Hausa novels 2023

  • Home
  • Ciwon Idanuna
    • Internet
    • Market
    • Stock
  • Agola
    • Dvd
    • Games
    • Software
      • Office
  • Mijin Biza
    • Child Category 1
      • Sub Child Category 1
      • Sub Child Category 2
      • Sub Child Category 3
    • Child Category 2
    • Child Category 3
    • Child Category 4
  • Kwarata
  • Health
    • Childcare
    • Doctors
  • Inda Ranka

Monday, September 25, 2017

SHINFIDAR MIJINA Page 1-5

 September 25, 2017     SHIMFIDAR MIJINA 1-END     No comments   

Na  Princess Eshat Aysm
.

_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_
.

Kuka take shek'awa da iya k'arfin ta, ANWAR ya dafe kanshi yarasa wani irin rarrashi zai mata ta fahimce shi, a duniya bayan iyayen shi babu abunda yake so kamar Maryam, Kukan nata har cikin ranshi yakeji.
"Maryam kema kinsan ina sonki bazan tab'a cutar dake ba, wannan aure zanyi ne kawai amma ki yadda kece muradina Maryam, idan har baki so abunda nake so ba nayadda kin daina sona, na fad'a miki ke kad'ai nake so auren ne kawai yazo bawai don kin rageni da komai ba".
kukan tad'an sassauta ya jawota jikinsa yafara share mata hawayen, ta saki ajiyan zuciya ta ce "Anwar kishiya abun tsoroce banaso a rabani dakai".
Murmushi yayi ya ce "wazai rabamu idan ba Allah ba, ki kwantar da hankalin ki, ki rok'i Alkairi kidaina wannan tunanin, Allah yasa auren yazamo alkairi agaremu baki d'aya".
kwantar da kanta tayi k'irjin shi kafin ta ce "Ameen Husby".
Ya dad'a rungumo ta yafara kissn d'in ta, bakin ta yake k'ok'arin cafkowa amma ta rufe gam kamar yadda yayi tsammani, ya koma kan wuyan ta yana shinshinawa yana d'an
lasa har ya iso k'irjin ta, ta d'an bank'are tana jin dad'i amma batasan me zata masa ya bashi k'arfin gwiwa ba, haka yayi ta romance d'in ta tana kwance, ko da yazo babban aikin ma bata ko motsa ba har yasamu ya biya buk'atan shi ya mik'e ba wani armashi balle aga annuri a fuskan shi, idan da sabo ya saba, shidai yasan yana son maryam amma sam baya samun nutsuwa da ita bai kuma san dalili ba, hakan yasa yaji yana so yak'ara aure kamar yadda zuciyar shi ta kwad'aitar dashi.
.
.
Da Baban Maryan da Baban Anwar Abokanai ne, sun taso tun suna yara suke son juna har suka girma kuma so me tsanani, ganin haka yasa iyayen suka had'asu aure, MARYAM ita kad'ai iyayen ta suka haifa ANWAR kuma yanada k'anne guda biyu maza AHMAD da ABDULLAHI sai mace d'aya ZULAIHAT.

Anwar irin dogayen mazannan ne masu d'an kaurin jiki k'arfaffa, wankan tarwad'a ne gashin kanshi a kwance yake luf2, abokan shi suna k'iran shi da Gentle Medo.

Wata ranar lahadi suka had'u da Fateema a garin JOS ya raka abokin shi saro kaya.
"Fateema wannan wandon bazai shige ki ba".
K'awarta Sakina ta fad'a tana jujjuya wandon a hanun ta.
"Ni yamun kyau haka zan d'auka da kad'an fa na jikina yafishi girma, kin san ba wani k'ibane dani ba".
"To ai shikenan kayan sun isa haka kinsan zamuje islamiyya kada kisa muyi late".
Bada kayan sukayi aka lissafa musu, duk abun da suke Anwar ya zuba musu ido, lokaci guda yaji sha'awar Fateema ya kamashi, sanye take da koriyar riga iya cinya tanada belt a tsakiyan ta sai dogon wando (skin tyt) kanta ba d'ankwali sai wani d'an yalolon gyale k'arami da ta nad'ashi ya sauk'o ta zagayen wuyan ta, farace ba laifi doguwa sai dai batada wani hips kamar na Maryam.
Bilal ne yad'an tab'a shi ya ce "ko dai zamu shiga ne".
Anwar yayi murmushi ya ce "ka gane kuwa nifa na mato".
Tafawa sukayi dai2 lokacin su Fateema sukazo ta gabansu suka wuce.
A hankali sukayi ta binsu a baya har suka iso school line, gidan nasu yad'an haura saman dutsi
kana ganin ginin kasan talakawa ne sai dai ace rufin asiri.
Daf zasu shiga Bilal yayi saurin shan gabansu.
.

"Saurin me kukeyi ana muku magana bakuji".
Sakina ta ce "Bamuji ku ba don Allah kuyi hak'uri".
ya ce "ok, naga kaman kuna sauri ki taimaka mun da numban ki idan bazaki damuba abokina yana jira".
yafad'a yana nuna Fateema, a tare suka juya wajen da Anwar yake nan kuwa fatee ta k'yasa, da sauri ta fara jiro mishi Numba (kunsan 'yanmatan JOS babu aji lolx kadafa kuji haushi).
.
.

wannan shine silan had'uwar Anwar da Fateema, Har maganar aure ya shiga tsak'ani.
Tun ana saura wata d'aya biki ake tsuma Fateema.
Babu irin had'in da ba'a mata ba saina matsine kad'ai ba'a mata ba.
Duk talaucin su Fateema saida suka had'a k'arfi da k'arfe da yayun ta da kuma d'an kud'in da take samu awajen Anwar Suka gyara ta.
yayunta biyune Aunty Fauziya da Aunty Hadiza duk suna aure a cikin garin Jos, ita kad'aice suke ganin za'a kaita wani gari kuma kan kishiya shiyasa basu mata da wasa.
Fetsara kuwa babu kalan wanda k'awayen ta basu koya mata itama kuma ba tayan baya ba.
.
.
.
Maryam dai duk tagama tsurewa ganin yanda Anwar yake
rawar k'afa akan auren idan tayi magana yayi ta rarrashin ta yana cewa ita kad'ai yake so, wani lokacin ma cemata yakeyi sadakan yarinyar aka bashi sau d'aya ya tab'a ganin ta. (nidai nace maza angaishe ku).
.

Gyara gidan yayi sosai amma falonsu d'ayane, ko wacce da d'akunan ta 2 da toilet a ciki sai nashi a tsak'iya.
Bai banbace lefe ba duk abunda yayi wa Fateema haka yayi wa Maryam.
'yan uwanshi sunsha mamaki da k'ara auren anwar ganin yanda yake masifar son maryam amma haka suka bishi da fatan alkairi.
yau take ranar ASABAR ranar da tayi dai dai da d'aurin auren Anwar.
Tun da safe Maryam take ta aiki har 'yan uwanta suka zo da wasu daga cikin 'yan uwan Anwar, Fuskar ta a sake babu wanda zaice wa ita za'ayi wa kishiya don mijin nata saida ya tabbatar mata ita kad'aice mace kafin yafita.

.

K'arfe goma aka zo akayi wa amarya jere, sun mata kaya babu laifi, Maryam ita da kanta tayi ta musu hidima har mamaki sukeyi.
D'aya daga cikin kayan da Hajiyan Anwar ta aiko mata ta saka, atamfa ce me kalar ja da bak'i d'inkin yayi d'aras ajikin ta ga wani d'aurin da Aunty Safiya tamata (k'anwar mamanta).
zuwa yamma gida ya cika fal da mutane kowa kafin yafita sai yasanya mata albarka ganin babu wani kishi aranta, ita kuwa harga Allah ta yadda Anwar baya son auren sadaka aka bashi kamar yadda yafad'a kuma taga kayan d'akin amaryar ba wani yawane dasuba shiyasa ta dad'a tabbatar wa.
Ana sallar isha ta sake cancara ado lokacin duk an watse saura 'yan danna k'irji suma ana kawo amarya zasu tafi.
K'arfe Tara dai2 aka fara cika gidan da gud'a, saida Cikin Maryam ya kad'a ta fara tsilli2 da ido.
Daurewa kawai tayi tafara innalillahi a zuciya, k'asan zuciyar ta tanajin kishi yana taso mata.
D'akin ta aka fara kawo amarya wai ankawo mata amana idan tayi ba dai dai ba tayi mata fad'a.

Duk K'ok'arin da Maryam tayi wajen ganin ganin fuskar amaryar ta kasa domin tana nannad'ene acikin mayafi sai wani uban k'amshin dayake tashi.
haka suka k'araci surutunsu suka wuce da Fateema d'akinta.
itama bak'in nata duk sallama suka mata suka tafi ganin dare yayi.
Tana Zaune ta rafka tagumi wai yau itace akayi wa kishiya itada saidai tagani a wani waje..
Dai2 kunnen ta yakai bakin sa yafara rere mata wak'a,
_nafad'a a rijiya sa mini k'ugiya yau zabari kizo ki tsamoni da k'ugiya_
Tureshi Tayi ta saki kuka.
Dariya yayi ya shige jikin ta yana shinshina ta, ganin bata daina kukan ba yasa ya tallafo fuskar ta still murmushi ne a fuskar shi ya ce "waye ya tab'amun ke ne, bai kamata ki zubar da hawayen ki a ranar da kika zamto shugaba agidan ki ba".
Harara ta watsa mishi ta kauda kai,
ya juyo da'ita tana fuskantar shi ya ce "kishi kikeyi da matar sadakar? idan kikace kada nashiga d'akin ta bazan shigaba, ni kinganni nan ke kad'ai kin isheni".
ya k'arasa fad'a yana kashe mata ido.
ko ba komai taji sanyi a ranta, ta kwanta ajikin shi batace mishi komai ba, yasa hanunshi ya zare zip d'in rigar ta yafara wasa da ita, gajiya yayi da wasan ya mirgina yana k'arewa silin kallo.
.
Ana kai Fateema d'akin ta tayaye mayafin tana kunkuni.
Aunty Hadiza ta dungure mata kai ta ce "me aka miki"?
"Aunty kun wani tukuikuye ni banga matar tasa ba".
Sakina tayi dariya ta ce "saurin me kikeyi tunda tare zaku zauna".
Abincin da tanada musu suka faraci, d'aya daga cikin k'awayen ta ce "Banga alamar kishiyar nan taki tanada matsala ba".

Fateema ta ce "ko tanada matsala ba ruwana da ita".
"yauwa 'yar albarka baruwan ki da ita duk abunda zata miki kiyi hak'uri kuma banda kai k'ara tunda ba lallai bane ya yarda kuma yawan kai k'ara yanasa a tsani mutum".
Aunty Fauzee ce tayi wannan maganar, haka sukayi ta bata shawara har bacci ya d'aukesu.
.

Da asuba Maryam ta tashi ta musu abun karyawa ta gyara gidan ta kimtsa komai ta koma d'akin ta tayi wanka ta tsala adonta ta kwanta abunta, bata da tunanin komai ganin tunda suka tashi Anwar baiko lek'a d'akin amaryar ba yashige d'akinsa ta tasake sakankance wa akan baya son auren.
sai yamma 'yan uwan fateema suka koma garin Jos.
Kimtsa komai tayi ta d'auro alwala tana jiran ayi magriba, ta juma tana mamakin Anwar ganin tunda aka kawota bai lek'a yanda suke ba, tasa aranta hala haka 'yan garin sukeyi.
.

Ledoji biyu ya shigo dashi ya wuce d'akin Maryam kai tsaye, ganin yanda ta bi ledan da kallo tana watsa mai harara yasa shi cire babban rigar jikin shi ya haye gado ya kwanta, bud'e ledan tayi wani
haushi ya turnek'e ta tanajin zafi aranta, da k'yar ta k'wak'ulo murmushi a fuskar ta, ta ce "Darefa yayi, ya kamata ka wuce".
ya saci kallon ta ya ce "in wuce ina, anan zan kwana bayanda zanje".
yanda yayi maganar kai kace har cikin ranshi ya fad'a.
Ta waro ido ta ce "karufamun asiri Anwar duniya ae sai ta zageni, kuma bakaso zaman lafiya ba kuwa kayi haka".
yad'an taso ya ce "Akan duniya ta zageki ai gara anzageni, zafi najeji bari nayi wanka ki rakani naje amma asuban fari zandawo nan".
murmushi ta bishi dashi har ya shiga toilet, ta kwanta ta lumshe ido tana tunanin irin son da Anwar yake mata, da wanine da yanzu tana kuka.
sabbin kaya ta fitar mishi cikin hanzari ya shirya, ta feshe shi da turare, pick yamata a goshi ya ce "nagode".
ledar ta d'auka yaja hanun ta suka nufi d'akin Amarya Fateema.

.
.
Madara Pick Milk ta juye guda biyu a cup ta had'a da zuma tana sha don bata fiye cin abinci da dare ba, jin kamar za'a shigo ne tayi sauri ta jawo dogon hijabin datayi sallah ta zura ajikin ta, yana sak'ale da hanun Maryam suka shiga, a d'aya daga cikin kujerun falon nata suka zauna, Marya tad'anyi dariya tace "amarya ansha k'amshi".
murmushi itama tayi ta ce "ina yini aunty".
"lafiya law ya bak'unta, koda yake kinzama 'yar gida tun daga jiya".
Anwar ya murza hanunta da yake rik'e dashi kad'an ya rage ta saki k'ara, Fateema duk tana kallon su, ta saki murmushi bata ce komai ba.
Anwar ya ce "Fateema ga uwargida ta Maryam, banaso ki zamto mata matsala saboda nasan batada matsala, kece k'arama dole ki mata biyayya idan kinason zamanki ya d'aure agidan..". sosai Maryam taji dad'i tad'an dungure shi alamar ya isa haka.
Fateema ta ce "Allah ya had'a kanmu ya bamu zaman lafiya".
Dukkan su sukace "ameen".
Maryam zata mik'e ya jawota yace "ina zakije kuma".
wani kallo ta watsa mishi ya sake ta da sauri tabar
D'akin.
Fateema ta sukunyar da kanta aranta tace akwai aiki a gabana.
Haka kawai yaji tausayin Maryam ya kamashi, shidai yasan auren sha'awa yayi bana so ba, shiyasa baya k'aunar yaga ya b'ata ran maryam. jiki a sanyaye ya mik'e isa kusa da Fateema ya ce "Bako gaisuwa ne 'yanmata"? sunkuyar dakai tayi tana murmushi.
"kunyata yau kikeji? kin manta hirar dakikemun ta text har kisani wanka ko". yafad'a yana rik'o hanunta, b'oye fuskan ta tayi cikin hijabi tana dariya. murmushi yayi yace "muje muyi alwala".
Ba musu tabi bayan shi, sallah sukayi raka'a biyu ya kama goshin ta yamata addua, tundaga kan farillan alwala yafara tambayar ta tana amsawa har ya iso kan wanka.

.

Shiru tayi tarasa ta ina zata fara masa bayani.
"Baki saniba"?
Tace "nasani".
"Inajin ki to".
"Ban iya bayani bane".
yayi dariya yace "gwadawa kenan? muje ki nuna mun inda akeyi".
Jawo hijabin tayi zata rufe fuska yayi sauri ya  jawota.

"Ban tab'a ganin amarya da hijabi ba sai amarya ta, amma yanzu zancire naga abunda ake b'oye wa".
k'ok'arin cirewa yakeyi ta ce "Fuska ta nake b'oyewa kuma haka amare sukeyi ai don Allah kabari".

Dariya ya sake ya ce "inane fuska kuma bayan wanda nake kallo yanzu".

kafin tayi wani yunk'uri ya cire hijabin ta fad'o jikin shi tana b'oye jikin ta, ita kanta kunyar kayan jikin ta takeyi, tela yaci mutuncin yadi sunan d'inkin, material ne d'inkin riga da siket daya kamata sosai, duk ilahirin k'irjin ta a bud'e yake.

k'amshin jikin ta ne
yafara bugar dashi, ya d'agota yana k'are mata kallo
tayi kyau sosai fiye da yadda yake ganin ta a baya sai dai bai wani yaba da kyawun ba saboda Maryam d'insa tafita kyau nesa ba kusa ba, sha'awar nan dai dayake ji akanta shi kad'ai yaji, idanunshi har
lumshewa yakeyi.

D'ankwalin kanta ya zamar ya warware gashin yafara hautsina shi, ya dad'a janyo ta jikin sa yasaka hannun shi ta baya yaja zip d'in rigar ya cire shi, harce yasaka a lungunun wuyan ta yana lasa numfashin sa har sama takeyi saboda turaren jikin ta shi yake dad'a ingiza shi.

kukan ta yafara ji mara sauti don ita duk tagama tsurewa ga wani irin kasalan da ya sauk'a mata.

ya d'ago fuskan ta ya ce "kukan menene"?
kafin tayi magana ya had'e bakinshi da nata yafara wani irin tsotsa yana zak'ulo harcen kamar ya samu swtt abunda bai tab'a sanin dad'insa ba a rayuwa, a hankali itama ta kama harcen sa tana mayar da martani gaba d'aya ta gama rud'a shi, yafara kissn d'in ta tako ina har iso kan cibin ta yazare siket d'in ya d'auke ta yamayar gado.
Anwar dai suma ne kawai baiyi ba don dad'i, aurensu da Maryam shekaru biyu amma ko daren farkon ta bai ji kwatan abunda yaji yanzu ba, duk kukan da Fateema takeyi baima sani ba burin shi yakai k'arshen aya.

Saida yadawo hankalin shi ya janyo ta jikinsa ya
k'ank'ame ta yana jin wani irin farinciki tare da sonta yana shigar sa.

ya share mata hawayen ya ce "kiyi hak'uri".
Ta d'aga masa kai kawai.

Da kanshi yaje ya gasata ya yaye zanin gadon ya d'auko wani ya shimfid'a, ya d'ora kanta a k'irjin shi, ahankali ya fara magana "Allah yayi miki albarka Fateema, ina sonki zan rayu dake har k'arshen rayuwar ta, kin zama sirrina kin jiyar dani wani irin dad'i uwa uba kin kawomun budurcin ki Allah ya miki albarka".
.

.

Maryam tana komawa d'aki tayi kwanciyar ta hankalin ta a kwance tasha baccin ta, washe gari da asuba ta tashi tayi musu brkfst tayi wanka, duk tsammanin ta zataga Anwar kamar yadda ya fad'a amma har 9 tayi shiru, ta fito ta lek'a d'akinsa bayanan, wasa2 har 11 tayi babu Anwar, batasan lokacin da ta fashe da kuka ba.

Baccin su sukesha abunsu Anwar yana rungume da ita ya k'ank'ame ta kamar wanda za'a k'wace masa ita, sau biyu yana yunk'urin tashi bayan sunyi sallah amma sai Fateema ta rik'o shi tana kuka dole ya biye mata sukayi ta bacci har k'arfe sha d'aya da rabi ya farka, ya zare ta ajikin sa ya mik'e da sauri ya nufi toilet, wanka yayi sai wani irin farinciki yakeji, sai da yashafa mai ya tuna babu kayan shi a d'akin, da towel d'in ya fita ya lek'a d'akin maryam yaga alamar bata kusa yayi sauri ya shige d'akin sa, k'ananun kaya yasaka jan riga me adon fari ajiki an rubuta MY LOVE ajiki, ya nufi d'akin Maryam sai sak'e2 yakeyi a zucizar shi bai san wani irin kalma zaiyi amfani dashi ba.
Kukan ta ya jiyo da sauri yaa k'arasa cikin d'akin.
"Maryam waye ya tab'amun ke".
Da sauri ta d'ago taga da wani irin ido zai kalle ta, ko ajikin sa bai damu da kallon da take mishi ba ya janyo ta jikin sa yafara shararo mata k'arya "meyasa bakije kin tasheni ba, bacci ne ya d'aukeni ina idar da sallar asuba saboda banyi bacci ba jiya
tunanin ki ya hanani sakat yau kam ko kince na kwana acan bazan je ba". ya fad'a yana dad'a kwanto da ita jikin sa, sai a lokacin tayi shiru, taji hankalin ta ya kwanta lokaci guda ta nemi fushin ta rasa. ta zunb'uro baki ta ce "fad'i nayi na buge kai na shi yasa nake kuka". "washh sannu, har yanzu kinajin zafi"?
Ta girgiza kai alamar ya daina, yayi murmushi ya ce "me kika dafa mana"? itama murmushin tayi ta ce "ka taso amaryar taka kuzo muyi brk".
ya d'an b'ata rai ya ce "ita batasan ta taso bane, batta kawai".
ta waro ido ta ce "Ba ayi hakaba, bak'uwa ce fa".
susa kai yayi yana dariya, yamata kiss a kumatu ya nufi d'akin Fateema, duk ta yaye bargon da ya rufe ta dashi gashi babu ko pant a jikin ta tana baccin ta, ya zuba mata ido na tsawon lokaci, tunawa yayi da dad'in dayasha, nanfa wani sabon sha'awa ta taso mishi, ya haye gadon yana d'an bubbuga ta, gyara kwanciyar ta tayi ta ci gaba da baccin ta, ya kai bakin shi kan k'afar ta ya fara lasa har ya iso wajen cinyar ta, kamar a mafarki takeji, jin ya wuce
gona da irine yasata bud'e ido, wani malalacin murmushi ya sakar mata, itama murmushin ta masa ta dad'a janyo shi jikin ta, cikin muryan kuka ta ce "Kar kasake mun da zafi".

ya shafi sumarshi ya ce "yanzu bazaki ji zafi ba".

Tunawa tayi da maganar Aunty Fauzee "Kada kiyi wasa da

*SHIMFID'AR MIJINKI*

shine gatan auren ki, idan har baki kula da shimfid'ar sa ba zaki wayi gari kiga ya daina b'are2 akanki, a sannu zaki nemi soyayyar ma ki rasa, kada kiga kina amarya yanzune yakamata ki gyara SHIMFID'AR ki basai lokaci ya k'ure ba, ki jure duk zafin da zaki sha na kwana biyu ne kawai.....

Murmushi tayi ta bank'aro k'irji, nanfa ya dad'a rikicewa, ta zura bakin ta a nashi ta fara jujjuya shi, tuni ya manta da maryam na jiran su, saida suka nutsu ya tuna, tare sukaje sukayi wanka sai shagwab'e masa takeyi yana lallab'a ta.
"muje muyi brkfst Maryam na jiranmu".

Ta ce "Ba yanzu ba bacci nakeji".

ya tsareta da ido ya ce "kinsan k'arfe nawa kuwa, idan kinci sai kiyi baccin".

"To amma bazan iya futa ba kad'auko mun sai
muci anan".
tsintar kanshi yayi da cemata "to".

yana barin d'akin tayi sauri ta saka key ta koma ta kwanta, wayar ta ne ya fara ruri ta tashi ta d'auko, ganin Sakina yasa ta saki dariya ta d'auka.

"Amarya Amarya".

"ke ina wani amarya nasha azaba, wlh dak'yar nake tafiya".

Sakina ta kwashe da dariya ta ce "Kice kin more, kinga yanzu ne ma yakamata ki kula da kanki kada kwana biyu aji kin buga, ki tashi yanzu ki da'au gyanyen magaryan nan ki dafa ki shiga ciki, 30mnt ki fito ki goga man zaitun zakiji kin warware, idan kin gama ki k'irani".

"to k'awata".

kettle ta kunna cikin hanzari ta dafa ta juye a baf, yana d'an hucewa ta shiga ciki harda 'yar k'ararta daga baya kuma tafarajin dad'i yana shigar ta.
.
.



Azaune ya sameta ta rafka tagumi.

"kinsan Allah yarinyar nan bata tashi ba".
binshi tayi da kallo kafin tace "shine ka shanyani kaje kayi zamanka"?

ya lakuce mata hanci ya ce "fanfon toilet d'in tane naji ruwa yanata zuba ashe b'aci yayi da k'yar nasamu na gyara".

Ta sauk'e ajiyan zuciya, ta fara zubawa yace

"ki zuba naki yanzu banajin yunwa sai anjuma zanci".

mamaki ya kamata, ta fara ganin canji har acikin k'wayar idon shi, ta basar ta zuba nata taci ta k'oshi ta wuce d'aki ta barshi, mamakin ta ya k'aru ganin bai biyota ba, ta lek'o shi taga waya yakeyi don haka ta masa uzuri.

Share this

WhatsApp
Email ThisBlogThis!Share to TwitterShare to Facebook
Newer Post Older Post Home

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts

  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 11 to 20
    Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima.     Casuke A...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 31 to 40
    Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gado...
  • RAINA KAMA Book 1 Page 1 to 10
    RAINA KAMA......!!♦_*                _{Kaga gayya}_          *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!._* 👉🏻1⃣      *Matsanan ...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 21 to 30
    Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”.         Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, murya...
  • BARIKI AUREN SOJA Page 51 to 60
    Motocine guda shida aka ajiye musu sababbi dal suna sheki ta tsakiyar tasha Adon balloon kana gani Kasan motar AMARYA ce ta fito tareda su ...
  • KASUWANCI NA Page 61 to 70
    Ameer kasa jurewa yayi gaba daya jikinsa ya fara rawa,tunawa Meenat tayi ba Muharraminta bane sai ta dan matsa kamar zata fada kasa ta wayan...
  • KASUWANCI NA Page 31 to 40
       A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, d...
  • UMURNIN IYAYE Page 51 to 60
    Suna isa asibitin emergency ward aka shiga dashi  Wani kujera suka zauna akai Hakeem yana shafa bayan Mami a hanakali yana bata hakuri shim...
  • UMMU AYMANA Part 6
      *UMMU AYMANA PART 6* Suna isa Asibitin likitoci suka rufu akanta,wanda da taimakon Allah bata jimaba ta farfaɗo se kuka takeyi,prince kasa...
  • MACIJINE SHI Page 31 to 40
    _________________Kai tsaye part ɗin nanny Adeeb ya nufa da fattu,suna zuwa kuwa nanny ta gyara ko ina sai ƙamshi ke tashi,dakin fattu suka...

Categories

  • 'YA'YA DA KUDI 1-END (8)
  • 'YA'YA MATA 1-END (9)
  • 'YAR BOKO 1-END (6)
  • 'YAR FULANI 1-END (14)
  • 'YAR GIDAN TSOHUWA 1-END (6)
  • 'YAR JAMI'A (9)
  • 'YAR MAFIYA 1-END (6)
  • 'YAR TALAKAWA 1-END (7)
  • AGOLA 1-END (17)
  • AKIDATA BOOK 2 Page 45 -End (11)
  • ANAL 1-END (12)
  • ANTIN YARA 1-END (6)
  • AUREN JARI 1-END (9)
  • BAKAR MACE 1-END (3)
  • BARIKI AUREN SOJA 1-End (8)
  • BINTU 1-END (7)
  • CIN AMANA KO FANSA 1-END (10)
  • CIWON IDANUNA 1-END (7)
  • CIWON IDANUNA AUDIO (2)
  • DAGA TAIMAKO 1-END (5)
  • DAKON SO 1-END (4)
  • DAMA TA BIYU 1-END (13)
  • DR BOBBY 1-END (11)
  • DUBU CIKAR MAI CARBI 1-END (7)
  • FULANI 1-END (11)
  • GURBIN IDO 1-END (1)
  • HADIN ALLAH 1-END (8)
  • HIBBAH 1-END (4)
  • INA ZAN GANSHI 1-END (7)
  • INAYA 1-END (9)
  • JIDDARTIL KHAIR 1-End (1)
  • JIHADI 1-END (10)
  • JUWAIRIYYA 1-END (7)
  • JUYAYI PAGE 1-END (6)
  • KASUWANCI NA Page 1-End (1)
  • MACIJINE SHI 1-END (1)
  • MAH NOOR 1-END (5)
  • MAIMOON 1-END (10)
  • MAKARANTAR KWANA 1-END (5)
  • MAKAUNIYAR KADDARA 1-END (10)
  • MATAR ALI 1-END (10)
  • MIWASMITI 1-END (8)
  • MOTAR KWADAYI 1-END (4)
  • NAMIJI BAYA KADAN 1-END (16)
  • NI AYS NAKE SO 1-END (16)
  • RAINA KAMA 1-END (1)
  • RAYUWATA 1-END (6)
  • SHIMFIDAR MIJINA 1-END (3)
  • SONE AJALINA 1-END (5)
  • SURBAJO 1-END (14)
  • TUDUN DAFAWA 1-END (4)
  • TUZURU 1-END (6)
  • UMAR KO FARUUQ 1-END (5)
  • UMMU AYMANA 1-END (8)
  • UMURNIN IYAYE 1-END (7)
  • WAMINAL HOOB 1-END (9)
  • YAN MATAN ZAMANI 1-END (6)
  • ZAYN MALIK 1-END (10)
  • ZUCIYA KOWA DA IRIN TASA 1 (10)
  • ZUMA SAI DA WUTA PAGE 1-END (7)

Social Plugin

  • facebook
  • twitter
  • instagram
  • youtube

Hausa novels 2023

Search This Blog

Powered by Blogger.

Blog Archive

  • July 2023 (7)
  • June 2023 (65)
  • April 2023 (33)
  • March 2023 (132)
  • January 2020 (10)
  • December 2017 (62)
  • November 2017 (33)
  • October 2017 (38)
  • September 2017 (39)
  • August 2017 (75)

Report Abuse

Total Pageviews

Copyright © 2023 To Hausa novels 2023 | Powered By WwW.aysnovel.com.ng
Design By Aysha Adam | Theme By WwW.aysnovel.com.ng | Distributed By Aysha Adam