanta dama acan ya kwana...

Neena ta tashi, tace ohh God, nayi latti yau, ta mike, daga ita sai singlet da wando iya cinya, kanta duk ya barbaje saboda barci...
       Amir ya bubbuga prince, papa papa! Prince ya mike yace miye ne?
Amir yace zanyi brush, prince yace kaje toilet kayi mana, amir yace brush dina na dakin momma..
  Prince ya mike yana cewa, ka cika rigima wallahi...

Ya nufi dakin neena, dama kusa ne da nashi..
.
Neena kuwa na shiga toilet, ta kwabe kayan jikin ta, dama ita first thing da takeyi da safe, tayi brush tayi wanka...
   Tana gama daura towel, ta nufi wurin ajiye brush, tazo dauka, taga wasu kyankyaso a ta wurin suna yawo...
   Ta saki kara...wayyo Allah na.....da karfi tayo waje..

Dai dai nan prince ya shigo dakin...
  Tayi wurinsa tana nuna toilet din...
  Prince ya ce miye ke kuma?
  Neena ta kankame shi tana nuna toilet, akwai akwai uhm kyankyaso a ciki wlh...
    Prince din yadda take kamkamesa, duk sai yaji wani yarrrr, da kyal ya iya saita kansa...
   Ya banbarota, ya rike ta..
  Is ok, bari na cire...
  Ya shiga toilet din, ya dauko su guda biyun..
   Yaje ya yarda ta window..
Neena na nan tsaye...ya dawo yace ki shiga kiyi wankanki na cire...
   Ta make kafada, ni bazan shiga toilet dincan ba yau...
Prince ya wani kura wa surar ta ido...
  Yadda taga yana wani kallon ta, up n down..
  Ta kalli jikinta, da sauri...
Tana ganin towel ne kawai ko cinyarta bai rufe duka ba..
  Ta ware ido ta kalli prince..
Tace miye kake ta kallo nahaka, tayi saurin jawo hijab dinta dake saman sofa, ta rufe jikin ta..

Ranar dai a toilet din prince tayi wankan.

Washegari, amir da neena na falo suna breakfast. .
Prince ya sauko shima,
  Ya zauna, ya shiga zuba abincin yana ci..
  Amir ya kalli neena ya juyo kuma ya kalli prince..
Ya mike yace after breakfast lets pay a game..
  Prince yace noo..
Amir ya turo baki pls pls, neena tace zamuyi little dont worry..
Prince ya kalli neena zamuyi? "Zamu" meaning?  Ta amsa dani kenan.
    Amir ya hau murna..
Suna gama cin abincin..
  Aka shigo falo, amir yace momma n papa group dinku daya..ni ne zan nemo ku..
  Ya rufe idon shi.
Ku boye kafin nayi counting 10.
Prince da neena sukayi wani tsaye...
  Sai jin amir sukayi yana fara kirgawa abunsa..
   Har yakai 5...6....7....
  Yana kokarin cewa 8..
Suka bazu neman wurin boya...
  Neena ta boye a bayan table, taga dai zai ganta ta mike..
Prince ya boye bayan kujera yaga dai nan ma za'a ganshii..
Suka mike a tare suka kalli juna..
  A tare idea din boyewa karkashin dinning table yazo musu. ..
   Amir na 9.....sukayi gudu da sauri suke shige karkashin table din..
Dai dai amir ya tsaya...
Prince da neena suka kurawa juna idoo..
Prince yace a hankali, meyasa kika biyo ni nan?
Neena tace, na tuna dana boye a karkashin table din garden, dad bai ganmu ba..
    Prince zai yi magana, ya hango jelar gyelen neena yadan fita waje, amir zai iya gane suna wajen...
   Yayi saurin jawota, ta matse dashi sosai, har bugun zuciyarsu suna ji...
     Prince ya dago fuskarta, yana kallon cikin idonta...ya fara matsowa da fuskarsa kusa da nata...
  Yazo dab da fuskarta sosai, har lumfashin su na cin karu dana juna...
  Ya kai lips dinsa kan nata..
Da sauri ta runtse idonta...
  Prince yayi kissing din ta....
Neena taji duk jijiyoyin jikinta sunyi sanyi, kirjinta kuwa sai bugawa yake..
_Dis is my first kiss_.......

Amir ya gansu da dadewa, amma bai musu magana ba, sai ma komawa yayi falon ya saka cartoon dinshi yana kallo..

Karar TV din ta dawo da su daga duniyar da suka lula...
   Neena tayi saurin matsawa ta fito..
Haka shima prince....kasa yiwa amir  magana sukayi ma...suka koma dakinsu.

Da daddaren ranar, amir yana ta kalon prince, yana aiki a computer, harya gama amir na nan na game..
   Ya cire kayansa, ya  shige toilet,  amir yayi murmushi, I took away his towel, ya dauko towel din daga under pillow ya ajiye kan bed din..
Dama yasan papa dinsa, idan yayi wanka to towel yake kasawa ya fito..
Baya iya maida kayan daya cire....

Amir na nan zaune, prince yace daga toilet. ..
  Amir.... miko min towel dina, I forgot na shiga dashi...
Amir ya mike da gudu..
Ya fita zuwa dakin neena.
Ya iske ta suna waya da zuby..
Yace momma, papa yace kije yana kira..
Neena tadan hade yawo, ta mike ta fita..

Tana shiga taji yana kiran amir...
Give my towel son, jin amir ya masa shiru, yaja tsaki, mayb ma yayi ficewar sa...
  Ya bude kofar toilet din....
  Ya fito....daga shi sai wandon ciki..
   Neena najin bude kofar ta kalli wurin
Sai ganin prince tayi ba kaya...
  Ta saki ihuuu...
Tayi saurin rufe idon ta..
Ta juya zata gudu...
  Amir dake tsaye wurin kofar, ya kulle da sauri ya saka key...
Yayi murmushi, momma da papa, sai kun shirya zan bude ku...I saw it in a cartoon, d bad guy n good guy, an kulle su a wuri daya, kafin gobe suka zama gud friends. ..yayi murmushi ya wuce dakin neena yaci gaba da game..

.
Neena jin kofar a rufe..ta tsaya ta kasa juyowa.
Prince yace waya ce ki shigo dama..
   Neena tace bakai ka kira ni ba..
  Prince na saka kaya yace , ni ban kira ki ba..kice dai kinzo wurin mijin ki kawai...
  Neena ta runtse ido...
Ni ka bude min na fita..
Prince na gama saka kayan barcin sa..
Ya tako wurin ta...
Yazo ya sagala hannun sa a kugun ta..
  Ta ware ido da sauri..
  Prince ya kwantar da kansa a kafadarta..
  Naso da , na barki sai nan da one yr, amma tunda kika kawo kanki I cant help it....
  Neena tayi saurin cewa, ni ban kawo kaina ba..kai fa ka kira ni...jikinta na rawa..
    Prince ya juyo da ita, ya daura yatsan sa a lips dinta...
Shiiiiiiish....
   Kada ki damu, it wont hurt dat much....
  Neena ta kware baki, wayyo ya prince..., ni wlh bani na kawo kaina ba, ka barni na tafi pls, naji one yr din yayi......

Prince yayi dariya....ya sauke ajiye zuciya, ya shafi hancinsa...
   One year, let me see 🤔....neena ta kura masa ido tana jira taji mai zai ce...
Ya kalle ta, na fasa ma gaskiya. ..I need a baby...amir kuma kani zamu basa..or maybe kanwa ko? Nasan ku mata akwai son baby gal..

Neena ta sake kware baki, wayyooo ya...kafin ta karasa..prince ya jawo ta, ya hada bakin sa da nata....
    Neena sai mutsu mutsu takeyi...
    Prince ya rungume ta tsam a kirjinsa.....
  Ya rada mata a kunnen ta...
*I love u so very much my neens*  
I know kema kina sona koh? Yayi saurin tasowa ya kura mata ido...
  Neena ta kasa furta komai, dan harshen ta dayayi mata nauyi, prince yace idan baki amsa ni ba, I will...ya matso da bakin sa..kiss u...
  Da sauri tace _I love u too_
Prince yayi dariya..I know  ai ya shafi fuskar ta tunda am gud looking. ...neena ta turo baki, wasa nake nima, I dont.....
  Bata karasa ba taji bakin prince a kan nata...
    A nan ya dauke abarsa, ina ganin ya ajiyeta a kan makeken gadon sa...
     Nace abun yazo fa
Make I find my way. ..
    .
Da asuba ya taimaka mata, tayi wanka tayi sallah, ya bata magani tasha, sannan suka koma barcin su, prince gaba daya yana cikin farin ciki.
Karfe 8 ya farka, yayi wanka ya zauna amsa wayar general.
Harya gama neena bata tashi ba..
Ya dawo ya zauna wurin ta yana kallon kyakkyawar fuskarta.
Ya kai bakin sa goshin ta..
Ya sumbace ta..
    A nan yaga idonta sai rawa yakeyi...
Kamar dai idan mutum na barcin karya...
Yayi dariya...
   Ki bude idon ma na gano ki..
Neena ta sake runtse idon ta ja blanket ta rufe kanta a ciki...
Har mintina sha takwai  neena na cikin blanket, taki fitowa..prince ya rike kugun sa, mrs Na'im alkali, get up nw...or else. ...kema kin sani, second round....bai gama maganar ba.
  Neena tayi saurin ture barkon...ta fito....ta shagwabe fuskarta....ya prince wallahi bana soo...
    Prince ya kwashe da dariya...oh really....ya haye saman gadon shima..
   Mrs Na'im alkali, na zata ke jaruma ce ai....but tunda rakguwa ce....zan nemo wata sweet hrt din...
    Ya daure fuska yana jawo wayarsa...dama akwai wata chick..data dame ni wai tana sona..let me call ha nace nayi accepting. .
.
Neena ta turo baki, nii nii taga dai da gaske  kiran zaiyi...ta hannu ta kwace wayar.....
  Prince yace bani wayata.!. Neena taki basa..
Prince ya shiga neman wayar a jikinta...
   Neena kara boye wayar tana cewa, ya prince Allah har nw inajin zafi stop it....prince yayi banza da ita...can ya fara mata cakulkuli....
  Ta fara kyalkyata dariya...
Amir na fitowa faga dakin neena..yaji muryarta tana dariya..
Yace yes" momma n papa sun zama frnds nw..
  Yaje ya saka key ya bude kofar dakin....
   Ganin su yayi suna wasan su a a saman gado...shima yaje da gudu ya haye...
  Yace papa...I will help u...ya shiga taya prince suna ta yiwa neena cakulkuli..tana ta dariya harda hawaye...

Bayan sati biyu, prince da neena sun shaku da juna, kullum suna manne da juna, amir baya takura su, cos mai lessons dinsa na zuwa.

Kullum tana waya dasu mum da mami, harma dasu  zuby da zarah, umma da yayaB suna kiranta suma...

Hankalinta a kwance, tare da mijinta da yaronta..
  Kullum cikin sata farin ciki suke..
  Yau suka shirya ziyarar zarah da zuby..
Sai da tayi ta rokonsa sannan ya amince zai kaisu..
.
Sun samu su zarah da yusuf lafiya, sai cin amarci akeyi..

Daga nan suka leka wurin zuby, tayi farin ciki sosai da ganin su...
  Neena sai tambayar yayan takeyi..zuby tace kedai ko wurin sa kikazo ba wurina ba...
Neena tayi dariya ta rungume zuby...wurin sis dina nazo.
  Sun shiga daki...zuby tace..ya yayan nawa ni, hope kuna zaune lafiya?
   Neena tace lafiya lau, ai duk yadda kuka dauki ya prince Allah ba haka yake ba, hes cool n.....zuby ta rufe mata baki, I knw I knw...
  Dama yanzu kina crazy inlove dinshi...ai bazaki fadi bad side dinsa ba...

Daga wurin zuby, amir yace, papa muje wurin baby intee, nagan ta, neena tace yes...pls...ta hade hannayen ta..
Prince yace like mother like daughter. ...

Yakai su gidan faruk, deeja taji dadin ganin su sosai...
  Neena na rike da intee sai wasa take mata..
Prince yadan karkato wurin ta..
Yace very soon
Zamu samu namu ko..neena tayi saurin kallon shi.
Ya kashe mata ido daya
Ta dauke kanta tana murmushi....

Bayan wata daya da auren su, results din neena sun fito ta samu grades masu kyau, prince ya koma bakin aikinsa, kullum sai sunyi yawa sau 20 or fi ma...
    Amir na mutukar kaunar ta, suna zuwa gaida mum da mami every Friday,  sannan suna zuwa gidan da sadeeq yabar wa su umma da yayaB..yana zama da zuby a gidan da company suka bashi...

Yau juma'a prince zai zo weekend. ...
  Neena ta shiga gyara gidan ta....
  Ta shiga dakinsa, ta shiga gyara sosai...
Dan ya jima baizo ba..
  Tazo wurin computer dinshi, books dinta ke wajen ta dauko, uhmm bari na maidasu a laka, tana dauka, wani picture ya fado daga cikin daya daga cikin books din..
  Ta duka tasa hannu ta dauka....
   Wata kyakkyawar mata ta gani...
  Ta dauka tana kallon matar, kamar ta taba ganin ta...
  Ta samu bed side ta zauna..
Ina ma na taba ganinta?
Ta kurawa pic din ido
Yes a kasuwar fruits dinmu..years back...
Matar nan data kirani *YAR talakawa* ya akayi pic dinta yazo nan?
Kuma wacece?
kuma ya akayi my prince charming ya samu pic dinta?.....
.

Tana juya bayan pic din taga an sa, *lateefa* ta mamaita sunan, lateefa???

Can a kasa falo taji sallamar zuby, amir na gaishe ta..
   Neena ta ajiye pic din a bed din prince ta fita.
    Da murna ta tari zuby..suka koma dakin ta, ta kawo wa zuby ruwa da juice ta ajiye mata..
    Zuby tace neena lafiya dai ko, naga fuskar ki kamar kina cikin damuwa...
    Neena ta zauna a bed gwajab, tace yaya zuby, nima bansan meke damuna ba, pic din wata na gani a dakin ya prince dazun, zuby tayi murmushi, kishi akeyi kenan, wacece ita? Neena tace bansan taba amma naga ansa lateefa a bayan pic din..
     Zuby tadan ware ido, lateefa?
Neena tayi saurin mikewa, kin san tane?
   Zuby tace dauko pic din na gani, neena ta mike ta koma ta daukowa zuby pic din..ta mika mata.
    Zuby ta kalli pic din tace, wannan itace....sai kuma wayarta tayi ringing, neena ta kasa sukuni, wacece wannan?
   Ta kagara zuby ta gama wayar..
Sai tada dan dade sannan ta ajiye wayar, tace yayanki na gaishe ki..
Neena tace ina amsawa, wacece wannan anty zuby?
     Amir ne ya shigo dakin, da gudu, yana cewa, momma I will be going to garden malam yazo..
  Neena tace ok my little, pls behave ur self kaji, amir ya kada kai ya fice..
 
Zuby tace _lateefa_ itace matar ya prince da suka rabu shekara da shekaru, lateefa itace mahaifiyar ameer...
     Gaban neena ya buga duuuum dumm, ta runtse idonta...tace tana raye daman?
  Zuby ta dafa neena tace *Eh tana raye* neena ta sulale kasa gwajab, ta dafa kanta, zuby ta sauko ta rungume ta, sis kada kisa damuwa a ranki, ya prince yana kaunar ki sosai, kuma lateefa bata ma a kasar nan yanzu...
.
Neena ta dago idonta daya fara canza launi, anty zuby, meyasa ba wanda ya sanar dani?
    Zuby zatayi magana wayar ta ta sake ringing, ta dauka tace,my hrtbeat ina nan fitowa yanzu...
   Zuby ta lallashi neena sosai, sannan ta tafi...

Gaba daya hankalin neena ya kasa kwanciya, da kyal ta kammala abinci, ta saka turaren wuta..
  Ta koma dakin ta ta kife a gado..
Mai ya faru suka rabu? Bacin har karuwa sun samu?

Da yamma prince ya shigo gidan, amir kawai ya iske a falo, amir ya rungume sa yana masa sannnu da zuwa.
  Prince ya shafa kansa, ina momma dinka?
  Amir yace tana dakin ta, prince ya haura sama..
  Yana mamakin rashin zuwa tarbarsa da batayi ba..
 
A kwancen ya iske ta, yazo ya zauna kusa da ita, ya hura mata iska a ido..
   Taki motsawa, gaba daya haushin sa takeji, mai yasa bai taba fada mata ba?
   Prince ya tallabo ta, taki ko motsawa, idon ta ma a rufe suke, ya zaunar da ita ya jinginar jikinsa, ya matso da fuskar sa daf da tata, yace mrs Na'im alkali, wat is wrong uhmm?
   Kimin magana pls, neena ta bude idon ta, prince yace subhanallah, mai ya sami idon haka, yayi ja, neena tayi banza dashi, ya mike ya cire jacket dinshi ta kayan soja, sai farar shirt dinshi ya bari ta ciki..
    Ya riko hannunta, tashi muje asibiti, neena ta kwace hanninta, ta juya masa baya...
  Dama maman amir tana nan? Dama ba mutuwa tayi ba? Dama....ta saka ida sawa sai kuka ya kufce mata...

Prince ya runtse idonsa, dan kukan har cikin ransa yakeji, ya zauna a bed din, ya jawo ta ya rungume tsam, tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa....
    Ya dago da fuskarta, suna kallon cikin idon juna..
  Zan fada miki komai, amma bana so bayan nan ki guje ni, kinji...
Neena ta kada masa kanta..
Yace yauwa, amma sai na fara yin wanka, naci abinci koh?

Neena ta kada kai, yace good gal, muje toh a taya ni..
Kuma ki daina sa damuwa a ranki,..
  I love u...I love u...n I am for u alone...
Kinji?
   Tayi murmushi...prince yayi back hugging dinta, yayi mata kiss a kumatu, mrs Na'im alkali, bakice kina sona ba ke?
Neena ta rufe fuskar ta, tace I love u too so much my prince charming. ..ta juyo ta rungume shi..
.
Sai da prince yayi wanka, ya kwashi girki, sannan yajawo neena dakinsa...
     Ya zaunar da ita a saman gadon, sannan shima yahau ya kwanta, ya dora kansa a cinyar neena..
Neena ta shafa gashin sa,tana jiran mai zai ce, prince ya jawo hannunta ya sumbata..
Sannan yace, mrs Na'im alkali, nasan kin kagara, kiji yadda muka rabu da lateefa ko?
Ta kada masa kai...
Ya runtse idonsa ya bude..ya saukar da lumfashi...
.
kafin na fara aikin soja, nayi nayi da su dad su barni naje makarantar sojoji, amma suka ki, sukace sai nayi decree dina da masters.

A kasar china, sha daya ga watan June, 2008, a wani restaurant, na hadu da lateefa, ta siya abincin amma ta manta credit card dinta, kuma bata da kudin biyansu, inajin su da masu restaurant din, tana rokon su, amma sunki yarda, na mike naje na biya duka tare da ita, cos yadda naji masu shop din na cewa sai ta musu wanke wanke.
   Bayan na biya mata, tazo tamin godiya sosai, har mukayi exchanging nums.
.
A university din da nake karatu, anan muka sake haduwa da ita.
   Munyi mamakin ganin junan mu sosai...
    Anan muka san school daya mukeyi..
   Mun fara shakuwa da juna sosai, har muka fara sanin sirrin junan mu, muka shaku sosai da juna...

Babanta , babban dan kasuwa ne, mai kudin gaske a kaduna..
  Amma mahaifiyarta ba mutuniyar arziki bace, yar business ce sosai.
  
Munyi shekaru biyu muna soyayya da lateefa...
Har na kammala masters dina a shekarar 2010, na dawo gida, nayi applying neman soja..
   Na samu  su dad  na fada musu aure nake so, sunyi bincike akan family dinsu lateefa sosai, mum tace bata yarda ba, saboda irin halayen  maman lateefa da takeji....
  Su abba ma suka ce basu yarda ba, na hakikance ni sai sun aura min lateefa.
   Da kyal suka yarda, akayi bikin mu da ita.
   Watan mu daya na samu aikin soja, aka maidani lagos, kullum muna kan aiki ba hutu, lateefa kullum cikin complaining take.
har dai mahaifiyarta ta gano halin da muke ciki, tazo ta ringa daukar diyar ta suna yawon kasashe suna business dinsu...
   Abun nan ya dame sosai, har su dad suka zo sukaji lbrn.
  Ba karamin fushi sukayi dani ba.
  Ana cikin haka, mukaje libya wani aiki, na kamu da ciwon zuciya da kidney failure. ..
Saboda tunani da yayi min yawa, da kuma rashin cin abinci.ga aikin karfi da muke.

An maido ni abuja wurin iyayena.
, abun haushin ma, su lateefa na kasar Cyprus lokacin.
   An min treatment sosai, amma shiru rashin lafiya sai karuwa take, dan basu gano kidney dina bata da lafiya ba..
An kaini india, anan suka gane, har koda ta sai an cire.
, sun min kedney transplant, lateefa zuwan biyu kawai dubani, saboda yanzu idonta ya bude da manyan masu kudin da suke business dasu.
  Mahaifiyarta ta zuga ta sosai, gashi lokacin tana dauke da cikina, ni banma saniba.
An maido ni gida nigeria,ina ta jinya, har wurin watanni biyar, na rame nayi baki, saboda yadda nake jin jiki.
  
Na dan fara samun sauki, dan iyayena na kula dani sosai, mami da mum suke jinya ta, lokacin zuby da zarah da faruk na makaranta.
  Ba karamin haushin lateefa naji ba, ko zaman jinya ta batayi ba? Zuwa gaishe ni sau uku kawai tayi, wai tana da abunyi..
    Ina wata na 9 da cinya, ta kawo yaro jinjiri ta bawa mai gadin mu, tare da letter
.
   Abun nan ya bala'in bawa iyayena haushi, suka tsaya akan na bata takarda kawai, dan rashin imanin ta yayi yawa, aikuwa, na rubuta takarda aka bawa wani ya kai musu kadunan.
    Mum da mami suka ci gaba da kulan min da amir, bayan dad yace aje ayi test a duba ko jini na ne.
Test ya nuna amir dana ne.
  Bayan na samu sauki na koma bakin aikina.
Toh har yau da nake baki labarin nan bamu kara haduwa da lateefa ba.
.
Neena ta share hawayenta, ta rike hannun sa, insha Allah bazan taba gudun kaba my prince charming, ko wane irin ciwo kayi, ko wane irin aikin kakeyi, I will always be by ur side....
   Prince ya mike ya zauna, ya rungume ta, yace I knw mrs na'im alkali, bazata iya kyamata ba, ko a wane irin hali nake zata kaunace ni.
   Neena ta kada masa kai, ta kara matse shi a jikinta, ba karamin tausayawa amir da prince tayi ba, ta dauki alkawarin kula dasu har karshen rayuwar ta....

.
.

Bayan sati biyu, su amir suka samu hutu.

Prince yazo weekend, suna falo suna kallo abunsu, amir ya juyo ya kalli papa dinsa, papa can we go for a vacation?

Neena ta kalli prince tana jiran taji mai zai ce, prince yace no son, ur momma wil start school, next week.
  Amir ya shagwabe fuska,plss papa, ai zamu iya zuwa for 1 week, plss
   Prince ya kalli neena, tayi saurin dauje idon ta daga kallon shi, yace okay okay zamuje....
   Amir yace papa, lets go to Italy. ..
Neena taji gaban ta ya fadi, take ta tuna da mahaifin su daya barsu..
  Prince yace yess son nice one, amir ya kawo hannu sukayi high five..

Prince ya nemi hutun sati daya..
Sunje gidan su umma da yayaB sun masu sallama, sannan sukaje wurin su mum da mami, sukayi musu suma, anan suka iske deeja da zarah, suka danyi fira sannan suka wuce.

Washegari, sadeeq da zuby suka zo suka kai su airport.
     By 9 jirgin su ya tashi....
  Sun isa Italy lafiya, prince ya sama musu hotel mai tsadar gaske...

Kwanan su biyu suna hutawar su a hotel din, suyi games dinsu har su gaji.

Yau sun shirya fita ganin gari, neena taci gayun ta, cikin English wears, riga three quarter sai wando skinny jeans. .tayi rolling gyelen ta, ta dauki gucci side bag dinta..
    Prince da amir ne suka shiga cikin dakin, amir yace momma kinyi kyau.
Neena tayi murmushi, ta duko tayi masa peck a goshin sa...
Prince yace saura papa shima..ya miko mata bakinsa ya kulle ido....
   Neena tayi murmushi, ta jawo hannun amir suka yi saurin ficewa daga dakin suna masa dariya..yana bude idon sa yaga sun gudu, yaya murmushi yace zamu hadu dake ne...

.
Sun sha yawo sosai ranar, sunyi pictures ba adadi...
   Sunje wani side fast food restaurants.
   Prince yace musu, ku jira ni a nan, ya shige cikin shop din..
   Suna nan tsaye suna fira da amir..
   Wani mutumi yazo shiga shop din, dai dai wurin su neena, ya dafe kirjin sa, sai ganin sa sukayi ya fadi a sume....

Neena ta rikice, tazo wurin sa tana bubbuga shi, mutumin da ganin sa dan nigeria ne...suna nan a wurin mutane sun zagaye su, prince ya fito daga shop din dauke da ledoji kuda biyu...
   Yana ganin halin da ake ciki, neena tace my prince mu taimaka wa bawan Allahn nan, da gani sa kasar mu daya..
   Please yadan tsaya na wasu minutes, sannan ya nemi taimakon wasu suka saka shi a taxi dinsu, suka tafi kai shi asibiti....

An musu bayanin cewa mutumin ya kamu da ciwon zuciya saboda tunanin da yayi masa yawa...

Sun tausayawa bawan Allahn sosai..
  Suka shigo dakin da aka kwantar dashi..
  Lokacin yama farka, ameer na basa labarin yadda momma dinsa da papa dinsa suka taimaka masa..
Suna shiga mutumin ya kurawa neena ido...
  Sukayi masa sannu..
Ya amsa yayi musu godiya..
Prince ya shiga tambayarsa ko dan nigeria ne.
Yace kwarai daga nigeria yake..
Prince ya fada masa abunda likita ya fada musu.
Sai ganin shi sukayi yana kuka.
Prince da neena suka shiga lallashin sa.
Prince yace idan ba damuwa suna so su san maike damun sa.
   Mutumin ya fada musu, yayi wani babban kurkure ne a rayuwar sa, yanzu abun ya dame sa amma yasan wadan da yayiwa da wuya su yafe masa.

Sun tausaya masa sosai.
Prince yace kada ya damu, zasu taimaka masa da addu'a amma yaje ya nemi gafarar mutanen nan.
Ya amsa da toh, inshaAllah cikin satin nan zai koma nigeria.
Prince ya amsa card dinsa, shima ya amsa na prince din.
sannan suka masa sallama suka tafi..shidai sai kallon neena yakeyi, itama sai kallon sa takeyi.

Sun sha hutun su, cikin jin dadi, sun yo wa yan'uwa tsaraba sosai.

Ranar da suka dawo,gidan su mum suka sauka, sai farin ciki sukeyi, kowa yazo gida ana ta fira da barkwanci.
    Sai dare dukka yaron suka yiwa iyayen su sallama suka tafi gidajen su..
.

Bayan shekara biyu...
   Neena na gani za'a shiga da ita dakin haihuwa, mum, mami, umma, yayab, zuby da wata yar baby a hannunta, sai zarah da tsohon ciki, deejah da intee dinta, suna ta zarya a bakin labour room din...

Faruk da sadeeq suka shigo, suka tsaya wurin mami suna tambayrta ko an haihu lafiya, mami tace tukunna dai...
   Prince duk ya rikice, yana kan jirgi dan zuwa ganin yanayin da matarsa ke ciki, sai kiran su faruk yakeyi....

Ya sauka daga jirgi, yazo daukar mai taxi, dan ba wanda yazo daukarsa..
    Wata katowar mota ta tsaya a gaban sa...
   Aka sauke mirror, prince na kallon cikin motar yaga wannan mutumin da suka hadu a Italy, mutumin ya sakar masa murmushi, yace shigo mana Na'im...
   Prince ya shiga shima yana murmushi..
  Mutumin yace, naji dadin kara haduwa dakai, dama a abuja kuke ne? Prince yace eh, yanzu ma matata na asibiti zata haihu...

Mutumin yace Allah ya sauke ta lafiya, nima nazo neman mahaifiyata ne, da kuma yan'uwana...
Prince yace Allah sarki, Allah yasa ka gansu toh, mutumin yace amin, muje na kai ka asibitin a ina ne?
  Prince yace a maitama ne.

.
Ya ajiye prince a bakin gate, suka yi sallama, prince ya basa address dinsa.

Prince na cikin buga sauri dan zuwa wurin matarsa...
   Sukaci karo da *Lateefa* wani irin burki suka ci a tare...
  Lateefa na ganin sa ta zube a kasa...
Ta saki wani irin kuka, wanda suke tare yace, lateefa lafiya, lateefa ta rike hannun sa, hafiz hafiz, wannan shine Prince shine na'im, din da muke nema....

Hafiz ya kalli prince, yace na'im ka taimaka ka yafewa matata, I know she did wrong u, pls ka yafe mata...
    Lateefa dake kuka kamar ranta zai fita, tace prince, ka yafe min ka yafe min nasan banyi daidai ba, ka yafe min ko Allah zaisa na sake ganin tsatso na.....

Prince ya tsaya tsak yana kallon ta, ya kalli hafiz, yanzu ina cikin sauri ne, matata na labour room...
Hafiz ya rike hannunsa, yace pls abokina...
   Prince ya sauke ajiyar zuciya, na yafe miki lateefa, amma ki nemi yafiyar danki shima...
   Ta mike da sauri, tace ina yake yanzu.
  Prince yace ga address dinmu, kuzo gobe inshaAllah....yaya saurin tafiya, har yana hadawa da gudu.....

Neena ta haifi diyarta mace, kyakkyawa sosai, kamar su daya da prince....
.
Sun koma gidan su mum.
Dad da abba na falo suna fira da yayab da umma dasu mum da mami, faruk ya shigo ya sanar musu sunyi bako..
Abba yace shigo dashi mana...
   Faruk ya fita ya shigo da bakon...
  Gaba dayan su suka mike..
Yayab tace almustafa kai neh!!!!??
Almustafa ya iso gaban su ita da umma ya shiga neman gafarar su...

Ansha kuka, kafin nan aka yafe wa juna...mum tace bari a kira yaran ku gaisa ..

Taje dakin da neena ke jego, ta kirasu duka..

Suna zuwa neena tayi ta mamakin ganin mutumin da suka taimakawa..
Prince da safeeq suka shigo suma..
  Shima prince yayi mamakin ganin mutumin...
    An dai aka sanar dasu ko waye...
  Neena da sadeeq, suna hawaye sukaje suka rungume baban su...
    Sai sallamar su lateefa sukaji...
  Gaba daya falon anji mamakin ganin ta, ta duga gaban su dad ta basu hakuri...
Hakama mu mum da mami...
Kowa ya yafe mata, yayaB ta nuna mata neena tace ga matar na'im...
   Suka kalli juna, lateefa tayi mata murmushi...
  Sai ga faruk ya shigo da amir...
  Lateefa na ganinsa tayi gunsa ta rungume sa,....
   Ya kalli neena yace who is she momma. ...
   Neena tace shes ur momma also..
Amir yayi murmushi,  lateefa tayi ta kallon yaron, tana sumbatar sa...
   Sai da sukayi mangariba sannan suka tafi, mijin lateefa yace idan ba damuwa, suna so amir ya ringa zuwa musu hutu kaduna...
  Prince yace ba damuwa, sukayi exchange din contacts, ya raka su har gate suka tafi....

.
Ansha suna, an sawa baby suna aysha, amma zasu ringa kiranta hanan.

     Zubaida ta haihu ta samu yaro namiji  ahmad suna kiransa Ayman.
    Zarah na dauke da tsohon ciki...

Baban su neena almustafa, ya kara gyara gidan sadeeq kuma ya dawo da kasuwancin sa nigeria, ya saka sadeeq a matsayin CEO, ya sai wa neena mota har biyu, sannan ya sake musu kayan daki dukkan su harda su zarah da zuby dama deeja.

.
Bayan shekaru ashirin.......
  Na sake cin gayu na naje dan kara samo wa masoyana rahoto..

Wani handsome sarauyi na gani yana saukowa daga jirgi....
  Na goge idanuna...like seriously wannan Amir ne....
Oh my G, ya girma ya zama cikakken saurayi.....

Ya amir ya amir! Over here brother. .....

Wasu pretty flowers na hango, babbar su yar shekaru 22(intee), sai mai binta mai kimanin shekaru 20 (hanan) sai dayar mai shekaru 19 (diyar zarah mai suna salma)
Gaba dayansu sunci gayun su cikin black arabian abaya...

.
Ameer ya karaso wurin su yana murmushi...
     Hanan tayi tsalle ta rungume shi, ya manna mata kiss a kumatu...
    Babbar ta cire sun glasses  dinta, tace welcome back brother,  amir ya kura mata ido, d little intee...ta shagwabe fuska brother kai koh...
   Karamar su ta juya masa baya tana kumbure kumbure...
   Ameer ya kallo ta Oh Oh, matar ya akayi ne?
  Salma tana dariya yeeh. Welcome brother ta rungume sa itama, intee tadan buge ta oh wasa ma kike yi da brother ko? Sukayi dariya duka..
Ameer yace gals lets get going na kagara naga momma dina....

Sun isa babban gidan su dad da abba da suka canza.

Kowa da kowa na gidan lokacin ana jiran babban jika ya dawo..
  Neena na hango sanye da riga gown ta yafa babban gyele a jikinta sanye da glasses. ..sai faman girke girke takeyiwa danta...
   Prince ne ya shigo kitchen din ya dan manyanta daka ganshi  kaga tsohon soja....
.
Yazo yayi bag hugging neena, wat is mrs na'im alkali still doing? Neena tayi murmushi ta juyo tana kallon shi, my prince charming, ta manna masa kiss. ina ka shige ne yau? Yayi murmushi ina tare da Aiman a garden....
    Neena tace nidai kun maida ni maman maza, anty zuby ta kwace hanan...
     Prince yace oh yes, kina da yaro lawyer, ga kuma Aiman soja....
  Neena tayi dariya prince ya janyota jikinsa, yakamata muyiwa hanan sister fa...
   Neena takai masa dukan wasa, shiiiiish a kicin muke...
Prince yayi dariya.....shigowar yayab sukaji, tana cewa ni faruk da sadeeq zasu hadewa kai, har zubaida da deeja zasu shige wa mazan su...
    Nima inada jikata ai, neena neeena, prince ya shige bayan kofa, toh matar nan uwar surutu zata shigo....
    Neena tayi dariya....

Babansu neena da umma, mum da mami, dad da abba duka suna falo suna firan su.....
     Aiman ya shigo cikin murna, grannies guess what?
    Mum tace Amir is back?
Aiman yayi dariya oh yes, my big bro is back yahau tsalle, zubaida tana saukowa kasa falon tace maza ka fadi....
    Amir ne ya shigo falon tare da yan'matan...
   Yayi wurin zuby ya rungume ta aunty, ta shafa kansa, our amir congrats an gama karatu..
   Yayi murmushi ya karasa wurin kakanninsa, ya shiga rungumar su suna sa masa albarka...
   Ya tsaya tsakiyar falon, ya rike kugun sa ya kalli nan ya kalli can...
    Ina dr ? Where's my momma, our dr....?

Neena ta fito daga kitchen din cikin sauri, my son an dawo, amir na korarin rungume ta, yayaB ta shige tsakani....
Ta rungume amir tana washe baki...
  Sannu da dawowa dan albarka....
Amir yace granyB mun same ku lafiya...?
.
Ya janye jikinsa ya rungume neena, ta shafa kansa....my son Allah yayi maka albarka..

Prince ya fito shima, amir ya karasa ya rungume sa...
  Deeja da zarah suka shigo gidan suma, tare da faruk da sadeeq, amir gaba daya cikin farin ciki yake.... 

Yayi wanka ya fito ya iske kowa da kowa  ana fira, intee ta mike da sauri ta kawo masa abincinsa...
   Salma ta mike itama ta kawo masa juice. ..
Hanan ta kalli aiman sukayi dariyar gulma...

Suna cikin firan su akayi sallama, mummy tare da ikram...
Mum, mami, neena, zuby, zarah, faruk, deeja, dad, abba, yayab suka mike...
   Mummy ta karaso cikin falon...
Ikram taje gaban prince ta duka har kasa ta nemi yafiyar sa, neena tazo ta mikar da ita tace mijina ya yafe miki ikram....
   Duka falon sukayi murmushi.  hanan, intee, da salma suka ringa damun amir, brother who's she?
  Ameer yace ur auntie. ..
  Sallama aka kara yi....lateefa da mijin ta hafiz, tare da diyarta minal suka shigo...
    Duka yaran sukayi gunta suka rungume ta....
  Ameer ya rike hannun minal, ta rungume sa itama tace welcome brother, dad yace woo ameer kai kam kannen ka har sunyi yawa...

Gaba daya falon suka kwashe da dariya....

Nima Afrah na murmusa....
  Sannan na bawa phone dina hot kiss, thanks for all your hard work durling...

.
Alhamdulillahi anan muka kawo karshen wannan littafin , sai kuma mun hadu a wani.

Jinjina ga marubuciyar wannan littafin Afrah

Sai ni kuma da nakawo muku Abdullahi Jafar Zaria (AYS) Nake cewa mu kasance lfy.

CALL or SMS
07066508080
.
Whatsapp
07066656752

Read More

Share this

WhatsApp
Newer Posts Older Posts Home

Popular Posts

  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 11 to 20
    Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima.     Casuke A...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 31 to 40
    Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gado...
  • RAINA KAMA Book 1 Page 1 to 10
    RAINA KAMA......!!♦_*                _{Kaga gayya}_          *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!._* 👉🏻1⃣      *Matsanan ...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 21 to 30
    Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”.         Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, murya...
  • BARIKI AUREN SOJA Page 51 to 60
    Motocine guda shida aka ajiye musu sababbi dal suna sheki ta tsakiyar tasha Adon balloon kana gani Kasan motar AMARYA ce ta fito tareda su ...
  • KASUWANCI NA Page 61 to 70
    Ameer kasa jurewa yayi gaba daya jikinsa ya fara rawa,tunawa Meenat tayi ba Muharraminta bane sai ta dan matsa kamar zata fada kasa ta wayan...
  • KASUWANCI NA Page 31 to 40
       A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, d...
  • UMMU AYMANA Part 6
      *UMMU AYMANA PART 6* Suna isa Asibitin likitoci suka rufu akanta,wanda da taimakon Allah bata jimaba ta farfaɗo se kuka takeyi,prince kasa...
  • MIWASMITI Page 31 to 40
    Kuka ta Kuma saki gamida kamo hannushi ta matse a tsakiyar qirjinta Dan jin wani irin suka da yake mata Ga jiri da takeji gaba daya bata gan...
  • MACIJINE SHI Page 31 to 40
    _________________Kai tsaye part ɗin nanny Adeeb ya nufa da fattu,suna zuwa kuwa nanny ta gyara ko ina sai ƙamshi ke tashi,dakin fattu suka...

Categories

  • 'YA'YA DA KUDI 1-END (8)
  • 'YA'YA MATA 1-END (9)
  • 'YAR BOKO 1-END (6)
  • 'YAR FULANI 1-END (14)
  • 'YAR GIDAN TSOHUWA 1-END (6)
  • 'YAR JAMI'A (9)
  • 'YAR MAFIYA 1-END (6)
  • 'YAR TALAKAWA 1-END (7)
  • AGOLA 1-END (17)
  • AKIDATA BOOK 2 Page 45 -End (11)
  • ANAL 1-END (12)
  • ANTIN YARA 1-END (6)
  • AUREN JARI 1-END (9)
  • BAKAR MACE 1-END (3)
  • BARIKI AUREN SOJA 1-End (8)
  • BINTU 1-END (7)
  • CIN AMANA KO FANSA 1-END (10)
  • CIWON IDANUNA 1-END (7)
  • CIWON IDANUNA AUDIO (2)
  • DAGA TAIMAKO 1-END (5)
  • DAKON SO 1-END (4)
  • DAMA TA BIYU 1-END (13)
  • DR BOBBY 1-END (11)
  • DUBU CIKAR MAI CARBI 1-END (7)
  • FULANI 1-END (11)
  • GURBIN IDO 1-END (1)
  • HADIN ALLAH 1-END (8)
  • HIBBAH 1-END (4)
  • INA ZAN GANSHI 1-END (7)
  • INAYA 1-END (9)
  • JIDDARTIL KHAIR 1-End (1)
  • JIHADI 1-END (10)
  • JUWAIRIYYA 1-END (7)
  • JUYAYI PAGE 1-END (6)
  • KASUWANCI NA Page 1-End (1)
  • MACIJINE SHI 1-END (1)
  • MAH NOOR 1-END (5)
  • MAIMOON 1-END (10)
  • MAKARANTAR KWANA 1-END (5)
  • MAKAUNIYAR KADDARA 1-END (10)
  • MATAR ALI 1-END (10)
  • MIWASMITI 1-END (8)
  • MOTAR KWADAYI 1-END (4)
  • NAMIJI BAYA KADAN 1-END (16)
  • NI AYS NAKE SO 1-END (16)
  • RAINA KAMA 1-END (1)
  • RAYUWATA 1-END (6)
  • SHIMFIDAR MIJINA 1-END (3)
  • SONE AJALINA 1-END (5)
  • SURBAJO 1-END (14)
  • TUDUN DAFAWA 1-END (4)
  • TUZURU 1-END (6)
  • UMAR KO FARUUQ 1-END (5)
  • UMMU AYMANA 1-END (8)
  • UMURNIN IYAYE 1-END (7)
  • WAMINAL HOOB 1-END (9)
  • YAN MATAN ZAMANI 1-END (6)
  • ZAYN MALIK 1-END (10)
  • ZUCIYA KOWA DA IRIN TASA 1 (10)
  • ZUMA SAI DA WUTA PAGE 1-END (7)

Social Plugin

  • facebook
  • twitter
  • instagram
  • youtube

Hausa novels 2023

Search This Blog

Powered by Blogger.

Blog Archive

  • July 2023 (7)
  • June 2023 (65)
  • April 2023 (33)
  • March 2023 (132)
  • January 2020 (10)
  • December 2017 (62)
  • November 2017 (33)
  • October 2017 (38)
  • September 2017 (39)
  • August 2017 (75)

Report Abuse

  • Home

Total Pageviews

Copyright © 2023 To Hausa novels 2023 | Powered By WwW.aysnovel.com.ng
Design By Aysha Adam | Theme By WwW.aysnovel.com.ng | Distributed By Aysha Adam