_A yau ba mafarki nai ba a fili na ji busar, amman ban ga kowa ba_
Bayan ta rubuta wannan ta sake buge wani fegin ta rubuta.
_Kuma yau ma naggen Bappa ta mutu, kuma kadangaren dake bandaki ya biyo ni_
Bayan ta rubuta ta rufe littafin ta aje a inda ta saba ajeshi tare da biron, haka take duk abunda ya faru a wunin ranar sai ta fada, idan tai mafarkin busar sarewar nan ko mutumen nan da yake bayanta ma rubutawa take, ita ala dole ga yar boko.
鈥淔ulani鈥�
鈥淚nna鈥�
鈥淲arre鈥�
Ta mike tsaye ta fito daga dakin zuwa inda mahaifiyarta take zaune tana kiranta.
鈥淕ashi nan an gama dauki ki je鈥�
Sai ta gama kirga gidar ko ta nawa ce sannan ta dauka ta dora saman kai, ta koma can kusa da dakinta ta dauki wani karen zana ta fice daga gidan. Dandali ta nufa tana tafe tana rera wakar da ake a dandalin ta Fulatanci, tun kan ta isa ta hango yadda dandali ya cika da mutane masu sana'a sun baza, masu samari kowa ya ja tashi gefe suna fira, masu rawa da wasar dandali na yi. An kunna wutar kara ta kama sosai ta haske ko'ina na gurin. A gurin da ta saba zama ta zauna ta aje gidar dake kanta a gabanta tana bawa idonta abinci.
Sai kusan sha daya sannan kowa ya watse wadanda sukai ciniki sun yi, masu samari kuma akai sallama kowa ya nufi gidansu. Ita ma kanta a gajiye ta dawo gida tana hamma, ko da ta iso Inna ta gyara mata gurin kwanciyarta sai kawai ta shige dakinta ta kwanta. Misalin karfe biyu suka fara jin tafiyar jakuna a rufin dakin na zana, can kuma ta fara kukan mage, kamin ta koma kiran sunanyen mutanen gidan. A take Fadime ta tashi zaune ta kwala wani uban ihu tana kiran sunan Babanta.
鈥淏appa Bappa Bapppa.......鈥�
Kamar jira ake sai ta fara jin kokan magen a bakin bukkatar tana koyonta da sautin kukan magen.
鈥淏apkwau Bapkwau鈥�
Sai kuma ta ji tafiyar dakuna a tsakar gidan, har da wani tuma suke suna direwa, sai kuma ta ji kamar kukan kare, a lokacin ne tai ihun na gaske wanda ya farkar da Bappa daga bachin da yake domin shi idan sabo ya saba da irin wannan abun, dan haka baya hana shi bachi ita din dai ce da ta kasa sabawa kuma a duk lokacin da ta ji sai ta yi ihu ta kirashi. Da sauri ya budewa zagen da suka sako wanda shi ne murfin bukkar ya fito, sai yai arba da bakar mage tsaye a kofar bukkar Fadime, cikin kuzari ya nufi inda tabaryar gidanta take ya dauk ya jefeta da ita da sauri tai tsalle ta haye saman bukkar tana masa kuka sannan ta sauka da can baya.
鈥淏appa....鈥�
鈥淜one Fulani addu'a akai idan kajji haka haba, kai kullum in zaka kwanta baka addu'a Fulani鈥�
鈥淣i addu'ar wuya take ba ni鈥�
Ta fada bayan ta ga mahaifinta a cikin bukkatar yana lalaben inda take ya riko hannunta suka fito, komawa yai da ita dakinsu ya saka ta a ta su bukkar, ya kunna ashana ya lika a kyandir yai mata shimfida a kasa, shi kuma ya hau saman gadon karan ya kwanta, mahaifiyarta na daga gefe kwance sai kwasar bachinta take.
03/12/2021, 08:22 - 馃馃馃馃: *馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*12*
SIRLEEM POV.
鈥淭un kwanan baya nai maka maganar, ya kamata mu fara hada lefe ba ka ce min komai ba鈥�
Ya daga kansa ya kalli Mahaifiyarsa, kamin ya sake kallon Jarma wanda tun da suka gaisa be sake ce masa komai ba, sai kuma ya sake kallon mahaifiyarsa.
鈥淵arinyar da aka ce sai ta gama makaranta, idan mu ka ce za mu hada lefe yanzu ai mun yi sauri鈥�
鈥淏a dole sai ta gama makaranta za ayi auren ba, ba zan iya jira har lokacin ba, idan muka hada komai mu kai musu su ce ba za su karba ba鈥�
鈥淎mman already an yi wannan alkawarin ai, be kamata mu tayar ba鈥�
鈥淭o ni na tayar sai ya? Malam ka fara bada kudin da za a hada maka lefe kaji鈥�
鈥淭o In-Sha-Allah鈥�
Ya mike tsaye yana gyara rigarsa ya fice daga dakin. Da wani kallo mai kamar harara ta bishi har ya fice, sannan ta kalli Jarma.
鈥淵aron nan idan ba mu yi da gaske ba, zai iya ba mu kunya鈥�
Jarma yayi murmushi.
鈥淜arki ji komai Hajiya, ai yana da biyayya ba zai tsaba miki ba, yanzu matsalarmu guda biyu ce, Mai Martaba da kuma Shattima, kuma na sama mana mafita鈥�
Hajiya ta mike tsaye duk da isar da take ji da kasaitarta ta isa bakin kofar ta saka mata key sannan ta dawo ta zauna.
鈥淲ace mafita ce?鈥�
Jarma yayi murmushi a karo na biyu sannan ya ce.
鈥淎kwai wani gari can yamma da Katsina, garin wasu matsafa manyan arna, ance aikinsu kamar yanka wuka yake鈥�
Hajiya ta dauke kai cike da kasaita.
鈥淣a saba jin irin wannan daga bakinka, sai mun gwada kuma mu ga ribar yar adan ce, ni yanzu masu yi da gaske na ke nema鈥�
鈥淲annan karon masu yin da gaske ne Hajiya, domin su ba a musu aike sai dai mai sako ya isa da kansa, bari ki ji na fada miki a yadda aka ba ni tarihin garin basa bako, sai da sanin manyan gari gudun kar rayuwar bakon ta shiga hadari, wanda ba jinin garin ba baya zama garin. Sannan aikinsu kamar yankam wuka ne, sha yanzu magani yanzu, tun kan ki fadi bukatarki za su sanardar ke dalilin zuwanki da inda mafita take, ke bari na baki wani labari gaba daya jama'ar garin ba su yarda da wani abu wai cigaba ba, na zamani ko mai moriyarsa, in yanzu kika ce a kashe miki Shattima take za su masa harbin kasko su aika shi lahira, mayan yan siyasa da masu kudin garin nan ance can suke yada zango dan biyan bukatunsu鈥�
Cike da gamsuwa Hajiya take kallon Jarma, yadda ya koda mata mutane da ace ba a gaske haka suke ba, zata iya yarda domin ta ji abunda ta dade tana nema.
鈥淎 ina ka san su Jarma鈥�
鈥淲ani abokina Malam sa'idu ne ya fada min su, shi mutumen Bandalo ne wani kauye da ke Katsina, sai dai cirani yake a garin nan sai dai shi din amintaccen na ne鈥�
鈥淢utumen da zai iya rike mana sirrinmu ne?鈥�
鈥淚dan ma zai tona mana asiri, sai dai ya fadi cewar ina nemawa yata maganin aure ne, domin na fada masa yata Nafisa ce take fama da bakaken aljannu da suka hana ta lafiya kuma suka hana ta, sai ya bani shawarar cewar da zan iya da naje can zan samu gani a take鈥�
Murmushi mai kyau Hajiya tai tana kallon tv dakinta kamar da gaske hankalinta yana can.
鈥淛arma sarki wayau鈥�
鈥淗ajiya kenan, wani ai be isa ya san sirrin mu ba, sai dai zuwan ne da kamar wuya a yanzu鈥�
鈥淶uwa ba shi da wahala duk inda samu yake zan iya kai kaina, ba ni da kowa a katsina amman zan iya karyar zuwa wani gurin sai mu je can, matukar zan samu biyan bukatata Jarma, bana tsoron ratsa ko'ina zuciyata a bushe take鈥�
鈥淶an neman takamaimen inda garin yake, da inda ya kamata mu sauka da kuma wanda zai magana jagora a cikin garin鈥�
鈥淜a nemo Jarma amman ka tabbatar idan muka tafi ba zuwan banza za mu yi ba, za mu samo maganin ciwon mu鈥�
鈥淚n-Sha-Allah鈥�
Daga haka yai mata sallama ya fice daga dakin, ita kuma ta mike tsaye ta isa gaban windows dakinta tana kallon bayan gidan, ji take kamar ta runtse ido ta ganta a garin.
FADIME POV.
A yau ma sai da ta rubuta domin ta yi mafarkinsu, sai dai a yau mutum biyu tai mafarki da nai busar sarewar nan da kuma dayan da yake tsaye a gefensa dukansu sun bata baya ne.
Daga bukkatarta ta fito ta nufo inda Inna da Amo suke zaune suna maganar sarautar garin.
鈥淣i ina ganin kamar abun nan zai zama rigima ne, tun da duka yayan suna son sarautar fa鈥�
Amo ta lashi baki da wata uwar tsaga da ta bata mata fuska tace.
鈥淢u dai na mu ido, ban da rashin hadin kai, yayan uku ba za su hakura su bar wa daya ba? Wannan ai ba burgewa ba ce鈥�
鈥淣i ma dai haka na ce鈥�
Fadime na zuwa ta zauna kusa da mahaifiyarta ta kwanta jikinta.
鈥淭o mage sarkin son jiki daga ni鈥�
Da sauri Fadime ta dago ta kalli Inna wacce tai mata maganar.
鈥淚nna jiya ma sai da mage ta zo鈥�
Hanzarin tashi tsaye Amo tai ta dauki kwayar danyen manshanunta ta dora saman kai.
鈥淭o muka zamu bunni sai wada hali yai鈥�
Bata ko tsaya jiran abunda Inna zata ce mata ba ta saka kai ta fice daga gidan da saurinta, har kusan karo su kai da wata makociyarsu wacce ta kunno kai cikin gidan rike da takarda hannunta.
鈥淢araba da Nene鈥�
鈥淣a yalle dam Inna Fadime鈥�
鈥淛anfelen鈥�
鈥淣a sukka蓳e?鈥�
鈥淛anfelen, na wurinde?鈥�
鈥淛anfelen鈥�
Ta zauna inda Amo ta tashi tana mikawa Fadime takardar hannunta.
鈥淔adime karanta mini injiya minana Mai samari yak aiko min鈥�
Fadime ta karbi takardar ta bude tana karanatawa, gaisuwa ce farko sai tambayar lafiyar mahaifiyarsa sannan ya sanar da ita sakon kudin da ya aiko mata dubu bakwai ta hanyar abokinsa, dan rani.
鈥淢unafwuki amman be ba ni komai ba, sai wasika, yalla ya aza babu me karanta min ita, bari naje yanzu na iske shi, mugun ba'adare鈥�
Inna ta saka dariya ita da Fadime dan sun san halin Nene da kudi bata jin has. Nene ta fita daga gidan sai fada take ko sallama bata tsaya yi ma Inna ba.
鈥淔adime tashi ki tahi rahe ki samo mana diyam鈥�
A take ta bata fuska ta fara shura kafafuwanta.
鈥淚nna ko hutawa ban yi ba, yanzu na farka daga bachi ai鈥�
鈥淲allahi ina sa miki sanda yanzu, wa zai dauko ruwan ni?鈥�
Ta tashi tana zabure zabure ta dauki tulun ruwa ta fice daga gidan, tana sanye da kayan fulani riga da zane cigiyarta a sake kanta kuma babu dankwali sai dan xaren kwaliya da suke daurawa akai ta raba gashinta gida biyu ko wane tsoro ya sauko bayanta.
A maimakon ta taje zafin da ta saba diban ruwa sai ta nufi babban gulbi garin da ba kowa yake zuwa can ba, saboda nisansa da kuma girman da gurbi yake da shi domin gulbi ne da ya hada mayan jihohin yanki.
Baki baki ya tsaya ta saka tulunta cikin ruwan ya cika ta cire ta aje, tana waige waige ko zata samu wanda zai dorata kasancewar safiya masu kamun kifi sun gama sun tafi sauran mutane kuma ba su fara hada hada a gurin ba.
鈥淜ai kado, ware鈥�
Ta kwalawa wani bahaushen mutum da ta hango can nesa da ita. Amman ko kula ta be yi ba. Zaune tai a gurin tana ta wasa da ruwa da kafafuwanta, kamar ance saurara ki ji sai ta fara jiyo busar sarewar nan can nesa da manyan duwatsun da suke gefen gulbi, da sauri ta mike tsaye, ta fara waige waige sai kuma ta fara gudu tana nufar inda duwatsun suke, gudu take sosai kafafuwanta babu talkami domin a can ta baro su gurin da ta cika tulun, manyan duwatsu ne wanda hanyewa samannsu ma wani sabon aiki ne amman a haka ta rika dafa tana rarrafe kamar dole har ta haye sama, mikewa tai tsaye tana kallon mutumen da take hange a saman wani dutsen da ke can nesa da ita yana busar, jikinaa babu riga sai walki sanye a kugunsa, ba zata iya tantance fuskarsa ba domin baya ya bata kamar yadda ta saba mafarkinsa, wani irin gwalo ido tai waje ta hangame baki tana kallonsa, ya mata nisa sosai bare ta jira shi ya jita ko kuma ta jarasa kusa da shi, sai dai busar da yake ya karade ko'ina saboda yau a saman dutsen yai ta sabanin a da fa yake yinta a kasa ko a saman ice.
Sai da ya gama busar sannan ya juyo ya fuskanci inda ya bawa baya, sai ya hango wata yarinyar da be tana gani ba ba kuma zai iya tantancewa ba tana kallon inda yake. Gangarawa yai ya sauka daga saman dutsen yana kallonsa tun tana hangoshi har ta daina ganinsa, a lokacin ne ita ma ta sauko da wani irin gudu kamar sabuwar mahaukaciya, tana isa gurin tulunta ta zubar da rabin ruwan ta dauki tulun ta dora a kai ta saka talkaminta ta nufi gida da sassafar zuciyarta na bugawa da karfi kamar zata fito daga kirjinta, numfashin ma daker take yinsa. Ta kasa yarda cewar abunda take gani a mafarki shi ta gani a zahiri, mutum ne ko aljanani? Miyasa yake zo mata a mafarkinta? Kuma a irin busar da ta ji yana yi a yau? Why ba shi da tufafi a jikinsa? Why yake busar a kusa da inda zata iya jinsa? Wanene shi? Duk tana bukatar wadannan amsoshin a yanzu. A bakin bukkar Inna ta aje tulun ta shige bukkarta, ta dauko littafinta ta fara rubutawa abun ya zame mata kamar wajibi.
AA POV.
Ba karamin dadi ya ji ba kudin da Nana ta saka masa a account, sai dai ko kadan hakan be bashi natsuwar ya cigaba da zama a unguwar ba, domin a ganinsa kamar ana dana masa tarko ne, line ma cire shi yai ya aje ya daina kira da shi ya dauko wani tsohon line sa ya saka a wayar.
Baya tafiyar da zai yi nisa da gidansu, ba dan komai ab sai dan ganin yake kamar idan ya bar unguwar za a iya kama shi, ita kanta Anti Rabi ta lura da rashin natsuwarsa har take ganin kamar ma ya fita tsoro.
鈥淚dan kana jin zaman ka a nan ba zai yi ba, ka koma cikin gari gurin Kawo ka zauna na kwana biyu tukuna, duk da dai na ga kamar ba za a maka komai ba鈥�
Ya sauke ajiyar zuciya ya kalleta.
鈥淎nti bayan faduwar da mu kai yarinyar ta sake ba ni kudi fa鈥�
Anti ta zaro ido.
鈥淵aushe ka hadu da ita har ta baka kudi鈥�
A dolen dolensa ya labarta mata yadda komai ya gudana da kuma irin tsoron da yake ji da kuma zargin an dana masa tarko da yake.
鈥淎i Allah ya kara maka, AA wani irin mayen kudi ne kai? Sai ka jawa kanka fitina ko? So kake azo a kulle mu gaba daya kuma kasan ba mu da gata sai Allah, idan ma ba tarko ne ta dana maka ba, wata kila yarinyar sato kudin take ko kuma tana samo su ta hanyar da be dace ba, duk ranar da dubunta ya cika kai zata nuna鈥�
A take AA ya ji kamar ya saki fitsari domin shi be kawowa kansa tunanin tana samun kudin ta hanyar da be kamata ba ne, sai yanzu da Anti ta fada.
鈥淎nty yanzu ya za ayi?鈥�
鈥淚na na sanar maka? Ai kara ka koma can unguwar Waziri gurin Kawo Bala, idan ma wani abun za maka kara ace kana kusa da wani babba namiji鈥�
Shiri yai ba dan yana so zai bi shawarar tata ba sai dan be da yadda zai yi, idan har sata take tabbas zata jefashi a cikin matsala kara ma ya koma unguwar da bata sani ba ko da ta zo gidan ta tararda baya nan. A take ya shiga cikin dakinsa ya hada kala biyar ya saka a jakarsa ya fito.
鈥淎A ka rika hakuri da rayuwa, rashi ba hauka ba ne, kai maraya ne kana ta neman jefa kanka a cikin matsala, kai kawarda idonka daga neman kudin nan dan Allah, idan kai hakuri sai ka same su cikin sauki, amman wannan bude idon da kake sai ka ga ka samu kudin ta hanyar da be dace ba, idan kai hakuri zaka samu duk abunda Allah ya rubuta maka cikin sauki鈥�
Anti ta fada cike da damuwa, ta san kanenta ba irin yan iskan samarin nan ba ne, ba zai aikata wani abu dan neman kudin ba, amman tana tsoron shedan da zuciya, domin son kudin AA ba na wasa ba ne ita kanta ta sani.
鈥淪hi ma wannan yana cikin rabo na ne Anti, yarinyar Allah ya kawo ta ne dan na yagi rabona鈥�
鈥淜o kuma ka yagi rabon wahala ba, gashi nan ai ka fara boye boye ka kasa komawa aikinka, ka kasa natsuwa鈥�
鈥淜e dai ke yi ta min addu'a kawai, Allah ya sa kar ta tona mana asiri, amman fa ko gobe ta bani sai na amsa鈥�
鈥淚dan an kama ka kar ma ka fadi sunana Wallahi鈥�
Ta fada a fusace sannan ta shige dakinta, shi kuma yai murmushi ya fice daga gidan.
HAJIYA KARAMA POV.
鈥淎bun da kike yi be dace ba Zainab, taya Shattima zai yi magana ki musa masa, a iya tunani Shattima ko cewa yai ki dauki wuka ki yanka ni za ki iya鈥�
Da mugun mamaki Zainab ta kalli Iya.
鈥淚ya kin san abunda kike fada kuwa?鈥�
鈥淣a sani, biyaya ya kama ace kina musu ta kowane hali kamin ki gina kanki鈥�
鈥淏a ki wulakanci da akai miki ba ne鈥�
鈥淲annan duk mai wucewa ne, ki koyo juriya da hakuri Zainab ki koyi kaskantarda kai sannan za ki samu nasara a komai, shakarata talatin a gidan nan na san ko waye Shattima kuma na san waye Ammy鈥�
鈥淏a fa siyasa na ke ba, balle ace na nemi soyayyar wasu, abun da akai miki be kamata ba sam鈥�
鈥淚dan har kin ji zafin abun da aka min ya kamata ki fara kishin mahaifiyarki ki taya ta yakin da take, har mu ci nasara, kuma ki fara tunanin gina kanki, ban yarda ki yi ma Shattima rashin kunya ba domin shi din wata rana shugabanki ne鈥�
鈥淣a fara tunanin gina kai na Iya, tabbas zan yi aure na bar gidan nan鈥�
Ta karasa tana kara zare manyan idanuwanta, Iya ta girgiza kai domin ba haka take son ji ba. Zainab ta mike tsaye ta isa gaban madubi inda wayarta take aje tana ringing ta dauka ta kai kunne.
鈥淗ello Ra'ees鈥�
鈥淣a'am Hajiya ya kike?鈥�
鈥淟afiya Kalau ya ake ciki?鈥�
鈥淜omai kalau, MBS ne suka shigar da gasa, suna son hoto da zai dace da kamfaninsu a week din nan鈥�
鈥淢iye hadina da kamfanin MBS?鈥�
鈥淪un bada damar photographers su turo hoton da suke ganin ya dace ya hau, idan kai nasara kai za su bawa ambassador na kamfanin na shekararar na kuam kin san ba kana nan kudi za a samu ba鈥�
鈥淶an yi tunani a kai鈥�
鈥淣a turo miki komai ta whatsapp idan kin hau za ki gani鈥�
鈥淥kay鈥�
Cike da gadara ta aje wayar ta ja stool din madubin ta zauna tana kallon kanta. Iya ce ta zo bayanta ta tsaya tana kallon irin kyau da yarta take da shi.
鈥淎 yadda kike da kyau nan, kamata yai ace Sarki ne ya auri ki, ba mijin kawa ba鈥�
鈥淢ijin kawar nake so Iya, ba zan iya auren tsoho ba鈥�
鈥淣i ma ban ce ki auri tsoho ba, amman kina iya auren mutumen da za ku tsufa kuna cin moriyarku鈥�
鈥淪hiyasa na ke son na auri Auwal ai....鈥�
鈥淜ashiiiii kin kasa ganewa鈥�
鈥淏abu fa abun da zan gane Iya, ni shi nake so kuma aurensa zan yi鈥�
鈥淎llah ya taimaka ya kai mu lokacin鈥�
Iya ta fada fuskarta ba yabo ba fallasa, sai Zainab ta juyo ta kalleta tana murmushin jindadi.
鈥淵auwa yanzu na ji magana, Amin thank you鈥�
Dan murmushi kadan Iya tai mata sannan ta ce.
鈥淎n jima ki samu Shattima ki ba shi hakuri鈥�
鈥淶an yi hakan In-Sha-Allah鈥�
Iya ta gyada mata kai sannan ta juya ta fice daga dakin.
NANA POV.
Tun da ta dawo school tana cikin dakinta bata fito ba sai la'asar, duk mutanen da ke zuwa gaisuwa sai dai su lekota ko kuma su tambayi lafiyarta Ammy tace musu tana ciki.
Tana fitowa daga dakinta ta nufi dakin Ammy, kai tsaye ta tura dakin ta shiga babu ko sallama, Shattima na zauna saman kujera Zainab na gefensa ita ma zaune, shigowarta yasa ya dago ya kalleta Zainab ta miko mata hannu.
鈥淗ey Baby zo nan...鈥�
Nana ta karasa kusa da ita ta tsaya, dan ba zaman take son yi ba, Ammy dake bandaki take jiran ta fito.
鈥淲aya taba ki?鈥�
鈥淣i bana son School bus tana kai ni makaranta鈥�
Ta fada a shagwabe, tana dan satar kallon Shattima da yaki ya sake kallonta. Kamin Zainab tace komai Ammy ta fito daba bathroom din fuskarta jike da ruwa. Kallo daya tai ma Nana ta dauke kai ta karasa bakin gadonta ta zauna, sai Nana ta matsa kusa da gadon tana turo baki domin kwata kwata yau bata jidadin yadda aka kaita makarantar ba aka dawo da ita.
鈥淎mmy ni bana son school bus tana kai ni makaranta鈥�
Kallonta kawai Ammy take.
鈥淣ana wai me yake damunki, tunanin ki dabam, ki duba yarinyar da take zuwa gyara dakin yaran can ba ta wuce warinki ba, amman aiki take zuwa nan, kina tunanin ita bata son gata nan? Ko bata son karatu? Me kika nema kika rasa ne? Tun da kika dawo school kika shige daki kika zauna duk masu shigowa sai tambayarki ake amman kin zauna a can kamar ba ki san rashi mu kai ba? Abinci ma ba ki fito kin ci ba, what is wrong with you?鈥�
Ta yi shiru bata ce komai ba, domin bata da abun cewa ita dai karatun ne bata so.
鈥淒river na ke son a daukar min鈥�
鈥淭o ba za a dauka ba, kuma dole ki je makaranta, Islamiya ma yaushe rabonki da zuwa?鈥�
Ammy ta amsa mata kai tsaye. Sai ta kara bata fuska.
鈥淲allahi ba zan karatun ba, indai ba a daukar min driver ba ba zan sake zuwa makaranta ba鈥�
鈥淚dan kin yi karatun ni zan karu ko ke? Shashasha, ba ki son a fada miki gaskiya, kin fi son a barki ki yi ta hauka, kuma Wallahi kika ki zuwa makaranta sai na sa sarkin bulala ya zane miki jiki鈥�
鈥淎i daman ba so na kike ba, shiyasa kika saka Baba Waziri ya kwashe komai na dakina....鈥�
鈥淓h bana son ki, je ki nemi wata uwar da take son ki, idan ba ki bata min rai ba hankalinki ba zai kwanta ba, idan so kike na miki ba ki wata rana zan miki, duk ranar da bana raye sai ki nemi mai fada miki gaskiya ki rasa, sakaryar kawai nai kukan ciwon Mahaifinki na yi na ki...鈥�
Ammy ta karasa cikin fada hawaye na sauko mata, da sauri ta tashi ta koma bandakin. Nana na juyowa Shattima ya wanke mata fuska da mari.
鈥淪tupid girl, wuce ki je ki hada kayanki yanzu nan driver zai kai ki gidan Baba Waziri鈥�
Fashewa tai da kuka ta fice dakin da gudu. Zainab ta mike tsaye tana kallon yadda ran Shattima ya bace.
鈥淪hattima ka rika daga mata kafa yarinya ce鈥�
鈥淭a fara wuce gona da iri, abun ta gaba yake ba baya, i hate nonsense鈥�
Ya amsa a fusace sannan shi ma ya fice daga dakin. Ko kadan Zainab bata jidadin abunda ya faru ba, amman ita tana kallon Nana da kurciya ne da kuma shagwaba, a gurin ta aje wayarta ta fice zuwa dakin Nana.
03/12/2021, 08:22 - 馃馃馃馃: *馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*13*
Tun ranar da Fadime ta ji ga mutumen nan mai busa bata sake ganinsa ba, hakan kuma be saka ta fasa zuwa gurin manyan duwatsun ba a kullum tana leka ko zata ganshi.
Kuma tun ranar bata sake jin busar ba, bata sake mafarkinsa ba, a lokacin ne ta fara rayawa a ranta cewar aljani ta gani kuma shi take mafarki.
Kasancewar yau friday da safe ta fito da shanun kiwo, daman duk Friday da safe take kiwon kasancewar jumma'a kurarren lokaci ne. Shanunta na gaba tana biye da su, kanta sanye da malfar sa茩a, ta daura zare a wuyanta da gaban goshinta, dan karamin kare na binta hannunta rike da sandar korar shanu bata fasa wakewaken da Inna take hanata ba.
Sai da suka isa bankin rafi sai ta nufi inda ta saba zama, ta zauna tana hango wasu shannun da wani bafullatani dake can nesa da ita yake kiwo.
Kanne ido daya tai ta fara kirga masa shanu daga inda take zaune, sannan ta dawo kirga nata.
鈥淣awa sauran 37, idan wata ta sake mutuwa yau sauran 36 idan wata ta kara mutuwa sauran 35...鈥�
Bata karasa kirgen ba ta soma jiyo busar sarewar tana karade dajin. Bude baki tai ta zaro ido ta fara dukuduku ta ratsa cikin marar sannan ta mike tsaye tana leken inda ta fi jin busar na fitowa, sai kuma tai dukuduku ta dawo ta haye saman dutsen ta mike tsaye. Hangoshi da tai a saman wani dutsen zaune yasa ta kara gwale idon.
鈥淜ai...........鈥�
Sai ta ji muryarta ta amsa duka dajin da kiran da tai masa.
鈥淟aaaaaaa鈥�
Ta yi dariya, wani dadi taji yadda ta ji muryarta ya gwauraye dajin, a yanzu ta gano dajin ne ke da daukar sauti. Saukowa tai saman dutsen da sauri ta fara gudu tana daga kanta sama tana hango dutsen da yake zaune, kamar wacce aka koro haka take yankan dajin tana gudu har ta isa gaban katon dutsen a lokacin ne ta ji sautin busar sarewar sosai a kunnenta, labewa tai jikin dutsen tana dariya marar sauti tana kara zaro ido.
Gaba daya ta manta da wani zancen aljani ne ko mutum, sai ta dan lekesa ta sake boyewa tana dariya har da su kyakyatawa kadan ta rufe bakinta.聽
聽 聽 聽 Zaune tai a gurin tana ta sauraren fusar sarewar dake shiga kunneta, har da wani lumshe ido take tana budewa. Lokaci daya ta daina jin busar saurara tai na dan lokaci ta ji ko za a cigaba, shirun da ta ji ne yasa ta tashi ta leka sai ta ga babu shi a gurin, hakan yasa ta fito gaba daya tana kallon dutsen.
鈥淚na yaje?鈥�
Ta tambayi kanta tana tare hasken ranar dake haskata da hannunta, domin malfar dake kanta ta fado bayanta igiyar malfar ce kawai a wuyanta, kara natsawa tai tana rabon ido, sai ta hangoshi yana saukowa saman dutsen. Saurin komawa tai ta boye tana yarfar da hannunta tana dariya da jindadin ganinsa da tai. Amman da yake saukowa ina zai je? Gurinta ko wani guri? Ta dan zaro ido kamin ta kara shan jinin jikinta jikin dutsen tana saurare ko zata ji takun tafiyarsa ko motsin wani abu, amman sai ta ji shiru hakan yasa ta fara takawa kadan kadan ta leka sai ta ganshi tsaye yana kallon inda take kamar daman can jiran yake ta leko ya ganta, da sauri ta koma sai a lokacin ne tsoro ya fara kamata.
鈥淲ayyo Bapppa.....鈥�
Ihun da tai ne yasa ya karaso kusa da ita yana kallonta, hannunsa rike da sarewa, sai dan walkin dake daure a kugunsa, fari ne sol kuma kyakkyawa gashin kansa ya kwanta luf kamar bafulatani idonsa ma fari kal kamar madara ga dogon hancin daya kara kawata fuskarsa. Dukewa Fadime tai kasa ta rufe ido tana kuka.
鈥淏apppa.....鈥�
Bappan kawai take kira kamar ance mata zai ji ta daga inda take, tasa hannayenta ta rufe fuskarta sai rusar kuka take kukan da ba hawaye. Shi dai kallonta kawai yake cike da burgewa ba yau ya fara ganinta ba, kusan a duk lokacin da ya bar gulbin dake kusa da garinsu ya iso wannan dan yi wwanka ko yin wani abu sai ya ganta ta zo kiwo ko deban ruwa, sai dai ita bata taba kula da shi ba sai a yanzu da yake busar kusa da inda take ji.
Jin be mata komai ba yasa ta dago ta kalleshi kadan ta runtse ido, gabanta sai dukan tara tara yake.
鈥淏apppa鈥�
Ta kira sunan Babanta da kuka, sai kuma ta sake bude ido ta kalleshi yanzu kuma so take ta tantace mutum ne ko aljani.
鈥淏an maka komai ba, ni ban maka komai ba, ni mutum ce ni ka yi hakuri ba zan sake ba鈥�
Bayan kallonta babu abun da yake, matsawa tai baya tana yi tana kallon gefensa inda hanya take sai kuma ta kallesa, cikin wayo ta zo da mugun gudu ta taba shi da yatsanta ta daka wani uban tsalle tana son ta ranta a na kare, sai yai hanzare cafko hannun nata ya rike gam. Wani irin shidewa tai ta dawo ta bude ido sosai tana kallon hannunsa da ya rike ta da shi tana bude baki kamar zata kwala ihu kuma ba tai ihun ba, sai ta sulele kasa tana wani jan numfashi, so take ta suma kuma suman be zo mata ba. Dayan hannunsa yasa ya rikota ya jinginar da ita jikin dutsen tana kallonta.
鈥淏apppa...鈥�
Ta sake kwala masa kira. Uffan be ce mata ba sai kallonta yake duk ganinta da yake bata taba burge shi ba irin yau, he never thought haka take da wauta sai yau and he like it.
鈥淏apppaa Na...... 鈥�
鈥淲uta na binki ba ki gani ba....?鈥�
Ya fada cikin siriyar muryarsa mai dadin sauraro yana daga mata kai alamar ta duba. Cikin wani irin tsoro marar misaltuwa Fadime ta waiga kasanta.
鈥淏a wuta dutse ne鈥�
Ta fada numfashinta na rawa domin a yanzu kam da gaske tsoro take ji. Matsowa da ita yai kusa da shi kamar zai rumgume ta dan filin dake tsakanin bayanta da dutsen yai wani abu da hannunsa kamar zai kama abu ya cafke hannunsa ya jimke sai ga wutar tana ci a cikin hannunsa.
Kadan Fadime ta juya ta ga wutar sai ta kara bude ido ta kwala ihu. Shi kam kallonta kawai yake har tai ta gama sannan ya juya ya fara tafiya.
鈥淜ai a aljanine?鈥�
Ya girgiza mata kai alamar a'a.
鈥淜ai ka saka min wutar?鈥�
Nan ma kan ya girgiza.
鈥淵a akai ka ga wutar waya saka min wutar?鈥�
Daga inda take tsaye take aiko masa tambayoyin cikin daga murya ta yadda zai ji ta, sai a lokacin ya juyo ya kalleta sai tai saurin rufe fuskarta da hannayenta.
鈥淲utar maita ce, mayu suke sakawa mutun ita, idan mutum yana da baiwa sai su kwashe ta su saka masa wuta, komai ya rika ko ya taba ba zai yi albarka ba, ba zai amfane shi ba, idan suka kasa cin kurwarsa sai su daddanketa mutum ya koma wawa ko mahaukaci ko musaki, akwai wanda ke bibiyarki鈥�
Yana fada mata haka ya juya ya cigaba da tafiyarsa yana murmushi, fitowa tai tana kallonsa har ya haye saman dutsen yai tsaye yana kallonta, daga inda take tsaye ta daga masa hannu shi ma ya dago mata sannan ya gangara ya sauka ta arewa da dutsen.
A lokacin ne ta samu kafafuwan gudu ta dawo gurin kiwon shanunta ta zauna tana ta tunanin abunda ya fada mata. Har ta gama kiwonta nagge ko daya bata mutu ba, cikin jindadi ta kora shannun suka nufi gida, kamin su isa gida duk ta matsu, suna isa bata ko tsaya saka hannun ciki gida ba, ta shige Bukkarta ta dauko littafinta ta fara rubuta abun da ya faru, sai da ta rubuce komai tsaf sannan ta fito waje tana neman Inna ta labarta mata.
FALMATA POV.
Tana cikin wanke wanke ta ji Tumba a bayanta tsaye, juyawa tai da sauri ta kalleta, sai Tumba ta risino daidai kunnenta tana fadin
鈥淲ai ke Falmata ba ki da irin samarin nan masu yi ma budurwa anko? Kullum suka zo ba su da abun yi sai kawo miki abu a leda ko su baki yan kudi a hannu, haba Falmata ki rika sakin jiki mana鈥�
Cike da damuwa Falmata ta sanda kanta kasa, ta fahimci inda Tumba da dosa a yanzu.
鈥淜e baki ga sauran yan mata yadda suke ba? Ki rika sake musu jiki da fuska kinji kina far'a samari suna son mace mai far'a鈥�
鈥淭o鈥�
鈥淵auwa yau duk wanda ya zo ki ce ya baki dubu uku ko biyar, in dai kina kawo min kudi haka zan rika miki komai鈥�
鈥淭o鈥�
Ta sake amsawa a ranta tana mamakin yadda Tumba take son ta zama, ta rasa me ta tare mata a dubiyar da bata son farincikinta, yau kwana uku kullum sai dare ya raba take satar kafa ta fita taje shago ta ci bashin garin kwaki ta saka a cikinta, sakamakon abincin da ba a bata a gidan.
Yanzu kuma tana nuna mata wani mugun hali wanda ba halinta ba. Tana wanke wanke tana hawaye, sai ta share ba tare da ta bari Tumba ta gani ba, haka tai aikin cikin rashin kuzari sannan ta fara shara, ta bi ko'ina na gidan ta masa tas, ta dawo ta zuba ruwa a bokiti ta shiga bandaki, ta nan ta samu damar kuka iya son ranta tana tuna irin gargadin da Mama ta yi mata kamin rasuwarta.
鈥淲annan farin jinin na ki kar ya kai ki ga halaka Fulani, tun kina yar jaririya Allah ya saka miki farin jinin jama'a yanzu kuma kin tasa samari sun fara miki sallama, bana son zuwa firar nan karki sake fita duk wanda ke son ki da gaske ya aiko gurin mahaifinki, kuma kin ga kin fara al'ada ko hannunki kika bari namiji ya rike za ki iya samun ciki, dan zai ja a wuce guri, karki kuskura bari a rike hannunki鈥�
Fashewa tai da kuka ta rufe bakinta dan kar kukan ya fito, farar fita zance da samari da take, bayan mutuwar mahafiyarta ne, wanda Tumba take bata umarni, tun tana jin kunya tana boya tana rasa abun fada har ta waye, ta iya magana da tarbar wanda ya zo gurinta. Yanzu kuma tana nuna mata hanyar da ba mai bullewa ba ce, taya za ta ce a bata kudi mai yawa haka?
Cikin rashin kuzari ta gama wankan ta fito ta shiga dakinsu ta shirya cikin wani farin yadi ta saka hijabinta ta fito tsakar gida.
鈥淣a tafi鈥�
鈥淭o Allah ya tsare yar albarka鈥�
Tumba ta fada cikin daga muryar tana washe mata hakora, Falmata ta dauke kai ta fara tafiya kamar bata son zuwan ta fice daga gidan zuwa gurin aikinta.
鈥淣a rasa yadda zan yi da yarinyar nan, komai nai mata kamar ban yi ba, kowa nai ma ya kama ban da ita, ban san me shegiyar uwar nan ta bata ba, kudi kawai na ke kashi a banza鈥�
Tumba ta fada tana rafka uban tagumi, tana tuna abunda Malam na zaure ya fada mata game da Falmata.
鈥淚dan ba ki yi da gaske ba, yarinyar sai ta gawurta, ina ji miki tsoron abun da zata zama nan gaba鈥�
Wani dogon ajiyar zuciya ta ja ta sauke.
鈥淣a rasa yadda zan yi da yarinyar nan idan nai wannan a banza, wacan a banza鈥�
Ta furta cike da jin zafin irin kudin da ta kashe akan Falmata amman har yanzu shiru, farinjinin da take son ya gushe ba daina ba, abu ma kamar 茩aruwa yake.
Falmata na tafe tana tunanin maganganun Tumba, wace karya zata mata ta tsira? Idan ma bata kawo mata kudin ba zata iya dukanta ko ta mata wani sharin. Bata hankara ta ji an taka burki da karfi wani abu ya bugeta ta fada can gafe, da sauri ta rike kafarta da bata warke daga daurin da Baba tai mata ba, yau kuma ta sake jin ciwo a kafar, da sauri Sirleem ya fito daga motar ya karaso inda take.
鈥淏a ki ji ciwo ba? Ina ta horn ba ki lura ba鈥�
Baki sake take kallonsa idonta kamar za su fito gaba daya ta manta da wani ciwo a kafa, ta masa yardar Sirleem take gani da gaske shi? Ko mai kama da shi.
鈥淪annu ba ki ji ciwo ba?鈥�
Yana tambayarta ta kuma ta kasa amsawa sai kallonshi take tana ganin abun kamar a mafarki, daman kuma ba jinsa take ba tun sai an yi da karfi take iya ji.
鈥淗ey鈥�
Ya kada mata hannunsa a fuska sai a lokacin ne ta dawo hayyacinta, a lokacin ne mutane suka fara taruwa kallonsa da kuma ganin abun da ya faru. Rawa jikinta ya fara yi idonta ya cika da kwalla bata san lokacin da ta riko hannunsa da sauri ba.
鈥淒an Allah kai ne Sirleem M2 ko kama ce kawai鈥�
Kallonta yake for few seconds sannan ya ce.
鈥淣i ne鈥�
Tana kallon yadda bakinsa ke motsi da yadda ya nuna kansa ta san magana yai, amman bata ji komai ba saboda be yi da karfi ba, gashi kuma tana son jin muryarsa.
鈥淏ana ji sosai sai ka fada da karfi, dan Allah kai da karfi na ji muryarka kanji鈥�
Ta sakin hannunsa tai ta rike kafafunsa ta fashe da kuka.
鈥淣i ne鈥�
Ya amsa mata da karfi yadda zata ji, ta ji muryarsa sai dai akwai banbanci a tsakanin muryarsa ta cikin waka da kuma ta zahiri, amman tabbas kamaninsa da wacan Sirleem din ba su da banbanci tun daga kan sajen har farin da tsaye da iya wanka.
鈥淲allahi ina matukar son ka, ni masoyiyarka ce sosai, ina kaunar wakokinka, ban tunanin Allah zai hada ni da kai cikin sauki haka ba, na gode na gode da ka kade na yafe maka na yafe maka Wallahi ina kaunar sosai鈥�
Jikinta har rawa yake sanadin kallonsa da take, hawaye kuma suna ta aikinsu a fuskarta, har yanzu ta kasa yarda ba mafarki take ba.
鈥淜o dai mafarki na ke yi鈥�
Ta tambayi kanta tana taba fuskarta, sai yai murmushi ya cire facing cap din dake kansa ya saka mata akai saman Hijabinta, yana girgiza mata kai alamar a'a ba mafarkin take ba fuskarsa da murmushi. Hannunta ta kai ta cire hular daya saka mata ta rumgune hular tana kuka, a nan wasu suka fara tsaki suna fadin wai abun ta yayi yawa sai kace wacce ta ga wani sahabi ko Annabi, ita kam ta san me take ji a kan Sirleem kuma ganinsa da tai a yau yasa ta kasa yadda ma a duniya take. Hannu yasa aljihunsa ya ciro wallet dinsa ya ciro kudin da za su kai 5k ya mika mata, sai tai saurin girgiza kai.
鈥淎 a ni bana son kudi, na gode da ka kide ni, na gode na yafe maka鈥�
Kai kawai ya kada mata daman kuma be jin zai iya kara ce mata wani abu tun da sai an yi magana da karfi zata ji, sai ya sara mata ya nufi motarsa ya bude ya shiga masu aikin daukarsa a hoto suna ta yi, da kallo ta bishi har ya tashi motar ya hau titi. Sannan ta mike tsaye ta saka hullar cikin hijabinta tana jin wani irin farinciki a ranta marar misaltuwa. Gaba daya ta manta da wani tunani da bacin rai, sai laleben hular dake kamshin turarensa take tana jan numfashi tana saukewa, yadda zata labartawa yan islamiyarsu da kawarta labarin yadda ta ga Sirleem yau kawai take tunani, har ta isa masarautar murmushi be gushe daga fuskarta ba, ji take kamar yanzu komai ya faru. Zancen wani haduwa da Iya da fargaban da take samunta idan zata shigo gidan duk ta manta sai murmushi kawai take tana jindadi a ranta. Door bell ta danna sannan ta samu guri ta zauna a gurin tana jiran a bude mata kofar, after like ten minutes aka bude kofar.
Mikewa tai tsaye sai tai arba da Iya hakan kuma ba karamin fadar mata da gaba yai ba, a take murmushin fuskarta ya gushe, Iya sai kallonta take irin kallon nan da ke nuna mata komai na jikinta har yadda jini yake gudana a jijiyarta, Falmata ta yi kasa da kanta ta saka cewa Iya ina kwana balle tace ta bata hanya ta wuce. Ba kallon bakinciki abun da ya faru kawai take mata ba har da na kurwarka dake ta yawa a saman kanta kamar fara, irin ta ce mai wuyar kamu, kurwar da ke yin kasa mai kamar hawainiya ita tafi saukin kamu sai kuma wacce take yawo a kasan kafafuwan mutum, wanda wani lokacin kasan kafafuwan mayu suke kallo su kama kurwar mutum. Akwai wance take kamar tantabara ita ma tana da wuyar kamu sai dai bata kai mai kamar fara ba wacce ke fira.
A take jikin Falmata ya fara wani tsamtsamtsam wanda hakan ke bata cewar ba mutumen arziki bace, a take ta fara karanta addu'o'in da ta iya, sai iya ta kauce mata da sauri tana mata alama da ta shigo da hannunta. Ita kuma tai saurin ficewa daga falon, sai da Falmata ta juya ta kalli ficewarta sannan ta juyo ta nufi hanyar dakinsu yan uku, tana ta mamakin yadda Iya ta rikirice saboda Addu'ar da tai.
鈥業dan zan sake zuwa sai na samu furen tumfafiya na hada da goro na zauna鈥�
Ta fada a ranta dan ta taba jin Tumba na fadar indai mutum yai haka yai arba da maye ba zai iya kallonsa ba. Yau ma bata tararda yaran ba, daman haka ya fi mata dan bata son tai wani abu ace ta yi ba daidai ba. For the first time yau tana ta ji tana sha'awar yin shara tana kirar suratul Baqara, surar da idan ka karanta shaidane sai yayi wata daya kamin ya sake shigowa gidanka, idan kuma ka karanta ayoyi goma na farkon surar a kullum, to kana cikin tsaron Allah babu wani abun da zai same ka, maita ko aljani ko wani shari kuma zaka wuni cikin nishadi.
Daga alif lam min ta fara karatun cikin muryarsa mai dadi da kwantar da hankali ga saukarda natsuwa kasancewar qur'ane take karatu, a yanayin yadda ta kare a kirar ma sai ka dauka wata balarabiya ce ba fulani ba. Har ta yi aikin ta gama karatunta take sai da ta gyara komai tsaf sannan ta fito ta janyo dakin ta rufe ta fito daga corridor, bata wani tsaya kula wadanda suke falon ba ta sa kai zata fice, sai Ammy ta kira wata mata dake zaune kasa tana kallon tv.
鈥淪alamatu kira yarinyar can鈥�
Jikin Salamatu na rawa ta kwalawa Falmata kira tana mikewa tsaye ta nufi inda take.
鈥淜e...
Falmata ta juyo a tsorace gabanta na faduwa, ita dai tsoron ta kar ace ta yi wani abu.
鈥淣a'am鈥�
Ta taho da sauri ta zube kasa ta gaishe da Ammy kamar yadda ta lura da mutanen gidan na yi, ko daga kai ta kalli Ammy bata yi saboda tsoron irin an talaka a gaban sarki. Sai ta karaso sannan Ammy ta yi murmushi kadan tana kallonta cike da burgewa, yadda ta ji tana karatun ya matukar burgeta ga natsuwa da kuzari aiki da take ganin kamar yarinyar tana da shi, ina ma ace Nanarta ce a haka.
鈥淒uk abun da na ce ki rada mata a kunne鈥�
鈥淭o ran ki ya dade鈥�
Salamatu ta amsa, sai Ammy ta maida dubanta gurin tv kamar ba zata ce komai ba, ba dan komai ba sai dan isa da kasaita irin ta matan sarakuna musamman idan suna cikin talakawa. Falmata kan cikinta sai kadawa yake tana ta tunanin abun da tai ba daidai ba.
鈥淵a sunanki?鈥�
Salamatu ta rada mata, sai Falmata tai saurin amsawa muryarta har rawa take kana jinta kasan tana daf da fashewa da kuka.
鈥淔almata鈥�
鈥淪hekarunki nawa?鈥�
鈥淐ikin ta sha bakwai鈥�
鈥淜ina zuwa makaranta?鈥�
鈥淓h islamiya, bana boko鈥�
鈥淪aboda me?鈥�
鈥淏a a saka mu ba鈥�
Ko wace tambaya sai Ammy ta bada tazara take yinta kamar mai tunanin wace tambaya zata mata ko kuma mai hutawa sannan yai wata tambayar.
Da hannu Ammy tai mata alama da ta tashi ta tafi, daman can Falmata shi take jira sai ta tashi da sauri ta fice daga katon falon jikinta har rawa yake.
Sai da ta fice sannan Ammy ta kalli Salamatu.
鈥淭ashi ki nemo min Gambo鈥�
鈥淭o ranki ya dade Allah ya kara miki lafiya da imani鈥�
Da sauri Salamatu ta fice daga falon, ba a dauki lokaci ba sai ga Gambo ta shigo ta zube kasa ta kwashi gaisuwa.
鈥淕ambo yarinyar nan da kika kawo tana da halin kwarai ko?鈥�
鈥淲allahi ranki ya dade ba zan dauko sheri na kawo a cikin iyalanki ba, ina wace ni, Wallahi sai da na duba na dubo na zabo sannan na dauko ta, kaf a unguwar nan ba yarinya matashi kamar ita wacce tai kunya da tarbiyar Falmata, Allah ya mata natsuwa da kamala, ga ilmin kamar ruwa, sai dai ace ba tai boko ba amman na muhammadiya kam babu abun da bata sani ba鈥�
Ammy ta yi shiru har na wani lokaci sannan ta ce.
鈥淢a-sha-Allah, ina son ki fadawa iyayenta za ta rika wuni nan tana rainon su Labib鈥�
鈥淭o ranki ya dade, yadda kika ce haka za ayi, yanzu ma daga nan can zanje na isar musu da sakon Hajiya, Allah ya kara miki imani鈥�
Da hannu Ammy tai mata alama da ta tashi ta tafi, sai ta mike da sauri ta fice.
***聽 ***聽聽 ***
Hajiya ta sauke ajiyar zuciya bayan Jarma ya gama yi mata bayanin salin inda garin yake, da kuma abokinsa da zai musu jaroganci.
鈥淛arma ina tunanin kai ya kamata ka fara zuwa, domin kai ka fada masa matsalar ta yarka ce, ganina zai iya gano wani abu, sannan ba zai yiyu na shirya tafiya a yanzu ba, kai ma kuma a nemeka a rasa cikin masarautar nan, za a fara zarginmu鈥�
Jarma ya jinjina kai.
鈥淣a yi wannan tunanin Hajiya, sai dai jin cewar ba a musu sako sai dai mutum yaje da kansa yasa dole ne mu yi tafiyar a tare鈥�
Hajiya ta yi shiru na wani lokaci kamin ta kalleshi ta ce.
鈥淶uwana kamar zuwanka ne Jarma, domin bukatar da nake da ita ita ce a kanka, idan ka je ka ga guri sai mu shirya wata tafiyar daga ni sai kai mu tafi ba tare da abokin ka ba鈥�
鈥淎bokina amintaccena ne Hajiya karki samu damuwa da shi鈥�
鈥淏ana saurin yarda da mutane kai ma ka sani, kuma ka san Shattima a can yake aiki, zai iya ganinmu鈥�
鈥淗aba Hajiya ya za ayi mu yi saken da Shattima zai gan mu sai kace wasu yara dai?鈥�
鈥淏aka san gayyadar da Zainabu ta tara ba ne, shi kanshi ba dan sa ido ne lamurran gidan nan鈥�
鈥淶an fara zuwan kamar yadda kika bukata, daman can na yi tunanin fara zuwa ni kadai鈥�
鈥淗aka yayi, ka karanta musu komai idan ka je, idan zai yiyu ka shirya tafiyar nan a cikin satin nan鈥�
鈥淎ssabar din nan zan tafi In-Sha-Allah, Allah dai ya bamu nasara鈥�
鈥淎min鈥�
Hajiya ta amsa tana kashe ido daya. Hannunta ta kai ta dauko wayarta ta soma neman number Talba, ta san ko yana a gari ba saba shigowa ya gaishe ta ba kamar Sirleem amman rashin ganinsa kwana biyu yasa ta damu. Ring biyu ya daga, sai da suka gaisa sannan ta ce.
鈥淭alba ina ka shiga kwana biyu?鈥�
鈥淚na nan鈥�
鈥淜wana biyu baka saka mahaifiyarka a ido ba, kuma hankalinka kwance鈥�
鈥淗ajiya idan wani abu ya same ki ai dole a sanar da ni, na san lafiyarki kalau ai鈥�
鈥淜ana da labarin dai za a daura auren Teema ko?鈥�
鈥淵eah na sani鈥�
鈥淭o kai nake son ka wakilci mai martaba鈥�
Ya zare ido kamar tana gansa.
鈥淲ane irin ni kuma Hajiya, kin san ban saba shiga irin abubuwan nan ba, kuma dai ga Baba Waziri ga Baba Jarma ga Shattima sai ace sai ni?鈥�
鈥淵anzu ina son ka fara shiga, duniya ta san da kai, wannan umarni ne ba shawara ba, idan ka shigo zan mu tattauna akai ya kamata ka fara mika hannu ana yin komai da kai鈥�
鈥淕askiya Hajiya ba zan iya ba Wallahi ban saba wannan ba鈥�
鈥淪hiyasa na ke son ka saba din ai鈥�
Ta kashe wayar bata ma tsaya jiran abunda zai fada ba. Idan ba tai da karfi ba, ba zata samu abun da take so ba, a komai sai Ammy ta tura danta ko'ina shi ake gani ita ba a san da nata dan ba, tana ganin yanzu ya kamata ta zage dange tai da gaske kar a mata yar gidan jiya.
03/12/2021, 08:32 - 馃馃馃馃: *馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*14*
Gaba daya ta koma kamar ba ita ba, daman a duk lokacin da suka zo gidan Waziri haka take zama wata saliha, bata sakewa har sai sun bar gida, wannan karon kuma zuwan gaba daya tai dan bata san ranar komawarta ba.
Gashi nan tana jinta kamar tana gidan yari, domin yaran Baba Waziri basa fita ko'ina daga makaranta sai gida sai kuma wata hidimar idan ta tashi, gara ma a can masarautar tana iya yin karyar zuwa wani guri Ammy ta barta ko ta samu Sirleem ya fita da ita ko Hajiya Karama, nan fa? Gaba ta kasa sakewa ko breakfast bata fitowa ayi da ita kamar yadda aka saba yi tare da kowa sai ta shige cikin daki ta zauna ita kadai sai idan an kawo mata nata abun karyarwa haka ma da rana, gashi nan dole ne taje makaranta kuma school bus din da bata so ce take kai ta kullum ta dauko ta.
Gaba daya ta rasa yadda za tai, wata zuciyar na raya mata ta ari wayar wani ta kira Hajiya Babba ta fada mata dan ita kadai ta ke da tabbacin zata taimaka mata ta cireta daga wannan kangin.
Misalin karfe biyu da yan mintuna Motar Hajiya Karama ta shigo gidan, ta window Nana ta leka tana hangota ta sauka saman gadon da sauri ta fita a guje har tile din na kokarin zameta ta fadi. Zainab na kokari rufe motarta sai ga Nana ta fito da gudu ta zo ta rumgume ta, Zainab ta saka dariya tana cire gilashin idonta.
鈥淵ou miss us right鈥�
鈥淵es Hajiya Karama ki ce Ya Shattima am sorry kuma zan ce ma Ammy sorry pls ya maida ni gida鈥�
Zainab ta taba kumatunta tana mata dariya.
鈥淪hattima ma baya garin nan, ya koma aiki鈥�
鈥淣i bana son nan Hajiya dan Allah鈥�
鈥淒ukanki suke?鈥�
鈥淣o鈥�
鈥淭au why? Kanen mahaifinki ne Nana yayansa kuma yan'uwanki ne, ni kaina idan na gaji da zaman gidan can wani lokacin a nan nake zuwa na kwana biyu sannan na koma, a gida nan ma ina da gata komai kike so za ayi miki, komai kike so shi zaki ci to miye matsalar ki Nana?鈥�
鈥淏a a zuwa ko'ina kuma dole sai an je school both islamiya and boko鈥�
Zainab ta rika fuskarta.
鈥淐an baya na san kina son makaranta yanzu miyasa ba ki so?鈥�
鈥淣i dai bana so kuma, kuma.... Ni bana son na gama bokon saboda kar na auri Sirleem鈥�
Kyalkyalewa Zainab tai da dariya.
鈥淪aboda ba ki son Sirleem sai ki lalata karatunki? To idan ba ki son zuwa makaranta ai sai ya ce ayi muku auren da wuri, Nana ki kwantar da hankalinki idan ba ki son babu dole ki bada lokaci kawai zan yi supporting din ki na hana auren Sirleem鈥�
Nana ta zare ido.
鈥淗ar da Hajiya Babba ma za ta goya min baya ko? Shikenan ma na huta鈥�
鈥淵a za ayi Hajiya ta goyi bayanki, ki ki auren danta na cikinta? Ke har yanzu ba ki da wayo?鈥�
鈥淎i tana so na鈥�
鈥淎mman ta fi son danta dake, ki daina wannan tunanin, yanzu dai zuwa nai na ganki kuma na dauke ki muje mu sha ice cream dan san kina so鈥�
鈥淵es yes, amman kina shiga cikin gidan nan Hajiya Maryam ba zata bari ba, zata ce Baba Waziri yace kar na je ko'ina鈥�
鈥淥kay je ki dauko veil ko hula mu je鈥�
Da gudu Nana ta juya ta koma dakinta dake cikin gidan ta dauko wani karamin veil ta saka a kanta, ko da ta fito har Zainab ta yi reverse ta bude nata front seat. Da sauri ta shiga Zainab ta fara tukin tana kai hannunta ta dauki kwakwarda ke gefenta ta ci sai kuma ta dauko wata ta mikawa Nana, ita kuma ta karba ta fara ci, tafiyar ta su ba tai nisa ba Nana ta hango AA tsaye kusa da wani gida mai karamar kofa yana waya.
鈥淗ajiya tsaya tsaya tsaya....鈥�
Da sauri Zainab ta taka burki ganin yadda Nana ke kokarin tsayar da ita kamar ta ga wani abu. Sai da Zainab ta faka motar sannan ta bude ta fita, AA na hangota ya yanke wayar da yake tana kallonta gabansa sai faduwa yake, wata zuciyar na raya masa cewar ya gudu, ko kuma ya shige cikin gidan ya boya. Wata kuma na ce masa ya daure, dan murmushi da Shaukin da ya hango a fuskar Nana yasa ya dan ji kwarin guiwar tsayawar.
鈥淎A AA鈥�
Ta fada tana jin kamar ta rumgume shi. Shi kuma ya kasa amsawa sai kallon motar da ta fito yake, sai da Zainab ta sauke gilashin motar ya ga macece sannan hankalinsa ya dan kwanta.
鈥淢e kika zo yi nan? Waya ce miki ina nan? Biyoni kika yi?鈥�
鈥淎 a ba mu fita ni da Hajiya Karama shine na hango ka na ce ta tsaya鈥�
Ta fada tana kara matsawa kusa da shi kamar ta rumgume shi wani irin shauki take ji idan ta ganshi.
鈥淣an ne unguwar ku?鈥�
Ya tambaya yana zaro ido wata zuciyar na ce masa ashe baka tsira ba.
鈥淎 a nan gidan aka kawo nan dai, wai bana jin magana shine za min horo鈥�
鈥淜amar ya?鈥�
鈥淲ai saboda gidan ba a zuwa ko'ina kuma dole aje school, shiyasa aka kawo nan鈥�
鈥淲ane gida?鈥�
鈥淲acan gidan mai Ash da white paint鈥�
Kai tsaye ya san gidan Waziri take nufi, baki sake ya ce.
鈥淕idan Waziri?鈥�
Ta gyada masa kai.
鈥淵a kike da shi?鈥�
Shiru tai tana kallonsa sai kuma ta fara dariya.
鈥淚na ruwanka kai me kake a unguwar?鈥�
Ya dan shafa kansa yana tunanin karyar da zai mata.
鈥淣a zo gaishe su ne, ko zan dan samu wani abu kudi na ke nema, ba ki da wani abu nan ki ba ni?鈥�
鈥淏a ni da kudi amman bari na ce Hajiya.... 鈥�
Yayi saurin dakatar da ita.
鈥淣o no no tsoro nake kar a kama ni, na sani ko kin fadi cewar ni kika bawa 20k din ki kuma ni na jefar da ke akan babur鈥�
Ta fara dariya.
鈥淲allahi ban fada ba, ai idan na fada Ammy zata min fada ne tace ashe bana zuwa school, cewa nai driver na ne鈥�
A nan ta fada mishi karyar da tai musu da kuma yadda ta isa gida a ranar. Sosai AA ya jidadin haka ta rufa mishi asiri yanzu kan hankalinsa ya kwanta.
鈥淏ari na karbo maka kudin鈥�
Ta juya ta koma gurin Motar Zainab ta lekar da kanta.
鈥淗ajiya kina da 10k ko 20k ki ara min, ko ma dai ki ba ni鈥�
鈥淢e za ki yi? 鈥�
鈥淪hi zan bawa鈥�
鈥淲aye shi?鈥�
鈥淢alamin mu ne na makarantar islamiya, na masa alkawarin ne shiyasa鈥�
鈥淜arbo account dinsa a tura bani da cash鈥�
Ta juyo da sauri ta zo ta fada masa, sai ya rubuta mata account din a wayarsa ya mika mata yana fadin.
鈥淕t bank鈥�
Sai da Zainab ta kare masa kallo sannan tai masa transfer 10k ta mika mata wayar.
鈥淵i sauri mu je鈥�
鈥淎 a na fasa zuwan ki tafi kawai鈥�
鈥淪aboda?鈥�
鈥淣i dai na fasa dan Allah ki tafi, Wallahi ba guduwa zan yi ba, zan yi magana da shi kawai na koma gida you have my word鈥�
鈥淧romise?鈥�
鈥淚 promise鈥�
Ta fada tana daga hannu alamar ta dauki alkawarin.
鈥淥kay take care of yourself, kuma kin san kika dade har aka fito aka ganki babu ruwana zan ce ni ban ma zo gidan ba鈥�
鈥淣a zan yi haka ba i love you鈥�
Zainab ta yi murmushi tana daga gilashin motarta, sai da ta wuce sannan Nana ta dawo inda yake ta mika masa wayar.
鈥淏an san ko nawa ta saka maka ba鈥�
Ya karbi wayar ya duba alert din da ya shigo na 10k.
鈥淒ubu goma ne thank you so much Allah ya biyaki鈥�
鈥淭o zaka ara min na kira Hajiyata?鈥�
鈥淵es ba dai tona min asiri zaki yi ba ai鈥�
鈥淎a鈥�
Ta karba wayar ta saka number Hajiya Babba ta aika mata kira, sai da ta jera mata miss calls kusan uku a ana hudu aka daga cikin tsawa.
鈥淲aye wannan?鈥�
鈥淗ajiya ni ce fa Nana鈥�
Hajiya ta sake fuska jin Nana.
鈥淒aughter da sabowar number?鈥�
鈥淓h to ba Baba Waziri ya karbe min waya ba, kuma gashi nan Ya Shattima ya dawo da ni gidan wai bana jin magana, Hajiya dan Allah ki zo ki dauke ni yau yanzu鈥�
Ta fashe da kuka.
鈥淲ai me yake damun mutanen nan ne? Gani nan zuwa yanzu鈥�
鈥淭o sai kin zo Hajiya yanzu pls ko minti biyu kar ayi鈥�
鈥淵anzu daughter鈥�
Ta katse wayar ta mikawa AA.
鈥淲a kika kira?鈥�
鈥淪tep mom dina ce ita ai tana so na, yanzu za ka ga ta zo ta dauke ni鈥�
Ya saka wayar aljihu yana kallonta.
鈥淜in rame鈥�
鈥淭o ina ruwanka?鈥�
Ta watsa mishi harara sai kuma tai yar dariya.
鈥淵anzu tana zuwa zan ce ina son ta daukar min kai driver鈥�
Ya kalleta da sauri.
鈥淜uma zata yarda?鈥�
鈥淓h so na take sosai鈥�
鈥淏ari na koma kar ta zo ta gan ni a hanya鈥�
Ta daga mishi hannu.
鈥淏ye鈥�
鈥淏ye鈥�
Ya amsata yana binta da kallo har ta isa gaban gate din gidan Waziri ta shige. Ba tai minti talatin da shiga gidan ba sai ga Hajiya Babba ta iso tare da driver ta furka a murtuke kamar da gaske ranta a bacen yake. Nana na hangota ta windows ta fara tsalle tana rawa tana jindadi.
Kai tsaye ta wuce bangaren Uwargidan bata biya inda kawarta kuma amiyarta Talatu ba, amasama ta gaisa da matar kanen mijin nata Hajiya Maryam daman can ba sa shan inuwa daya sannan tace.
鈥淶uwa nai na tafi da Nana鈥�
Hajiya Maryam ta kalleta.
鈥淣ana kuma? Shattima ne ya kawo ta nan ta kwana biyu鈥�
Hajiya Balki ta yi mata wani kallo.
鈥淚kon Allah kina nuna min ban isa da Nana ba kenan? Ko kuma kina nuna min ita din ba yata ba ce? Ban gane ba?鈥�
鈥淎 a Wallahi ba wannan, kawai dai ance ana son ta kwana biyu nan ne shiyasa na fada miki鈥�
鈥淭o bata kwana biyu ba, Nana ba ta kusa sati a gidan nan ba?鈥�
鈥淏a wai ana nufi kwan nan biyu ba, kwana biyu na malam bahaushe ake magana Hajiya鈥�
鈥淲ai wacece ke da kike fada min wannan maganar? Banza a banza kashi a masai? Shattima ya fi ni iko da Nana ne ko kuma me? Ke kina kara nunawa Ammy wannan bakin abun na ki na wani yan uba, mu yaran gidan mu ba su san wannan ba, kowata da yai nan ma ai bata mata tarbiya za ayi鈥�
Hajiya Maryam ta yi dariya
鈥淗ajiya kenan, ke kuma abun da kike gyara mata tarbiya ne? Shattima ai ya san da ke a gidan amman ya dauke ta ya kawo ta gurin kanen ubanta kuma be ce a kawo ta ko'ina ba sai a nan bangarena, har waya sai da ya daga ya kirani yace na kula masa da Nana, kin ga kuwa dan gyara aka kawo ta ba baci ba鈥�
鈥淓h Lallai Hajiya Maryam, ni kike fadawa magana haka? Yanzu da Ammy ce za ki mata haka? A a sai ni da nake kishiyarta ko? Ba komai komai yana da lokaci ai wata rana sai labari, Ke Zarah tashi ki kira min Nana鈥�
Hajiya Balki ta karasa tana kallon karamar yar Hajiya Maryam. Zarah ta tashi ta fita daga falon zuwa bangaren da dakunansu suke, ta kira Nana suka fito tare, Hajiya na ganinta ta mike tsaye.
鈥淚dan Waziri ya zo ki ce masa na dauki yata, idan kuma ban isa da ita ba, sai ya zo ya dauko ta鈥�
Haka ta saka Nana na gaba suka fice daga falon, tun kan su karaso driver ya bude musu baya, Hajiya ta shiga Nana ma ta zagaya ta shiga ko tsinke bata dauka ba a gidan. Sai da direban yaja motar suka fita daga gidan sannan Nana ta rungume Hajiya a cikin motar.
鈥淣a gode Hajiya鈥�
Hajiya ta yi murmushi.
鈥淎nything for my daughter鈥�
鈥淜e ba kamar Ammy kike ba kina so na sosai kuma kina min duk abunda nake so i love you so much Hajiya鈥�
鈥淚 love you too Daughter鈥�
鈥淜uma Hajiya ina son sabon driver, bana son school bus tana kai ni makaranta, shi zai rika kai ni islamiya da boko ma, tun da can na fadawa Ammy ta dauka min sabon driver ta ki鈥�
鈥淜arki damu zan daukar miki sabon driver, duk abunda kike so shi zan miki daughter zan saka a samo sabon driver ya rika kai duk inda kike so鈥�
Ta dago da sauri tana kallon Hajiya cikin wani irin jindadi marar misaltuwa.
鈥淎kwai wanda yai min magana Hajiya, yace zai iya kuma yana so鈥�
鈥淭o ki nemo shi daga gobe zai fara tukaki ki bashi keys din motar kuma ki fada masa yadda ake biyan wacan driver ni zan din ga biyansa every month鈥�
Da sauri Nana ta kara rumgume ta ta kwanta jikinta tana jin wani son ta fiye da Ammy.
*** *** ***
Kofar wani gidan ta kwankwasa aka bude mata, matashiyar matar ta leko.
鈥淗ajiya kuna siyen danyen man shanu?鈥�
鈥淎 a muna da Allah bada sa'a鈥�
鈥淭o amin鈥�
Ta amsa tana lasar bakinta, a nan ta janyo kurwarta ta warware zanenta ta saka yar tsokar ta kulle, ta maida zanen ta daure ta yi saurin bari wajen har da hadawa da gudun, duk da bata matsi kurwar ba ta ta ga matar tana da aljanu kuma za su iya tashi, ko da yake na Amo sun fi na matar karfi.
Cikin unguwar Nasara ta shigo gidan data saba kawo musu danyen manshanu suna siye, tana buga gate din mai gadin ya bude mata, ta gaishe shi da far'arta tana kallon kurwarsa dake kasan kafafuwansa.
Nisa kai tai cikin gidan har ta isa bakin kofar falon da ke bude ta zauna kasa tana sauraren hirar da Hajiyar ke yi da kanenta yaranta su ka zo da gudu suka rumgume Amo.
鈥淥yoyo Amo ta zo Oyoyo鈥�
Ta muku ya zaunar da su saman kafafuwanta tana dariya tana musu wasa.
鈥淪hi fa be ma san da maganar ba, kuma ita Ammy tace kar na bari ya ji sai komai ya kama鈥�
鈥淭o sai matsalar wannan abun da ke tare da shi鈥�
鈥淭o ai ni ma shine, kar a aura masa yar mutane ta mutu, shi kansa yanzu abun da yake tsoro kenan shiyasa ya cire ransa daga auren ma鈥�
鈥淪ai dai idan ba za a fada ba鈥�
鈥淚dan kuma ba a fada ba, ai an cutar da yar mutane, kuma ita yanzu Ammy tace ta damka min ragamar komai, wai ko a nan Katsina din ne su zauna tukunan鈥�
鈥淎i kam samun mata yanzu ga Shattima aiki ne, ga kudi ga kyau ga ilmi ga sarauta amman fa ana tsoron mutuwa鈥�
Ra'ees ya shafa kansa cike da damuwa dan wannan aikin da Ammy ta bashi ba karamin aiki ba ne. Karamar yar Hajiyar ta shigo tana tsalle.
鈥淢omy ga Amo can ta zo鈥�
鈥淭o yar gidan Amo鈥�
Ta fada tana dariya sannan ta mike tsaye ta fito waje suka gaisa da Amo. Sai da ta bude manshanun suka fara ciki ta siye wanda zata siye sannan Amo tace.
鈥淗ajiya na ji kuna neman mata鈥�
Hajiya ta yi dariya.
鈥淢una nema kan amman ai shi mai son matar ne da matsala鈥�
A nan Hajiya ta labarta mata waye Shattima. Sai Amo tace.
鈥淜ai duk canfi ne Hajiya, ku bar wannan maganar ma, karku sake fadin haka abun da Allah ya kawo ai shi yake kasancewa, ni da za ku yi shiru da bakinku akwai yar da nake riko sai a bashi ita, indai za a saka ni gaba ayi komai鈥�
鈥淎iko da kin kyauta mana, zancen fadin haka daga yanxu ma mun daina鈥�
Amo ta yi dariya tana kallon sabon cikin Hajiya take dauke da shi, da be wuce sati biyu ba, amman ita tana ganinsa da idonta hudu na maita. A nan ta fada musu addirenshi da wanda za a nema idan aje.
鈥淚ndai da gaske suke suka je Malam zai bashi aurenta, dan shi kanshi neman mijin da zai aureta yake, shekara goma sha 16 babu wanda ya taba tambayar amrenta鈥�
Har lokacin tana kallon cikin, wata zuciyar na ce mata ta taba wata na cewa ta bari sai ya kara kwari. Bayan sun gama yanke komai ta siye manshanun ta sallame ta taso tana ta jindadin indai ta zama jagaba ita ce zata samu kudin komai ai.
FADIME POV.
A yadda ta kabartawa Inna labarin cewa tai wani ta ji a jikinta akwai wata wuta tana binta kuma wutar maita ce, bata son ta fadawa Inna gaskiya dan kar ta mata fada ko kuma ta hana ta zuwa gurin kiwon.
鈥淒ubi kike ne da kika fara ne Fulani?鈥�
鈥淢inene Dubi Inna?鈥�
鈥淏okaye suke yinsa su duba hannun mutu ko idonsa su fada masa abu, ana basu kudi鈥�
Gyada kai Fulani tai tana dariya a ranta tana tunanin ta samu sana'a.
鈥淭o yanzu idan nai miki Inna za ki ba ni kudi ko?鈥�
Inna ta watsa mata harara.
鈥淏ari Malam ya ji da wannan dabi'ar sai ya zaneki kin san dai babanki malami ne ko?鈥�
鈥楾o ni ina ruwana da wata malantarshi鈥�
Ta fada a ranta tana turo baki gaba, a dayan bangaren kuma tana ayyana irin kudin da zata samu idan tai wannan sana'ar. Waya sani ma ko aljani ne ya zo ya taimaka mata?
Bayan kwana biyu Inna da Fadime na zauna waje, Amo ta fito daga bukkatar tana fadin.
鈥淚nna Fadime na yi ma Fadime miji鈥�
Kamin Inna tace komai Fadime ta nufe ta da far'a tana dariya, kwatakwata a rayuwarta babu wanda ya taba zuwa yace yana sonta sai yau.
鈥淒a gaske? Ina miji?鈥�
鈥淜e arrr Fulani babu kunya鈥�
Inna ta fada cike da jin haushin yadda Fadime take rawar jiki. Fadime ta rufe ido ta dawo da gudu ta rufe kanta jikin Inna sai a lokacin take jin kunya wai.
Amo ta zauna tana dariya ta labartawa Inna.
鈥淎 can bunni inda nake kai mansanu, samarayin gidan abokaine yake neman mata nace ga Fadime nan tun ita yar boko ce kuma tana da kyau ba kamar hajjo ba鈥�
Inna ta jidadi sosai cikin ranta duk da tasan Amo ba zata kawo mata abun alheri ba, amman jin yau ana son yarta yasa ta jidadi abun da ba a taba ba ko da wasa.
鈥淎i na ce su zo su yi magana da Malam indai da gaske suke.鈥�
Amo ta fada sai Fadime ta ce
鈥淎llah yasa su zo Allah ya kawo su lafiya, yana da kyau?鈥�
Inna ta rafka uban tagumi tana kallonta, Amo kuma ta saka dariya domin ita dadin rashin kunyar da Fadime take, take ji domin ba al'adar fulani ba ce. Ganin yadda Inna take hararta yasa ta fita daga gidan da gudu tana dariya, kai tsaye ta nufi gidansu Ma'u ta fada labari, tana isa ta tarardar Ma'u na yi ma wasu mutane kwatancen wani gari da ke yamma da su. Mutum uku ne da wata dalleliyar mota daya na tuki daya a baya daya kuma a mazaunin gaba. Gurin madubin motar Fadime ta je tana duba fuskarta kamin ta fara shafa motar, wanda hakan ya ba Jarma tsoro yana ganin kamar lekensa take ta ga ko waye ne, kamin a gama musu kwatance su kama hanya duk ya takura.
鈥淜iyaye....鈥�
Ta fada tana daga musu hannu kamar ta san su, ta bi motar da kallo sai da ta daina hangota sannan ta talkamo kawarta ta fara bata labari.
*** *** ***
Jarma yaja tsaki cike da jin haushi.
鈥淲ai yanzu kai Saminu ka san baka san gari ba kasa mu ka kamo hanya haka?
Saminu dake gaban mota ya juyo yana kallon abokinsa.
鈥淎 a fa na san hanya, garin da shi jafaru yake zuwa ci rani ne ban sani ba, amman muna isa muka ce gidan liman ance babu wanda be san shi ba a garin, ka ga sai mu tambayi Jafarun sai ya shige mana gaba mu shiga cikin garin tun da shi ya san yan garin da yawa kuma yana yi wa mutane jagoranci amman mu kai tsaye ai ba za mu shiga garin ba鈥�
Jarma be koma cewa komai ba, har suka isa garin Dan burki, suna tambayar gidan liman aka nuna musu, a gidansa suka sauka yai musu tarbar ban girma duk da be san su sai dan karamci irin na mutanen kauye. Sai da suka huta sannan aka kira musu Jafaru suka kama hanyar garin, ba Saminu ba ko Jafaru da ya saba zuwa garin sai da tsorata da suka kusa isa balle kuma Jarma danke jin kamar fitsari za su zubo masa ganin yadda ake ta yankan daji kamar ba a dubiya ba.
鈥淎i dai ba za su mana komai ba ko Jafaru?鈥�
鈥淏abu abun da za su mana tun da ina tare da ku, amman ba za mu shiga garin da motar nan ba鈥�
Cikin manyan duwatsu suka ratsa har suka isa bakin kofar gate din garin da ba zaka iya fadar da me kai ta ba, itace ko katakaye ko kafara katuwar kofa ce mai tsayi sosai ga masu gadin kofar sanye da warki sai kallon su motar su Jarma suke. Jafaru ne ya fita yaje yai magana da su sannan ta dago musu hannu suka fito suka karasa inda yake. Shine gaba suna biye har suka shiga cikin magarin, sannan aka kawo musu motar jaki suka hau aka nisa cikin garin da su. Sai da aka isar da su gurin sarki suka gaishe shi ya san da zuwansu sannan aka wuce da su gurin boka, duk abunda ake Jarma be wani motsin kirki ko kallonsu be son yi gudun kar yai laifi, shi a rayuwarsa be tana ganin mutane haka ba sai yau, you ashe akwai irin mutanen nan har yanzu. Amman kam garin akwai kyau ga manyan duwatsu da itatuwa ga kuma ruwa ta ko'ina gwanin burgewa kowa sai hada hadarsa yake.
A nan ma sai da Jafaru ya shiga yai magana da su sannan akai musu iso, sun san Jafaru sosai dan ya saba kawo musu mutane kala kala kuma yana cikin irin mutane da suke bawa kudi ayi musu sako a burni ko daga wani gari zuwa wani gari.
A saman agalami suka samu mutanen mai kama da munanan tsofi kansa da aski an masa tas idonsa kamar garwashin wuta, kana ganinsa ka san aka gawurtaccin ifiritai a tare da shi, yawanci mutane garin suna jin yaren hausa da fulatanci duk da kasancewar ba su cika mu'amala da kowa ba, sai wanda suka yarda da shi, amman ban da wannan baya jin ko wane yare sai na su. Sai dai a kusa da shi akwai mai fassara musu komai.
Suna zama ya fara karaton musu abun da ya kawo su.
鈥淜a zo nan saboda a kawarda dan'uwanka, da matarsa da dansa ka hau sarauta, kana son a kashe Shattima da Talba da sannan a nakkasa Zainabu da Balki鈥�
鈥淲allahi haka ne鈥�
Jarma ya fada yana kara gyara zamansa mamaki duk ya cika shi, ta dayan bangaren kuma yana jin kunyar jin sirrinsa da abokinsa Saminu yai.
鈥淭o ga tafiya nan da ba dawowa, ga Fadime nan ga Falmata, ga Sardauna su za su lalata muku shiri鈥�
Jarma ya nisa a cikin tunani yana ta neman gano waye Fadime waye Falmata? Kuma waye Sardauna? Sardauna na na Yola ko kuma wani sardauna nan dabam?
Wata kwarya ya dauko mai ruwa ta aje gaban Jarma, ya fara karanta wasu abubuwa sai ga Mai Martaba ya bayyana a cikin ruwa, wani irin zabura Jarma yai ya matsa baya.
鈥淎 harbe maka shi? Yanzu nan za mu yi masa harbin kanko鈥�
Jikin Jarma sai rawa yake yayi sauri cewa.
鈥淎a shi ai mun samu nasarar kwantar da shi, yanzu Shattima muke son a fara harbewa tukuna鈥�
Mutumen ya fara karance karance yana kiran sunan Shatttima amman ya ki ya bayyana a cikin ruwan. Tun yana daukar abun da wasa har ya fara yi da gaske Shattima ya ki bayyana a cikin ruwan sai sunansa.
鈥淎kwai abun da ke kare shi, lallai shi ma be tsaya haka nan ba鈥�
鈥淵anzu ba a iya harbe shi kenan?鈥�
鈥淶a a iya amman idan akai be same shi ba, zai dawo gurinka鈥�
Jarma ya mike tsaye yana lalaba jikinsa.
鈥淎 a bari dai sai mun yi shawara tukuna鈥�
鈥淏a a shawara a nan ku tafi can gari鈥�
Jarma ya mike tsaye da sauri ta ciro kudin da za su kai dubu 30k ya aje musu, sai ya girgiza masa kai mutumen ya fassara masa.
鈥淜udin siyen dabba ake ba mu鈥�
Jarma ya karo 50k ya aje musu sannan suka juya jikinsa sai rawa yake. Duk shige shigensa be tana shiga irin wannan gurin ba, ba tana ganin tsafi kararsa irin yau ba.
_________
Sauran page daya mu gama free pages.
03/12/2021, 08:32 - 馃馃馃馃: *馃悇馃悇 FULANI 馃悇馃悇*
By Khadeeja Candy
*15 -Last Free Page*
Fadime ta kara lakkamo Ma'u tana dariya
鈥淲allahi kuwa鈥�
Ma'u da rufe baki tana zaro ido.
鈥淜uma Wallahi da gaske koko na sa da safen nan, Fulani da gaske kin iya鈥�
Wani kalar dadi ya kara rufe Fadime jin ta canki abun da Ma'u ta karya da shi yau, bayan ta gama fada mata ita tana da aljannu kuma suna sa ta gane komai na mutum.
鈥淵anzu kenan za ki iya fadawa mutum abun da zai same shi鈥�
鈥淓h amman sai na yi bachi, amman dan Allah Ma'u karki fadawa ko sai wanda kika yarda da shi, idan Bappa ya ji zai min fada ko ya doke ni ma鈥�
鈥淏a zan fada ba鈥�
Fadime ta yi dariya.
鈥淚nna tace masu irin wannan abun kudi ake ba su, idan kina ga wani na son a masa ya bada kudi ki kawo shi zan masa amman a boye鈥�
鈥淎iko zan ta kawo miki mutane Wallahi, sai ki sammin wani abu ni ma鈥�
Sai da hantsi ya bude sosai sannan Fadime ta bar kofar gidansu Ma'u ta dawo gida. Kai tsaye ta nufi bukkatarta ta dauko biro da littafinta ta fara rubuta hau Amo tace zata kawo mata miji, kuma ta fadawa kawarta Ma'u cewar tana dubi.
Gaba daya wunin ranar wuni tai cikin farinciki da jindadi kana ganinta kasan dadi take ji tana murna wai Amo ta mata miji kuma a bunni.
Amo dai sai kallonta take a ranta tana fadin
鈥榋aka si ubanka idan ka aureshi mutuwa za kai, idan ka gagaran ci ai ba ka gagari wani ba鈥�
Ta fada tana dan murmushi sai da Fadime ta mike tsaye tana kora shanu zuwa daji Amo ta lura yau wutar nan bata biye da ita, a razane ta mike tsaye tana bin bayanta da kallo.
Inna ma ta mike tsaye daga can cikin bukkar da take zaune tana kallon Amo, wacce razanar ta bayyana, Inna daman can ta dade tana zargin Amo da maita ba tun yau ba, tun daga lokacin da ta bata labarin cewar suna da maitar gado wacce ake bawa yara tun suna kanana amman ita Allah ya tsareta ba a bata ba, ga yayan wabin da Inna tai ta yi a duk inda take neman magani sai ace manya ce take cinye mata yaya, wani cikin ma tun kan ya zo duniya zata yi barinsa, Fadime ce kawai ta rayu ita ma daker dan babu kalar ciwon da ba tai ba, Allah ne dai ya rata ta da kuma addu'oin da take yawan yi mata, Bappa ma yana mata sosai har rubutu yake mata ya bata ta sha, tun a wacan lokacin idan Inna ta fada masa tana zargin Amo sai ya karyarta yace baya son tashin hankalin, har yake ganin kamar kamar Inna tana haka ne saboda Amo kishi, bayan kuma ita ta zo ta tararda Amo.
Sunsunsun Amo ta shige bukkarta da mugun mamaki, ta sani wani sa'in ana samun akasin abun da tai mata, sai dai ba ko yaushe ba, domin Fadime babu ruwanta da addu'a sai dai idan yi mata akai, kuma wannan wutar ta dade da saka mata ita tun Fadime na karama, taya yau rana daya za a wayi gari babu ta? Ko dai Inna ta karbo mata wani maganin ne? Idan ba haka ba gaya wutar ta bar binta? Adakin ta kasa zaune ta kasa tsaye sai safa da marwa take gaba daya hankalinta ya kasa kwanciya.
A kullum idan Fadime zata je kiwo sai ta saka shanun gaba tana binsu a baya, ban da kwana biyun nan da take son sake ganin Wasim, kullum baya take baro shanun sai idan sun kawo kansu. Tana isa ta haye saman dutsen ta fara kiransa.
鈥淢ai busa鈥�
Haka take kiransa a duk lokacin da ta iso gaban dutsen, duk kiran da zata masa kuma ba zata ganshi ba, ba zata ji busar ba, bata kuma fasa kiran ba. Sai dai shi yana saukowa kasa ne ya boya jikin dutsen yana kallonta har tai abunda za tai ta gama.
Sai da ta sauko saman dutsin sannan ta ganshi kasa tsaye ta inda zata ganshi yana kallonta fuskarsa da murmushi, dan tsoro ta ji.
鈥淜enan shi aljanin dutse ne?鈥�
Ta raya a ranta, a fili kuma sai ya kara hayewa saman dutson alamar ba zata sauko ba. Ganin hakan yasa ya fara haurowa saman dutsen still yana mata murmushi.
鈥淜a yi hakuri ni ba dan wani abu na kira ka ba鈥�
Ta fada tana kokarin sauka ta dayan bangaren, ganin hakan yasa shi ma ya juya ya sauka. Sai suka koma kallo kallo ita da shi, ta kira shi ne kawai ba dan tana da abun cewa ba, kuma bata san zai ji ta ba, tun da ta saba kiransa kwana biyu bata ji shi ba. Da hannu yai mata alama da ta zo sai ta kanne kafada alamar ba zata zo ba, ta girgiza masa kai. Zaunawa yai a gurin ta dauke kai daga barin kallonta. Hakan yasa zuciyarta ta raya mata cewar ko aljani ne shi ba zai cutar da ita ba tun da har mafarkinsa take. A da idan Inna tace mata tai addu'a sai tace mata wuya take ji, amman a yau da take son zuwa kusa da shi sai da ta tsaya ta karanta addu'oin data iya sannan ta tunkareshi tana takawa kadankadan kamar mai tsoron ya ji takunta, kansa na kasa har ta kawo kusa da shi ta risina ta leki fuskarsa, sai ya sakar mata murmushi ita kuma tai masa dariya irin dariyar nan ta dole kuma ta tsoro wacce mutum ke yi a rikice.
鈥淜ai aljani ne?鈥�
鈥淎a鈥�
Ya amsa mata yana dagowa ya kalleta da kyau.
鈥淭o miyasa na ke mafarkinka?鈥�
Kallonta kawai yake irin kallon nan na son tantace gaskiyarta. Kamar tasan irin kallon da yake mata sai tace.
鈥淲allahi ba karya na ke ba, ina mafarkin, da wani mutum kuma da wani kana rike da wannan abun busar kana busa amman kullum baya kake bani, shiyasa lokacin da na ji busarka na zo har nan dan gani idan da gaske ne, kuma busar iri daya ce鈥�
鈥淣i ba aljani ne bane鈥�
Ya fada cike da mamakin mafarkinsa da tace tana yi.
鈥淜uma tun lokacin nan nagge bata sake mutuwa ba, miyasa kake saka wannan abun鈥�
Ta nuna warkin dake kugunsa, sai yai murmushi.
鈥淗aka muke, kayan garin mu鈥�
鈥淚na ne garin ku?鈥�
鈥淕aruk鈥�
Ta gwala ido tana matsowa kusa da shi, sai a lokacin ta tuna da taba jin labarin garin ance mutanen ciki basa saka tufafi kuma matsafa ne.
Ta zauna a kasa tana kara kallonsa.
鈥淜ai kake min tsafi nake mafarkinka kenan?鈥�
鈥淎a鈥�
鈥淵a za'ayi na tabbatar da kai mutum ne?鈥�
鈥淚dan kika taba jikina za ki ji shi kamar na ki, idan na aljanine za ki jishi da sanyi ko taushi ko gashi ko kiji kamar ba hannun mutum ba鈥�
Dan matsawa tai kusa da shi, sai ya miko mata hannunsa ta taba sannan ta taba nata, sai ta ji shi normal kamar ita. Amman hakan be sa ta gansu ba.
鈥淜a yanke kanka na ga jini sai na yarda鈥�
Wannan karon dariya yake, a ransa yana mamakin wauta irin nata taya zata ce ya yanka jikinsa.
鈥淪amo min kare ko dutse mai tsine鈥�
Ba musu ta tashi taje ta samo masa, ta kawo ta zauna kusa da dan tabbatarwa idan da gaske yankawan zai yi ko a'a.
鈥淢iye sunanki?鈥�
鈥淔adime鈥�
Ta amsa mashi tana kallonsa da manyan idonta masu haske da daukar hankali. Murmushi yai ya mike hannun na dama ya saka hannunsa na hadu ya karkari hannunsa na dama kadan jini ya dan fito. Da sauri ta rufe ido tsigar jikinta na tashi.
鈥淚nnalillahi, da gaske ka yanka ni wasa nake maka fa鈥�
鈥淏a hakan zai sa ki yarda da ni ba鈥�
Ya fada yana kallon gashin kanta.
鈥淣a yarda鈥�
Ta fada bayan ta bude idon.
鈥淢iye sunanka?鈥�
鈥淲asim鈥�
Haka ta fara masa tambayoyi kala kala yana bata amsa, duk abun da ta tambaya sai ya bata amsa, tun tana da sauran tsoron har ta sake jiki da shi.
Har da karbar sarewarsa ta busa, sai nata busar bata fita saboda bata iya ba. Har sai da ya karba da kansa ya fara busar tana ta kallonsa cike da burgewa.
鈥淲aya koya maka?鈥�
鈥淲ani tsoho鈥�
鈥淎 ina yake?鈥�
鈥淕arinmu鈥�
Ya amsa yana kallonta, mugun burgeshi take, ko wane motsi nata the way da take tambayarsa yadda take sake jiki da shi far'arta kyauta and everything. Ta gyada kai tana murmushi, da yamma lis ta koro shannun ta sako su a gaba ta jeru ita ta shi suna tafiya, sai ya rakota har kusa da hanyar gidansu sannan ya tsaya ita kuma ta daga masa hannu, shi ma ya dago mata sai ta juya ta cigaba da tafiya sai kwasar dariya take.
Daman tun dazun take jin dariyar take son ta yi ta kasa, wai basa saka rika kuma basa son shiga cikin mutanen da na nasu ba, gaba daya kallon mahaukata take musu.
Sai ta kai shannun gida ta shigarda da su gurin da aka saba ajesu, sannan ta sunsuda ta fita, sai da ta kama hanya sannan ta hango Bappa tafe tare da wani makocinsu, da sauri ta boya bayan wata bishiyar dogon yaro. Kasancewar bishiyar katuwa yasa Bappa da mutunen ba su lura da ita ba, domin gaba daya hankalinsu baya gurin yana kan abunda suke tattaunawa ne.
鈥淕askiya ina baka shawarar ka kara aure kawai鈥�
Shine kawai abun da ta ji, duk da bata san abunda ake tattaunawa akai ba, amman tabbas ta ji Bappa na ce masa ya kara aure, a gurin tai ta tsayi har sai da suka karyar kwana sannan ta fito yana girgiza kai tana dariya.
Juyawa tai ta canja hanya zuwa gidansu Ma'u, ko da ta shiga ta samu Ma'u na alwala sallah magariba, sai ta risino kusa da ita.
鈥淢a'u nan da kwana biyu mijin Ande Hanne zai fara maganar aure ce ni na fada miki鈥�
Ma'u ta kalleta da sauri.
鈥淎ljanin ne ya fada miki?鈥�
鈥淓h, yau da naje kiwo ma a fili ya ganshi yace zan rika ba da magani zan rika fadawa mutane komai鈥�
Ma'u ta kara zaro ido gaba daya ma sai ta ji tsoron Fadime ya fara kamata.
鈥淒a gaske?鈥�
鈥淎llah amman karki fadawa kowa鈥�
鈥淏a zan fada ba鈥�
Gaba daya tsoro ya gama kama Ma'u, Fadime ma ta lura da hakan kuma ta jidadi, ita gaba daya tun da Inna ta fada mata masu magani kudi ake ba su su fadawa mutum matsalarsa ta ji tana sha'awar abun. Haka ta kwana da tunani kala kala na irin karyar da za ta yi ma Inna ta yarda ta fara bada maganin.
Sai da Fadime ta gama karyawa da fura mai tsami sannan ta zauna saman tabarmar da Inna ke zaune tana gyaran gida.
鈥淚nna na sake mafarkin aljanun nan sun ce zan bada magani fa鈥�
Inna ta daka mata tsawa.
鈥淔ulani kar na sakd jin maganar nan a bakin ki, da kin sake maganar nan sai na fadawa Malam鈥�
Da sauri tace.
鈥淣a bari鈥�
鈥淕ashi kije ki debo ruwa鈥�
Ta tashi da sauri ta nufi inda tulun daukar ruwan yake ta dauka ta fice da sauri ta nufi gurin deban ruwa, tasan Bappa sarai be son irin abubuwan nan. Tana tafe tana wakewaken har ta isa, sai da ta duka ta fara cikon ruwa sai ta ji a na kirata.
鈥淔adime鈥�
Da sauri ta juyo suna hada ido ta sakar masa murmushi kamar yadda shi ma yake mata murmushi. Tsaye yake nesa da ita.
鈥淎she kana zuwa nan da safe鈥�
Ya gyada mata kai yana karasowa kusa da ita, har yanzu bata daina jin tsoro ba sai dai ba kamar na da ba.
鈥淩uwa kike deba?鈥�
鈥淓h鈥�
Ta fada tana dariya sannan ta duka ta cigaba da cikon, sai kuma ta juyo ta kalleshi.
鈥淒an Allah ka taimaka min ka min wani abu鈥�
鈥淢inene鈥�
鈥淪o na ke idan na cika tulun nan, ka masa tsafi tun da ku matsafa ne ai zaka iya ko?鈥�
鈥淪aboda me?鈥�
鈥淪aboda Inna ta yarda cewar ina mafarkin aljanun, so na ke ka masa tsafi sai na je gida na aje tulun sai ruwan su zama maciji鈥�
鈥淏a ki jin tsoro?鈥�
鈥淎i ba anan ba sai na je gida, amman ka min alkawarin ba za ka cutar da ni ba鈥�
鈥淜o wani ba zan bari ya cutar da ke ba鈥�
鈥淭o ka min ka ji鈥�
Ya daga mata kai. Sai da ta cika tulun dam sannan ta matsa tace yai mata ita dai burinta kar Inna ta karyartata, burinta Inna ta bata hadin kai ba sai Bappa yaji ba. Matsawa yai kusa da tulun ya saka hannunta yana ta kallonta be wani dade ba ya cire sai ta zaro ido.
鈥淵anzu shikenan da naje gida zan ga ruwan ya zama maciji?鈥�
Ya daga mata kai alamar Eh yana ta kallonta, sannan ya tallaba tulun ya dora mata saman kai, tsakanin dora mata tulun da fara jin motsin abu mai rai a cikin tulun be yi minti 1 ba.
Yana kallonta sai ta fashe da kuka.
鈥淏a yanzu na ce ba, Wayyo Bappa wayyo Bappa wayyo Bapppa鈥�
Sai fitsari, ta fara kukan da gaske gasken hawaye kamar ruwa.
鈥淚dan kika sauke tulun macijin ciki zai cijeki, karki sauke sai kin isa gida鈥�
Ya fada yana dariya. Gaba daya jikin Fadime rawa yake kafafuwanta sai lankwashewa suke kamar zata fadi, numfashinta ya fara sama sama, faduwa tai kasa ta fara rarrafe dan bata ma iya tafiya, haka nan ta isa gari duk da bata zanenta da zawo sai kuka take tana kiran Bapppaa, ga tulun saman kanta. Duk wanda ya kalleta sai ya ganta da tulu saman kai ga kan maciji ya leko, mutane sai gudu suke, kamin ta isa gida har ta canja kammani.
鈥淏appppa wayyo Inna na bani na taro aljalina鈥�
Ta kasa tashi tsaye gani ba take idan ta mike macijin zai iya saukowa, mutane aka fara taruwa ana kallonta tai zaure a kasa sai rusar kuka take fuska duk da bace da majina da hawaye zuciya kuma kamar ta fashe dan tsoro, ita gaba daya bata dauka ma da gaske yana iya yin tsafi ba sai yanzu.
鈥淢ike tsaye ki zafar da tulun鈥�
Kowa abun da yake fada kenan, ita kuma babu kuzarin mikewar tsaye gashi yace mata idan bata isa gida bata sauke zai cijeta.
鈥淵ace sai na kai shi gida, ku dauke ni ku kai ni gida, wayyo Bapppaa na wayyo Bapppaa鈥�
Ta fada tana ta yarfe hannu, idonta har ya kumbura saboda kuka.
FALMATA POV.
Da tunani kala biyu Falmata ta isa gida, tunanin saukin kai da jindadin kadeta da M2 yai ga kuma kiranta da Ammy tai ta mata tambayoyi, ko miyasa tai mata haka oho. Sosai ta so ta biya ta gidansu kawarta Khadija ta labarta mata yadda ta ga M2 sai ta tuna da Baba ya mata iyaka da gidan. Hakan yasa tai hanzarin cira kafa ta isa gida, da zimmar ta gama aikinta dan ta samu isa Islamiya da wuri ta labarta musu. Ko da ta isa gida har Gambo ta sanar da sakon Ammy ta bar gidan dan ita abun hawa ta hau ba kamar Falmata ba da take tafiya a kafa.
Falmata na isa ta manta da wani kunci da tsoron fada ko wani abu, ta hau bawa Naja labarin yadda ta ga M2.
鈥淒an Allah matsa can mahaukaciya, hala M2 ne banza da zaki ganshi a bagas, sannu kakar farin jini, dan kin ji ana cewa kina da farinjini shine kike wani karya kin ga M2 mahaukaciya鈥�
Ko kadan bata ji abun da Naja ta fada ba, amman a yanayin yadda take harararta take jan tsaki tasan karyarta tayi, hakan yasa Falmata ta kara boye hular da ya bata a cikin jikinta ta mike tsaye cikin rashin jindadi ta nufi dakinsu. Tumba dake zaune bakin kofar dakinta ta bushe da dariya.
鈥淲allahi yarinyar can ta fara haukacewa, mugun son M2 da take ne yasa ta fara ganin mutane na zame mata haka鈥�
Naja ta ja tsaki.
鈥淜o mai wankewa M2 takalmi ta isa ta gani balle M2, ita fa yadda ake fadar tana da farin jinin nan wani jin kanta take鈥�
鈥淜ira min ita鈥�
Tumba ta fada tana dariya, daga inda Naja take zaune ta kwala mata kira.
鈥淜e kurma zo ana kiranki鈥�
Falmata har cikin ranta ta ji sunan, wani abu na rashin jindadi ya ratsa zuciyarta, ta saka hular M2 can ciki bakkon kayanta sannan ta fito ta tsaya bakin kofa jiki ba gwari tun da babu wani abincin kirki a ciki.
鈥淜e yar kurma, dazun Gambo ta zo tace zaki rika wuni can kina rainon yara鈥�
Tumba ta fada mata tana mata alama irin na kurame. Naja ta saka dariya.
鈥淏an cin kurmanta har da hauka na son kamaki, kin fara ganin mutane kina ce musu M2 ko?鈥�
A nan ma Tumba ta saka mata dariya, a gurin Falmata ta duka ta fashe da kuka, ba karyatata da suke take ji ma ciwo ba, kiran da kurma da suke a yanzu.
鈥淛i munafuka salon a shigo ace wani abu Umma tai miki kike kuka mu kuke dariya ko? Da shegen baki kamar zunubi鈥�
Naja ta fada cikin tsawa, sai Falmata ta mike tsaye ta shige dakinsu ta cigaba da kuka tana rufe bakinta dan kar sautin kukanta ya fito.
Sai da tai mai isarta sannan ta fito ta zuba surfe ta fara, sai da ta surfe tiya da rabi sannan ta shiga tai wanka ta saka uniform dinta na Islamiya ta dauko qur'ane ta da littafai ta fice.
Kusan kullum cikin rashin jindadi taje zuwa makaranta, saboda rashin jin da take a yanzu, idan akai karatu sai Khadija ko wata ta rada mata abun da Malam ya fada a kunne sannan ta ji, sai kuma idan Malamin yayi da karfi, Falmata ba yarinya ce mai yawan surutu ba, amman hakan be hanata fadawa yan ajin su cewar ta hadu da M2 ba, most of them sun karyatata wasu na fadin dan dai tana son shi sosai ne yasa ta ga mai kama da shi.
Haka dai ta bar Islamiya cikin rashin jindadin yadda suka karyarta daman ta san ba za su yarda ba, ita ma dai a lokacin ta fara kwankwanto da gaske M2 ta gani ko mai kama da shi?
Ko da ta iso gida sai ta tararda wani tashin hankali, yaron da aka aiko yana tsaye yana jiran dawowarta Tumba kuma ta yi wani shegen zama tana rawa da kafa. Ta shigo da sallama Tumba ta hau ta da matsifa.
鈥淎she Falmata zuwa kike kina cin bashin garin kwaki a shago da sunana?鈥�
Dakan shida-shida gabana yai, ta sani yau asirinta ya tonu, tabbas tana zuwa karba kuma idan ta je Tumba take cewa saboda tana jin kunyar tace ita zai bawa bashin gari.
鈥淪aboda asan ba a baki abinci ko kuma dan ki bata min suna ni da ubanki? To ya aiko yace a bashi kudinshi bari ubanki ya dawo sai kin fadi dalilinki na bata min suna鈥�
Kamar an tureta haka ta fadi gaban Tumba kamar mai neman gafara hawaye sai sallama suke a fuskarta.
鈥淒an Allah dan darajar Annabi karki fadawa Baba Umma, ki rufa min asiri, zan samu kudinsa yanzu na bashi, ki yi hakuri Umma ba zan, idan na sake ki kashe ni, Umma wallahi yunwa take damuna shiyasa na ci bashin amman daga yanzu ko zan mutu ba zan sake ba, na rantse da Allah Umma, dan manzon Rahama ki rufa min asiri Umma ba zan sake ba har abada鈥�
Tumba ta fisge kafarta tana kallon.
鈥淭afi idan Babanta ya dawo za a fada masa鈥�
Yaron ya juya ya fice, sai Falmata ta mike tsaye da sauri.
鈥淣a bani na lalace na shiga uku wayyo ni Allah na Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un鈥�
Ta furta ta karfi kuka na subuce mata, sai ta saka hannunta da sauri ta rufe bakinta, da gudu ta shiga dakinsu ta fada kan shimfidar da take kwana.
鈥淲ayyo ni Allah na yau asiri na ya bonu, wayyo Mama Mama ina ma ni na mutu ba ke ba, Allah ka karbi raina kamin Baba ya dawo Allah na shiga uku鈥�
Ta fada tana yarfe hannunta hawaye sai zubo mata suke kamar ba gobe.
ZAINAB POV.
Ta dan yi shiru sannan tace.
鈥淣a ce mishi ya bari har na dawo daga tafiyar da zan yi鈥�
Ammy ta kalleta.
鈥淣i fa ina tsoron lafiyar nan Zainab, kin san kasar ba wani tsoro kuma ki ce za ki je garin cikin mutanen da ake fadar basa saka tufafi? Kina ganin ma za su aminta ki dauke su hoto ne?鈥�
鈥淣o ba wai kai tsaye zanje can ba, zan sauka garin dake kusa da su ne, nai magana da mutanen tukuna sai na isa garin, kuma ko ban samu zuwa can ba ai ance akwai manyan duwatsu a kusa da su da ruwa, kuma ance akwai Fulani irin masu yin bukka da gidan zana su zauna a kusa da su, ko da ban samu isa can ba na san ba zan sara abun dauka ba鈥�
鈥淭o Allah dai ya tsare鈥�
鈥淎min, Ammy dan Allah ki mata magana, ban zan abun da mutunen nan yai mata ba, ta ki ta saurare ni, ni kuma ina son shi, shi yanzu yace yana son ya turo kuma ya sanar a gidansu amman sai ya samu tabbaci daga gareni鈥�
Ammy ta yi murmushi.
鈥淜arki samu damuwa, zan yi magana da ita, idan ta aminta sai a sanarwa yan'uwan mahaifinki鈥�
鈥淣a gode Ammy鈥�
Mikewa tai tsaye tana sanye da riga da wando English wears, kanta sanye da dankwalin nan da ake yayi blue.
鈥淏ari na duba dakinta idan tana nan sai na turo miki ita鈥�
Kai kawai Ammy ta daga mata, ta maida dubanta gurin tv dake dakinta, kallon kawai take amman hankalinta baya can, bata da damuwar da ta wuce ta Mai Martaba a yanzu, a iya tunaninta ta rasa gane abun da yake damunsa, gashi idan an gwada yi masa na hausa sai abu ya karu a maimakon raguwa. Kiran wayarta nd ya katse mata tunanin da take, sai ta mika hannu ta dauka.
鈥淎ssalamu Alaikum鈥�
Ra'ees ya amsa daga dayan bangaren.
鈥淲a'alaiki-Assalam, Ammy barka da yamma鈥�
鈥淵auwa Ra'ees ya gida鈥�
Ta fada cike da kasaitar da ta zame mata jiki.
鈥淎l-hamdulillah Ammy an samu wata, amman dai ba mu je, sai dai marikiyar yarinyar tace zata iya aura masa ita鈥�
鈥淜a fada mata matsalar sa ne?鈥�
鈥淓h ta ji komai, firar ma ta ji muna yi shine tace tana da 拼a zata ba shi, amman dai ba mu je ba tukuna鈥�
鈥淭o yayi kyau, amman fa ba sai kun bayyana dan wane ba, kuma ka yi duk abun da ya dace, karka bari Shattima ya ji komai, sai an kammala yadda ba zai iya ce mana aa ba鈥�
鈥淚n-Sha-Allah Ammy鈥�
鈥淣a gode Allah ya maka albarka鈥�
鈥淎meen鈥�
Tana kokarin aje wayar aka kwankwaso kofar dakin kamin a turo a shigo. Hajiya Balki ce Nana na biye da ita a baya, a baki kofa ta tsaya tana kallon Ammy sai cika take tana batsewa.
鈥淵anzu an kyauta kenan? Sai a dauke yarinya akaita gurin Waziri bayan kin san ita da Waziri ba jituwa suke ba?鈥�
Ammy ta kalleta da mamaki kamar ba zata ce komai ba.
鈥淎n kaita gidan Waziri kamar wacce aka kai gidan yari? Kanen ubanta ne fa鈥�
鈥淣a san kanen ubanta ne ai, amman tun da bata son zuwa ai sai a kyaleta鈥�
Ammy ta dauke kai bata sake ce mata komai ba. Ganin hakan yasa ta juya ta fita Nana kuma ta zauna saman kujera tana matsar yatsun hannunta tana kallon Ammy. Ko da wasa Ammy bata kalle inda take ba har ta gaji dan kanta tace.
鈥淚'm sorry鈥�
Ammy ta watsa mata wani mugun harara.
鈥淒akinki dai kike so ko? To gashi can idan kin mutu a haka rame a saka ki a ciki, tashi ki fata鈥�
鈥淎mmy ki yi hakuri....鈥�
Bata karasa ba Ammy ta daka mata tsawa.
鈥淕et out鈥�
Ba shiri ta mike tsaye jikinta na rawa ta fice daga dakin tana fashewa da kuka.
_________________
Al-hamdulillah, a nan na kawo karshen free pages, duk mai son cigaban wannan labarin ya biya 300. Pages din da za su biyo bayan wannan na kudi ne ba kyauta ba, ko kun ganshi a waje na sata ne.
Patronize me if ku masoyana ne na gaskiya, show me that love.
Son so Fisabilillah.
*FULANI -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence to 08036126660 拼an nijar za ku tura 500cf to +22790165991*
Wadanda ba su account za su iya turo mtn card ta 08036126660 bana karbar transfer.
03/12/2021, 09:20 - 馃馃馃馃: A gaban wani madaidacin gate ya faka motar, budurwar ta bude ta fita sannan ta budewa Falmata tana mata alama da ta fito.
Cikin rashin kuzari Falmata ta sako da kafafuwanta sannan ta fito daga motar tana jin sanyin ace motar na saukar mata da mura, sai kokarin boye ledar hannunta take tana karewa na unguwar kallo, ba unguwar masu kudi bace haka kuma ba za a kirata da unguwar talakawa ba, irin unguwar nan ce mai kama da sabuwar unguwa wance mutane ba su gama dawowa ba, domin akwai gine gine da yawa da ba a karasa ba, ga kuma ciyawa da tai yawa a ko'ina, tsakanin wani gidan da wani kuma akwa tazara mai tsawo ta filayen wasu mutane. Hannu ta saka a jakarta ta ciro makulli tana kikarin sakawa sai gate din ya bude, ta dan bude ido da far'a sannan ta tura ta shiga.
鈥淪higo鈥�
Bayan Falmata ta shiga ta rufe kofar gate din, arba da tai da wata hadaddiyar mota yasa murmushin fuskarta ya kara fadada da sauri ta nufi entrance har tana hadawa da gudu, hakan kuma ba karamin tsoro ya ba Falmata ba, tana a wani gari da ba na ta ba, a wata unguwa kuma a sabon gida da matar da bata sani ba.
鈥淜araso mana ko kina jin tsoro ne?鈥�
Matar ta fada ganin Falmata ta tsaya daga can kusa da gate din tana karewa madaidacin gida kallo. Sai da ta tura kofar falon sannan Falmata ta karaso kusa da ita
鈥淪higa鈥�
Cikin tsoro da fargaba ta nasa kafarta a cikin falon, bayan ita ma ta shiga ta maida kofar ta rufe.
鈥淶auna a nan鈥�
Ta nuna mata kujera, cikin rashin natsuwa ta zauna saman kujerar dake kusa da kofa.
鈥淢ansura daga ina kike?鈥�
Budurwar ta juyo da sauri tana kallon kofar kitchen din. Sirleem ne tsaye jikin kofar rike da gorar ruwa yana kallonta. Cikin murna ta karasa kusa da shi ta rumgume shi.
鈥淥yoyo ban taba expecting zaka zo yau ba, what a surprise鈥�
Ya dan kawar da fuskarsa daga kiss din da take kokarin yi masa yana kallon Falmata,聽 juyawa ta yi ta kalleta sannan ta sake kallonsa tana kokarin kai hannu ta taba sajen fuskarsa, sai ya rike hannunta ya tureta gefe ya dawo falo ya zauna.
鈥淣a hadu da ita ne a tasha, an kawo min sako daga kano shi ne na je karba sai na hadu da ita, tun cikin tasha tana kuka har waje da na tambaye ta sai tace bata san kowa ba a nan gudowa tai鈥�
Tun da ta fara maganar yake kallon Falmata yana jin kamar ya taba ganin fuskarta but zai iya tuna a ina ba ne. Ya kalleta a natse irin kallon da ita ta san me yake nufi. Sai ta nufo shi tana cire Veil din kanta.
鈥淵ou know idan na ga mutum a damuwa ina son na taimaka masa, because ni ma na taba shiga a irin wannan matsalar鈥�
Ya sake kallon Falmata da tai mutuwar tsaye tana kallonsa. Shi din ne ko kum har yanzu idonta gizo yake mata? Ko kuma masu kama da shi ne take gani? Ai ta baro yola ya akai ta ganshi a nan?
鈥淢e yasa ta gudu daga gidansu?鈥�
Ta zauna daf tashi har jikinta na gogar nashi.
鈥淵a za a yi na sani yanzu yanzu fa na hadu da ita ban tambaye ta ba鈥�
鈥淎nd kika bata masauki, what if karya take? Kika san abun da ya rabota da gidan?鈥�
鈥淏an sani ba, amman zan sauketa a nan zata zauna tare da ni, tana bukatar taimako鈥�
鈥淭his is my own house not yours, hope kin san da wannan?鈥�
鈥淎nd that mean?鈥�
鈥淏a zata zauna a nan ba鈥�
Ya fada mata kai tsaye yana kallon cikin idonta, fuskarsa babu annuri.
鈥淔ine idan baka son ta zauna tare da mu, zan sallame ta, amman rayuwarta zata iya fadawa a hadari ka sani鈥�
Ya mike tsaye yana shafa kansa.
鈥淚dan rayuwarta ta fada a hadari ina ruwanki? Kin santa ne? Idan kina tsoron ta fada a hadari then take her to her parents house鈥�
鈥淎mman ka san abun da yasa ta baro gidansu? Duk ba mu sani ba bata son zama kusa da kowa na ta that's why she run鈥�
鈥淜in fi kowa sanin hali da mace take fadawa idan ta rubu da iyayenta, uhmmm?鈥�
Ta yi shiru tana kallonshi.
鈥淟okacin da kika gudo daga gidan iyayenki da kika fada mugun hannu ba karuwanci kika fara ba? So on kika bata future dinki that's why Hajiya ta hana na aureki, kowa kallon karuwa yake miki kina son ki koma cikin familynki kin saka saboda kin lalata alakarki da su, look at her bata wuce 15 ba, and if you want to help her take her back to her parent house鈥�
Hawaye ne masu zafi suka fara sauko mata, ta kalli Falmata a tsawa ce tace.
鈥淜e tashi ki fita鈥�
Falmata ta kasa motsi balle ta mike tsaye ta fita kamar yadda ta umarta, bata ji duka kalmansu ba amman ta ji wannan tsawar kuma ta ji turancin da Sirleem yai mata a karshen maganarsa da ya karasa a fusace, and now hawaye Mansura take, hakan na nufin matsala ta samu da mijinta a dalilinta.
鈥淎s how? Ki kawo ta unguwar da bata san kowa ba kuma ki ce ta tashi ta tafi idan aka tambaye ina ta fito tace a nan gidan ko?鈥�
鈥淭o ya kake son nai mata?鈥�
Ta fada a tsawace tana hawaye, tass ya wanke mata fuska da mari.
鈥淗ow dare you, dan ina son ki ba shi zai baki damar yin duk abunda kike so da ni ba, kamar yadda so na be hanaki kula wasu mazan ba鈥�
Sai a yanzu ta gane fushinsa ba na shigowa da Falmata kawai ne ba, har na fitar da tai da Yasir, durkushewa tai a gurin ta fashe da kuka. Falmata dake rike da fuskarta sakamakon marin da akai wa Mansura ta mike tsaye ta sauri ta nufi kofa.
鈥淜e....鈥�
Ya kirata a watsawa sai ta juyo jikinta na rawa ta fashe masa da kuka tana girgiza kai. Kallonta kawai yake kamin ya nuna mata kujera alamar ta zauna, sai ta dawo kusa da kujerar ta zauna a kasa tana hawaye. Ganin tana ta boyon hannu a hijab ga hawaye sai sauko mata suke yasa ya nufo inda take sai ta kara fashewa da kuka tana bashi hakuri.
鈥淒an Allah kai hakuri, dan Allah karka min komai鈥�
Hannunsa ya kai ya daga hijabinta sai ta mike tsaye tai saurin sakin ledar hannunta shinkafar dake ciki ta fadi kasa. Kallon shimkafar yai kamin ya sake kallonta da fuskar dake nuna alamar ba wani abun zai mata ba, cikin tattausan lafazi ya ce.
鈥淒aga ina kike?鈥�
Bakinsa kawai take kallo kamin ta kalli fuskarsa da kwarjininsa ya cika mata ido.
鈥淏ana ji sosai sai an yi kusa da kunnena ko an fada sosai鈥�
Kallonta kawai yake for no reason, kamin ya kai hannanyensa ya dafa kafadarta ya zaunar da ita saman kujerar.
鈥淵a zaka taba ta, ina ruwanka da ita鈥�
Ta fada tana mikewa tsaye ta nufo inda yake tsaye kusa da Falmata. Dan murmushi yai irin murmushin nan na mamaki daman ya san za tai magana, saboda Mansura tana kishinsa ko sunan wata macen ya fadi a gabanta sai ta nuna kishinta, amman ita ta kasa tsare masa kanta duk kuwa da irin kudirin da yake da shi na aurenta.
聽
Falmata ta kalleta a tsorace gaba daya ta firgice ta rasa gane kansu yanzu, gashi ba komai take ta ji ba. Juyowa Sirleem yai ya kalleta sai ya nuna mata kofa alamar ta tashi ta fita, sannan ya juyo ya kalli Mansura.
鈥淢e yake damunki ne Mansura?鈥�
鈥淜ai ba ka ga abun da kake ba?鈥�
Be ce nata komai ba ya hade rai ya fara bin bayan Falmata sai ta riko rigarsa.
鈥淚na zaka je? Ina zaka kaita?鈥�
鈥淏a zan ga wata mace zata aikata irin abunda kika aikata ba na kyaleta, sake min riga鈥�
Ta saki ba dan ta so ba, sai dan ya karasa a tsawace yana kara hade rai kamar be taba dariya ba. A kujerar ta Falmata ta tashi Mansura ta zauna ta hade kai da hannu tana hawaye wani irin abu take ji a zuciyarta yana taso mata, ta san waye Sirleem bayan ita baya mu'amala da ko wace mace amman tana kishin ganinsa da mace ki da ko yar'uwarsa ce. And the most annoying part is duk abunda za tai ba zai saurareta ba a yanzu saboda ta fita tare da Yasir, da ace a gida tararda da ita, to zai saurari duk kalar haukar da zata masa saboda yana sonta shi ma.
Ya sauka entrance din yana kallon Falmata da ta kusa isa gate tana waigensa, motarsa ya shiga yai warming dinta sannan yai reverse ya isa gate din da Falmata ta kasa budewa, fitowa yai daga motar ya zagaya ta dayan bangaren ya bude mata front seat, da hannu yai mata alama da ta zo sai kawai ta fashe da kuka ta dukushe a gurin tana girgiza masa kai.
鈥淏a wani abun zan miki ba鈥�
Ya fada cikin daga murya, sai dai ba irin muryar da zata ji ta tsorata ba, ni ta yadda zata ji shi.
鈥淎a bana so鈥�
Ta fada hawaye na sauko mata, tana jin wata sabuwar nadama da dasani na barin garinsu da gidansu da ke cike da kuncin rayuwa, gaba daya ta tattara zancen da tunanin Sirleem ne ki ba shi ba ta aje a gurin daya, ta rayuwarta take. Ya rufe motar ya karasa inda ya risina yana kallon fuskarta da tsoro ya gama bayyana a kammaninta.
Dark skin dinta sai shining take duk da kasancewar kana ganinta kasan rayuwar wahala take, ga golden eyes dinta masu haske da take ta kallonsa da su. Kallonta kawai yake zuciyarsa na raya masa ya santa amman a ina? The first thing daya kamata yai shi shine ya gusar da tsoronsa da take ji a yanzu, ya kara matasawa kusa da ita sosai kamar zai tabe ta.
鈥淜in san ni?鈥�
Ya rada mata da a kunne. Sai ta yi shiru tana ta kallon fuskarsa da sajensa da ya karawa fuskar kyau. Bata son tace eh ko aa tun da bata da tabbacin shi din ne Sirleem ko waninsa? Ko kuma gizo idonta ke mata.
鈥淜in taba jin wani Sirleem M2 mai waka? Ko ganinsa ko da a hoto ne?鈥�
Nan ma shiru tai sai dai ta dan bude ido alamar wani abu ya zo a tunaninta. Ya dan kalli kofar falon sannan ya sake kallonta ya kai bakinsa kunnenta.
鈥淜in san shi?鈥�
Ya gyada kai sai ya saka mata murmushi ya nuna kansa. Da wani irin karfi zuciyarta ta fara bugawa tana kallonsa.
鈥淛i nake kamar na sanki a ina na sanki?鈥�
Kallonta take kamar ba zata ce komai ba, a yanzu ba kallon tsoro take masa ba na mamaki da tunani.
鈥淜a taba kade ni a mota鈥�
Yayi shiru yana nazari, sai ya sake sakar mata murmushi.
鈥淵eah few days back ko? Har na baki fula? Amman ai a Yola ne鈥�
Ta daga masa kai ba dan ta san abun da yake nufi da few days din ba, sai dan karasa mata maganar da yai da zancen bata fula ta kara tabbatar da shi din ne ba tantama. Sai ya dan bude ido yana kallon kyakkyawar fuskarta.
鈥淗akan na nufin ke yar garin mu ce鈥�
Ta sake gyada kai tana nuna shi.
鈥淒a gaske kai ne?鈥�
鈥淣i ne mana鈥�
Ya fada yana daga mata kai ba dan yana da tabbacin zata ji ba, tun da ta fada masa bata ji sosai kuma ya ga zahiri sai dai daga mata kan da yai ya isar da sakonsa. Da sauri ta mike tsaye tana masa wani irin kallo kamar ta hade shi, ga wani shauki da mamakin sake ganinsa da tai yana cikata. Sai shi ma ya mike tsaye yana kallonta da murmushi a fuskarsa.
鈥淚na son ka sosai, ina yawan sauraren wakokinka lokacin da ina ji, ina son ka sosai kana burgewa ban taba mafarkin zan hadu da kai ba, kuma ban sake saka ran zan sake ganinka ina son ka sosai鈥�
Ta karasa muryarta na rawa idonta kuma yana cika da kwalla irin na fan ya hadu da celebrity.
鈥淲ow鈥�
Ya fada still yana murmushi kamin ya kama hannunta.
鈥淶o muje鈥�
Ba musu ya bishi yana rike da hannunta idonta suna kan fuskarsa, har ya zagaya da ita ya bude motar ya saka ta gidan gaba shi take kallo ji take kamar a mafarki ne. Rufe motar yai sannan ya je ya bude gate din ya dawo cikin motar yaja suka fita ya sake rufewa ya dawo ya rufe gate din sannan ya dawo cikin motar yaja suka fara tafiya.
Bata kallon komai sai fuskarsa wani abu mai kama da jindadi yana ratsata zuciyarta kamar zata fito waje akan bugawar da take da karfi, time to time yake kallonta sai ya dan sakar mata murmushi har suka isa wata kyakkyawar unguwar da tafi kama da GRA.
Horn yai ba bata lokaci aka bude masa katon gate din, sai da ya kalleta sannan ya ja motar suka shiga cikin katon gidan. Gaban entrance ya faka motarsa ya bude ya fita sannan ya zagayo ya bude mata ba tare da yace komai ba, ita ma din bata jira yace ba ya sauko da kafafuwanta ta fito. Kato gida ne mai kyau gaske an kawata ko'ina da flowers an masa kwaliyar zamani gwanin burgewa.
聽 Hannunta ya rika ya fara takawa tana biye da shi har yasa key ya bude kofar ya shiga tare da ita. Tsaye tai bakin kofa ganin babu alamar mace tana rayuwa a cikin gidan, sai ya juyo ya kalleta, hakan ya bata damar janye hannunta daga rikon da yai mata. Sai ya dawo kusa da ita ya tsaya ita kuma ta daga kai tana kallonshi, ko bata fada masa ba ya san abun da take nufi wanda hakan kuma ba halinsa ba ne, ko ma halinsa ne shi me zai yi da teenager irinta. Yana kokarin yi mata magana wayarsa tai ringing, ciro wayar daga aljihun wandonsa ganin sunan Hajiya yasa shi daga kai masa ya sauke sannan yai picking.
鈥淪irleem ban isa da kai ba ne? Ban isa na maka magana ka ji ba?鈥�
鈥淗ajiya i swear to the seven heaven zan dawo gobe, ba gurin Mansura na je ba, wani aiki ya kai ni鈥�
鈥淣a ai dai fada maka karka wuce yau ko gobe, wato mallakar da take maka ta fara yawa har zaka bar garin Yola kaje gurinta ba tare da ka sanar da ni ba ko?鈥�
Yayi shiru dan be san abunda zai ce mata ba kuma.
鈥淭o ya maka kyau ka cigaba da abun da kake karka fasa, taya dan albarka zai kula yarinyar da mahaifiyarsa bata so? Ka cigaba karka fasa鈥�
Kit ta kashe wayar cike da fusata, sai ya sauke ajiyar zuciya ya busar da iskar bakinsa ya kalli Falmata.
鈥淜e ma mamarki na miki fada kamar ni?鈥�
Ya rada mata a kunne, sai ta girgiza masa kai.
鈥淣i ba ni da Mama, Mamata ta rasu鈥�
鈥淎yyyah... 鈥�
Ya fada yana kallonta cike da tausayi, sannan ya cire talkamin kafarsa ya karasa cikin falon sai kuma ya juyo ya kalleta ya dago mata hannu.
鈥淜araso mana鈥�
Ta girgiza masa kai.
鈥淟ook ni ba wani abu zan miki ba, za ki kwana nan ne gobe sai na maida ke gida鈥�
Ya fada da muryar da zata ji yana ware hannayensa, sai tai saurin girgiza masa kai.
鈥淎 a ni ba zan koma ba, idan na koma Babana yanke ni zai yi鈥�
鈥淭o shigo ki zauna鈥�
A hankali ta fara takawa har ta iso cikin falon, ya nuna mata kujera sannan ya dauko remote ya kunna plasma dake falon, ya nuna mata wasu dakunan dake facing inda plasma take.
鈥淜in ga daki can idan zaki yi alwala da sallah ko fitsari, kuma a can zaki kwana, ni zan je masallaci yanzu鈥�
Yana fadar hakan ya nufi hanyar fita, gaba sai tsoro ya kamata gidan ya mata girma ita kadai kuma tana ji a jiknta be kamata ta kebi da namiji duk kuwa da bata da tabbacin zai mata wata illar ko akasin haka. Sai da taji kara rufe kofar ta kara raina kanta sai ta zauna kusa da kujerar ta fara kuka a hankali tana tuna gidan, no matter irin wahalan da yake sha ta fi sakewa a can fiye da wani gurin, a yanzu ta kara nadamar guduwa da tai, tunawa da yace zai maida ta gida. Har yai sallah ya dawo tana nan a inda ya barta banbanci dazun da yanzu shine a yanzu rabe take jikin kujera tsakanin dazun da ya fita ya barta a tsaye. Be ce mata komai ba ya karasa inda take zaune ya rika hannunta ta mike tsaye sai ya nufi dayan dakin da ita.
鈥淒an Allah karka min komai dan Allah ka rufa min asiri鈥�
鈥淲aya fada miki idan na kebe da mace iskanci nake wai? Me zan yi da ke?鈥�
Ya fada a tsawace duk ta wani hada mishi zafi, ga fadan da Hajiya take da shi ga fitar da Mansura tai da Yasir yanzu kuma tana son kara masa wani ciwon kan. Ba shiri Falmata ta sha jinin jikinta.
鈥淲uce kije ki yi sallah na ce鈥�
Ya daka mata tsawa, da sauri ta wuce ta shiga dakin mai kama da na mata, an tsara komai an jera furniture ga wani kyakkyawan zanin zago an shimfida. After ta shiga ya karasa shiga ya kunna ac ya karasa gaban windows din ya dage labulayen sannan ya bude mata kofar bathroom. Ba tare da yace mata komai ba ya juya ya fice ya sakawa dakin key daga waje.
Zaunawa tai a kasa tana hawaye tana kallon dakin da bata taba mafarki wata rana zata kwana a irinsa ba, sai da ta ji ana kiran sallah isha'i sannan ta tashi ta shiga bandakin, sai ta rasa yadda zata kunna fanfon dan domin bata saba ganin irinsa ba bata taba amfani da irinsa ba. Har ta juya zata fita sai kuma ta dawo ta kai hannunta ta murda sai ta ga ruwa ya fara sauka.
Fisari ta fara yi sannan tai alwala ta kuma tara hannunta ta sha ruwan ta fito. Dankwalin da ke kanta ta cire ta shimfida ta fara rama sallolin da ake binta sannan ta gabatar da isha'i.
FADIME POV.
sai kusan magariba Fadime ta farka, gaba daya mafarkinta na abun da ya faru ne, duk mutumen dake shigowa suna Allah kyauta sai dai su ganta tsakar gidan tana sharar bachin wahala. Amo na aiki tana kallon Fadime da tunani kala kala wasu ranta, ita kanta a yanzu ta yarda Fadime ta hadu da iska da suka fi nata karfi to ga zahiri ta gani, bayan nan kuma ga wutar da ta saka mata an cire mata. Jin tai yatsanta na zafi kamar wutar, wanda hakan ke nuna alamar a cikin kuryoyin da take ajiya akwai wacce masu ita suka matsanta da addu'a da kuma neman taimako, kwayar da ke hannunta ta aje ta tashi daga gaban murhun ta nufi dakinta. Dukawa tai karkashin gado tsobuwar kwaryar da take ajiya a ciki ta bude ta dauko wani abu mai kama da laya tana dubawa, sai jin zafin tai yana shiga har cikin kanta, kan ta ankaro ta soma ganin daki na juya mata sai zafin ya game ilahirin jikinta, can cikin kanta ta soma jin wasu muryoyi na kiranta duk da bata san inda kiran ke fitowa ba amman sai son tafiya take. Da sauri ta fito waje ta nufi bandaki ta warware zaren ta daga yar tsokar marar kyau ganin a sama ta wurga iya karfinta, a maimakon ta fadi kasa ko ta fada wani guri sai ta zama yar tantaba yar karama tai sama sosai zuwa ga mai ita.
Daga ita sai ire-irenta suke iya ganin kurwar da ta kakareta ci.
Masai ta bude ta jefar da zaren ta fito tana jin wata rahama na sauko mata.
鈥楲allai wannan kurwa ba ta ci ba ce鈥�
Ta fada a ranta, a fili kuma maganin da Inna ta aje gaban Fadime take kallo, tana ganin Inna ta shige daki tai saurin isa gaban Fadime ta saka hannunta tana taba ganin, ba karamin dadi ta ji ba na samun sa'ar lalata aikinsa, daman can idan maye ya taba magani baya aiki komai aikinsa kuwa musamman idan na maganin mayu ne.
鈥淪ha za ki yi Fulani?鈥�
鈥淓h maganin mayu ne Inna tace min鈥�
鈥淎i wlh kam sun yi yawa yanzu ko'ina Allah dai ya kyauta鈥�
Ya mike tsaye ta karasa gaban murhu ta gyara wutar, sannan ta koma dakinta ta dauko hijabi mai kaloli ta saka ta fice da sauri daga gidan.
Bata yada zango a ko'ina ba sai gidan aminiyarta Lami, tana yi sallama Lami taja ta sukai cikin bukkarta dan kar kowa yaji abunda za su fada.
鈥淟ahiya kike kau Amo鈥�
鈥淚na lahiya Lami, kurwa nan da nace zan sai da miki na sake ta yau?鈥�
鈥淪aboda me?鈥�
鈥淲allahi ina zaune na fara jin wuta da azaba, daga gani gurin wani babban malami suka kaita, dan har kirana yake, da asiri ya tonu ai kara na sakar musu kurwar 拼a鈥�
鈥淜ai kiken Amo baki da juriya Wallahi, ai da kin gwada rikewa ki gani, ba a saurin saki fa yanzu, ko kuma ki sassauta mata daurin ta samu lahiya suna barin gurin mai magani ki kawo min ita na yanke shegiya鈥�
鈥淭o nikam na sani, ke ai kika maida abun wasa da kin bani kudi da yanzu na siyar miki ita, kuma Wallahi mai garita, daurin da na mata har wani naso take鈥�
鈥淎ikin gama ya gama tun da kin sake, amman Wallahi da kin sha kudi, kuma irin wannan cikin ruwa zaki ajenta saboda mai kitse kin san bata son zafi in dai ba yankawa za ayi ba, saboda gudun irin haka, kila kin aje ta guri mai zafi azaba ta yi ma macce yawa dole aje neman magani鈥�
鈥淎a Wallahi cikin kwarya na aje ta, ni yanzu damuwa ta Fulani ce, an cire mata wuta?鈥�
Lami ta rike baki.
鈥淒azun aka kawo min labari wai anganta da kan maciji鈥�
A nan Amo ta kwashe labarin duk abunda ya faru ta fada mata.
鈥淭o ai ba gajiya ake ba, ki sake aika mata wutar idan kuma kika samu sa'a ki kame kurwar daddake mata kai hankali ya juye鈥�
鈥淎i in bata ciwo gareni ba zata mutu, dan na samo mata wani miji mai kashe mata, ance duk mace da ta aureshi sai ta mutu ina tunanin shi ma maitar yake amman ta sayarwa dan ance kudi gareshi sosai, kin san masu saidawa sun fi arziki ba kamar mu ba鈥�
鈥淎 ina? Kuma?鈥�
A nan bata kowaye amiyar ta ta komai ba.
鈥淏ari na yi sauri na koma na bar girki kan wuta鈥�
鈥淭o ko kam kar Malam Jaure ya dawo ya fara nemanki, bari sai dare mu hade gurin rawa鈥�
鈥淎 a yau ba ni fita tun da dakina yake, sai jibi鈥�
Daga haka tai mata sallama ta dawo gidan a guje, ta shige cikin daki ta cire hijabin ta aje ta fito waje tana kallon kofin maganin da Fadime ta sha magani da shi. ta san ta sha ne kawai amman ba zai mata aiki ba tun da saka masa hannu.
Bayan sallah magariba Bappa ya shigo shi da wani abokinsa Malam Isuhu Inna ta shimfida musu tabarma aka kira Fadime ta fito daga bukkar Inna bayan ta kare sallah magariba ta zauna saman tabarmar.
鈥淜ina da alwala?鈥�
鈥淓h yanzu nai sallah鈥�
Ta amsa tana kallon wata doguwar takadar da Malam Isuhu yake budewa.
鈥淭o Malam Bissimillah鈥�
Malam Isuhu ya matso kusa da ita ya haska fitilarsa yana ya fara karanta mata ayoyin kona aljanu, tun da aka fara karatun Fadime take zaune guri daya tana saurare, idan ya karanta ya karanta sai yace
鈥淲anene?鈥�
Sai Fadime tace
鈥淣i ce Fulani鈥�
Tun yana yi yana tsayawa ya tambaye ta har ya gaji ya daina sai karatun kawai yake mata, da Fadime ta ga abun nasa ba mai karewa ba ne sai ta fara lankwashewa tana burkice ido kamar da gaske aljannu ne suka zo.
鈥淢una aljanu gamu nan mun zo, mu ne鈥�
鈥淜u suwa?鈥�
鈥淢u aljanu鈥�
鈥淢iye sunanka?鈥�
Ta dan yi shiru tana tunanin sunan da zata fada, can kuma ta fadi sunan Bappa.
鈥淪unana Sama'ila鈥�
鈥淢iyasa kika shiga jikinta?鈥�
Mutumen ya tambaya.
鈥淪aboda.....saboda... Muna son mu bada magani鈥�
鈥淎 ina kuka hadu da ita鈥�
鈥淎 daji..... 鈥�
鈥淭o ku fita daga jikinta ko na kona ku鈥�
鈥淏a zamu fita ba鈥�
Ta fada tana ta mulmula a kasa kamar wata mai aljanun gaske, sai mutumen ya cigaba da karatunsa da nufin kona su, Bappa kuma ya shiga dakinsa ya dauko bulalar dorina ya shada mata, a take tai saurin tashi ta zuba da gudu zuwa wajen shanun da suke gidan.
鈥淢un fita ba zamu sake dawowa ba鈥�
Malamin yace.
鈥淜arya suke haka suke idan suka ga ana kona su鈥�
Bappa ya bita har can ya zuba nata wata bulalar yana fadin
鈥淜u fita daga jikinta yanzu nan鈥�
鈥淏appa sun fita tun dazun ni ce dan Allah ka tsaya鈥�
Ina Bappa be yarda Fadime bace sai auna mata bulalar yake, tun tana fadin sun tafi har ta fara kiran Inna ta ceceta.
鈥淚nna nice Wallahi ni ce dan Allah ki zo kar Bapppa ya akashe ni鈥�
Inna ta zo da sauri ta rike bulalar tana fadin.
鈥淪un fa tafi Fulani ce kake duka鈥�
Sai a lokacin Bappa ya sarara mata bayan ta sha buloli da sunan aljannu.
HAJIYA BABBA POV.
Tsananin mamakin da yake fuskarta ya wuce misali, ta san Jarma ba zai mata karya ba, amman sam bata gane inda labarinsa ya dosa ba, Fadime Falmata Sardauna za su watse musu shiri?
鈥淲acace Fadime?鈥�
Ta tambaya a fili tana kallon Jarma.
鈥淣i ma abunda na gagara sani kenan, balle kuma Falmata da Sardauna, amman ni ina ganin kamar Sardauna na Yola yake nufi鈥�
鈥淪ardauna ai yana da nisa da Sarautar nan, balle nai tunanin haka, idan na shi ne to su waye Falmata da Fadime?鈥�
鈥淎bun da na gagara sani kenan, kuma na yi wauta ko da yake tsoro ne a ya hanani tambayar ko me suke nufi, kuma ita Ammy ai Zainab ne sunanta ba Fatima ba balle nai tunanin ko ita ce....鈥�
Be karasa ba Hajiya ta daga masa hannu alamar yai shiru sai dai har lokacin mamaki be bar fuskarta ba. Kwankwasar dakin da ake take saurari kamin ta ji muryar Nana.
鈥淗ajiya Hajiya....鈥�
鈥淒aughter ke ce?鈥�
鈥淣i ce鈥�
Hajiya ta tashi da kanta ta bude mata dakin tana kokarin kirkiro murmushi.
鈥淒aughter na ya aka yi?鈥�
Ta tambaya tana rike da kofar dan bata son Nana ta hango Jarma a dakinta, duk da ta san ya saba shigowa sai dai rufe dakin da makulli da akai zai saka shakku a zuciya.
鈥淲ayarki za ki bani sai na kira wanda na ce miki ina son ya zama driver na鈥�
鈥淭o tsaya nan bari na dauko miki鈥�
Hajiya ta rufe kofar ta dawo ta dauki wayar sannan ta koma gurin kofar ta bude ta mika mata.
鈥淭afi da ita can idan kin gama ki bawa Karima ta aje min鈥�
鈥淥kay鈥�
Ta karba ta juya cike da jindadi, dan ta san Number AA na cikin wayar Hajiya, saboda ta ari wayar shi ta kira Hajiya da line, duk kuwa da bata da tabbacin number tana nan har yanzu ko an goge, ba dan zata iya ganewa number ba sai dan ta gwada sa'arta.
Bayan ta wuce Hajiya ta sake rufe dakin ta dawo ta zauna. Sai Jarma ya rage murya yace.
鈥淎she Nana ta fara dan hali?鈥�
Hajiya ta yi murmushi.
鈥淎i har abun da yafi dan hali sai Nana ta yi, matukar ina raye 拼a拼an Ammy ba za su taba albarka ba Wallahi har a abada kuwa, yadda take son ganin bakincikina ita sai na ga nata kukan鈥�
Ta karasa tana wane kashe ido zuciyarta cike da kiyayyar Ammy.
*FULANI -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence to 08036126660 拼an nijar za ku tura 500cf to +22790165991*
03/12/2021, 09:20 - 馃馃馃馃: *Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
Tana cikin bukkarta Hajjo ta leko tai mata ya jiki, daker ta amsa mata da sauki kamar ita taja mata akai mata dukan, Amo ma dake ta mamaki ta leko.
鈥淔ulani ya jiki?鈥�
鈥淣a ji sauki鈥�
Sai da ta kare mata kallo sannan ta juya ta fita, cikin jin haushi Fadime ta fito daga dakin ta zauna a waje, Inna ta dauko koko ta kawo mata ta saka mata ludayi.
鈥淜i sha yana da zafi鈥�
Kallon kokon kawai tai ta dauke kai tana ta jin haushin dukan da akai mata, gaba daya yanzu laifin Wasim take gani domin shi yaja mata koma minene.
鈥楢i ban ce yai min a lokacin ba, amman wai yai min mugunta鈥�
Ta fada a ranta, a fili kuma sai tai kwafa har sai da Inna ta juyo da tsoro ta kalleta, domin yanzu tsoronta take ji ganin abunda ya faru jiya. Mikewa tai tsaye ta karasa gurin Inna tana dan murmushi kamar ba ita ba.
鈥淚nna yaushe shi mutumen zai zo?鈥�
鈥淲ane mutume?鈥�
鈥淪hi mana鈥�
Ta rufe ido tana dariya wai ita kunya. Inna ta tabe baki, ta wani bangaren bata ganin laifin Fadime, tun da ba a taba cewa ana son ta ba ba a taba sallama mata ba da sunan fira ba dole kuwa idan ta ji ana sonta ta jidadi.
鈥淏an sani ba鈥�
鈥淚nna in be zo ba ni a kai ni to, kin san su mutane birni basa zuwa kauye ko saboda irin hanyar nan, kin ga tun da na iya boko shikenan sai mu yi ta magana da turanci zai ji na burge shi鈥�
Ta fada tana ji wani irin dadi a ranta, jiya har mafarkinsa tai, ta ganshi wani mummuna amman bata ji komai ba saboda neman mijin kawai take ita dai burinta ta ga miji. Jin Inna ta mata shiru yasa ta tashi ta koma inda take ta zauna tana kallon yadda Inna ke raba kokon da ta dama.
鈥楴i ma idan na yi aure haka zan yi, sai na yi girki nai komai irin na mata, kuma na haihu ni ma鈥�
Ta saka a ranta tana shafa cikinta murmushi ya wanke fuskarta. Mikewa tai tsaye ta nufi gurin ruwa ta dauko wani tulun.
鈥淚na zaki je?鈥�
鈥淩uwa zan debo鈥�
鈥淎a ba yanzu ba, jiya jiya kika je kika kwashe aiki yanzu kuma kice zaki je, a a ban yarda ba, waya sani ko gulbin ne ke da aljanunn鈥�
Amo dake cikin daki ta fito tana amsawa Inna.
鈥淟allai kam indan ruwa bari Hajjo ta debo sai ta cika mana gidan鈥�
Ba dan ranta ya so ba ta aje tulu ta koma ta zauna ta fara motsa kokon tana ta tunanin abun da zata yi ta fita. Bata sha rabin kokon ba sai ga Ma'u ta shigo gidan bakinta har rawa yake sai dai gani Inna yasa tai shiru bata ce komai ba bayan gaishe da ita da tai sai kuma ya jikin da tai mata. Can dai Ma'u ta tashi tana kyafta ma Fadime ido.
鈥淣a tafi Fulani Allah kara sauke鈥�
Sai Fadime ta mike tsaye tana satar kallon Inna.
鈥淭o bari na rakaki鈥�
Har sauri saurin take ta riga Ma'u fita daga gidan. Suna fitowa Ma'u taja ta gafe
鈥淔ulani Wallahi naje na fadawa Inna Bubakar kin ce mijinta zai kara aure nan da kwana biyu鈥�
Fadime ta zaro ido.
鈥淢iyasa kika fada ba nace miki sirri ba ne鈥�
鈥淒an dan ta tabbatar idan da gaske ne kuma ni na tabbatar, yanzu ta aiko tace a kira ki鈥�
鈥淲allahi ba zan je ba, dan ta karyata ta ni ko? Ko taja Bappa yai min duka鈥�
鈥淏a duka zata ja miki ba, kika san ko kudin zata baki tace ki fada mata wani abun鈥�
Duk yadda Ma'u ta so taje kiran da Matar take mata sai Fadime ta ki saboda ta san bata da gaskiya, idan aka ce waya fada mata dole tace aljannun ne kuma tasan Bappa zai iya dukanta ko ya sake mata wani karatun.
鈥淜i ce mata anjima zan zo鈥�
Ta juya ta koma ba tare da jira abunda Ma'u zata fada ba. Dawowa tai ta zauna, da an yi sallah sai ta ji gabanta ya fadi dan gani take kamar matarce zata so ta fadi maganar a gaban Inna. Can dai ta tashi ta shiga daki ta rubuta abunda ya faru jiya tun daga kan yadda su kai da Wasim har zuwa karatun da akai mata da aljanun karya da tai. Ana gama sallah la'asar Fadime ta kwance shanu wai zata je gurin kiwo.
鈥淔ulani kin san yadda kika yi jiya, ki bar zuwa kiwon nan sai gaba idan kin samu lafiya鈥�
鈥淣i lafiya ta kalau, idan ina zaune ma sai na ji kamar nai ihu ai kara naje dajin dai鈥�
Duk yadda Inna ta so Han Fadime zuwa kiwo a yau abu ya ci tura, dan Fadime tsayawa tai kai da fata akan sai taje ganin Bappa ya tafi gari, ta sani idan shi ne bata isa ta musa masa ba duk kuwa da irin son da yake mata.
Haka ta kora shanun suna gaba taba biye har suka isa cikin daji, a iya alkawarin da tai a yau ba zata yi magana da Wasim ba, kuma ba zata sake kusantar inda yake ba, duk kuwa da irin burin da take da shi na wani taimako da take son yai mata, kin magana da shi na nuna fushinta ne, ta dayan bangaren kuma tana jin tsoronshi, dan ta san duk mutunen da zai iya dabon maciji a take ba karamin matsafi ba ne.
A inda ta saba zama ta zauna, tana ayyana cewar ko ta ji busarsa ba zata leka ba, zuciyarta na raya mata dole zai zo inda take. Kamar yadda ta saka haka ta faru tana jin takun mutum a gefenta ta ki ta daga kai ta kalli gefen dan ita ala dole tana fushi. Murmushi ne mai kama da dariya a fuskarsa, ya zauna kusa da ita yana kallonta, sai ta ki ta juyo balle ta san da mutum a gurin, dauke kai yai yana cigaba da murmushin mai kama da dariya yana cin guava dake hannunsa, can kuma ya leko fuskarsa wacce ita ce tafi komai daukar masa hankali a cikin hallitarta, bayan kyau da fari da gashi Fadime bata da wani abu da za a kalleta da shi a ce ana sonta, domin kirjinta da shi da babu duk daya, balle ayi maganar mazaunai.
Wata uwar harara ta watsa masa, har ga Allah haushinshi take ji kuma da ace ba shi bane tabbas da mai raba su a yau sai Allah, amman tana tsoron tai masa wata rashin kunyar ko wani sherin yai mata wanda ya ci uban nata.
鈥淚na ta tunaninki tun jiya鈥�
Ya fada yana kokarin danne dariyarsa, domin babu abun da be sani ba na isa da tai da maciji a kanta. Ta masa banza tana son ta harare shi ba dama tun da tana tsoro. Ya mika mata guava hannunsa.
鈥淜arbi ki ci鈥�
Ta yatsina fuska alamar kyama, daman can bata jin ragin kowa ciki har da Babanta da Inna balle kuma shi. Dan karamin bakinta ta kurawa ido yana ta kallonsa sai ta soma jin halshenta na motsawa, ta kalle shi da sauri.
鈥淢e ka min?鈥�
Ba shiri ta rufe bakin jin muryata kamar ta wani kwaro. Ta mike tsaye da sauri tana zaro ido.
鈥淲ayyo Bapppa鈥�
Kamar wani karamin kwaro na magana haka muryarta ta zama, zata ranta ana kare ya riko ta.
鈥淶aki min magana?鈥�
Ta gyada kai da sauri hawaye na sauko mata, sai yai murmushi yana kallon fuskarta yana jin kamar ya hade ta, duk wani motsi nata burgeshi yake. Bakinta ya sake kurawa ido sai ya halshenta ya sake motsawa bata bari ya kara ta sa hannu ta rufe baki tana fashewa da kuka, sai ya kara rike ta gam yana dariya domin fisge fisgen take tana son ta subuce daga rikon da yai mata.
鈥淜i zauna idan ba haka ba, ba zan gyara miki halshen ba, kuma zaki tafi da shi gida a haka, zaki zauna鈥�
Ta gyada kai da sauri, sai ya sake ta har lokacin dariya yake, ta zauna saman karamin dutsen sai ya mika mata guava daya bata dazun ta ki karba, kamin yace komai ta karba ta saka a baki ba ta ma wani tsaya taunawa da kyau ba ta hade.
鈥淣a hade鈥�
Sai ta ji muryar kamar duro, a take ta fashe da wani irin kuka, sai kuma tai saurin yin shiru ta rufe bakinta domin ita ma kanta tsoron muryar take, ji take kamar kukan da muryar ba a bakinta suke fitowa ba. Ta fara masa na kurame alamar roko tana nuna masa bakinta. Sai ta sake jin halshen ya motsa zata saka hannu ta rufe ya rike mata hannun. Wani uban ihu tai shi kanshi sai da ya duke kanshi ya runtse ido saboda kyakyar muryarta har cikin kai take shiga.
Wani mamaki ne ya cika ta jin muryarta ta dawo daidai, sai tai dan murmushin tsoro tana kallonshi.
鈥淒an Allah da gaske kai ba aljani ba ne?鈥�
Ya zauna kusa da ita yana ta kallonta.
鈥淣i mutum ne mana, bana fada miki muna tsafi ba鈥�
鈥淣a yarda...鈥�
Ta fada cikin tsananin mamaki tana kallonsa.
鈥淢iyasa kake kallo?鈥�
鈥淏urgeni kike鈥�
Ya ansa mata still yana kallonta, sai ta nuna kanta.
鈥淜ana so na kenan?鈥�
Sai ya dauke kai yana murmushi, ita kuma ta ji kunya ta rufe ta, ai be kamata ta tambaya, idan yana sonta shi ya kamata ya fada, ba ita ba. Ta sinne kai kasa tana yan zanezane.
鈥淏a ni labari鈥�
Ta dago kai amman sai ta kasa kallonshi saboda kunyar maganar dazun.
鈥淏a ni da labari... 鈥�
Ta yi shiru, shi dai sai kallonta yake can kuma tace.
鈥淜ishiyar Innata tace ta min miji a birni, amman har yanzu be zo ba鈥�
鈥淎ure za a miki?鈥�
Ta yi shiru ita dai kam tana son aure a rayuwarta, da za a mata auren ma a take da ta huta. Ta kalleshi
鈥淶aka iya min tsafi na gan shi? Ko ka kira shi ya zo?鈥�
Yayi murmushi yana kallon cikin idonta.
鈥淜ina son ki san mijinki?鈥�
Ta daga kai ta sauri.
鈥淓h鈥�
Ya mika mata hannunsa.
鈥淜awo hannunki鈥�
Sai ta miko masa hannun, ya dora saman tafin hannunsa yana kallon idonta.
鈥淲ashhhh sanyi hannu sanyi sanyi鈥�
Ta fada tana saurin janyewa.
鈥淭o duk namiji da ya taba hannunki kika sake jin irin wannan sanyin shine mijinki鈥�
Da dan bude ido tana kallon hannun nata.
鈥淒a gaske? To mu gaisa鈥�
鈥淚dan kika ji sanyi a hannunki fa?鈥�
鈥淪hikenan kai ne mijin鈥�
鈥淚dan kuma ba kiji ba fa?鈥�
鈥淪hikenan ba kai ba ne鈥�
Ya mike tsaye yana murmushi ya ciro guava a yar karamar jakar da ke kugunsa, sai tai saurin kai hannu ta taba hannunshi, saurin fisgewa yai.
鈥淭afin hannunsa zaki taba ko ya taba naki, idan tafin hannunki da hannun wani namiji su kai taba juna kika ji sanyi to shine mijinki鈥�
Yana fadar hakan ya fara tafiya yana cin guava.
鈥淚na zaka je?鈥�
鈥淕arin mu鈥�
Tayi shiru tana kallonshi.
鈥淢iyasa jiya nan kai min tsafin maciji a nan ba a gida ba?鈥�
鈥淏a ke kike ce a miki ba鈥�
鈥淎mman ai ban ce a nan ba, a gida na ce鈥�
鈥淚na son ki ba ni nishadi ne shiyasa鈥�
Ya fada yana ta kallonta. Sai tai dariya.
鈥淗ar da karyar aljanu nai nace sunan aljanina Sama'ila, kuma sunan Bappa na ne鈥�
Shi ma dariyar yai, ya sake kai guava bakinsa sannan ya mika mara ragowar. Sai ta girgiza kai alamar a'a tana kyankyami, be ce mata komai ba yai murmushi ya juya ya cigaba da tafiyarsa har ya haye saman dutsen ya dago mata hannu ita ma ta daga masa, sannan ta sauke tana kallon hannun na shi.
鈥淵ana zuwa zan taba h.... 鈥�
Bata karasa ba ta ji muryarta ta zama kamar ta shanuwa saboda kara da munin sauti, da sauri ta rufe bakin ta fara hawa saman dutsen tana nemansa amman ko alamar sa bata gani ba, ta sauko a firgice ta nufi gida bata ko bi ta kan shanun ba.
Kamar wacce aka koro haka ta iss gida, Inna na zaune da Rammu Fadime ta shigo gida babu ko talkami.
鈥淜e lahiya Fulani abun ya tashi kuma?鈥�
Har ta bude baki tai magana sai kuma ta rufe bakin ta fara mata na kurame, tana nuna mata bakin nata. Inna ta taso da sauri tana fadin.
鈥淏ude na gani鈥�
Ta hangame bakin tana hawaye kamar ba ita ba.
鈥淜e babu komi ciki Fulani ya kai ne wai?鈥�
Bata son ta yi magana Inna ta ji murya, ita kanta tsoron muryar take dan ji take kamar ba a bakinta take fitowa ba. Babu juyin duniya da Inna ba tai ba amman Fadime ta ki magana sai dai tai nuna. Shanun ma Hajjo aka tura ta dawo da su gida, hankali Inna duk yabi ya tashi, a zatonta Fadime ta daina magana ne, gashi ita kadai cikin gidan dan Amo bata nan kuma bata son kiran makota kar Bappa ya dawo ya hau ta da masifa, tun da komai cewa yake sirrinsu ba sai wani ya ji ba.
Sai daf da magarina Bappa ya shigo gidan da yar tsarabarsa, daman a duk lokacin da yaje burni ya dawo sai ya musu tsaraba, Bappa irin mazajen nan ne da basa son shigowa gida hannu sake. Sai dai tashin hankalin da ya tarar a gurin amaryarsa ya kawardar komai, domin kuka ya tarar tana yi kamar yadda Fadime ma take kuka. Bappa ya nufo Fadime cike da mamaki da kuma tsoro a lokaci daya.
鈥淔ulani ba zaki iya magana ba?鈥�
Kasa cewa komai Fadime tai sai hawaye take, tsoro take kar tayi magana ta sake jin murya, ga kuma tsoron Bappa kar yace zai kira mai karatu ko ya daketa.
鈥淶an iya鈥�
Ta fada da muryarta mai ban tsoro, gaba daya Bappa jin yai kamar muryar ta cika duniyar nan gaba daya, be san lokacin da ya jefar da kayan hannunsa ba ya riko rigar Inna wacce ta kusa wuce da gudu ya dawo ta ita baya ya kara ma kafarsa giya.
0 comments:
Post a Comment