FREE PAGE.
FALMATA POV.
Yola...
Tun tana surfen da kuzari har ta kai bata iya daga tabaryar da karfi, babu komai a tare da ita sai tarin yunwa da gajiya ga wani uban ciwon kai da ya saka ta gaba. Cike da dauriya ta
karasa surfen sannan ta risina tana kwashewa tana zubawa a kwayar da ke gefen turmen, sai da ta kwashe shi tas sannan ta hade da sauran da ta surfe, mikewa tai tsaye tana rike da surfen ta nufi gurin tukuyar ruwansu.
"To mai kunne kashi ban fada miki idan kika yi surfenki ki rika zuwa bohal kina debo ruwanki ba? Ke wai Fulani sau nawa za ayi miki magana ne?"
A wahale Falmata ta kalli Tumba wacce ke mata maganar, ta amsa mata tana jin kamar ta fadi a tsakar ranar da ke dukan kanta.
"Inna idan na gama zan je na debo wasu sai na cika"
"Ban yarda ba, kije ki fara debowa ki yi abunda za ki yi wannan wanda kike debo mana na aiki ne bana wankewa wasu banza surfe ba"
Uffan bata sake ce mata ba, sai ta nufi gindin bishiyar dogon yaro ta aje surfen, sannan ta sake komawa ta dauko wani katon bokoti ta riko shi a hannu ta nufi kofar fita jiki ba gwari, tafiya take a hankali kanta a kasa bata kallon kowa sai hanya, gaisuwar girmama ce abunda yake fitowa daga bakinta sa'adda duk tai arba da sa'ar iyayenta. A yayinda ta isa bohal din sai ta nemi guri ta tsaya tana ta kallon yadda fanfon bohal din yake cike da mutane yara da manya. Matsawa ta kara can gefe tana daga zanenta kamar mai kyankyamin ruwan da ke zube a kasa.
Kallo daya za ka yi mata ka karancin irin natsuwa da tarbiyar dake tare da ita, sa'aninta na gaban fonfon suna gogoriyon dibar ruwa ita kuma tana tsaye gefe abunta tana kallonsu kamar ba diban ruwan ta zo yi ba.
"Falmata kawo na baki bokiti daya"
Cewar Khadija kawarta, abun ka da mai nema sai tai saurin cira kafa ta isa gurin da Khadija take tsaye rike da kan fonfon ta mika mata bokitinta.
"Na gode kawata"
"Karki damu, indai akwai mu ba kya rasa komai kawata"
Khadija ta fada tana daga mata gira, murmushi ne ya fadada kansa a fuskar Falmata ya bayyana fararen hakoranta wanda ya karawa bakar fatarta sheki.
"Yau ba za ki je gidan Sarki ba? Kin san fa ke ce mai gyara dakin yan uku da kula da su"
Khadija ta tambaya tana daga muryar wai dan mutane da ke gurin su san kawarta na aiki a gidan Sarki. Wata irin kunya ce ta rufe Falmata abun ka da bakauyen mutum sai duk ta ji ta muzanta.
"Ke Madam ba za ki ba yau?"
"Na tafi, har na dawo sai kuma gobe"
Ta amsa mata kamar ana matso maganar daga bakinta, gaba daya kunya ta gama rufe ta, kamin bokitin ruwan ya cika duk ta tsawwala, bokitin na cika Khadija ta kama mata ta dora a kai sannan ita ma ta dora nata suka kamo hanya tare.
"Mtswwwww Wallahi Falmata ba ki hadu ba, wai ina son ayi kurin nan ke kuma kin wani noke ba ki ma son amsawa"
Abun nan dai da ya zame mata al'ada ta yabawa fuskarta, wato murmushi sannan ta soma magana da muryarta mai taushi da dadin sauraro.
"Khadija kunya na ke ji"
Wani banzan kallo Khadija tai mata.
"Kunyar me? Aikin a gidan sarki? Allah ya kai Khadija Wallahi har tafiya sai na sauya"
Wannan karon dariyar marar sauti Falmata tai, tana jinjina lamarin kawarta, daman can indai kaudi ne da iyayi da ba ni na iya ba dai Khadija ba.
"To ai na ga ni ban wani dade da fara aikin ba, da har za a ce na fara kuri wannan zuwan da nai dazun fa shi ne zuwana na uku, kuma ni na ga..... "
Sai kuma yai shiru bata karasa ba, sai dai karara yanayinta ya nuna akwai damuwa a tare da ita kamar yadda fuskarta ta nuna akwai tarin maganganu a kasan halshenta.
"Miya faru?"
Tsayawa tai tana kallon Khadija kamar yadda Khadijar ma ta tsaya tana kallonta.
"Sai na ke ganin kamar ba su yarda da ni ba...."
Fuskar Mamaki Khadija tai.
"Ban gane ba?"
"Kin ga tun da aka dauke ni aikin, har yanzu ban ga yaran ba, sai dai na gyara dakinsu, kuma idan zan gyara sai a saka dogari ko wata baiwa sun tsayaa dakin har nai na gama"
"Suna da wulakanci ne?"
"Aa har yanzu ba a taba min ba, ban ga alamun hakan a iyalan gidanba, sai dai da alama suna da wuyar aminta da mutum"
Hannu daya Khadija ta saka ta daga kafadarta.
"Karki damu, daman su yan sarauta basa saurin aminta da mutun, amman dai da sannu za su fahimci kawata mutuniyar kirkice su aminta da ita"
Ta karasa tana dariya tare da rika fuskarta.
"To Allah yasa"
"Amin, kuma bari na fada miki ba wai saboda wannan bakar Tumba ta tura ki aiki dan ki samo mata kudi ba, ba wai duk abunda aka ba ki za ki bata ba, albashin ma rabi za ki bata ki boye rabi, dan alherin idan kin samo karki kuskura ki bari ta gani, ke abinci wannan ma da ki kawo mata Wallahi kara ki 蓳arar dashi a akwata"
Har wani yatsine fuska Khadija take tana jin kamar ace ita ce a matakin Falmata take da step mother kamar Tumba da Allah kadai ya san irin sherin da zata kulla mata.
"Mahaifina yace idan ban mata biyayah ba be yafe min ba, ko da ace bata san yawan kudin aikin ba zan bata dika balle kuma ta riga ta sani, idan ma na hana ta zata iya duka ko taja Baba da kansa ya doke ni, ba ni da wani yanci a gidan nan Khadija kin sani"
"Hmm ai har da ke Wallahi da kike biye mata, ke ko yar ketar nan ba ki iya ba, Wallahi da ni ce da sai ta sha wuya, shiyasa na tsani shegiyar matar nan bakar Tumba kawai"
Falmata da dai bata ce mata komai ba, ta cigaba da tafiyarta, sanin kanta ne idan zata ce Khadija ta daina kiran Step mom dinta gatsasa sau hansin sai Khadija ta aikata sau dari biyu.
"Ki duba ki ga fa saboda ki Wahala ta tura ki aiki a gidan, ga yayanta, muna wai dan tsabar zalinci tace ita zata karbe albashin, bayan babu abunda take tsinana miki"
Tafiya suke Khadija na jifar Tumba da kalamai marasa dadi, Falmata dai bata ce mata uffan ba har suka raba hanya, kowa ya dauki hanyar gidansu. Da sallama ta shigo cikin gidan amman aka rasa mai amsa mata kamar masu gaba da ita ko kuma wadanda ba su ji sallamar ba. Ko kadan hakan be dame ta ba, inda da sabo kusan ta saba da wannan rayuwar. Kallo daya tai ma Naja ta dauke kai ta hade wani abu daya tsaya mata a makoshi, yar gata kenan masu yin yadda suke so a gida ba kamar ita ba, wacce aka hana wanke surfen da ruwan da ita da kanta tai aikin jigilar debo su da safe, an bar yar gaban goshi tana wanki da su.
Sai da ta sauke ruwan sannan ta nufi gurin da surfen yake ta dauko ta wanke, ragowar ruwan ta juye a karamin bokiti ta shiga bandaki tai wanka, dakinsu ta nufa ta shafa mai abun ka da mai son kwaliya sai ta dauko ragaggin kayan kwaliyarta ta tai kwaliya har da su jan baki. Ta yi kyau sosai duk kuwa da kasancewar ta baka sai dai bakin be rage ta da komai ba daga kyaun sura kwarjini ta halitta da kuma cikar sura da zati irin na ya mace. Baka ce amman ba mummuna ba, baka ce kyakkyawa irin kyau ne mai shining. Bakinta mai kyau ne wanda ya kara fito da manyan idonta kuma farare tas, sai dai bayan ido da hakora da tafin hannunta da na kafa babu sauran wani gurin da fari ya bayyana a jikinta. Yana daya daga cikin dalilin da ya saka Falmata bata sha'awar saka bakin kaya, domin ganin take ita da tufafin za su saje ne.
Bayan ta gama shiryawa ta mike tsaye tana cigaba da kallon kanta a madubi kamin ta maida dan karamin madubin a mazauninsa da ke cikin kayan kwaliyarta.
Tsakar gidan ta fito ta nufi kitchen dinsu ta dauko abinci da ke rufe a langa (Kwano) ta zauna jikin kitchen din ta soma ci tana ta kallon awakin gidan da ke ta aikin kuka suna fada da junansu, sun 蓳ata turkensu sun masa kacha-kacha kamar ba dazun ta gama gyara shi ba. Can kuma ta maida dubanta gurin mayan shanun da ke daure guda biyu a gafen garken awakin.
"Idan kin gama ki taso ga surfen masarar nan ki surfa ko tiya daya ne"
Kam ta gama cin abinci Tumba tai mata furucin, a take yanayinta ya canja tai narai narai da fuska kamar ta fasa kuka.
"Inna ba kin ce sai gobe ba"
"To masu masarar yau suke son abunsu, kuma da safe ai sai dabobi su samu abunda za su ci"
Kalma daya idan ta kara fitowa daga bakinta ta san ba tasha ji da dadi daga bakin Tumba. Bata da wani zabi da ya wuce ta gama cin abinci ta taje tai surfen kamar yadda ta umarce ta. A hankali tai ta cin tuwon marar har ta gama ta tashi ta nufi gurin butarda ke gindin ice ta wanke hannunta sannan ta nufi gurin da masarar take ta dauka ta bude turmi ta fara surfawa. Tsakanin fara surfen da sallamar Maman Baby makociyarsu ba zaka iya tantance wanda ya riga wani ba. Tumba da ke tsakar gidan ta amsa sallamar tare da kallon Falmata da sauri.
"Kina da son wahalar da kai Fulani, ina ke ina surfe da tsakar ranar nan? Dan Allah ki aje har zuwa anjima ko kuma idan Naja ta gama wanki sai ta surfa"
Kallonta kawai Falmata tai ta sadda kanta kasa ta cigaba da surfen.
"Aa zan iya"
Sai kuma ta fada kasa-kasa idanuwanta na cika da kwalla, haka take mata a duk lokacin da wani a shigo gidan ko kuma idan a gaban mahaifinta ne. Kowa a unguwar ya shaidi Tumba akan kaunar da take nunawa Falmata agaban idanuwansu, wani lokacin har da ita ake bada kwacen matar uba wacce ta rike yar kishiya da amana.
"Oh Tumba ikon Allah, ke dai ba ki kaunar ganin Falmata tana aiki"
Cewar Maman Baby tana dariya.
"Mahaifiyarta amana ta bar min ita, idan ina ganin tana wata wahalar sai na rika ganin kamar na ci amanar mahaifiyarta"
Daga inda Falmata take tsaye tana surfen ta dago manyan idanuwanta masu kamar madara ta kalli Tumba wacce ta shantake da makociyarta suna fira ta sadda kanta kasa ta cigaba da surfe idonta tab da kwalla...!
FADIME POV.
Katsina State...
Shanun na gaba ita kuma tana biye da su a baya tare da karenta, hannunta rike da yar karamar sandarta ta dukan shanun, tana sanye da tufafin riga da zane na fulani gashin kanta a cinkushe. Sosai hankalinta yake akan ko wace shanuwa da ke gabanta, zuciyarta cike da fargaba da zullumi irin wanda ya saba ziyartar a duk sa'in da ta fita da shanun. Ba ta natsu ba har sai da ta isa da shanun a gurin da ta saba tsayawa da su, sannan ta nemi guri ta zauna saman wani karamin dutse ta zuba musu ido.
Haka take wuni a cikin tashin hankali da fargaba a duk lokacin da mahaifinta ya tura kiwo, ba tsoron kiwon take ba, ba dan bata saba ba, sai dan fargabar abunda zai samu shanu a duk lokacin da ta fita da su.
Ba kasafai take zuwa kiwo ta dawo da shanun lafiya ba, wani lokacin a hanyar tafiya wata zata mutu, wani a hanyar dawowa wani sa'in ma har sai ta iso gida.
Tun shanun suna arba'in da uku har sun dawo sauran goma sha bakwai.
聽聽 Mikewa tai tsaye tana kallon wata bakar mage mai jajayen indanuwa, wacce ke tsaye saman dutsen da ke gabanta, ba yau ta saba ganin magen ba, kusan kullum idan ta fita kiwo sai ta ganta, tun tana tsorota har ta daina, sai dai su yi ta kallon kallo ita da magen, sai dai a duk lokacin da tai arba da magen sai tsigar jikinta ta tashi, tsakanin ita da magen aka raba mai daukewa wani ido, ba m kamar magen da ke kyakar hakora.
聽 Can dai Fadime ta nemi guri ta zauna ta dauke kanta daga kallon magane da take, ta maida hankalinta gurin shanunta.
WASIN RAU POV.
As usual, yau ma sai da hasken rana ya fara haska kyakkyawar fuskarsa sannan ya bude idonshi a hankali yana kallon birds din dake saman icen suna rera masa waka kamar yadda suka saba a ko wace safiya.
Lumshe ido yayi sai kuma murmushi ya biyo baya mafarkin da yai yake kokarin tunawa, jinke hannunsa yai gam yana maida numfashi a hankali tare da dantse hakoransa.
Kamar an tsikareshi sai kuma yai saurin bude idon yai hanzarin saukowa daga kan icen ya doro kasa, jikinsa ya girgiza har sai da kowace ga蓳a ta jikinsa ta motsa.
Babu riga a jikinsa sai dai hakan be hana shi jin zafi ba, duk kuwa da irin tsananin sanyin da ake kasancewar yanayin safiyar yau a akwai hadari da ya karade ko'ina a sararin samaniya.
For the first time a yau yaji a kasa yake sha'awar yin busar sarewa abunda be taba ba, a kowace safiya a saman dutse yake yin busarsa mai dadi saurare da kawarda duk wata damuwa. Jingina yai jikin icen ya ciro sarewarsa ya kafa bakinsa ya soma busar cikin kwarewa da shauki, a take duk dajin ya dauka, yanayin haduwar hadarin da kuma busar sarewar, da iskar da ke kadawa sai ya bada wani kalar yanayi na musamman wanda ko wace irin halitta zata so kasancewa a ciki. Sai da yai busar ya gama sannan ya kai hannunsa a gefen walkin da ke jikinsa ya kwance wata yar karamar jakar tsaba ya bude bakinta ya zubo hatsin da ke cikin jakar a hannunsa ya watsawa tsuntsaye a kasa, a take suka sauko kasa suka baibaye gurin suna ta cin tsabar har wasu na hawa kan wasu, kallomsu yake suna cin abinci har sai da idonsa ya gundura da abincinsa sannan ya juya ya kama hanyar shiga cikin burninsu.
聽聽 Safiya ce amman kowa hada hadarsa yake, kai tsaye ya wuce cikin fadarsu, gaba dayan mutane da suke cikin fadar babu mai tufafi kowa walki ne a jikinsu, fuskarsu babu annuri kamar sun yi arba da mutuwa.
聽 Kafarsa ya kai kasa dayar kuma ya gurfana da ita ya sirinar da kansa ya gaishe da mahaifinsa. Da mafecin da ke hannunsa ya daga ya dora masa a kai alamar ya amsa gaisuwar sannan ya mike tsaye ya nufi cikin gidan sarautar mai kamar wani karamin burni.
聽 Ta wani bangaren ruwan korama ne ke da guduna ga shukoki a gefenta daga can nesa da shukokin kuma wasu manyan itatuwan ayaba ne, idan ka tada kanka ka kalli gabanka kuma ginar kasa ta zakanin da irinnta kaka da kakkanin, wacce aka kawata ta da fatar damisa wani gurin kuma an kawata shi da gashin tsuntsaye kalakala da suke cikin dajin.
聽 Masarautar GARUK babban masaurata ce mai karfi tsafi, tun daga kakannin har jikoki su ba su yarda da cigaban zamani ba, a duk inda za su je a duniyar nan sai dai su taka a kasa ko su yi tsafi ko su hau wani abun hawa daga dabbobinsu ya kaisu, fita su bar garin ma abu me mai wahala, ba kasafai yam garin ke nesa da garin ba saboda yanayin rayuwarsu da kuma suturarsu, kamar yadda ganganci ne wanda ba dan garin ba ya kawo ziyara a garin ba tare da sanin wani a garin ba. Yawancin abincin mutanen garin yayan itatuwa ne sai alkama danyar kwakwa.
ZAINAB POV.
Yola...
Kadan ta kurba tea da ke gabanta ta aje karamin kofi a hankali sannan ta tattara dukannin hankalinta da natsuwarta ta maida akan laptop din dake gabanta.
Hotunan da ta dauka jiya take kokarin gyarawa, tunanin yadda zata banbanta su da sauran take, domin a halin yanzu bata da wani buri da tunani da ya wuce ganinta a matakin da kowa be taba kaiwa ba, tana bukatar sabuwar idea.
Tunani take tana wani tsuke karamin bakinta, tare da dora kafa daya saman daya. Wayarta ta dauko聽 ta kunna data, ba da niya ba ta shiga whatsapp, da gangan ta duba sakonin da ake aiko mata na dan ta bada amsa ba, ta saba halinta sai ta bude sako ta bar shi a bude ba tare da ta mayar da amsa ba, ji take ta isa da hakan, kuma ra'ayinta ne dole kowa ya bi.
聽 Kai tsaye ta nufi status, sai da ta fara duba adadin mutane da suka duba nata status din wanda ta saka sannan ta fara duba na mutane.
鈥淲ow.......鈥�
Ta furta tana kara zooming wani hoto na wani namiji tare da matarsa da yayansa biyu.
鈥淎mman mijin nan na ki ya hadu fa鈥�
Ta kara duba hoton da kyau da sauran hotunan da suke biye da shi duka na miji wani guri da yaran wani gurin ita da shi wani gurin kuma shi kadai, sai a lokacin ta lura da matar ta goge hoton ma, sai ita a gurinta be gogu ba saboda tana using GB whatsapp.
鈥淗appy anniversary dear zan zo cin cake鈥�
Ta rubuta mata sannan ta shiga wani sashen tai saving hoton. Wata Dattijuwar mace ce ta shigo dakin tana daure da zane kanta kuma ya yafin atamfa kalar zanen da ke jikinta.
聽 Ganin matar yasa Zainab kara relaxing akan kujerar tana wani lankwafar da kai.
鈥淚ya..... 鈥�
鈥淜yakkyawa, kowa yana can yana karyawa ke kina nan鈥�
鈥淚ya inata tunanin abunda zan yi this week na haska duniya, kuma na amsa sunana na photographer, ina da mabiya miliyan uku da rabi a media, ina yan hamayya ya kamata ace na hara kura na daga musu hankali, kin san mu photographers kullum burinmu mu dara kowa鈥�
Ta karasa tana kai kafarta ta tana wata karamar camera dake gabanta da kafartata. Iya ta yi murmushi irin nasu na manya, sannan ta lasa bakinta ta dan daga jajayen idanuwanta kadan tana kallon Zainab tace.
鈥淣a fada kullum idan kina bukatar wani abun, ki rika kiran yayanki, shawara kike bukata ko wani taimako ki rika fada masa鈥�
鈥淚ya kin san baya son waya mai tsaye ne, kuma baya gari balle na same shi mu yi magana鈥�
鈥淵ana gari be dai shigo gidannan ba鈥�
Da sauri ta tashi zaune tana kallon mummunar fuskar Iya.
鈥淵a akai kika sani?鈥�
Iya ta yi dariya.
鈥淜ina wasa Zainab, sirrin masarautar nan a hannuna yake, sai ki rika abu kamar a nan aka haife ki ba, ni na fada miki Omar yana cikin garin Yola鈥�
鈥淚dan hakan ne, ba shi da amfani tun da baya bukatar shigowa cikin gidan nan....鈥�
鈥淜ira shi ki fada masa dansa Labib, be da lafiya鈥�
鈥淏a zai jidadi ba idan nai masa karya鈥�
Ta fada tana dan turo baki tare da komawa jikin kujerar ta kwanta.
鈥淣i kuma mahaifiyarki sai nace ki yi karya? Da gaske ne dan sa be da Lafiya, bari na dauko miki shi yanzu nan鈥�
Iya na fadar hakan ta juya ta fice daga dakin, sauka tai kasa gaba daya downstairs, ta nufi wani bangare na masarautar, a tsakanin bangaren da ta nufa da kuma wanda ta baro yayi nisa wata karamar unguwa zuwa wata.
聽 Da kanta take tafiya hadiman gidan nata aika mata gaisuwa ita ko tana amsa musu baki har kunne, haka take da kowa fatfat kusan ta fi kowa far'a gidan.
聽 Sai da ta fakaici idon mutane sannan ta shiga garken dawakai tana tambayar mai gadinsu.
鈥淵au ka duba su kuwa?鈥�
鈥淩anki ya dade duba su kuma ai dole ne tunda shine aikina鈥�
Ta yi murmushi.
鈥淗akan na da kyau bari na duba dokin Babban mutum.... 鈥�
Haka take kullum sai ta fake da sai ita da kanta zata duba dokin ba dan komai ba sai dan ta samu damar shiga ciki, cikin gurin ta shiga tana takawa ahankali tana duba dokuna kamar mai duba lafiyarsu, har ta isa gaban wani farin doki wanda ake kebe can shi kadai aka zagaye shi da katako, bude gurin tai ta shiga, ta kai hannu ta shafa dokin wanda kusan ya saba da ita, sannan ta duka kusa da shi ta fara tonon kasa, wasu abubuwa da fiddo guda uku dane a cikin zare, na tsakiyar ta matsa sai kuma taja zaren da karfi.
聽 Daga inda take ta jiyo kukan Labib a kunnuwanta, da kuma maganar Nana wace ta tsorota da yadda yai kyalowa ta nufo shi tana ambaton Allah. Cikin saurin ta mayarda kulolan ta rufe ramen ta nade hannunta cikin zanenta gudun kar a ganshi da kasa sannan ta fito daga gurin.
OMAR....
YOLA...
Kofin tsamiya ne a hannunsa, dayan hannunsa kuma rike da lemun tsami yana matsawa a karamin kofin, farar singilat ce jikinsa sai farin tawul din da ke daure a 茩wugunsa, kafafaren kafafuwansa kuma sanye da takalminsa na bedroom.
Sai da ya gama matsa lemun sannan ya saka tea spoon ya garwaye lemun tsamin da tsamiyar suka hade jikinsu, a take ya daga kansa sama ya hanye, a gurin ya dire kofin ya mike tsaye ya nufi bathroom, he spent more than thirty minutes a bathroom din yana jika kansa da ruwa sannan ya fito rike da wani karamin tawul yana goge kyakkawan jikinsa, gaban madubi ya tsaya yana goge gashin kansa. Fari ne kyakkyawan gaske, irin kyau nan mai daukar hankali, bafulatani gaba da baya amman idan ba sani kai ba sai ka rantse da Allah baasbine ne ko shuwa, ko'ina na jikinsa yana amsa sunansa na namiji kamar yadda muryarsa da siffar zatinsa take haska surarsa. Wani farin mai, mai sanyi ya dauka ya shafa a hannunsa ya murza sannan ya shafa shi a jikinsa, kana ya ware hannayensa yai mika, wacce ta sanarwa dukan jikinsa.
聽 Wayarsa da ke kan gado ce tai ringing, sai da ya kwance tawul din jikinsa sannan ya nufi wayar ya dauka.
鈥淣ana鈥�
鈥淣a'am Labib ba Lafiya yana ta ihu鈥�
鈥淲aya taba shi?鈥�
Ya tambaya sanin cewar daman can ba lafiya ta isheshi ba.
鈥淏abu ina ma dakin, sai kawai na ji yayi kyalowa ya fashe da kuka, jikinsa ma duk yayi zafi鈥�
鈥淜u kira Doc鈥�
鈥淎mmy ta kira shi鈥�
鈥淕ani nan zuwa鈥�
Ya fada yana sauke wayar daga kunnensa, kiran Nana na sauka na Muhseen ya shigo wayarsa, da murmushi Omar yai picking call din.
鈥淥mar kana gurin Ammy? Ko kana sokoto鈥�
鈥淜a shigo gari ne?鈥�
鈥淵eah ina Yola yanzu haka鈥�
鈥淲ow gani zan je fada yanzu鈥�
鈥淥kay mu hadu a can鈥�
Daga haka ya sauke wayar yana murmushi he can't remember when last ya ga Muhseen mutanen Abuja.
聽 Daukar tawul din yai yaaje shi a muhallinsa sannan ya bude wardrobe ya dauko farin jean and blue t-shirt ya saka, a gagauce ya shirya ya saka agogon hannunsa ya fesa turare ya dauki abubuwan bukatarsa ya fice daga dakin.
聽
鈥淏aba Adamu.... A tashi mota yanzu nn zamu je fada Labib ba lafiya鈥�
Tun kan ya sauko ya fara kwalawa Baba Adamu kira, abunka da mai jira jikin na rawa Baba Adamu ya nufi motar yai mata key sannan ya fito ya budewa Omar. Tun kan su shiga motar mai gadi ya bude gate Omar na shiga Baba Adamu ya fisgi motar kamar ba Dattijo ba.
鈥淎haaa haka nake so, a dinga taka mota kamar mu kadai ne a garin nan鈥�
Omar ya fada yana jindadim yadda Baba Adamu ke gudu da motar kamar dominsu kawai akai titi.
________________________
Did i ever write something about witch? (Mayu)
Do you remember other family Mama Fulani da suke Yola? The story is about them now 馃
03/12/2021, 08:06 - 馃馃馃馃: I just published "Free Page -2" of my story "FULANI". https://www.wattpad.com/1104521181?utm_medium=com.fmwhatsapp&utm_source=android&utm_content=share_published
*馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*Free Page -2*
Police din da suke gadin Masarautar ne suka bude masu gate, suna dagowa Shattima hannun duk kuwa da kasancewar ba su da tabbacin yana ganinsu domin bakin gilashin motar ba zai basu damar ganin ya karbi gausuwarta su ba ko akasin haka
鈥淔ada za mu biya ranka ya dade?鈥�
鈥淎 a sai na fara duba Labib鈥�
Kai tsaye Baba Adamu ya nitsa da motar cikin harabar Masarautar kamin ya dauki wani bangare da zai sadashi da bangaren Momy.
Kamin su karasa wayar Shattima ta sake ringing cirota yai daga aljihunsa yana dubawa Hajiya Karama ce rubuce a gaban wayar, sai da tai ringing kamar ba zai daga ba sai kuma yai picking.
鈥淪hattima, Labib ba lafiya鈥�
鈥淚 know na shigo cikin Masarautar ai鈥�
Mikewa tai tsaye daga saman kujerar da take zaune ta fito daga dakinta ta zagayo ta fito backyard ta tsaya tana hango motarsa.
鈥淥kay鈥�
Ta sauke wayar da already ya kashe kiran tun da ya bata amsa.
A gaban wata katuwar kofa wacce ta sha ado kamar ba za a mutu ba Baba Adamu ya faka motar sannan ya fito da sauri ya budewa Shattima. Cikin wata irin isa da kasaita Shattima ya sako da kafafuwansa waje ya fito daga cikin motar yana wata irin tafiya ta takama kamar wanda baya son taka kasa, a zahirin takamarce da isa da kuma kasaita a tare da shi kamar yadda idon kowa na cikin Masarautar ke gani, sai dai a badini sam babu hakan a tare da shi ko da rana daya be tana jin ya fi wani ba dan yana dan sarauta, be taba jin wani ba sa'ansa ba ne dan yana da dukiya da ilmi, ba zaka taba fahimtar hakan ba har sai idan ka zauna da shi ka fahimce shi sosai da sosai.
聽 Fadawan da ke gadin kofar ne suka bude masa da sauri suna risinawa tare da zuba gaisuwa, dayan kuma nata aikin isar da kirari, ko kallonsu be yi ba balle ya amsa musu gaba daya hankalinsa yana gun dansa kiran da Zainab tai masa bayan na Nana yasa hankalinsa ya kara tashi.
Cikin tafiyarsa ta kasaita ya natsa kafarsa cikin wani babban guri.
Wani irin katon falo ne mai dauke da Turkish furnitures tun daga kan kujeru har carpet da center table, da kuma side table dake kowace kusurwa ta kujerun, ga katon Hoton mai Matarba, sai kuma hoton Ammy sai na Hajiya daga gefe na mai Martaba a tsakiya sai hotunna wasu muhimman mutane na Masarautar dake tsaye a falo, idan ka cire farin fentin da ya kawata falon komai na cikinsa ja ne gwanin sha'awa, falon ya sha ado sai dai ba ado irin na komai a zuba ba, a a adon yan zamani wanda za a kawata falon da abu kadan amman masu kyau da tsada ta yadda duk wanda ya shiga ciki sai ya manta a wace duniyar yake, idan kana a cikin falon za kayi zaton akwai hadari a waje ne ko kuma yamma ta yi ko ma kai zaton farkon budewar safiya ne sakamaon hasken da aka kawata falon da shi kadan ne, mai daukar hankali, sanyin ac ta ko'ina, ga wasu manyan kyandira irin na zamani masu aiki da wutar lantarki suna bada haske a falon gwanin burgewa, ta dayan bangaren kuma wani irin kamshi ne ke tashi a cikin falon kashin da ba zaka iya tantance wane irin kalar turarene ba.
Wata babbar kofa ya nufa mai kyau da kyalle kamar an am mata ado da zinari, ya kai farin hannunsa ya tura kofar ya shiga, sai ya tsinci kansa a wani matsakaicin corridor mai kama da karamin falo an cika ko'ina da na gurin da manyan fulawoyin na kasko da jan carpet.
Mikewa yai straight zuwa katon stairs din da ke gabansa, gabansa kawai yake kallo har ya haye sama, kofar farko ya fara turawa tun kan ta karasa budewa ya jiyo kukan dansa, hakan yasa shi hanzarin cira kafa ya shiga cikin falon mai kama da da wata karamar fadar turawa, a wannan falon kam komai na cikinsa blue ne idan ka cire farin fentin mai kawata ko'ina na gidan, ta bangare daya kuma wani gini ne akai a cikin gurin mai kamar swimming pool sai dai wannan anyi shi da dan yi tsayi, an masa kwalliya da kwaryar da kuma rudayi sai dawusu a samansu yana furzo ruwa gwanin sha'awa, a iya cikin gilashin ruwan ke tsawa ko kadan basa digowa kasa balle har su sauka.
聽 Falo ne mai dauke da set din kujeru uku kujerun farko kanana ne an jerasu kamar kujerun dinning wato a zagaye, sai dan karamin tebur a tsakiya da kuma wani karamin carpet blue, na biyun su kuma manyan turkish ne masu daukar hankali, sai聽 wasu daga can karshen falon su ma blue kamar dai sauran an zagaye gefen da su, su ma kuma suna da karamin carpet da center table.
A gaban falon kuma wani katon kirsten tv stand ne fari mai gloss fronts da haske blue, left and right na tv stand din matsakaicin show glass ne mai haske a ciki blue color an masa kwaliya da turaruka na alfarma masu kyau da tsada gwanin burgewa.
Ga wani katon plasma da aka kawata tv stand da shi kamar matanen ciki za su fito waje.
A dayan gefen kuma wani karamin madubi ne na aka manna mai dauke da gurin wanke hannu, yamma da falon kuma matattarar cin abinci ce mai zamam kanta wacce aka ware mata kofarta dabam kusa da wani katon freezer mai kofa biyu, a dinning area din ma akwai madaidaicin plasma wanda zai bawa duk wanda yake zaune a dinning din damar kallo.
Kofar da Umar ya shigo ce kawai gini a cikin falon sauran duka glass ne gwanin burgewa.
聽 A dayan bangaren kusa da dinning akwai wata karamar kofar glass, shiga cikinta na sadarda mutum da wani kebantaccen guri mai dauke da set din karamin dinning har biyar an rarrabasu an jera ko wane set dabam da wani.
Ta backyard din mutum zai iya hango wanda ke tafe da kuma abunda ke gudana a harabar Masarautar sai dai ba zai bawa mutum damar hango bangaren mai Martaba ba, dama da shi kuma wanda ke tsaye a gurin zai iya hangon garden din dake bangaren Momy, shi ma kuma ganin mai shiga ko mai fitowa ne kawai mutum ke da damar yi ba wai komai da komai na cikin ba kasancewar garden din na da manyan itatuwa da katon Swimming pool a gafe na dutse.....
Nana na ganinsa ta mike tsaye rike da Labib da tana jijjigashi ta nufi gurinsa. Cike da kulawa da tausayi da kuma kaunar dansa ya sa hannu biyu ya karbe sa.
鈥淲hat happened?鈥�
鈥淏a wanda zai fada maka ga abunda ya faru fa, ina dakin kawai yai kyalowa鈥�
鈥淣o karya kike na fada muku a daina barinsu su kadai鈥�
Bata sake unkurin cewa komai ba ta koma ta zauna tana kallonsa.
A kafadarsa ya dorashi yana jijjigashi tare da karanta masa ayatul kursiyu ya tofa masa sannan ya nufi hanyar dake kusa da dinning da kansa ya bude kofar ya shiga, yana shafa bayan Labib a hankali yana kallon abunda ke gudana a kasa.
Ta kofar farko Hajiya Karama ya fito ta nufo inda yake tsaye.
鈥淗ar ka iso, ya jikin na shi?鈥�
鈥淒a sauki鈥�
Ya amsa mata domin ya daina kukan da yake.
鈥淢e ke damunshi鈥�
鈥淏an sani ba鈥�
鈥淜awo shi鈥�
Ta karbe shi tana jijjigashi cike da kulawa domin ita ma kanta tana kaunar yaran.
鈥淣ana tace kyallowa yai, na fada musu a daina bar min yara su kadai, if not zan dauke su daga gidan nan鈥�
Ya fada yana juyawa ya kalli wata harabar dabam kana ya aje numfashin da sautin da ke nuna ba da wasa yake ba, biyoshi tai tana girgiza kai.
鈥淣ono Ammy ba zata jidadi ba, am samu mai kula da dakinsu fa, na ce a barta ta kula da su Iya tace bata yarda da ita ba鈥�
鈥淲acece?鈥�
Ya juyo yana tambaya.
鈥淲ata ce ba zata wuce 16-17 years ba鈥�
鈥淢iyasa ba ta yarda da ita ba?鈥�
鈥淚 don't know ko maybe saboda ta yi kankanta ne鈥�
Kare mata kallo yai ya dauke kai
鈥淛i dress dinki, na sha fada miki ki daina irin shigar nan鈥�
Ya karasa yana takawa a hankali zuwa gurin karfen dake gabansa. Sai ta kalli jikinta.
鈥淲hat's wrong with my dress?鈥�
Be amsa ta ba ya juya ya fice daga gurin ya barta rike da Labib din a kafadarta.
Murmushi tai tana kara kallon kanta, dogon wando ne da wata riga mai guntun hannu wacce ta tsaya iya kwankwasonta, ba laifi kayan sun matse ta sai dai ba irin matsuwa can can sosai ba, a gurinta hakan normal ne ko ba komai tana jindadin yadda hankalin maza yake tashi idan sun yi arba da irin halittar da Allah yai mata, hakan na mata dadi sosai wai sai dai a gani a hade yawu babu yadda za'ayi da ita.
Bin bayansa tai ta kofar da ya shiga tana cigaba da murmushi, a kujerar da ke kusa da kofar ta zauna ta sa dayan hannunta tana gyara yar karamar jar hular da ke kanta.
鈥淵ayi shiru?鈥�
Nana ta tambaya tana nufo inda Zainab din take zaune.
鈥淵eah i think yayi bachi鈥�
Ta taba jikinsa sai ta ji shi da dan zafi za tai magana Zainab ta mike tsaye tana kallon Doc Deen wanda ya shigo rike da dan karamin akwatin magani, fuskarsa sanye da farin gilashi.
鈥淪annu da zuwa Doctor鈥�
鈥淗ajiya Karama鈥�
Ya amsa mata yana murmushi tare da kallon Shattima wanda ke tsaye jikin window ya rumgume hannayensa ta baya yana kallon harabar gidan.
Har Doc ya zauna Zainab ta mika masa Labib ya fara duba shi Shattima be juyo ba.
鈥淢iya same shi?鈥�
鈥淏a komai haka kawai yai ihu鈥�
Nana ta amsa shi tana zaunawa kusa da Doc kamar ita ce zata duba yaron, Doc Deen yayi murmushi yana kallonta.
鈥淜o na baki ki duba shi?鈥�
Dariya tai mai sauti ta make kafada tana girgiza masa kai. Zainab ta yi murmushi ta nufi gurin da Shattima yake tsaye ta tsaya ta jera tare da shi tana kallon dokin da yake kallo wanda ake yi wa ado irin na sarakuna.
鈥淵aushe ka dawo?鈥�
鈥淛iya....鈥�
Ya amsa mata a takaice duk kuwa da kasancewar yana a cikin yanayin da baya son magana, amman ba zai iya kin amsa ta ba, babu abunda Zainab zata bukata ya kasa mata, bayan girman da tai a kusa da shi ta bude ido, kusan ta fi shakuwa da shi fiye da kowa, tana jin maganarsa kamar yadda shi ma yake saurarenta yana girmamata a ciki har da sunan mahaifiyarsa da ta ci, wanda hakan yasa ake mata lakabi da Hajiya Karama, gashi tana da sirri idan ya fada mata A babu mai ji sai idan shi ya umarce ta data fada, babu abunda za tai ba da saninsa ba, babu abunda take boye masa ita da shi abokai ne kuma shakikai.
鈥淲annan shi ne karo na biyu da ka sauka wani guri ba Masarautar nan ba, and i don't think hakan zai mana dadi鈥�
A hankali ya busar da iskar bakinsa ya zuba hannyensa aljihu yana cigaba da kallon dokin ta cikin gilashin falon ya ce.
鈥淎bubuwan gidan nan basa min dadi鈥�
鈥淵eah amman some time muna bukatar shawararka, ko bukatar wani abu kusan kai ne Sarki a gidanan tun da Mai Martaba bashi da Lafiya, be kamata ace kana nisa da gida ba, and the way you act Ammy ba zata jidadi ba鈥�
Murmushin gafen baki yai ya kalleta.
鈥淶an gyara Hajiya Karama鈥�
鈥淕ood鈥�
Ta fada with smile on her face, sannan ita ma ta saka hannunta aljihu tana wasa da dayar kafarta, shiru ne ya biyo baya kamin ta kalleshi
鈥淭his time around ina son nai wani abun da zai bawa kowa mamaki as a photographer i want to do something differently like..... 鈥�
Sai kuma ta kasa karasawa ta ware hannayenta kamar mai tunanin abunda zata fada. Kallonta yai kadan ya dauke kai.
鈥淲ell i think ki shiga kauye, ki duba wata culture ko yare ki duba wasu addinai na wasu da suke wanda ya sha banban da wanda ake gani sai ki dauka鈥�
Ta wara idonta tana murmushin jindadi.
鈥淲ow shiyasa bana son kai nisa da ni, a duk lokacin da na nemi shawara sai ka sama min mafita鈥�
Murmushi yai mata kamin ya juyo da sauri jin muryar Muhseen.
鈥淲ow wow wow..... Longest time Dude鈥�
Tsakanin shi da Muhseen aka rasa wanda ya fi wani sauri, a tsakiyar falon suka hadu suka rumgume junansu ko wanensu fuskarsa dauke da dariya da farincikin arba da dan'uwansa.
Nana ta taso da sauri ta rumgume Muhseen.
鈥淵a Muhseen oyoyo鈥�
鈥淗ey Little One鈥�
Zainab ma side hug tai masa tana welcoming dinsa, sai da ya kai wa Doc Yazeed hannu suka gaisa sannan ya zauna kusa da Zainab.
鈥淗ajiya Karama how far?鈥�
鈥淔ine ya Abuja?鈥�
鈥淜alau鈥�
鈥淚na Aliyu and Mama Fulani?鈥�
鈥淵ana nan kalau Mama kuma tana kasa tare da Mai Martaba鈥�
Shattima ya karbi Labib dake bachi a hannun Doc Deen yana fadin.
鈥淒oc me ke sa su yawan zaburar nan ne wai?鈥�
鈥淭o Wallahi ba zan iya fada ba, adai rika yi ana hada musu da addu'a especially idan za su kwanta bachi ko idan sun farka, and a daina barinsu a duhu ko barinsu su kadai鈥�
Yana fadar hakan ya mike tsaye ya rufe akwatinsa yana musu sallama, sai Nana ta mike tsaye ta bi bayansa suka fita falon tare, yana saukowa stairs din ta ce.
鈥淒oc yaushe zaka kai ni gurin wannan sister taka wace kace tana kama da ni鈥�
Kallonta kawai yai ya dauke kai yana murmushi be ce mata komai ba har ya sauka ita kuma bata fasa tambayarsa tana masa magiya ba har ya isa gurin motarsa.
鈥淵ou know what? Sometimes dabi'unku daya da Ya Shattima, sai ku rika yi ma mutum wulakanci idan kun ga yana son abu鈥�
Sai da ya bude motarsa ya saka akwatin sannan ya juyo ya kalleta daga sama har kasa, green lace ne jikinta kanta ba dankwali ta kulle gashin kanta, babu yan yankunne a kunnenta babu makeup a fuskarta amman hakan be hana kyauta fita ba, kallo daya zaka mata ka san cewar jini daya ce ita da Shattima domin kamarsu ta bace kamar an tsaga kara.
鈥淏a a nan take ba鈥�
Ya amsa mata with smile.
鈥淎 ina take?鈥�
鈥淎buja鈥�
鈥淎buja ai gurin zuwan mu ne zan iya binka na kaini na ganta, tun ranar da ka fada min nake son na ganta har yau鈥�
Ya zaro ido
鈥淜i bini? So kike ace na sace ki?鈥�
鈥淎 a zamu je da sanin Ammy da kuma Hajiya kuma zan fada musu ba za su hana ba鈥�
鈥淏a za su bari ba鈥�
鈥淭o mu tsere idan mun dawo sai mu fada musu鈥�
Wannan karon dariya yai sosai.
鈥淣ana ba ki da wayo鈥�
鈥淚na da wayo mana, amman ai ina da hankali鈥�
Ta fada ita ma tana dariya kamar shi.
鈥淔ine, zan san abun yi ko dai na dauko miki ita na kawo ko kuma na baki address dinta idan kin shiga Abuja ki je ki ganta鈥�
鈥淥kay鈥�
Ta fada tana daka tsalle, kamar ance ta daga kai ta gani, sai ta hango Sirleem a sama daga can bangarensu yana kallonsu.
鈥淚dan kai tunani ka kira Ya Shattima ka fada masa sai ya fada min ka ji?鈥�
Tun kamin ya amsa mata tai saurin barin wajen ta koma sashensu.
Kai Doc Deen ya daga ya kalli Sirleem wanda ke watsa masa wani irin kallo na rashin kima, murmushi Deen yai ya bude motarsa ya shiga.
Daga backyard din da yake tsaye zuciyarsa take wani irin tafarfasa ganin Nana da Yazeed da yai, ba tun yau ya lura a duk lokacin da Deen ya shigo聽 Masarautar sai ya tsaya yayi magana da Nana yake tafiya.
A fusace ya nufi bangaren Ammy zuciyarsa kamar zata fito tsabar kishi, cikin fusata ya tura kofar falon ya shiga sai ya samu Shattima da Muhseen Zainab da Nana zaune a falon, dukan su kallonsa sukai ban da Shattima da yai kamar be san da shi a duniya ba, be damu ba ya soma gabatar da abunda ya kawo shi.
鈥淜e me kike yi waje da Deen?鈥�
鈥淚na ruwanka?鈥�
Ta amsa masa ita ma tana turo baki gaba kamar za tai kuka sannan ta mike tsaye rike wayarta ta nufi hanyar da zata sadata da dakinta.
Zainab ta daga kai tana masa wani shegen kallo.
鈥淟ook at you Sirleem sai ka rika yin abu kamar wani fool ya zaka shigo a gaban mutane kana tambayarta miye take a waje? Kamar wani ubanta鈥�
Runtse ido yai ya bude cikin bacin rai ya ce
鈥淗ajiya Karama babu ruwanki a cikin wannan maganar, idan ina magana da Nana ki daina saka min baki鈥�
鈥淥h really? To ko dukana zaka yi?鈥�
Ta fada tana mikewa tsaye, daman can ita da shi ba sa shan inuwa daya.
Sai a lokacin ne Shattima ya daga ido ya kalleshi ya kalli Zainab.
鈥淧lease Hajiya Karama tafi dakinki鈥�
鈥淎mman....鈥�
Bata karasa ba maganar ta makale sakamakon kallon umarni da Shattima yai mata sai ta duka ta dauki wayarta ta fice daga falon. Shattima ya kalli Muhseen yana murmushi kamar ba shi ba yace.
鈥淢uje sashena ka huta na san yanzu za a fara jera maka abinci dan gidan Mai Martaba鈥�
A tare suka fice da Muhseen din aka bar Salim tsaye a falon kamar wani wawa.
FADIME POV.
Busar sarewar nan da take yawan ji a mafarki ta soma jiyowa tana tashi a hankali.
Kwantar da kanta tai jikin kafafuwanta tana sauraren yadda busar ke ratsa kunnuwanta tana saukar da nishadi a zuciyarta busa ce mai ban tausayi mai saka shauki da dadin saurare, a iya lissafinta tana tuna mafarkinta ne shiyasa take jiyo busar, hakan yasa ta rufe idonta tana ta ganin mutumen nan mai busar sarewa na mafarkinta, a kullum idan tai mafarkinsa baya yake bata bata taba ganin fuskarsa ba, yana daure da walki jikinsa babu riga.
Jin kamar a zahiri ake busar yasa ta bude idonta ta mike tsaye ta saki sandar korar shannun da ke hannunta, sai ta ji karar busar sarewar yana karuwa kamar ana kusantota, waige waige ta fara yi sai kuma ta juya da sauri ta nufi gurin itatuwan masara ta kusa kai ciki domin a ciki take jin kamar busar na fitowa, tana tafiya tana juyawo tana ratsa shukar masara ta ko'ina, can kuma ta juyo sautin kamar a inda ta baro ta juyo a guje ta dawo gaba daya hankalinta ya tashi domin bata taba jin busar a zahiri ba sai a yau, saman katon dutsen dake gaban shanunta ta haye tana hawaye tana waige waige ko zata hango mai busar ko kuma tabbatar da inda sautin busar ke fitowa amman sai ta ji abun ya karade ilahirin dajin gaba daya, faduwa tai a gurin ta dafe kanta tana kuka domin a yanzu ta fara tunanin ba azahiri take jin busar ba a cikin kwakwalwarta ne.
鈥淚nnalillahi wa'inna ilaihirraji'un鈥�
Ta furta tana kara runtse ido tana girgiza kai domin har lokacin bata daina jin busar sarewar ba, ta dade a gurin tsugune, sai da ta daina jin busar sannan ta mike tsaye tana kallon shanunta da ke kasa, a take saniya daya ta yanke jiki ta fadi a gurin tana shure shuren mutuwa, Fadime na ganin haka ta sauko da mugun gudu ta nufi hanyar gida tana wani irin kuka na tashin hankali, @250 ta isa gida kamar wata mahaukaciya ta fada cikin gidan tana kururuwa.
鈥淚nna Inna yau ma nagge guda ta fwadi, gata can tana shure shure Inna mutuwa za tai鈥�
Ta fada da yaren Fulatanci tana haki kukan kuma ya ki ya tsaya mata. Da sauri mahaifiyarta ta aje tasar nonon da take ta nufo inda take ta rikata.
鈥淵au ko mun shiga uku da wannan lamari haka kullum za yi tai zama? Tafi ki fada ma Malam yana gonarsa鈥�
Ta amsa masa ta yaren da suka fi gwarewa, a take Fadime ta tashi da gudu ya fice daga gidan zuwa gonar mahaifinta, Inna Amo ce ta fito daga bandakin lullube da bakin gane ta nufo tsakar gidan tana.
鈥淚nna Fadime lafiya kike?鈥�
鈥淣agge ce ta sake faduwa da sannu naggen Malam sai karewa suke Amo鈥�
鈥淎llah ya kyauta鈥�
Shine abunda ta fada ta nufi bukkatarta tana koda tsatsagar hakora.
聽 Ko da Fadime ta isa ta fadawa Mahaifinta ya tafi tare da mutunensa da suke aiki tare sun isa a kuraren lokaci domin kuwa tuni saniyar ta mutu sauran kuma na tsaye suna kiwonsu. Faduwa Fadime tai ta dafe kai tana kuka, har sai da Mahaifinta ya tasheta tsaye.
鈥淗aba Fulani komai ai na Allah ne? Ki daina wannan kukan鈥�
鈥淏appa kullum fa idan na fita kiwo sai Nagge ta mutu, ni kadai take ma haka鈥�
鈥淎 a daman can haka Allah ya rubutu鈥�
Ya amsa mata cike da karfin hali, sai daya daga cikin mutanen da suka zo tare da shi dayan ya ce.
鈥淢alam da dai ka daina barinta tana fita kiwo da su鈥�
Malam Jauro yayi murmushi yana girgiza kai.
鈥淎 a babu abunda za a fasa, idan mutanen gari sun canfa ta ni ai be kamata na yarda a matsayi ne na mahaifinta, idan Fulani bata ji dadi a gurin iyayenta ba a gurin wa zata ji? Ko da duka sanu na za su kare ba Fulani ba zata daina zuwa da su kiwo ba鈥�
鈥淭o Allah Hukkumo sa'a鈥�
Dayan ya fada cikin jin haushin be dauki shawararsa ba. Malam ya dafa kan Fulani ya ce.
鈥淜i cigaba da kiwon idan yamma ta yi sai ki dawo da su gida, annani?鈥�
鈥淚yyiye鈥�
Ta amsa masa tana gyara kai har lokacin bata daina hawaye ba, kuma bata san ranar dainawar ba domin wannan matsalar ta shiga cikin jininta ta zauna ta hanata sukuni da walwala duk kuwa da irin ficen da tai a cikin kauye na amsa sunan yarinya daya tilo wacce ta iya turanci kuma ta iya rubutu da karatu a kauyen.
Sai dai wannan abun yasa mutane na tsoronta ga rashin farin jinin da yake damun mahaifiyarta, tun tasowarta har ta girma ta kawo yanzu babu namijin da ya taba nuna yana ra'ayinta balle har ya furta yana sonta, ko irin zuwa dandalin da take sai dai taje wani lokacin dan ta kai sana'arta wani lokacin kuma dan tai kallo, domin ko da ta shiga tai rawa babu namijin da zai mata kari, sai dai tai wasa da yan 'uwanta mata duk kuwa da irin kyau da Fadime take da shi.
Haka ta zauna a gurin tana kula da shanun har rana ta raba sannan ta nufi sandarta ta dauka ta kora shanun suka nufi hanyar gida tana tafi tana rare wakarsu ta fulani kamar ba ita ce ta gama kuka dazun ba.
Ita ta kanta ta saka shanun a gurin zamansu sannan ta daure ko wanne ta dauki abun shan ruwansu ta debo musu ruwa ta kawo musu sannan ta fita daga wajen.
Bukkarsu ta nufa ta shiga ciki tana cigaba da rera wakar da take tun da ta turo shanun har ta kawo gida, tufafin Fulanin dake jikinta ta cire ta daura zane ta fito tsakar gidan ta dauki wata karamar roba ta nufi tukuyar ruwansu ta debo ruwa a ciki ta nufi bandaki, sai da ta tube tufafinta sannan ta lura da kadangaran dake leke da windin da aka zagaye akai bandaki da shi suna a kai suna kallonta, bayan mutane abu na biyu data tsana yana kallonta kadangaru ne, dan ta lura har wani kada kai suke idan suna kallonta, abun haushi ma kallonta suke ba kakkautawa ko dauke ido basa yi.
Haka ta debi ruwan ta rika watsa musu suka fara gudu banda daya wanda ya tsaya yana kallonta sai wani rausayarda kai yake.
Hakan yasa ta tsorata ta fara ja da baya tana cigaba da watsa masa ruwa, aiko kamar jira yake sai ya sauko da sauri yai cikinta, tsakanin ihunta da fallawa da gudu da kuma sakin robar ruwan ba a san wanda ya riga wani ba, kamar bera haka ta shige bukkarsu har wani tsale take sama tsabar gudu da tsoro.
鈥淚nna Kadangare ne ya bijoni鈥�
鈥淏a dai zaki daina watsa musu ruwa ba ko? Wata rana sai kin watsawa aljani鈥�
鈥淚nna wannan ma da gudu yake, ba zan iya wanka a ciki ba鈥�
Duk maganar da take da Inna ba ta dago ta kalleta ba sai aikin auna gi蓷a take a kwarya, sai da ta mike tsaye sannan tai arba da yarta.
鈥淚nnalillahi Fulani a tsirara kike fa, zindir Subhanallahi鈥�
鈥淭o Inna kadangaren ne ya biyo ni ai ba zan iya tsayawa daura zane ba鈥�
Ta fada tana turo baki tare da sa hannu ta kare kirjinta wanda da shi da babu duk daya kamin ta nufi inda zane yake ta dauka ta daura. Sai da ta ga mahaifiyarta ta fito sannan ita ma ta fito waje tana labe bayanta kamar wacce zata sake arba da shi.
鈥淣i ban ga komai a bandakin ba鈥�
鈥淭o Inna ki tsaya na gama wanka tukuna sai ki tafi鈥�
A bakin kofar bandakin Inna ta tsaya Fadime ta dauki robar taje ta debo wani ruwan ta tsaya daga baki-baki tai wankan ta fito da sauri...
*FULANI -it's not free, if you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
03/12/2021, 08:06 - 馃馃馃馃: *馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*-3*
FALMATA POV.
Bayan gama sallah isha'i Baba ya shigo gidan rike da yar ledarsa, da sauri ta karasa ta karba tana masa sannu da zuwa, ya amsa mata can ciki yana dauke fuska kamar wanda baya kaunar ganinta.
Dakin Tumba ya nufa tana biye da shi a baya rike da ledar sai da ya shiga sannan ita ma tai sallama ta shiga ta aje ledar ta juyo ta fito kamshin tsire na dukan hancinta, guri ta samu a saman tabarmar dake shimfide tsakar gidan ta zauna tana ta bitar karatunta na iziya. Hango mahaifinta ya fito daga dakin Tumba zai kama ruwa yasa tai sauri tashi ta karasa ta dauki butarsa ta zuba masa ruwa ta mika masa tana sirinawa kamar yadda ta saba.
Sai da ya shige bandakin sannan Tumba ta fito ta rike kofar dakinta tai tsaye tana watsa mata harara.
鈥淔ulani dauki bokiti kije ke samo mana ruwa鈥�
Juyowa Falmata tai ta kalleta da fuskar tausayi tana jin kamar tace ta dauki bokiti taje ta debo wuta, har ga Allah bayan surfe deban ruwa ne abu na biyu data tsana, sai dai babu yadda za tai kullum sai ta yi surfen sai kuma ta yi deban ruwan abu ne da ya zame mata dole ko a ciwo ko da lafiya dole ne tai.
鈥淯mma na debo ruwa dazun da safe fa sai da na cika komai鈥�
Ta fada da muryar dake nuna rokon take a tausaya mata.
鈥淏a gabanki Naja tai wanki ba? Ruwan ya kare ko so kike mu tashi da safe babu ko na alwala?鈥�
Umma na kai aya Abba ya dauka yana daka mata tsawa.
鈥淒auki kije debo ruwa aka ce sha-sha -sha kawai鈥�
Ya karasa yana daure zariyar wandonsa karen sigari a bakinsa. Kamar wacce tai arba da mutuwarta haka ta nufi inda bokin ruwan yake ta dauka da sauri jikinta har rawa yake ta shiga dakin da suke kwana ita da naja ta dauko hijabinta ta saka ta dauki bokintin ta fice daga gidan tana ala ala kar ma tai numfashi da karfi mahaifinta ya ji.
Sai ta fito daga cikin gidan sannan ta shara hawaye, ina zata je debo ruwa yanzu cikin dare? Ta san ko wane gida a yanzu sun rufe rijiyarsu, gashi babu wuta balle taje bohol domin idan babu wuta to bohol din baya aiki.
Hanya ta mike tana tunanin wace rigiyar zata dosa, hawaye na ziryo mata, da karfi da yaji dazun Umma ta hana ta deban ruwan ta wanke mata surfe amman ta bar Naja yar gata tai wanki da ruwan yanzu kuma sai ace ita ce zata je ta debo wasu. Hawayen idonta ta share ta nufi gidansu kawarta Khadija, tun a bakin kofar gida take sallama amman babu wanda ya amsa ta sakamakon kure volume da sukai da wakar fitattacen mawakin nan da Falmata tafi kauna fiye da komai da kowa a duniyar nan, wato Sirleem M2. A take ita ma ta bi sahu cikin yaran makota da suke zaune bakin kofar dakin Maman Khadija suna kallo, ba ta ko bi ta kan neman Khadija ba ta zauna saman bokitin ta fara bawa idanuwanta abinci, a take murmushin ya gauraye fuskarta ranta yai fes kamar ba ita ba, daman can haka take indai tai arba da wakarsa ko hotonsa wani irin dadi take ji saboda burgeta yake kaf a mawakan duniya babu wanda take so irin Sirleem har wani shauki take ji idan ta tuno wakarsa.
鈥淜e鈥�
Khadija ta dafa ta aje butar hannunta da ke nuna cewar daga bandaki ta fito.
鈥淚na kika fito da bokita da daren nan?鈥�
Falmata bata kula ta ba sai da wakar Sirleem ta kai karshe kaf sannan ta juyo tana kallon kawar tata kamar wacce ta dawo daga hayyacinta.
鈥淢e kike cewa?鈥�
鈥淥h na shiga uku ni Khadija wato tsabar son wakar M2 har baki ji abunda nake fada ba鈥�
Dariya Falmata tai.
鈥淲allahi ina son M2 sosai Khadija ya iya waka sosai yai ta hausa yai ta turanci har kasashen waje ance yana zuwa yai waka kuma kin ga dan Yola ne ai dole mu so shi ko?鈥�
鈥淜e dai kike sani, dan yana dan Yola aka ce miki zama suke a garinsu ne, yawanci kasashen turawa suke zuwa ko Abuja su zauna鈥�
鈥淜hadija kin san me? Da ace na yi boko na iya rubutawa da karanatawa ko? Da nima na rika koyon wakokinsa ina yi鈥�
Cewar Falmata tana dariya har kyakyatawa.
鈥淟allai Falmata abun na ki babba ne, ina zaki je da dare ke da ba a barin kina fita?鈥�
A take yanayinta ya canja murmushi da far'ar dake fuskarsa ta gushe tunawa da duniyar kuncinta, cikin rashin kuzari ta labartawa Khadija abunda ya faru sannan ta dora da.
鈥淒an Allah muje ki kara ni idansu Binta tun da kawarki ce kila Mamanta zata yarda na debi ruwan ko maya biyu ce dan Allah鈥�
鈥淕askiya dai tsakani da Allah Falmata Umma tana cutarki, shi kuma Baba ya zama wani iri duk abunda tace shi yake amfani da shi, yadda fa iyaye suke da hakki akan yayansu su ma yayansu suna da hakki akansu, ni kam da ma ke aka kai kauye aka bar kanenki nan wannan wahala ta miki yawa Falmata鈥�
Ta zaro ido.
鈥淎 a ke idan su Aisha n suke nan ai wahala za su sha sosai tun da su kanana ne, kara dai ni da nake da girma yanzu ni dai muje ki rakani鈥�
鈥淕a ruwa can a jarka je ki deba ki yi uku da bokitin ki鈥�
Kamar ta dauki kawar tata ta goya haka ta ji dan dadi, da sauri taje ta bulbula ruwan ta cika bokinta ta kai gida ta sake dawowa ta kara wasu har sai da tai bokiti uku sannan ta hankalinta ya kwanta. Bayan ta aje bokitin a mazauninsa ta nufo kofar dakin Tumba kamar mai labe ta tsaya daga bakin kofa murya can kasa tace.
鈥淕a ruwan nan na debo鈥�
鈥淭o Allah yai miki albarka Fulani ya baki miji na gari鈥�
Tumba ta fada da far'arta, Falmata dai bata ce komai ba dan tasan ba da zuciya daya tai mata addu'ar ba sai dan ganin mahaifinta yana nan, daman can haka take mata a gaban idon jama'a ko kuma a gaban mahaifinta. Dukawa tai ta dauki takardar tsiren ta nufi hanyar dakinsu tana lasar yajin dake jiki, hakan be gamsar da ita ba sai da ta cire wani sashe a takardar dake da mai da yaji ta saka a baki ta tauna ta tsotse ruwan tass sannan ta jefar ta shige dakinsu.
聽 Wani tsohon zanen gado ta dauka ta shinfida saman gadon karar da take bachi sannan ta kashe kyandir din ta kwanta tana karanto addu'o'i kamar yadda ta saba, Naja kam tuni tai nisa da bachin.
聽 Asubar fari Falmata ta fito daga dakin ta dora alwala ta shiga ta fara nafila kamin ta gabatar da sallah Asuba, ta saba da wannan dabi'ar ta yin nafila kamin asuba da kuma addu'o'in safe da maraice da na bachi tun tana karama, duk da kasancewar tana da kananan shekaru hakan be saka ta watsar da koyarwar mahaifiyarta ba, ko kadan Falmata bata wasa da addu'a da kuma sallah akan lokacin komai take zata aje taje tai sallah, idan kuma lokacin addu'ar yamma yayi ko aiki take haka zata rika karanta addu'inta, abun har ya zame mata jiki idan ba tai ba sai ta ji bata cikin natsuwa.
Sai da rana ta fito sannan ta fito daga dakin ta fito harabar gidan ta tattara kayan wanke wanke ta wanke komai tas ta share gidan sannan ta cika karamin bokiti da ruwa ta nufi bandaki, sai ta ta tube tufafin jikinta sannan ta daga wani karamin dutse ta dauko ragowar amon da tai wanka jiya ta saka a soson ta soma wankanta.
Bayan ta gama ta fito tana ta tsanda domin ban dakin a kasa kasa ce ba suminti ba idan kana wanka ruwan dake sauka yana tartsatsin yana sa kafar bandakin ta watso maka a kafafuwa.
聽 Gindin biyar ta nufa ta zauna ta saka dutsen gugar kafafuwa ta goge kafafuwanta tas ta sake wanke su sannan ta shiga dakinsu, bata 蓳ata lokaci ba gurin shiryawa sanin inda zata je gashi rana ya soma takewa.
聽 Duk da irin saurin da take hakan be hana ta kwaliya ba sannan ta saka atamfa tare da Hijab ta fito cikin sauri tana saka talkaminta na roba.
鈥淔ulani zo ga abincin ki鈥�
Cewar Umma daga gindin murhu da take zaune tana kallon Falmata, abun ka da mai neman sai ga Falmata ta karaso cikin sauri ta cire hijab dinta ta rataya a igiya sannan ta tsuguna taja kwanon da Umma ke nuna mata mai dauke da dumamen tuwo masara.
鈥淔ara shan wannan tukuna鈥�
Umma ta mika mata wani ruwan rubutu dake karamin kofi, jiki a sanyaye Falmata ta mika hannu ta karba tai Bismillah da muryar da tasan Umma ba ta ji ba ta shanye, inda sabo da saba da shan magani daga hannun Umma wani lokacin ma a cikin kunu ko madara take kada mata ta mika mata kuma ta karba ta sha, sai dai bata taba mantawa da Bismillah idan zata ci abunda yafi komai batawa Umma rai kenan wani lokacin har hana ta take idan ta ji.
MASARAUTA....
Kowa a dinning din fuskarsa a sake take ana fira ban da Nana wace ta tsuke fuska kamar wata tsohuwa sai wasa take da abincin da ke gabanta.
鈥淗akan dai be hana ki zuwa makaranta, da ki ci abinci da karki ci duk uwar su daya ubansu daya a gurina, kullum cikin latti kike shiyasa suka aiko suka ce baki zuwa makaranta鈥�
Mama Fulani dake kokarin daukar cup din tea ta kalleta.
鈥淣ana ba ki son makaranta why?鈥�
鈥淏a makaranta ne bana so ba Mama Fulani auren Sirleem ne bana so鈥�
Murmushi Mama Fulani tai.
鈥淭o miya hada aurenki da Sirleem da kuma zancen karatu?鈥�
Ta bata fuska kamar zata fasa kuka bata dai ce komai ba. Shattima ya kalleta kadan ya dauke kai yana kai plantain baki ya ce.
鈥淕askiya ne yarinya Wallahi ba ki cancanci auren mawaki ba, yar Sarki Abdallah Umar Jari ace ta auri mawaka ki, abun ai be yi ba鈥�
鈥淢iye matsalar mawaki ne Shattima? Waka ba a sana'a ba ce? Bayan waka kuma ai yana aiki da Unicef ko duk shi din ba aiki bane? He is graduated kasan gaba ina Allah zai kai shi ne? After that yana da restaurant yana da katon Boutique, yana da shagon siyarsa phones and what else kake son ya mallaka kamin a aura masa Nana?鈥�
Ammy na kai aya, Mama Fulani ta wara ido.
鈥淎a ba laifi gaskiya kuma kin ga yadda yai popular din nan kudi suke samu sosai indai yana da rufin asiri ai ba laifi ta auri abunta鈥�
Nana ta kara bata fuska tana kallon Mama Fulani.
鈥淢ama ni dai bana son shi yanzu鈥�
Sai kuma ta kalli Shattima
鈥淣o ki daina kallona kar ace ni nake kitsa miki komai鈥�
Ammy ta tabe baki tana fadin.
鈥淜o dai minene kyaji da shi ba abunda za a fasa idan ka ga an fasa auren nan sai idan shi ne da kansa yace ya janye ba zai aureta ba鈥�
鈥淗aba Ammy sai kace na yi alo ace sai idan shi ne ya fasa Fisabilillahi鈥�
Ta fada tana kara bata fuska. Zainab dake aikin chakuda wainar kwan da ke ba gabanta da fork ta yamutsa fuska tana fadin.
鈥淢atsalar ba wai ta aikinsa ko kudinsa ba ne, matsalar wakar da yake ne be dace ace zuri'ar gidan nan ta auri mawaki ba鈥�
鈥淒aga ke har Shattima wayayyen mutane ne, kin san miye waka ai kina tare da masu yinta, ba photographer ba ce ke miyasa mazan da suke zuwa neman aurenki ba su ce ai ba zasu aureki ba saboda yanayin sana'arki, kuma yarinyar a gaban kowa Mai Martaba ya tsayar da ita ya tambaye ta tana son shi ko irin kunyar da yan mata ke yi ita ba tai ba, tace tana son shi kuma aurenshi za tai, to sai yanzu dan Mai Martaba bashi da lafiya sai ku kitsa mata magana ku ss ta tsane shi ace ni na hana aure? Daman ance ni da yaya mu ke mulki Masarauta, ku dai kawai saboda ba kya son M2 shiyasa kuke wannan abu ita kuma yarinya ce karama duk inda kuka a zata dauka hawa za tai鈥�
鈥淣o No Ammy i'm out of this鈥�
Shattima ya fada yana mikewa tsaye tare da ware hannayensa alamar babu ruwansa a ciki ya fita daga dinning are din, Hajiya Karama ma mikewa tai tsaye daman can bata saka komai a bakinta ba tun zamanta gurin.
鈥淚na da inda zanje ne, ayi breakfast Lafiya鈥�
Daga haka ta bar wajen, sai ya rage daga Nana Sai Ammy da Mama Fulani ne kadai a dinning din.
鈥淶aki tashi ki wuce makaranta ko sai na bata miki rai? 9:14 ace baki shiga school ba, anya wai makaranta ma kike zuwa Nana鈥�
Ta mike tsaye tana kuka har da tara hannu a fuska ta fice rike da jakar makarantarta, kofar falon ta bude ta fara sauka saman stairs din kadan kadan har ta sauka gaba daya, sannan ta bude kofar corridor ta fice, ta sani sarai Ammy bata son ana bi ta fadarta idan za a fita amman ita da dan'uwanta abun ya zame musu al'ada ala dole sai ta nan za su fita ko su shiga bangaren Ammy.
聽 Kwankwasa kofar tai fadawam dake can ta gaba suka bude mata da sauri suna gaisheta, ban da turo baki gaba babu abunda take har ta isa gurin direbanta wanda aja tanadar dan kaita school kadai ya faka motarsa, tun kan ta karaso ya fito ya bude mata mazaunin baya ta shiga ya rufe sannan ya shiga ya tashi motar suka fice.
鈥淗ajiya har da yau ma can zamu je?鈥�
鈥淓h kullum ma鈥�
Ta fada tana ta kara turo baki gaba.
鈥淎mman Hajiya idan aka gane ina cikin matsala鈥�
鈥淭o wa zai gane? Kai zaka fada?鈥�
鈥淎 a ni na isa ki sa amin daurin rai da rai, Wallahi ba zan taba fada ba鈥�
Ta yi yar dariya tare ta bude school bag din ta dauko 3k ta bashi, haka take masa kullum na rufe baki dan kar ya fada cewar ba makaranta take zuwa ba, a kullum X&Z Restaurant take zuwa tai zamanta sai idan direban ya auna lokacin komawarta gida yai sannan ya zo ya dauke ta.
聽
UNCLE AA POV.
鈥淪ai sardaunan samarin Yola鈥�
鈥淵es amman na marasa galihu, komai kuke so za ayi da yardar Allah鈥�
Ya fada yana dagawa Wanda yai masa kirarin hannu, bayan ya gama ajewa na kusa da teburin Nana abinci ya kalleta, bachi take hankalinta kwance ta dunkule kanta yadda ba za a gane ko wacece ba. Ba yau ce ranar farko yana fara ganin yarinyar nan ba, yau kusan sati biyu kenan tana zuwa nan, kulluk kuma idan ta zo ruwa kawai rake order ta yi zaman awanin sannan ta tafi kuma kullum da uniform take zuwa, tunani kawai yake anya ba wani rashin gaskiya take tana gudo nan ba?
鈥淜e Ke鈥�
Ya daki teburin, sai ta farka a firgice.
鈥淣a'am Na'am Na'am鈥�
Suna hada ta watsa masa harara ta turo baki gaba.
鈥淢iye bashi ko tara?鈥�
Ya dan wara ido sannan ya risino yadda babu wanda zai ji ya hade rai.
鈥淢e kike zuwa yi nan?鈥�
鈥淚na ruwanka ai na biya kudin ruwa鈥�
鈥淩uwa kawai suke kawo ki a nan? Daga gani wani laifin kika yi shiyasa kike zuwa ki boya or maybe kina gudun makaranta ne ko?鈥�
Ta yi saurin rufe baki tana zaro ido.
鈥淜arya kake ni bana aikata komai kuma bana gudun makaranta, yayana ne yace na rika zuwa nan ina jiranshi kullum鈥�
鈥淜ullum yau kusan two weeks kenan!鈥�
鈥淭o wai ina ruwanka wai? Ba na biya kudin ruwa ba鈥�
鈥淏a kudin ruwa kawai ake biya ba sai kin biya kudin zaman da kika nai awoyi, dan mu nan karanci mutum yai zaman 2 hour ya tafi amman ke har bachi kike, ki biya kudin bachi da na zaman awoyi da kika yi鈥�
Ta bata fuska.
鈥淲allahi ni ba zan biya ba haka kawai鈥�
鈥淭o ko zan saka security can ya fitar da ke waje kin ga dai akwai mutane ko za ki sha kunya鈥�
Yana fadar hakan ya mike tsaye ya juya, sai ta ka karewa kowa kallo tana ayyana yadda zata sha kunya idan yai mata korar wulakanci a gurin wata kila ma akwai wadanda suka santa ita bata san shi ba.
鈥淏aka ji ba鈥�
Ya juyo ya dawo daman Kadan-kadan yake tafiyar yana jiran ta kira shi.
鈥淣awa ne kudin bachin da kudin zaman?鈥�
Yayi wani shegen murmushi yana shafa kansa.
鈥�5k鈥�
Ya bude school bag dinta ta ciro kudin da zai kai 50k ta kirga 5k ta mika masa.
鈥淕ashi nan鈥�
Karba yai a ransa yana.
鈥楽hegiyar yarinyar ta gani diyar yar masara tausayin kasar ne bata san zafin kudi ba鈥�
Aljihunsa ya saka kudin daman aljihunsa babu ko sisi, sannan ya juya ya bar gurin mutane da ke vip din suna ta kallonsa shi kam a jikinsa.
FALMATA POV.
Daga unguwarsu zuwa unguwar da take aiki akwai yar tafiya mai nisa sai dai ba sosai ba, wata kila kuma ita din ce bata ganin nisan unguwar sosai kasancewar ta saba da tafiyar kasa daga wata unguwar zuwa wata a cikin garin Yola tun mahaifiyarta na a raye balle yanzu da Umma bata tausaya mata bata isa ko wani garin tace zata aikata da kafa ta ki ba.
Bata sha wahala gurin masu gadin masarautar da kuma polisawan da suke gurin ba kamar kwana biyu da suka wuce yanzu kam sun wayance ta ganin wannan shine zuwanta na uku bayan gabatar musu da ita da akai, sai dai a duk lokacin da zata shiga Masarautar ko ta fita sai ta rika jin tsoron dogarawan da kuma police din da suke gurin, domin Allah ya dora mata tsoron yan sanda sosai da sosai.
Ko'ina na masarautar mutane ne wasu da uniform wasu kuma babu kasancewar safiyata ko wa sai aikin gabansa yake.
聽 Ta kofar data saba ni ta bi ta dauki doguwar hanyar da ke sada mutum da bangaren Uwargidan Mai Martaba, tafiya ta wata karamar unguwar tsakanin Gate din karamar kofar gate din Ammy.
Ta kofofin da ta saba shiga ta fi tana tafiya sai kara karewa gidan kallo take tana ganin kamar ba a duniya take ba, saboda yadda aka tsara gidan da kuma kwalliyar da aka masa, ta bangare daya kuma tana mamakin irin girman gidan wai ace duk ba mutum daya ne, bayan bangaren Ammy ga wani bangare can ta hango wanda aka ce na Amaryar sarki ce can nesa da shi wasu gine ginen聽 na da ta mutane na fitowa ko na miye oho ita dai kallo kawai take, ga wasu manya manyan motoci na alfarma an faka a harabar space din Ammy, wata kila can bangaren Amaryar ma akwai motocin ko ina ma bangaren sarkin yake oho.
Ta fada a zuciyarta tana cigaba da tafiya tare da daga kanta sama tana kallon yadda aka jera windows din dakunan gwanin burgewa.
聽 Sai ta isa bakin karamin gate din mai gadin gurin dake rike da bulalarsa ya dakatar da ita.
鈥淜e ina zuwa?鈥�
鈥淣i ce Falmata wacce take gyara dakin yan uku鈥�
Ya mata wani kallo daga sama har kasa ya santa tun da wannan shine zuwanta na uku amman kullum ta zo sai ya mata tambaya, da gangan ya bata mata lokaci sannan ya bata hanya ta wuce. Da sauri ta raba ta wuce daman tsayar da ita da yai a gurin cikinta ya duri ruwa abun ka da mai tsoro, kamin ta karasa kofar shiga tsakar gidan dan ita ba ta falo take bi ba sai dai ta zagaya ta can baya kamar yadda aka nuna mata ta shiga ta inda mutane suke shiga haka ma idan zata fito.
鈥淜e.....鈥�
Iya dake tsaye lullube da zane ta kwala mata fira fuska a murtuke kamar bata taba dariya ba daman kuma fuskar ba ta dariya ba ce. Suna hada ido Falmata ta fara karanto addu'o'i ta nufe ta sam hankalinta ba kwanta da matar da duk kuwa da bata san aikinta ko matsayinta ko alakarta da yan gidan ba, sai dai ta lura kamar batsa shan inuwa daya domin ko ranar da aka kawota sai da tace ba a dauke ta ba dan kawai Ammy na gurin ne tace a dauke ta, kusan kullum idan ta zo aiki gidan sukai arba sai ta ji gabanta ya fadi ga wani kallo tsana da iya take mata, sannan ta hana ta ganin yaran kullum idan zata fara aikin sai tace a dauke yaran kuma sai ta saka dogari ya tsare ta har tai ta gama.
鈥淭afi tafi tafi tafi karki karaso nan鈥�
Iya ta fada yana runtse ido, ba karamin dadi Falmata ta ji ba, sai ta juya ta nufi hanyar shiga cikin gidan, sai da ta gaisa da mutane da yawa kamin ta samu isa bakin kofar farko ta falon Ammy. Haka ta ratsa falo kusan uku sannan ta isa gaban wata haraba tana kallon Hajiya karama dake tsaye a backyard tana kallon wani gurin dabam, Falmata ta kasa dauke mata ido, domin ta hadu iya haduwa tana da kyau sosai irin kyaun nan mai daukar hankali ga mayan ido sai dai ba manya can sosai ba, bayan tufafin jikinta mai kamada na turawa da ta saka wato English wears ta saki gashin kanta ya sauko sai tai kamar wata baturiya abun ka da Fulani.
Ba karamin burge Falmata Hajiya Karama tai ba, domin fari na daga cikin abunda Falmata ta rasa kuma yake burgeta iya burgewa idan ta ga wani da fari sai ta ji kamar ta cire ta sakawa kanta, ba dan tana da siffar Fulani ba da kuma yaren da take ji ba zaka ka taba kallonta kace ita Fulani ce saboda bakinta.
鈥淜o wacece? wata kila yar sarkin ce?鈥�
Ta tambayi kanta tambayar da bata da amsa a gurinta. Wani abun mamaki tana kwankwasa kofar corridor Iya ta bude mata tana watsa mata wani kallo mai kama da harara. Falmata ta bata yarda ta yi ido hudu da ita ba ta sanda kai kasa ta shiga. Kato falo ne mai cike da kayan alatu ga sanyin ac da katon plasma, an jera wasu 蓷akunan daga gafe, kai tsaye stairs din ta nufa ta fara takawa a hankali saboda tana gudun kar tsantsin gurin yaja ta ta zame kasa, sai da ta waiga taga babu kowa bayanta sannan ta risina kasa ta shafa tile din, sai a lokacin ta tabbatar ba ruwa ba ne kuma ba mai ba, a iya tunaninta yadda take jin tsantsin gurin da yadda take ganin yana shining a zatonta ruwa ne ko mai duk kuwa da kasancewar bata jin ta taka abu makamancin haka.
聽 Dan abun da aka nuna mata na jikin kofar ta danna wato door bell sannan ta ja ta tsaya sai rabon ido take, sai da ta danna shi sau kusan uku sannan aka bude mata kofar. Har kasa ta risina tana gaishe da Muhseen.
鈥淚na kwana?鈥�
鈥淟afiya kalau鈥�
Bayan ya amsa ya juya yana kallon Momy wacce ke tambayar waye a kofar.
鈥淲ata ce ban santa ba dai shigo鈥�
Ya matsa daga kofar wanda hakan ya bawa Falmata damar shigo cikin falon mai kama da aljannar duniya. Da sauri ta fadi ta kasa tana gaisar da Ammy, Ammy ta amsa mata ba yabo ba fallasa sannan ta cigaba da danna wayar da take.
鈥淩anki ya dade zan gyara dakinsu Yan uku ne鈥�
Ta fada muryarta kana ji kasan tsoro ne ya cika mata ciki fal, tsoron irin amsar da za a bata tsoron kallon matar sarki tsoron mutane da suke falon duka suka taru sukai mata tsaye a kai, kamin Ammy ta bata amsa har idonta ya soma cika da kwalla cikinta har murdawa yake kamar wacce tai wani laifi.
鈥淭o ai kin san inda dakin yake鈥�
Ta yi saurin mikewa tsaye ta nufi corridor da zai sadata da dakin yaran, a nan ma wasu hadiman ne suke ta aikinsu, Falmata sai gaishe su take kowa ta gani sai tace nasa ina kwana da wanda ya kamata da wanda be kamata ba, ta kasa daga ido ta kalli kowa.
Sai da tai Bismillah sannan ta kai hannu ta tura kofar dakin ta shiga har lokacin gabanta be daina faduwa ba, tsoron da take ji be gushe ba, haka take samun kanta a duk lokacin data shigo Masarautar, abun ka da wanda be saba shiga mutane sosai ba balle kuma manya kamar gidan Mai Martaba.
聽
Wannan karon ba tai mamakin ganin Iya a dakin ba, daman ta saba ganinta a kullum idan ta shigo sai dai wani abun da yake bata mamaki yau kusan kwananta uku da fara aiki a gidan amman bata taba ganin yaran ba ko hotuna, a kullum kuma sai ta tararda Iya a dakin, haka ma a kullum sai Iya ta saka dogari yai mata gadin dakin har Falmata ta gama gyaranta ta fita.
聽
鈥淜a sa ido, irin wadannan yaran ba abun yarda ba ne鈥�
Iya da fadawa dogarin tana wani yawo da manyan idonta akan Falmata kamar zata ciro su.
鈥淭o ranki ya dade鈥�
Ya amsa mata yana risinawa sannan ta fice tana ta wani shinshine虏. Falmata dai bata ce komai ba bayan gaisuwar da ta mikawa dogarin har da risina masa, sannan ta hau gyare gyaren dakin tana yi tana satar kallonsa domin gani take kamar wani abu zai mata.
Muhseen ne kadai zaune a dinning domin kowa ya karya a kama gabansa, wayar makkale a kunnensa yana ta fira da matarsa sai faman zuba murmushi yake kana ganinsa kasan yana cikin nishadi. Sai da ya gama breakfast din sannan ya yanke wayar ta taso ya nufo gurin Ammy yana fadin.
鈥淲ai har sun wuce ne?鈥�
Da kallo Ammy ta bishi tana murmushi har ya karaso kusa da ita ya zauna a kasa.
鈥淜a dade kana bachi ne shiyasa鈥�
鈥淕ajiyar jiya ce, gashi kuma yau zan kama hanya shiyasa na tsaya hutawa鈥�
Shiru tai na yan mintuna kamin ta kalleshi ta ce.
鈥淵au zaka koma kenan?鈥�
鈥淓h daman Mama Fulani kawai na kawo, ba dan ma yamma yayi ba ai da tun jiya zan koma dan ina da aiki yau鈥�
鈥淎i ka kyauta shi Aliyu ya dauke mana kafa ko?鈥�
Muhseen yayi murmushi kamar ba zai ce komai ba sai kuma ya shafa kansa ya ce.
鈥淪hi ma zai zo soon da Matarsa鈥�
Ammy ta tabe baki.
鈥淪hi dai ya sani, babu ruwansa da dangi daga Momy sai Fulani su kawai ya sani a rayuwarsa, ko da yakeba laifinsa ba ne laifin Fulani ne da bata nuna masa ba鈥�
Ammy ta karasa maganar tana aje wayar hannunsa.
鈥淜o da yake ga Shattima ne nan muna fama da shi, idan na ce yaje gurin yan'uwa kamar na kira masa mutuwa, sai dai azo a iske shi, wani irin jin kansu suke kamar wasu Sarakuna鈥�
鈥淎mmy ai kara ma Shattima da Aliyu, tun da shi zai zauna ayi fira da shi kuma zai sakewa kanensa Fuska, Aliyu kuwa idan kika ga yana fira to da Mama Fulani ne ko matarsa ko Momy sai kuma Abba鈥�
Ammy ta tabe baki.
鈥淯hm Abunda yai Aliyu shi yai Shattima idan ya ganka ne yake nuna shi na kwarai ne鈥�
Har Muhseen ya bude baki zai yi magana sai ga Iya ta shigo falon fuska daure.
鈥淩anki ya dade wai yarinyar nan za a bari tai ta kula da dakin yan uku?鈥�
Ammy ta mata wani kallo cike da kasaita.
鈥淎kwai wata matsala ne?鈥�
鈥淩anki ya dade ni kam sam ban yarda da ita ba, kuma yarinya ce karama ina zata iya wani abun kirki, yanzu ga masu aiki bila'adadin a gida amman ace sai an dauko wata daga can waje ta zo gyara dakin jikokin Mai Martaba?鈥�
Kallonta kawai Ammy take na wasu yan dakiku kamin ya bude bakinta cike da kasaita ta ce.
鈥淭o yanzu challenge dina kike yi Iya? Ko umarni kike ba ni?鈥�
Da sauri iya ta risinar da kai.
鈥淏a ko daya ranki ya dade Allah ya kara miki lafiya, shawara ce kawai ni kaina idan aka bar ni zan iya kula da su鈥�
鈥淭o Mahaifinsu yace baya bukatar kowa ya kula masa da su a nan sai daga waje, kuma shi yace baya son tsohuwa ko mai 拼a拼a, sai ki same shi ki bashi shawara鈥�
Kasa kasa Iya ta watsawa Ammy harara tana wani kashe ido.
鈥淩ana na zuwa Zainabu鈥�
Ta fada a ransa sannan ta juya ta fice bayan ta bawa Ammy hakuri. Sai da Iya ta fice sannan Ammy ta daga kai ta kalli Katuwar kofar ta dauke kai ta mike ta nufi hanyar dakinta.
Tsab Falmata ta gyara dakin yaran daman can ba datti yai ba sai dai kullum sai ta tisa gyaran ne ta goge ta saka turare ta canja sanin gadon yaran, tana gamawa ta fice ba tare da ta yi ma kowa sallama ba. Sai da ta fito daga Masarautar gaba daya sannan ta samu sallama da natsuwar zuciya domin a yanzu har numfashinta take jin ya daidaita tsabanin idan tana gida bata son yin numfashi da karfi wai kar su ji ace ta yi laifi. Ta mika kafa sai tafiya take ita kadai a titin da babu mutane sosai, idan ka cire kofar Masarautar da a kullum take cike da mutane sauran makotansa kowa yana cikin gidansa sai idan fitar ta kama, unguwar manyan mutane ce mai kama da GRA, ko'ina manyan gidaje ne gwanin sha'awa.
聽聽 Sai da ta shigo cikin gari sannan natsuwarta ta kara daidaita domin ta fi son unguwarsu fiye da wacan da take ganin kamar wata rana za a iya sace ta a can, da ganganta ta rage tafiyar da take ta soma tafiya kadakadan tana saurarin wakar Sirleem dake tashi a shagon wani mai charji, cikin zuciyarta take bin baitin wakar tana jin muryarsa na shiga har cikin kanta.
03/12/2021, 08:06 - 馃馃馃馃: *馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*Fadime dabam ta kauyen Katsina ita ce take jin busar sarewa. Falmata dabam ita ce ta Yola mai aikin raino a gidan Sarki, sai dai dukansu ana musu inkiya da Fulani. Fatar kun gane za ku daina rudewa 馃榾*
*4*
SIRLEEM POV.
鈥淗ajiya ina jin kamar ba zan iya jira har Nana ta kare Karatu na aureta ba....!鈥�
Ba Hajiya kadai ba gaba daya kanensa kallonshi su kai. Da Mamaki Hajiya tace.
鈥淏an gane ba?鈥�
Ya cika ma bakinsa iska ya busar sannan ya shiga murza hannunsa kamar mai shafa mai.
鈥淜awai dai bana iya jira, tana kula wasu bayan kuma kowa a Masarautar nan ya san ni zata aura, sannan ina ganin kamar yan gidansu basa son hadin nan nawa da ita idan abun ya kai wani lokacin za su iya lalata shi鈥�
Ajiyar Hajiya ta sauke.
鈥淕askiya ne, za su iya lalatawa amman zancen tana kula wasu kar ya dame ka kai auren a haka ai zata daina kuma idan ka gani ka rika magana鈥�
鈥淣a ganta da Deen din nan da yake zuwa duba yaran Shattima, na je har Part din su na yi magana babu wance komai karshe ma Hajiya Karama ta taso tana fada ni wai ina takurawa Nana kamar wani ubanta鈥�
Hajiya ta yi murmushi mai kama da dariya.
鈥淜ar hakan ya dame ka Sirleem kai dai ka aureta kawai komai zai wuce鈥�
Ya kalleta cike da gajiyar jin abunda take yawan nanata masa idan yai mata complain akan Nana.
鈥淏ut Hajiya miyasa dole sai Nana? Tsakanin da Allah neman auren nan na saka kaina ne kawai saboda kin tirsasa ni amman ni kaina yarinyar nan bata kwanta min ba, ni kuma na fara gajiya gaskiya ba zan jure daukar wulakanci a gurin kowa ba na fi karfi haka, dan kawai tana yar sarauta ubanta yana sarki mahaifiyarta tana matar sarki yayanta yana dan sarki ba zan dauki wannan wulakanci ba na fi karfin wulakanci a gurin kowa ni鈥�
Ya fada yana daga kafadunsa, Rima ta tabe baki tana ture kofin tea dake gabanta tare da kallon yayan nata.
鈥淣i kaina ba son auren nan nake ba, dan dai kawai Hajiya ta matsa ne akan ayi, amman miye amfanin hada alaka da makiyi alakar ma ta aure haba dai...鈥�
Murmushi Hajiya tai ta taso daga kujerar da take zaune ta dawo bayan Sirleem ta tsaya.
鈥淢2 ba haka duniya ta sanka ba? Kai a yadda kake Celebrity sai kaje ka auri wacce bata kai ba? Ga yar sarauta yar masu naira kuma kyakkyawa yarinya mai kurciya a gidanku? Ba ka lura ba? Maran manyan mutane suna auren yar manyan mutane? A yadda kake sannen a duniya ai kamata yai ace ka auri yarinyar da ta isa gaba da baya, taya za a tashi maganar da kasan zata iya saka Mai Martaba a cikin wani hali bayan gashi kwance ba lafiya? Baka tunani ya takama mu sakawa Mai Martaba da irin hallacin da yai mana? Idan mahaifiyarta matar sarki ce kai ma taka uwar matar sarki ni da Zainabun Jirgi daya ya dauko mu domin dukanmu Mai Martaba muke aure. Ke kuma Rima da kike fadar hakan ai kyautatawa ce wanda yai maka sheri sai ka saka masa da alheri, ba ni da burin da ya wuce na ga Sirleem ya auri Nana a yanzu ku karfafawa dan'uwanku guiwa ba wai ku sare ba鈥�
Ta karasa tana kallon Rima. Sirleem ya juyo yana kallon mahaifiyarsa tasa.
鈥淎mman Hajiya ai ba Nana ce kadai yar sarauta ko yar masu arziki ba, akwai da yawa mi yasa ba zaki bar ni naje da kaina na zabi wacce tai min ba?鈥�
鈥渋dan zaka auro yar sarkin Makka, dan arzikinsu da Sarauta ba ka cika min burina ba matukar baka auri Nana ba, idan kuma zaka auri yar sarkin talauci na duk duniya bayan ka auri Nana to ba zai tana damuna ba, ni dai burina Nana ta zama uwargidanka鈥�
A hankali ya aje numfashi yana kallon kanensa wanda shi ma kallonsa yake suna mamakin furucin mahaifiyar tasu. Talba ya ce.
鈥淎mman Hajiya miyasa?鈥�
鈥淪aboda ta wannan hanyar ce kawai zan iya sakawa mahaifinka da abunda yai mana鈥�
Gaba daya kanensa mata su uku tashi sukai daga dinning, kaf a duniya basa da makiyiya irin Ammy wato uwargidan Mai Martaba, su kam ba su da dalilin na cewa ala dole sai yayansu Sirleem ya auri Nana ba bayan shi kansa ba sonta yake ba. Da kallo ta bisu tana murmushi kamin ta kalli Talba ta ce.
鈥淩aheen a kira min Kulu鈥�
Tana fadar hakan ta nufi hanyar dakinta cikin wani irin taku kamar wacce ba zata mutu a saka a kasar ba, tsadadar shaddar dake jikinta sai motsi take tana wani maiko. Tashi Talba yai ya fita domin zuwa kiran Kulu kamar yadda ta Umarta, Sirleem kuma ya ciro wayarsa daga aljihu yana kallon kiran Mansura da ke shigowa wayarsa.
Gaban madubi ta tsaya tana kallon kanta fuska babu annuri kamar ba ita ce dazun ta gama dariya ba, a zahirin sarkar gold din dake wuyanta wacce ta sauko har saman kirjinta take kallo a badini kuma zuciyarta na can wani gurin tana wani tunani na dabam,聽 stool din madubin ta ja ta zauna tana cigaba da kallon kanta abubuwan da suka faru a baya take tunawa, ta dayan bangaren kuma tana kitsa yadda wasu abubuwa za su tafi a nan gaba. Yanayin yadda take motsa bakinta kadai ya isa ya sanar da cewar zance zuci take.
鈥淪higo鈥�
Ta fada tana dauke kai bayan an kwankwasa dakin minti uku da suka wuce. Kulu ce ta shigo dakin tana sanye da doguwar riga ta atamfa an mata irin dinkinsu na tsohu kanta lullube da mayafi, gaban Hajiya Bilki taje ta zauna tana mika mata gaisuwa.
鈥淎llah ya taimake ki ya kara miki lafiya, Sardauna yace kina nemana鈥�
Tashi Hajiya tai daga kan Stool din ta koma saman shimfidarta da ke gefen gado ta kishingida tana kallon Jekadiyar ta ta.
鈥淜ulu wane Likita ne yake zuwa duba yaran Shattima?鈥�
鈥淲allahi ban san shi ba ranki ya dade鈥�
Wani kallo Hajiya tai mata.
鈥淭aya za'ayi kina cikin masarautar ace baki san masu shiga da fita a ciki ba?鈥�
鈥淩anki ya dade na ga kamar bangaren Ammy ne, ni kuma na fi kula da abunda ya shafi bangarenki ne Allah kara miki lafiya鈥�
鈥淭his is nonsense, Ammy da bangarenta ba a cikin masarautar nan suke ba?鈥�
Hajiya ta fada a tsawace har tana tashi zaune fuska babu annuri.
鈥淐iki suke Allah ya baki yawan rai, tuba nake鈥�
Cewar Kulu tana kara noce kai kasa.
鈥淜ina da matsala Kulu, duk abunda ya kamata ki saka ido akai ba kya yi鈥�
鈥淶an bincika ko waye shi Allah ya huci zuciyar ki ya kara miki lafiya鈥�
鈥淜ira min Jarma鈥�
鈥淎n gama ranki ya dade鈥�
Kulu ta mike da sauri ta fice daga dakin ganin yadda Hajiya ta hade rai kamar bata taba dariya ba. Ba a dauki dogon lokaci ba Jarma ya shigo dakin yana sanye da babban riga ga wani uban rawani a kansa, inda Kulu ta zauna ya zauna tana kallonta hankalinsa kwance sai dai har ya zauna ta kira shi ya amsa ta kora masa bayani bata kalleshi ba.
鈥淛arma鈥�
鈥淗ajiya鈥�
鈥淎kwai wanda ke son shiga tsakanin Sirleem da Nana鈥�
鈥淎 cikin masarautar nan yake?鈥�
Jarma ya tambaya cike da mamaki, sai a lokacin ta kalleshi.
鈥淏are ne, yaron da yake zuwa duba yaran Shattima鈥�
Jarma yayi murmushi.
鈥淒oc Deen? Kar hakan ya damu Salim, wayayyace kawai irin ta yan zamani ke kinsan ai ba zan bari wani ya dauki hankalin Nana ba鈥�
鈥淚dan ma ka ga zai kawo mana matsala ko wasa, aka yi masa sanadi da gidan nan鈥�
鈥淏aki da matsala da wannan Hajiya Salim ya cigaba da neman yarinya babu abunda za a fasa鈥�
Ta dan yi murmushi tana kallon wata doguwar Fulawa dake gabanta.
UNCLE A A POV.
Ya yamutsa shinkafa da waken dake gabansa a kwano yana bata fuska.
鈥淎nti Rabi sai ayi ta mana wake da shimkafa ba wani canji鈥�
Anti Rabi dake aikin damawa dabbobinta kasari ta yi dariya.
鈥淗mm Unclen dinsu wani lokacin iskancin ka yawa yake, wani na can be samu kamar wannan ba amman kai ka raina, da alama dai kana da kudin cin wani abinci shiyasa鈥�
Ya shafa kansa yana yar dariya.
鈥淲allahi kuwa wata yar marasa sanin darajar naira na samu nai mata na yan talakawa na ci kudinta鈥�
鈥淏an gane yar marasa sanin darajar naira ba鈥�
Yayi dariya a karo na biyu sannan ya labartawa Antinsa yadda ya yaudareta.
鈥淎mman dai Uncle din yara baka da tausayi鈥�
鈥淲ane irin tausayi kina ganin yarinyar nan kin san yar masu abunce ce karamar yarinyar yar secondary school ta ciro kudi sun kusan 50k ta bani 5k ya maida saura, uwayensu ne barayin Jihar mu ai鈥�
Ya mike tsaye yana ciro kudi, 2k ya cire a ciki ya mikawa Yayar tasa sannan ya maida sauran aljihu.
鈥淣i bari naje waje na ci abu mai kyau鈥�
鈥淣i wannan aikin na ku yana bani mamaki kuma aiki a restaurant amman ba zaku iya cin abinci a ciki ba?鈥�
鈥淎i wannan mutumen be da kirki ko ruwansa ka sha sai ka biya shi, zaka ci idan kana so amman zai cire a cikin albashinka鈥�
鈥淎llah dai kyauta ni kam ban taba gani ba鈥�
鈥淎i ina samun wani aikin zan bar na shi Wallahi鈥�
鈥淎llah dai ya kawo rabo mai amfani鈥�
Da amin ya amsa sannan ya fice daga gidan. Abun ka da unguwar mai mutane yana fita abokasa suka fara dago masa hannu.
鈥淪ai Sardaunan samarin Yola鈥�
Ya nufe su yana dariya.
鈥淎mman na talakawa鈥�
Ya karasa ya basu hannu suka gaisa sannan ya kara gaba ya siye alalen gwangwani gurin wata ya cika cikinsa a titi.
Washe gari ma fa yaje restaurant din sai da ya sake tararda Nana a inda ta saba zama, wannan karon ba bachi take ba idonta biyu suna hada ido ta watsa masa harara ta kawardar da kai, a iya ganinta da yake yi a yanzu kam ya tabbatar karya take da tace yayanta ne yake cewa ta jira a nan, ya lura idan ta ga mutane sai ta boye fuskarta kar a ganta haka yai ta aikin raba ma jama'ar da suke shigowa abinci yana kallonta zuciyarsa na karantarta tana tsara masa yadda zai sake samun wasu kudin a gurinta.
聽 Sai da ya koma gurin zamansa ya zauna sannan ya dauki biro da takaradar yai rubutu a kai ya dauki bottle water ya nufi inda take ya aje mata takardar a saman tebur din tare da ruwan ya koma ya zauna yana kallonta.
Tun da ya nufota take turo baki tana harararsa har ya karaso ya aje mata ruwan da takardar ya koma, a zatonta zai ce yau ma sai ta biya kudin zaman dana bachi amman bata ji yace mata komai ba, sai dai ta lura duk abunda yake idonsa na kanta.
鈥淣i nace ka kawo min ruwa ne鈥�
Ya fada tana turo baki cikin sautin da ita kadai zata iya jin kanta, na kusa da ita ko kuma mai kallonta sai dai yaga bakinta na motsi sai hararar da take watsa masa ta isa ta sanar masa cewar da shi take. Hannu ta kai ta dauki takardar ta jefar a kasa tana cigaba da turo baki ita ala dole ga shagwa6a66iya.
鈥淏a za a karanta ba鈥�
Daga can inda yake zaune ya gwalo mata ido ya hade rai yana mata alamu da ta dauki takardar ta karanta ko ya daketa, sai ta make masa kafada tana murguda masa baki, sai da ya unkura kamar zai taso ta karaso inda take sannan tai saurin kai hannu ta dauki takardar ta bude.
鈥淚dan kina so zan iya kai ki wani guri inda zaki rika boyewa ba tare da kowa ya sani ba, amman nan ai public place ne kowa zai iya ganinki, idan kin aminta fita waje mu yi magana鈥�
Da sauri ta dago ta kalleshi tana gyada masa kai alamar eh ta amince din, da ido yai mata alama da waje sai ta dauki school bag dinta ta nufi hanyar fita tana waigensa. Sai da tai kusan minti biyar da ita sannan Sardauna ya fakaici idon mutane ya tashi ya fita. Can gefe ya hangota ta juya baya dan kar a ganta sai boye boyen fuska take.
鈥淜e鈥�
鈥淣i ba ke ba ni Nana Aisha鈥�
鈥淭o ina ruwana da wani sunanki鈥�
鈥淭o nima ina ruwana da kai鈥�
Ita ta amsa masa ta shigar da yai mata maganar wato da fada fada, sai yai kwafa ya juya alamar zai tafi ya barta, da sauri ta riko hannun rigarsa.
鈥淭o akwai ruwana鈥�
Ya sake yin kwafa sannan ya kalli security camera dake gurin ya kalleta.
鈥淚dan kina so zan iya kai ki gidan ku sai ki boya a can idan lokacin da direban ki zai dauke ki yayi sai na dawo da ke鈥�
鈥淚na zuwa鈥�
Ta fada kai tsaye cike da jindadi, kallonta ya tsaya yi a ransa yana ayyana cewar idan shi barawo ne sai ya sace ta salon alon.
鈥淭o ai zamu aro babur da zamu je can unguwar鈥�
鈥淭o aro鈥�
鈥淶aki hau?鈥�
Ya tambaya da mamaki dan be dauka zata yarda ba.
鈥淓h鈥�
鈥淭o ai kudi ake biya kamin a bamu aron babur din鈥�
鈥淣awa?鈥�
Tunani ya tsaya yi kamin ya ce.
鈥�2k kuma a can gidan da zaki zauna sai kin biya kudin zama鈥�
Ta dan bata fuska.
鈥淣awa?鈥�
鈥�3k鈥�
鈥淭oh, ai dai ba zaka sace ni ba ko?鈥�
鈥淓h shekararki nawa?鈥�
鈥�16鈥�
鈥淎mman dai ke wawuya ce鈥�
Ya fada yana dariya a ransa sannan ya juya ta nufi cikin restaurant din, abokinsa Mu'az yai ma magana ya karbi makulin mashin dinsa sannan ya fito ya same ta a inda ya barta.
鈥淜i fita can titi sai na zo na dauke ki鈥�
Ba musu ta kama hanya a ranta tana jin zafin wawuyar daya kira ta dazun, karasa yai gurin da suke aje abun hawan a gurin ya bude mashin din sannan yasa masa key yai tashi mashin din sannan ya fara tukawa ya fito da shi bakin titi can ya hangota ta boya a kusa da wani shago, karasa yai gurim ya faka mata ta hau yana fara tafiya ta rirrike shi gam ta boye fuskarta a bayansa, kusan sai ta rantse a rayuwarta bata taba hawan achaba ba, iyakarta keke shi ma tana yin wayo Ammy ta hana ta hawa saboda tana mace.
鈥淜e dallah sake ni kin wani rike ni kamar yar iska haka zan shiga da ke a unguwar mu kina tabani, ni ba dan iska ba ne ba a saba ganina da mace ba balle kuma ta rike ni鈥�
鈥淭o ni ba tsoro nake ji ba ko kuma ni aka ce masa yar iska ce, ni yar iska ce kai ne dai dan iska mai sato yarinyar mutane kaje ka kaita wani guri ta boya鈥�
Ta fada tana turo baki har lokacin bata yarda ta dago kanta ba. Tafiyar ba tai nisa ba ya faka mashin din gefen titi ya sauko ya fuskance.
鈥淣i ne ma dan iska mai sace yaran mutane? Ai ke ce stupid girl mai guduwa daga makaranta kina boya a wani guri, kuma ba zan kai ki din ba na fasa鈥�
Ya karasa yana dangwararta da yatsansa.
鈥淎i Wallahi ba zan sauka ba, zan maka ihun ka yi satar mace鈥�
Yadda ta daddage kan mashin din kamar na gidansu tana watsa masa wani kallo ya sani sarai zata iya iya masa ihun abunda ba halinsa ba, kwadayi yaja masa bala'i, ya san ma it's risk tsayinsu a gefen hanyar dan wani wanda ya santa zai iya ganinta da shi, ba shi da wani option da ya wuce kaita gidansu din ko kuma maidata inda ya daukota. Da farko yayi kudirin maidata inda ya daukota sai dai zuciyarsa na son kudin nata da yake gani kamar na banza a dole ya daure ya cije ya cigaba da tafiyar idan ta riko shi ya buge hannunta har suka kusa isa unguwar sannan yai mata dabara da ta rike karfen mashin din ta sake shi.
Bata yarda ta dago fuskarta ba sai da ya faka mashin din kofar gidansu ya sauka sannan ita ma ta sauka tana wani kyankyamin unguwar balle kuma da aka shiga cikin gida har wani dage kafa take sama sama kar ta taka kasa.
Shi yai sallama Anti Rabi dake aikin hada kwado ta amsa masa, ita kam banda aikin bata fuska da karema gidan kallo babu abunda take. Anti Rabi ta bishi da kallo har ya shiga dakinsa Nana na biye da shi ya dauko tabarma ya shimfida mata bakin kofar Anti Rabi.
鈥淶auna a nan鈥�
Ta karewa tabarma kallo tana kyankyami.
鈥淲allahi ba zan zauna ba, wannan gida duk kazanta ni ba na son nan鈥�
Ya zaro ido
鈥淜an uban gidan na mu ne duk kazanta? Idan ba ki zauna ba zan bata miki rai鈥�
Ya fada a tsawace amaimakon ta ji tsoro kamar yadda yaran Anti Rabi suke idan yana musu fada ita sai ta make kafada.
鈥淲allahi ba zan zauna ba, gida duk datti gidan dokin mu yafi wannan鈥�
鈥淶an zane ki zan miki bulala鈥�
Ya fada yana nuna mata icen dogon yaron dake gidan, sai ta sake make kafada.
鈥淲allahi ba zan zauna ba, kuma ba zan koma can ba, kuma ba zan biya kudin ba鈥�
鈥淣a rantse da Allah karya kika sha鈥�
Ya fada yana buga kafa a kasa dan kudin sune damuwarsa. Anti Rabi ta tashi ta shiga dakinta jikinta na bari ta kwalowa kanen nata kira.
鈥淎A...鈥�
鈥淭saya nan sai na fito鈥�
Ya fada mata bayan ya amsa kiran Anti Rabi, sannan ya nufi dakin ya cire takalminsa ya shiga cikin rada Anti Rabi ta fara masa magana har lokacin jikinta rawa yake dan tsoro ya gama kamata.
鈥淚na ka dauko wannan yarinyar?鈥�
鈥淚ta ce wanda na baki labari jiya鈥�
鈥淭o miyasa zaka dauko ta ka kawo nan? Kidnapped dinta zaka yi?鈥�
鈥淎'uzubillahi haba Anti kamar dai baki san ni ba? Ce mata zan kaita inda zata boya sai ta biya kudin鈥�
Hannu biyu Anti Rabi ta hada tana rokonsa.
鈥淒an Allah dan Annabi ka rufa min asiri ka maida yar mutane, karka jamin masifa ka jawa kanta, daga ganin yarinyar nan yar manyan mutane ce, ka duba kaga irin kallo da ake mana a unguwar nan na masu rufin asiri amman ita kallon kazamai ma take mana har da cewa gidan dokinsu ya fi gidan nan kyau ka rufa min asiri ka maida ta karka sake kallonta ma kar sheidan ya sake raya maka wani abun鈥�
鈥淎nti Rabi.... 鈥�
鈥淎 a bana son jin komai indai kana jin maganata ka maida yarinyar nan inda ka dauko ta dan Allah鈥�
Juyawa yai ya fito daga dakin, sa cin karo yai da Nana tsaye a kofar dakin da alama labe tai musu.
鈥淲allahi ba zan koma ba, sai direbana ya zo kuma ba zan zauna a nan ba鈥�
Anti Rabi ta fito da sauri ta hade hannayenta ta risina har kasa tana rokonta.
鈥淒an Allah dan ma'aiki ki rufa mana asiri yarinyar nan ki koma inda ya dauko ki鈥�
Ta make kafada daya lallai ita ba zata koma ba.
鈥淪ai idan direbana ya zo鈥�
鈥淗aba Anti ya zaki duka kina rokon yarinya kamar wannan dan Allah tashi鈥�
AA ya fada cike da jin haushin yadda yayar tasa ta risina tana rokon Nana, wanda hakan ba karamin dadi yai ma Nana ba domin ko a gidansu aka risina mata dadi take ji tana ganin an bata girma yadda ya kamata tun da Mai Martaba ba ma haka ake masa. Anti rabi bata bi ta kansa ba ta ce.
鈥淵anzu ya kike so a yi?鈥�
鈥淪ai ya duka ya roke ni yadda kikai鈥�
鈥淣i din? Ashe ko zaki tsufa a tsaye鈥�
AA ya tambaya yana kallonta da mamaki ganin take kokarin zame masa kashin wuya.
鈥淏a zan zauna akan wannan ba鈥�
Ta nuna tabarma sai Anti tace.
鈥淚dan na dauko miki katifa na shimfida miki a waje zaki zauna?鈥�
Tayi wani abu da kai kamar mai yanga sannan ta amsa da eh. Abun ka da mai nema cikin sauri da kuzari Anti Rabi ta dauko katifar dake kan gadonta ta aje a waje ta dauko zanin gadon data wanke ta ninke ta shimfida mata har da su filo. Sai da Nana ta karewa katifar kallo sannan ta cire takalminta ta hau ta zauna tana kara karewa gidan kallo.
Anti Rabi ta kuma ta cigaba da hada kwadon da take cikin rashin natsuwa dan ita tsoro ma take kar wani wanda ya santa ko ya san yan gidansu ya shigo ya ganta a gidanta.
Bayan ta gama ta zubawa AA ko da wasa batai ma Nana ta yi ba dan ta san ba zata ci ba, ita dai tana zaune tana kallon yadda AA yake aikin auna kwadon a bakinsa kana gani kasan yunwa yake ji.
鈥淕ashi nan ba kiba sai mugun ci鈥�
Ta fada a ransa, kamar ya san ta yi maganar sai ya juyo ya kalleta.
鈥淶a ki ci?鈥�
鈥淎llah ya tsare ni da cin ragin abincinka kazami da kai ma鈥�
Ta fada tana dauke kai, har cikin ransa ya ji zafi ya kalli Anti sai tai masa alama da yai shiru, a iya tunanin Anti Rabi yarinyar tana neman rigima ne ayi mata wani abu taje tace an taba ta babanta yasa a dauresu ita da AA duk kuwa da kasancewar bata san waye uban nata ba.
Sai karfe daya da yan mintuna direbanta ya kirata ya fada mata cewar zai zo ya dauke ta yanzu, sannan ta tashi wanda yai daidai ta dawowar yaran Anti daga makaranta.
鈥淜i ce masa ya maida ni鈥�
Ta fada ta sigar Umarni kamar yadda take wa bayin gidansu. Anti聽 Rabi ta kalli AA dake aikin danna karamar touching dinsa tace.
鈥淎-A tashi ka kaita鈥�
Ba musu ya mike tsaye ya saka wayar aljihu.
鈥淚na kudin zaman da kika yi dana katifar duk sai kin biya鈥�
Ta bude jakarta ta kirga kudin da za su yi 8k ya mikawa Anti.
鈥淕ashi na zaman da nai da na katifarki, ai ba gidanshi ba ne ba katifarshi ba ce鈥�
AA ya saki baki yana kallonta.
鈥淭o waya kawo ki gidan? Ki bani kudina malama鈥�
Ta maida ragowar kudin.
鈥淲allahi ba zan bayar ba, kai da kace min ma kai dan iska鈥�
Anti ta zaro ido.
鈥淪ubhanallahi AA鈥�
鈥淣a rantse da Allah karya take wannan yarinyar munafuka ce鈥�
Ya karasa yana kara dangwararta a karo na biyu bayan wanda yai mata a titi.
鈥淜in gani ko haka dazun yai min a titi dan yace na taba shi na ki wai sai dai na rika taba shi idan muna kan babur din hadda cewa yai zai sace ni鈥�
Bayan kallon Anti Babu abunda AA yake, gaba daya kunya ta gama rufe shi shi da ko budurwa be taba yi ba yau ace wai yana neman mace ta taba shi, ji yai kamar kasa ta rabi biyu ya shige ciki, Anti ta kasa cewa komai sai kalloshi take da mugun mamaki.
鈥淜aje ka aje ta inda ka dauko ta鈥�
Ta masa maganar da sigar da shi kansa ya san ba da wasa take ba.
鈥淭o鈥�
Ya juya sululu ya fice, Nana ta risina ta aje kudin da Anti ta ki karba saman katifar sannan tai mata sallama ta fice. Ko da ta fita har ya tashi babur din ita kawai yake jira, kamar dazun yanzun ma tana hawa ta sake rike shi sai da ya buge mata hannu sannan ta maida kan karfen baya ta boye fuskarta a bayansa.
Tun da suka kama hanyar bata ji yace mata komai ba, a tunaninta zai mata magana ko yai mata fadan karyar da tai masa a gurin yar'uwarsa amman sai taji shiru.
鈥淣i ba zan sake biyoka ba鈥�
鈥淜i ga ma Uban da zai sake zuwa da ke, ko a restaurant din nan na sake ganinki sai na fadawa shugaban mu yasa an koreki鈥�
Ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ba.
鈥淜a yi hakuri ba zan sake ba鈥�
Be ce mata komai ba har suka kusa isa, sannan ya faka gefen hanya ya sauka kan babur din ya kalleta.
鈥淏a ni 5k dina, kin ga dai taimakonki nai ko? Dan Allah ki bani kudina dan Allah鈥�
Bata ce komai ba sai kallonshi take. Hakan yasa ya koma rokonta ta sigar tausayi yana mata magiya a iya ganinsa idan ta tafi ba ta bashi kudin nan a yayi aikin banza kenan.
鈥淗aba baiwar Allah, ki ji tausayina kin ga nan ni maraya ne ba uba ba uwa komai ni nake yi ma kaina kuma gashi ba wani aiki sai na restaurant dan Allah ki ba ni kudin kinji?鈥�
鈥淏a kace ba zaka sake kawoni ba鈥�
鈥淶an sake kawoki, mota ma zan aro ba babur ba kin san ya fi sirri鈥�
Ya amsa mata da sauri.
鈥淜a iya mota?鈥�
鈥淓h鈥�
鈥淚dan kana zo zan iya maida kai direbana sai ka rika kawo ni nan kullum idan lokacin tashina yayi sai ka maida ni gida鈥�
鈥淒a gaske?鈥�
Ya kara masowa kusa da ita.
鈥淓h yau zan ce ma Ammy bana son driver din ta canja min wani鈥�
鈥淜uma zata amince?鈥�
鈥淓h鈥�
鈥淭o kawo wayarki na saka miki number ta idan ta amince sai ki kirani鈥�
Ta bude jakarta ta dauko iPhone yar yayi ta kunna sannan ta mika masa.
鈥淭o sa min a nan鈥�
Da mugun mamaki da kuma dan tsoro ya karbi wayar, how yarinya karama kamar ita ace tana rike irin wannan wayar? Lallai babanta ba karamin barawon kasa ba ne.
鈥淲aya saya miki wayar?鈥�
Ya tambaya bayan ya saka mata number.
鈥淎mmy na ce ta siya min bata siya min ba, Ya Shattima idan na masa maganar baya sai ya ce sai na gama makaranta, Hajiya Karama ce ta siya min?鈥�
鈥淲acece Hajiya Karama?鈥�
鈥淵ayata ce鈥�
鈥淲aye mahaifinki Nana?鈥�
Ya tambaya mamaki na kara bayyana a fuskarsa, har ta bude baki ta bashi amsa sai kuma ta fasa bata son ya san asalinta gudun kar ya tona mata asiri ko kuma ya sace ta.
鈥淲ani ne ba shi da lafiya ma, baya son mutane idan an yi taro da yawa sai ya rika jin tsoro shiyasa baya fita muma ba kullum ake bari muna shiga ba, ance wai sammu ne wasu kuma su ce jiface amman dai Ammy tace mu daina cewa haka mu rika cewa be da lafiya kawai鈥�
Ya maida wayar a jakarta bayan ta kashe, wannan karon kallon tsoro yake mata sai a yanzu yake fahimtar yaren da Anti Rabi take masa, wata nawa yana kokarin ganin ya canja wayar hannunsa ya siye ko ta 50k amman abun ya gagara, yau sai gashi yaga karamar yarinya da wayar 500k lallai mayan kasar nan ba karamin dadin rayuwa suke ji ba, ya raya a zuciyarsa a take sai yaji ya ba kansa tausayi matuka.
鈥淗ow babur na maida ke鈥�
Bata ce komai ba ta bude jakarta ta ciro 7k ya mika masa.
鈥淕ashi鈥�
Ya kalli kudin be karba ya ce.
鈥淲a yake ba ki wadannan kudin?鈥�
鈥淗ajiya Babba鈥�
鈥淢ahaifiyarki?鈥�
鈥淎 a Step mother dinta, wani lokacin kuma Hajiya Karama ma tana ni kudi sosai idan ta samu Ya Shattima ma yana bani amman ba sosai ba, sai Ya Sirleem shi ma yana ba ni sosai, ka karba鈥�
Ya kara mika masa, ya dade yana kallon kudin da mugun mamaki sannan ya karba yana tunanin anya ma mutum ce? Ko dai garin shegen son kudinsa ya kwaso aljana? Yanzu akwai yarinya karama mai rabon kudi haka dan bata san zafin su ba?
Ya hau babur din ita ma ta hau baya suka cigaba da tafiya, be yarda ya isa har cikin restaurant ba ya sauke ta a titi ya shiga ciki, ita kam bata ma shigo ciki ba sai ga direbanta ya zo daukarta sai kawai ta shige mota suka kama hanyar gida.
03/12/2021, 08:07 - 馃馃馃馃: *馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*5*
HAJIYA KARAMA (Zainab) POV.
Ta bude motar ta fito tana karewa gidan kallon kamar wani bakonta, ko da yake kusan gidan bakonta ne domin tun zuwanta na farko ba ta sake ba sai yau, Zainab irin matan nan ne da basa bin kawaye sai dai kawaye su bi su dan suna jin sun isa, tana ji da Sarautar da ba ta jininta ba tana jin naira ga kuma daukaka da ta samu sakamakon aikinta na daukar hoto wanda ba kasafai kake mace bahaushiya kuma musulma tana yi ba, bayan daukar hoto Zainab fitattaciyar yar daukar wanka ce聽 Instagram hakan yasa hotunanta suka yawo a duniya kamar wata yar film ko mawakiya ga kuma kyau da Allah ya hore mata da cikar sura irin ta ya mace.
聽 Katon bakin gilashin idonta ta cire tana kara kallon mijin kawarta da kyau, sai ta ga yafi kyau a fili ma fiye da hoton da Humaira ta dora lokacin anniversary su. Daga inda take tsaye sanye da dogon wando na jean da half gown ta atamfa kanta da jar hulla waccw ta bayyana rabin gashin kanta daya sha gyara, ta daga masa hannu alamar HI tana wani yauki da fingers dinta kamar ba farata ba sai wani murmushi take masa na daukar hankali. Da mugun mamaki ya dago mata hannun shi ma wai celebrity ta dago masa hannu da kanta ya santa dan yana daya daga cikin followers dinta na instagram, secondly kuma Humaira na yawan ba shi labarinta ta nuna masa hotonta ya fi a kirga third kyauta ya wuce yadda yake ganinta a hoto domin a fili farinta har wani haske yake kana ganinta ka ga yar fulanin asali kuma wayayyiyar mace.
鈥淏a laifi bayan kyau kana da naira鈥�
Ta fada a ranta tana karewa tsaddadiyar motar da yake kokarin hawa kallo, sannan ta doshi cikin gidan tana wani irin taku na daukar hankali, murmushi ya cika kyakkawar fuskarta ko ba komai zuwan da tai yau saboda mijin kawarta ne domin tun a lokacin fa Humaira ta saka shi a status dinta na happy anniversary ta ji ranta ya biya, kuma bukatarta ta biya tun da ta yi arba da shi.
Door bell din ta danna in few minutes house help din Humaira ta bude mata kofar, sai ta nasa kafarta a katon falon tana kare masa kallo, a ranta ta raya ba laifi ita kam ta ga gurin zama. Cike da far'ah da jindadin ziyarar Humaira ta fito ta rumgume ta.
鈥淥yoyo manyan kasa yau ke da kanki Hajiya Karama鈥�
鈥淭o ya za'ayi muna so ne ai dole mu biyo, ykk鈥�
鈥淟afiya kalau ya gida ya su Hajiya da Ammy鈥�
鈥淪una nan kalau ina yaranki?鈥�
鈥淪una makaranta鈥�
Ba laifi Hajiya Karama ta saki jiki suka sha fira da Humaira har abun ya bawa Humaira mamaki domin ba kasafai Hajiya Karama take sakewa tai fira da kawaye haka ba no matter how close they are, ita din tana da wani irin jin da kai da isa idan ana fira sai dai ta rika jefo zance can sama-sama, hakan kuma be hana kawaye binta domin tana kashe musu kudi kamar bata san zafinsu ba, ga kyauta da alheri ga kowa.
鈥淏ude min wayar na ga hotunan anniversary tun da ba a fada mana ba鈥�
Ba musu Humaira ta cire mata password tana dariya tare da fadin.
鈥淏a mu gayyaci kowa ba fa daga ni sai yara mu kai sai uban gayyar鈥�
Cikin hotuna Hajiya Karama ta shiga tana dubawa, sai da ta bari Humaira ta tashi sannan ta shiga long calls dinta tana bin numbers din da kallo, number da aka sakawa Alone da hoton heart ta bude tayi copying digit din ta shiga message ta saka number ta ta aika ma kanta da number sannan ta goge sakon ta aje wayar tana murmushi.
鈥淗umi zan wuce daman na biyo ne kawai na gaishe ki鈥�
Har gurin motarta Humaira ta rakota tana ta mata godiya domin ba karamin dadin ziyarar taji ba, ba ta bar Hajiya Karama ta wuce ba sai da su kai hoto.
Cikin farinciki ta dawo Masarautar ranta fes domin ta samu abunda take so, part din Ammy tai parking sannan ta fito tana wani irin taku na kasaita kamar wata yar sarki ta shiga cikin gidan. Ko kallon mutane dake gaisheta ba su isheta ba, balle har ta amsa gaisuwar da suke miko mata, yadda take lumshe ido ta bude ma kadai wani abun kallo ne. A natse ta shiga katon falon na Ammy, babu kowa a ciki sai plasma da Ac dake ta aiki bada sanyi, ta kalli farantin dake cike da sweet an dora shi saman kujera, ko ba a fada ba ta san aikin Nana ne ko Yusra. Kusa da farantin ta zauna ta bude wayarta ta soma dannawa, can kuma ta kai hannu ta dauki sweet din ta bude ta fara sha. After like 30 minutes Ammy ta fito daga dakin sanye Holland Nana na rike da gyalen nata tana kuka kamar wata yar 6 years.
鈥淏aby what happened?鈥�
Hajiya Karama ta tambaya tana kallonta cike da kulawa. Nana kamar mai jira ta saki hannunta ta dawo gurin Hajiya Karama ta zauna tana kukan da ba hawaye.
鈥淎mmy ce Hajiya鈥�
Hajiya Karama ta kalli dake kokarin zama a dinning.
鈥淎mmy me aka mata?鈥�
鈥淚skancinta ne ya motsa鈥�
Ammy ta fada ba tare da ta kalli inda suke ba. Hajiya Karama ta kamata ta dawo da ita saman kujera ta zaunar da ita.
鈥淔ada min me kike so baby?鈥�
鈥淲ai na ce ma Ammy bana son driver dake kai ni school a canja min shine tace wai ba za a canja ba鈥�
Ta karasa tana rushewa da kuka kamar gaske alhalin idon nata ko hawaye babu. Hajiya Karama ta kalli Ammy.
鈥淗aba Ammy dan wannan dai?鈥�
鈥淜i tambaye ta me direban yai mata da za a canja shi? Tsabar iskaci da jindadi? Wata na can kullum a kafa zata je makaranta ta dawo a tsakar rana ke dan kin samu ana kai ki a dauko ki a mota da ac da komai ki dawo mana wani zance na banza yanzu鈥�
Hajiya Karama ta kalli Nana.
鈥淢i driver yayi miki?鈥�
鈥淗ajiya Tsoho ne fa, kan shi har da hurhura ni bana son gani鈥�
Ta karasa da kukan da ba hawaye tana buga kafa kasa, Hajiya Karama ta mike tsaye ta nufi dinning room taja kujera ta zauna tana kallon Ammy.
鈥淗aba Ammy idan ba yi ma Nana abunda take so ba wa za ayi ba? Canja driver ba wani abu ba ne fa, ita yake kai wa kuma ya dauko idan bata ra'ayinsa ba dole鈥�
Ammy ta tsayar da cin abincin da take ta kalli Hajiya Karama.
鈥淣ana da ban isa na saka ta aiki ba, ko kofi na ce ta dauko yanzu zata ce min ta gaji jikin ta ciwo yake bla bla bla iskanci kala kala, tun dazu na ce yarinyar nan ta dauko min abin ci na ci a daki ta ce min kafarta ce ciwo, na ce taje waje ta kira min wani daga masu aikin gidan nan a kawo kin abinci a daki na ci tace kafartana ciwo ba zata iya sauka kasa ba, and now kina tunanin tace na canja mata driver saboda wani selfish interested na ta kuma na yi saboda ita ta haife mu鈥�
Shiru Hajiya Karama tai, ita kanta ta sani idan halin Nana za ayi mata abu to ba za a mata ba, domin ko ita da take mata gata bata isa ta saka ta aiki ba, wani lokacin ko cewa tai ta dauko mata abu sai tace kaza nata ke ciwo bata iya tashi.
鈥淕urin Mai Martaba janye na fada masa, ai Wallahi shi komai na ce ina so yi min yake, yana so na鈥�
Nana ta fada cikin daga murya dan Ammy ta jiyota domin akwai tazara sosai tsakanin falon da dinning room di. Ammy ta juyo daga inda take zaune tana nuna Nana da yatsa da fuskar dake nuna babu wasa a tare da ita.
鈥淜in fi kowa sanin halin da Mai Martaba yake ciki, Wallahi ko da wasa kika kuskura taba kofar dakinsa da sunan kai masa complain sai na baki mugun mamaki Nana kuma ki gwada鈥�
Tashi tai ta fice tana kuka kamar gaske.
鈥淶ainab ki daina biye Nana kuna kara lalata, duk abunda take da gangan take dadi ne yake mata yawa鈥�
Ammy ta fada ba tare da ta kalleta ba, domin har cikin ranta bata jindadin yadda Hajiya Karama, Shattima da Hajiya Babba suke yi ma Nana. Hajiya Karama ta yi murmushi tana mikewa tsaye.
鈥淎i mun kusa bar miki gidanki Ammy, ina yin aure zan dauke Nana mu tare a can鈥�
鈥淎uren da babu rana鈥�
Ammy ta fada tana tabe baki, sai Hajiya Karama tasa dariya.
鈥淣o very soon Ammy, domin na samu wanda na ke so鈥�
Ammy ta kalleta.
鈥淒a gaske?鈥�
鈥淲allahi Ammy, yana da mata daya yara uku ban dai san real name dinsa ba amman dai ya min, ban fada masa ba but very soon zan sanar da shi ina son shi kuma zan aure shi da gaske鈥�
Magana Zainab take kamar abunda take fada ba komai ba ne. Ammy ta kalleta irin kallon nan na mamaki da tunani.
鈥淜e za ki ce kina son shi? Ban gane ba鈥�
鈥淵eah normal ne ai Ammy鈥�
Tana fadar hakan ta nufi hanyar sauka downstairs dake dinning, bata son tsayawa kar Ammy ta fara karanta mata wasu haruffan da ba zata iya hadasu ta tada ba.
Tana saukowa, ta nufi dayan stairs din da zai sadata da bangarenta ita da mahaifiyarta, kamar ta wuce dakinta sai kuma ta nufi dakin mahaifiyar ta ta. Zaune ta same ta hannunta rike da wuri, sai dai ganin Zainab din yasa tai yi saurin boye wurin a bayanta ta kalli yarta ta manya idanuwanta da suka rine su kai ja kamar barkono.
鈥淣a fada miki ki daina shigo min daki babu sallama鈥�
鈥淣a manta ne鈥�
Ta fadi hakan bayan ta zauna kusa da ita, sannan ta bude wayarta ta shiga gallery ta kamo hoton mijin kawarta ta nuna mata.
鈥淚ya kin ga surukinki鈥�
A razane Iya ta kalleta kamin dubanta ya kai gurin hotonta sai da ta kare masa kallo sannan ta dauke kai ta hade rai.
鈥淪hi kika zabo bana?鈥�
鈥淵es kuma wannan karon da gaske aurenshi zan yi, mijin kawata ne, thought dai ban fada masa ina son sa ba amman zan fada masa soon鈥�
鈥淶ainab kenan, kin san miyasa ake kira da Hajiya?鈥�
Iya ta tambaya tana kare mata kallo, kamin Zainab tace komai Iya ta bata amsa.
鈥淪aboda ina son ki zama isashiya, tun da aka haife ki na saka mahaifinki da kansa ya rada miki sunan Zainab uwargidan Mai Martaba, ni da kaina nai miki lakani da Hajiya sai dai ganin akwai wata Hajiyar matar Mai Martaba ta biyu yasa ake kiranki da Hajiya Karama, so a komai ki isa, kuma ki amsa sunanki yadda Mahaifiyar Shattima take matar Sarki kuma uwar Yarima da Gimbiya ke ma ki taka wannan matsayin鈥�
Zainab ta tsotsa mintin dake bakinta tana jin maganar Iya na wuce mata ta bayan kunne.
鈥淚ya ba mu da gadon Sarautar nan fa karki manta, kuma ni bana son wani an mutu an dawo, finally dai na samu miji kuma shi zan aura that's all鈥�
Tana gama fadar hakan ta mike tsaye ta fice daga dakin dan ba gane yaren mahaifiyarta take ba. Iya ta bita da kallo har ta fice sannan tai murmushi ta fiddo wurin dake boye a bayanta.
鈥淏a ki da miji a waje Zainab, mijinki a cikin masarautar nan yake, idan ba mu da gadon sarauta to ya kamata jikokin mu su gaji sarauta.....鈥�
Ta karasa tana daga wani bakin kullin da aka nade da zare kamar laya ta matsashi.
鈥淢ai Martaba ko kuma Labib?鈥�
Ta tambayi kanta tambayar da ita kadai ta san amsarta tana lasar bakinta.
FALMATA POV.
鈥淪allamu Alaikum wai an ce ana sallama da Falmata a waje鈥�
Almajirin ya fada yana tsaye daga bakin kofar gidan.
鈥淔almata aka ce ko dai Naja?鈥�
鈥淔almata鈥�
Ya amsa mata, sai da tai kamar tace aje ace tace ba zata zo ba, sai kuma ta tuna da yan kudin da take shigo mata da su na zance.
鈥淭ashi ki tafi鈥�
Falmata kamar tana jira ana fadar hakam tai saurin mikewa ta saka Hijabinta ta fice, Tumba taja tsaki.
鈥淣i wannan abun mamaki yake ba ni, kamar a kasa nake zubarwa, a maimakon abu ya ragu sai karuwa yake na Naja na raguwa?鈥�
Ta fada slowly tana mamakin lamarin Falmata. Da mugun far'a Falmata ta fito dan ta san mai kiran nata Maniru ne, har zumudin zuwansa take saboda yana kunna mata wakar Sirleem M2 audio da video, wannan ya saka duk a cikin samarinta ta fi kaunarsa.
Sai da ta fara masa sallama ya amsa mata da murmushi suka gaisa sannan ya zauna a dakalin dake kofar gidan suka dasa hira, can kuma ya kunna mata wani sabon video da M2 ya fitar, tsabar zumudi da farinciki sai ta ji kamar ta rumgume shi. Bayan sun gama zance ne ya bada dari uku da lemun yanka a leda, cikin kunya ta karba domim har ga Allah bata son karbar abu a hannun wani sai dai ta sani idan ya koma cikin gidan ba tare da komai baa Tumba za ta iya mata fada ko ma ta doke ta.
Cikin natsuwa ta shigo cikin gidan ta nufi inda Tumba take ta aje mata ledar lemun a gabanta sannan ta mike mata kudin da hannu biyu.
0 comments:
Post a Comment