Hausa novels 2023

  • Home
  • Ciwon Idanuna
    • Internet
    • Market
    • Stock
  • Agola
    • Dvd
    • Games
    • Software
      • Office
  • Mijin Biza
    • Child Category 1
      • Sub Child Category 1
      • Sub Child Category 2
      • Sub Child Category 3
    • Child Category 2
    • Child Category 3
    • Child Category 4
  • Kwarata
  • Health
    • Childcare
    • Doctors
  • Inda Ranka

Monday, November 13, 2017

HIBBAH Part 11-15

 November 13, 2017     HIBBAH 1-END     No comments   

HIBBAH Part 11-15
.
Lokacin Ummah tayi shirin tafiya k'auyensu don duba mahaifiyarta ba lfy, kwana biyu da tafiyarta matar Baffah tazo ta d'aukeni Wai idan Ummanah ta dawo zata dawo dani Lokacin dana koma gidan da zama ba laifi ina samun kulawa duk inda zata tare muke zuwa kullum cikin ado nake.   Lokacin da Umma ta dawo bata taga ana kula dani bata nemi indawo garetaba Tunda taga banda wata matsala.   Kud'in data kaima aminin mijinta dubu talatin da biyar ya cika dubu biyar yazama arba'in yasamusu gida Saidai unguwar ba mutane sosai kuma yawancinsu ba musulmai bane, tace bazasu koma yanzunba sai wajen ya cika da mutane,tasami Kawu Usman akan tanaso ta nemi gidan haya ta koma sabida nauyi yayi yawa a kanshi, ba yadda baiyiba da ita akan ta hakura taci gaba da zama Amma taki tace "gara yaje ko wankin kud'i da wanke_wanke zatayi don rik'e yaranta"  haka ya hakura ta nemi gidan haya a unguwar Dutsen Tanshi, ta kwashi yaranta suka koma chan da zama.   Bayan komawarsu tasamama Sadeeq wajen gyaran mashin idan yadawo makarantar boko yakanje wajen gyaranshi da yammaci kuma su tafi Islamiya, ita kuma tana d'an sana'arta tana samin abunda zasusa abaka.    

*YARAYUWAR HIBBAH YAKE CIKI*
.
Tsawon wata biyu *HIBBAH* nashan gata   ashe duk kiwonta suke daga baya komai ya chanza ta dawo tamkar baiwa, itake share share daga d'akuna har cikin gida ga lodin wanke_wanke ga aika kamar me duk nisan aika ita kezuwa ga yaransu ba abunda suke akatawa.   Umma tana kokari sosai wajen kula da yaranta da basu tarbiya wani lokacin abunda zasucima gagararsu take, yadda Allah ya taimakesu mutanen dasuke hayar sunada kirki suna d'an taimaka musu.  
.
Lokacin da yara suka sami hutu duk ta tattarasu suka tafi kyauye hutu, sanda taje taga sauyi sosai wajen mahaifinta, abun ya mugun bata mamaki Amma sam bata nunaba, bayan dare yayi sun ke'be da mahaifiyarta take tambayarta meke faruwa taga mugun sauyi gurin mahaifinta. Nan take gayamata sharrin da kishiyoyinta suka mata "iyayenkine suka sami Babanku Wai ninama yaransu asiri shiyasa sukaki auruwa, Tunda ga nawa yara mata uku sunyi aure don haka dole inje in karya asirindana na musu, namasu rantsuwar 'ba sanin gurin wani mai asiriba balle har inje in musu, munyi rikici sosai har maigari saida yashiga zancen tukunna nasamu sukuni." "Lallai mama kina cikin ukuba"  "Humm!  "kedai bari Allah ne kawai zai fiddani, domin yanzu zaman rashin y'anci nake a gidannan, ace Tunda yarantarmu bamuyi hakanba da mahaifinku saida tsufa   yazo mana, danasa abun araina Amma daga baya na cire don nasan bayin kanshibaba k'ullaliya akamai." "Amma wannan abun da tashin hankali, ina tunanin baba yaje dahar zai zauna mata su shiryama wannan kullin? Allah tona asirinsu kekuma yakara miki hakuri da juriya."           "Ameen"  Sundau lokaci mai tsawo suna hirarsu daga baya suka kwanta.   *Washe gari* Bayan umma taje gaida mahaifinta da k'ar ya amsa yana cin magani, hakadai ta bashi tsarabar data kawomai, shaddace yadi biyar da takalmi da hula ko kallonsu baiba yace ajiye acan "idan kin karya kizo zamuyi magana"  "toh"  Saidatabi kowani d'aki ta gaidasu har makwabtansu duk tashiga ta gaidasu sanda ta dawo tasamu ancikasu da abun karyawa, bayan tad'an taba ta nufi d'akin mahaifin nata, yace "takoma ta kira mahaifiyarta yanason ganinsu"  Juyawa tayi taje ta kirata sannan suka dawo, gyaran murya yayi sannan yafara magana "Hadiza!  Saida Umma taji wani iri don baisaba kiranta da sunantaba kasancewar itace d'iyarshi ta fari,  " Naam baba" Inaso yaran dake hannunki ki maidasu wa dangin mahaifinsu don anfara kawomin korafin kinabin maza acan,   Atare Umma da mahaifiyarta sukad'au salati INNALILLAHIWA'INNA'ILAIHIRRAJI'U  
.
  Daga Mama har Umma kuka kawai sukayi, Wai yau mahaifintane da kanshi yake gayamata tanabin maza, yau Mahaifintane kece tana zina, mahaifindaya bata tarbiya tundaga tsumman goyonta har yazuwa yanzu Amma shike mata wannan mummunan zato. _innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un_  wannan wacce irin jarabawar rayuwace take shirin fuskanta. Haka yagama maganganunshi wani zancenma dagaji had'ine, saida yagama tsaf sannan ya sallamesu.  Abun mamaki sukagani lokacin da suka fito daga d'akin Matan Baban Umma su biyu suna la'be agefen k'ofar sai murna suka ga dukkan alamu sunji me akace.  Wucesu kawai sukayi aiko Umma suna bada baya suka kwasheda dariya sukace "kad'an kuka gani"  Mama tace "ALLAH yafiku dashi muka dogara."   Wunin ranar Umma a d'aki tayishi don data fito za'a mata habaici.   *
.
*CIKIN DARE*  Ummane da Mama ke magana Mama tace "Saidai ki hakuri don yanzun saikin toshe kunnenki don zakisha maganganu, tunda kina zaman gdn hayane ba tare da wani nakira don Allah idan kinkoma kiyi k'ok'arin fidda miji cikin manemanki ki aure hakan zaisa ki fita zargi.  " Nifa ba aurenne bansoba wanda zai rik'eni da yarana hud'u shine abun tunani tunda kinga duk dagin mahaifinsu ba wanda yakuma waiwayansu badon kuma basunan ba suna raye kuma dukkansu sunada rufin asiri daida gwargwado. " " kidainasa damuwarsu aranki kedai ki kula da yaranki koda wasa ban yarda kibasu yarankiba" "Insha Allahu zan sadauk'ar da rayuwata don kula dasu, ran Monday insha Allah zamu koma don zamanmu zai zame miki 'bacin rai tunda wunin yau bak'ak'en maganganu kawai suke jifarki dashi a dalilina" "Allah yakaimu gobe asabar da lahadi saiki zazzaga gidajen y'an' uwa"  Saida sukasha hirarsu sannan sukayi bacci dama yaran sun jima da bacci.   *Washe gari* Umma taje ta gaida mahaifinta sannan tabiya d'akin matan Baban nata biyu ta gaidasu da kyar suka amsa gaisuwar, yaranma sunje sungaida kowa, wanka sukayi sukafice ziyara gidan y'an'uwa.  Basu suka dawoba saidare suka dawo gida, washe garima haka suka sake ficewa Saidai yau da wuri suka dawo don shirye_shiryen tafiya.   'Dakin Mama cike yake da kayan abinci irinsu Wake, gyad'a, gero, dawa, masara, bushashshen ku'baiwa, Kuka,  daddawa, shinkafa, tsintsiya duk mutunene suka turo musu dashi a hakanma harda basu hak'uri. 
.
Da daddare saida Umma tabari kowa ya rufe k'ofa ta nufi d'akin Baba ahankali ta tura k'ofar tareda sallama tashiga zaune yake kan kujera yana saurarar Radi'o amsa sallamar yayi tare da fad'in "lafiya da darennan"  "lafiya lau Baba. " waja tasamu ta zauna tafara magana "nazone dama inbaka hak'uri kan abunda ake fad'a game dani, nasan sharri akamin kuma kowaye nabarshi da Allah. Da sannu Allah zaimin sakayya, nayi mamakin yarda da kayi akan maganar kafi kowa sanin wace ceni, kafikowa sanin irin tarbiyar da kamin, tunda yarintana banyi Zinaba saida girma yazomin ribar mezanci, bayan nasan girman zunubi irinna mazaunai. Tayaya zanciyar da yarana da haram bayan nasa dukkan jikin da aka raimeshi da haram bazai shiga Aljannahba."kukane yaci k'arfinta tace "gobe insha Allah zamu koma ina mai neman afwarka ka gafarceni Insha Allahu dana koma zanyi Aure domin kare kaina da zargi." batajira amsarshiba ta tashi tayi gaba shikam yayi mutuwar zaune tana fitowa taga kishiyar Mama mak'ale da alama taji duk abunda tace, wucewa tayi tare damata addu'ar shiriya ita kuma ta shige d'akin Baba.     ~
.
  *WASHE GARI*   Umma sungama shirin tafiya zuwa k'arfe takwas motarsu zai tashi, yanzu wajen karfe takwas da minti hamsin tana jiran Baba ya dawo suyi sallama amma bashi ba labarinshi, tun asuba daya fita sallah bai dawoba, k'arshe dai tafiya sukayi ba tareda sallamabah.   _
.
Su Ummah Allah kiyaye hanya, yabada hak'uri_  Tun dawowarsu Umma taje taga Hibbah takuma basu tsarabarsu, bata kuma komawa gidanba, don randa ta koma gida tayi kuka sosai yadda taga Hibbah ta dawo, duk wani aikin gidan ita keyi hatta gjrkin gidan itace bata da wani lokacin kanta, da zarar ta tashi tun asuba tayi sallah zata fara sharan gida tana gamawa ta fara abun karyawa sai ta sallami kowa sau tari haka take tafiya makaranta ba tare data karyaba, tana aji biyar na primary Allah yabata baiwar ilmi na boko da arabic.   _(ba doleba tunda Umma da Abba ba dama wajen ilmi ta kowani fanni)_  Haka rayuwa tacigaba da tafiya wani lokacin asamu wani lokacin arasa, Umma sun daidaita da wani bawan Allah yanada yara Uku biyu mata d'aya na miji, Allah yama mahaifiyarsu rasuwa.   Lokacin da suka daidai tamai maganar yaranta guda hud'u yace "ba komai d'a na kowane."   Lokacin da sukayi aure komai yana tafiya daidai daga baya kuma halinshi na asali ya nuna, ba abinci, sutura, duk wani hak'k'i daya rataya kan miji baya baya badawa, da Umma taga haka tuni ta ware ta fara wankin kud'i shima ba kullum ake samuba gashi lokacin tana da ciki, haka suke rayuwa idan tasamu tayi wankau kud'i suci abinci inbabu su hak'ura daga baya ya tsiri sabon salon iskanci idan yadawo aiki saiya siyo abinci yashige d'aki ya k'ira yaranshi suci, da Umma ta fuskanci hakan bata nuna damuwartaba don tasan ba wanda zai iya mata d'awainiya da yaranta tunda dangin ubansuma sun gaza balle wanda bai had'a jini da suba.         
.
    Haka Umma ta ware tana neman abun rufin asirinsu ita da yaranta.

Share this

WhatsApp
Email ThisBlogThis!Share to TwitterShare to Facebook
Newer Post Older Post Home

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts

  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 11 to 20
    Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima.     Casuke A...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 31 to 40
    Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gado...
  • RAINA KAMA Book 1 Page 1 to 10
    RAINA KAMA......!!♦_*                _{Kaga gayya}_          *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!._* 👉🏻1⃣      *Matsanan ...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 21 to 30
    Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”.         Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, murya...
  • BARIKI AUREN SOJA Page 51 to 60
    Motocine guda shida aka ajiye musu sababbi dal suna sheki ta tsakiyar tasha Adon balloon kana gani Kasan motar AMARYA ce ta fito tareda su ...
  • KASUWANCI NA Page 61 to 70
    Ameer kasa jurewa yayi gaba daya jikinsa ya fara rawa,tunawa Meenat tayi ba Muharraminta bane sai ta dan matsa kamar zata fada kasa ta wayan...
  • KASUWANCI NA Page 31 to 40
       A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, d...
  • UMMU AYMANA Part 6
      *UMMU AYMANA PART 6* Suna isa Asibitin likitoci suka rufu akanta,wanda da taimakon Allah bata jimaba ta farfaɗo se kuka takeyi,prince kasa...
  • MIWASMITI Page 31 to 40
    Kuka ta Kuma saki gamida kamo hannushi ta matse a tsakiyar qirjinta Dan jin wani irin suka da yake mata Ga jiri da takeji gaba daya bata gan...
  • KWARATA Part 46,47,48,49,50
    🅿 ------ 46           Tsare Mamy nayi da ido na kasa magana duk saida ta gama buɗemin komai ta ƙare da cewa harma ta gayyato shi zaizo kats...

Categories

  • 'YA'YA DA KUDI 1-END (8)
  • 'YA'YA MATA 1-END (9)
  • 'YAR BOKO 1-END (6)
  • 'YAR FULANI 1-END (14)
  • 'YAR GIDAN TSOHUWA 1-END (6)
  • 'YAR JAMI'A (9)
  • 'YAR MAFIYA 1-END (6)
  • 'YAR TALAKAWA 1-END (7)
  • AGOLA 1-END (17)
  • AKIDATA BOOK 2 Page 45 -End (11)
  • ANAL 1-END (12)
  • ANTIN YARA 1-END (6)
  • AUREN JARI 1-END (9)
  • BAKAR MACE 1-END (3)
  • BARIKI AUREN SOJA 1-End (8)
  • BINTU 1-END (7)
  • CIN AMANA KO FANSA 1-END (10)
  • CIWON IDANUNA 1-END (7)
  • CIWON IDANUNA AUDIO (2)
  • DAGA TAIMAKO 1-END (5)
  • DAKON SO 1-END (4)
  • DAMA TA BIYU 1-END (13)
  • DR BOBBY 1-END (11)
  • DUBU CIKAR MAI CARBI 1-END (7)
  • FULANI 1-END (11)
  • GURBIN IDO 1-END (1)
  • HADIN ALLAH 1-END (8)
  • HIBBAH 1-END (4)
  • INA ZAN GANSHI 1-END (7)
  • INAYA 1-END (9)
  • JIDDARTIL KHAIR 1-End (1)
  • JIHADI 1-END (10)
  • JUWAIRIYYA 1-END (7)
  • JUYAYI PAGE 1-END (6)
  • KASUWANCI NA Page 1-End (1)
  • MACIJINE SHI 1-END (1)
  • MAH NOOR 1-END (5)
  • MAIMOON 1-END (10)
  • MAKARANTAR KWANA 1-END (5)
  • MAKAUNIYAR KADDARA 1-END (10)
  • MATAR ALI 1-END (10)
  • MIWASMITI 1-END (8)
  • MOTAR KWADAYI 1-END (4)
  • NAMIJI BAYA KADAN 1-END (16)
  • NI AYS NAKE SO 1-END (16)
  • RAINA KAMA 1-END (1)
  • RAYUWATA 1-END (6)
  • SHIMFIDAR MIJINA 1-END (3)
  • SONE AJALINA 1-END (5)
  • SURBAJO 1-END (14)
  • TUDUN DAFAWA 1-END (4)
  • TUZURU 1-END (6)
  • UMAR KO FARUUQ 1-END (5)
  • UMMU AYMANA 1-END (8)
  • UMURNIN IYAYE 1-END (7)
  • WAMINAL HOOB 1-END (9)
  • YAN MATAN ZAMANI 1-END (6)
  • ZAYN MALIK 1-END (10)
  • ZUCIYA KOWA DA IRIN TASA 1 (10)
  • ZUMA SAI DA WUTA PAGE 1-END (7)

Social Plugin

  • facebook
  • twitter
  • instagram
  • youtube

Hausa novels 2023

Search This Blog

Powered by Blogger.

Blog Archive

  • July 2023 (7)
  • June 2023 (65)
  • April 2023 (33)
  • March 2023 (132)
  • January 2020 (10)
  • December 2017 (62)
  • November 2017 (33)
  • October 2017 (38)
  • September 2017 (39)
  • August 2017 (75)

Report Abuse

Total Pageviews

Copyright © 2023 To Hausa novels 2023 | Powered By WwW.aysnovel.com.ng
Design By Aysha Adam | Theme By WwW.aysnovel.com.ng | Distributed By Aysha Adam