Hausa novels 2023

  • Home
  • Ciwon Idanuna
    • Internet
    • Market
    • Stock
  • Agola
    • Dvd
    • Games
    • Software
      • Office
  • Mijin Biza
    • Child Category 1
      • Sub Child Category 1
      • Sub Child Category 2
      • Sub Child Category 3
    • Child Category 2
    • Child Category 3
    • Child Category 4
  • Kwarata
  • Health
    • Childcare
    • Doctors
  • Inda Ranka

Monday, March 13, 2023

UMURNIN IYAYE Page 41 to 50

 March 13, 2023     UMURNIN IYAYE 1-END     No comments   

Shi wayanshi yake kalla se tafiya takeyi tana murmushi ita daya  
Yana dagowa seya ga wani store
Ta hango anyi hanging wani riga ae da sauri ta tsayar da motan
Ta cire belt din tana kukarin fitowa yace ina zaki
Ciki mana tace kana ta fito shima ya fito suka shiga tare
Gun rigan ta fara zuwa ta cira ta shiga ta gwada daidai ita daga nan ta fara sayan shirman mun kaya shi kuma yana tsaye a bakin basket dinda take ajiyewa idan ta lebu da wayanshi a hannu danshi mayen waya ne kuma be wani social media kawai tsaban karatu ne online

Can ita ta shiga gwada wani wando data gani crazy shi kuma still yana tsaye se wata budurwa tazo tayi mai sallama 

Dan rashin mutunci irin nan Adeel ya nuna bega wani halittaba agun ta sake mai magana a lokacin ne ya dago ya cire glasses dinda ke idonshi tace sannu se ya daga mata kai kawai ya maida

Tace dan Allah tamabaya nakeson nayi maka
Seya sake daga mata kai

Yarinyan nan dake ajiye kaya anan matarkace koh sister kah
Sedaya bata mata lokaci kana yace sister na can i help you??

Setayi murmushi tace toh dan Allah zan iya samin phone number ka cus inason mu zama frndz ne
Wannan karan gabadaya ya cire glasses din ya kalleta daga sama zuwa kasa ya yamutsa fuska yace Nah!! Not intrested yaja basket din ya wuce inda ake biyan kudi

Abun ya kular da ita dan ba'a taba yi mata irin wannan disgin ba a rayuwanta ta dauka tsinman kafafuwanta da wuce
Ita irin matan nan ne yan duniya dan daga shigansu ma zaka gane hakan

Yana zuwa aka juye kayan ana lissafa kudin shi kuma yanata kalla2 inda ze hango Ameenah har aka gama bata zo bah
Ita koma taje inda ta barshi amma bata ganshi bah seta fito ta ganshi a tsaye agun bada kudi ta ajiye wandon dake hannunta ta kalla Adeel ya sakan mata wani harara itama ta maida mai 

Yace an gayan maki ni bawan gidanku ne
Tace waya sani tana kukarin bude wallet dinta

Haka kikace koh Hmmmm.
Aka mike masu bags kaya seya nuke ya wuce ya barta agun be amsa koh daya bah
Ta mika ma matan gun creadit card dinta danta cire kudin setace mata ae mijinta ya biya
Ta kalleta tace waya gayan maki mijina ne toh yayana ne ta amsa bags ta wuce tana zuwa gun motan tasa a baya shi kuma tuni ya shige gun driver 
Tana budewa zata shiga taga mutun agun 
Ya mika mata hannu alaman ta bashi keys din 

Ta kalleshi ta kalla hannun tace tahb nida motana
Yace wlh idan baki bani bah zan maki abunda baki so kuma maganan school you should just forget about it haka zaki ta zaman gida babu ke ba fita harki tsofa

Badan taso bah ta buga mai keys din a hannu ta koma dayan gefan ta zauna tana kunkuni wai ita da motanta za'a mata karfin hali
Beyi magana bah dukda yaji abunda take cewa yaja motan suka koma gida suna isa ya fito haka ta jido kayan ta shiga dasu dakinta

Ana gobe zata fara zuwa school dan ya rigada ya gama mata komai xuwa kawai ya rage 
Duk se zumudi takeyi ta hau kan kujera ta sauko da akwatin lefanta dan duk sunyi kura ta ajeye ta zaba kayan da zatayi amfani dashi su inner wears kayan kwalliya jakankuna talama da sauransu duk ta zaba raguwa ta maidasu dan ba kalanta bane atamfa kowa koh daya bata dauka bah 
 
_Washe gari_

Tana tashi ta duba time table dinda Adeel ya bata wuraren 12 takeda lectures dan haka ta shiga kitchen ta soya dankali da kwai ta hada mai akan dining ta gyara gidan taje tayi wanka riga da wand tasa seta zunbula katon hijab ta dauka designer bag dinta na _kylie_ wanda Abbah ya bata sanda zeyi mata dadin baki ta fito parlo sannan shima ya tashi ya fito a shirye yana break-fast ta sama karamin bowl ta zuba a ciki itama tana ci ya kalleta yace tunda kike baki taba kamada musulma ba se yau

Koh kallonshi batayi ta cigaba da cin abincin ta abunda ya tsana kenan yayi magana ayi banza dashi amma shi yanason ya ringa ma mutum ya mike ya dawo kujeran kusa da ita ya juyo da kujeranta yana facing dinshi yace nayi maki magana kinyi banza dani yana magana amma tana jin nunfashin shi a fuskanta 
Tace naji thank you!
Yayi murmushi ya mike ya kuma inda yake zaune yace you are welcome ta sakan mai harara ita tun ranan dayayi kissing dinta seta fara jin tsoranshi ta wani gefan dan haka daya gano se yake using dinshi agenst her.

Tare suka fito dan ita bata san makarantan bah saboda haka shi ze kaita harta kama hanyan zuwa gun motanta ya kalleta yace do you expect me na kaiki kuma na bar maki motan Mmm!
Dan haka seta dawo gun motanshi black *KIA* ta shiga suka fita se makarantan lokacin har 11 tayi 
Suna isa babban makatanta ne suka shiga ciki da mota kan suka fito ya kira wani mutum a waya yazo hargunsu ya hadusu da Ameenah dan abokin Adeel ne class mate dinshi a secondary school kuma lecturar ne a makarantan dan haka shine ze nuna mata makaranta shi kuma ya koma dan yaga time-table dinta yasan nawa zata gama seya dawo ya dauketa

Yana tafiya gun wani katon gini ya tsaya a gaban ansa *LAWIZAS* ya fito daga motan ya shiga yaune first day dinshi dan ze fara aiki ne saboda ya gaji da zaman gida dan haka idan yanada game seya ringa dauka live kawai tunda shi daman architec ne abunda yayi studing yana shiga aka kaishi office dinshi aka nuna mai Asistant dinshi wata mace ce 

Ameenah ana kaita class dinsu ba'a dade ba aka fara lectures dayake english suke dashi 
Suna gamawa ta fito ta sama kujera ta zauna tana jiranshi yazo ba'a dade ba se gashi suka taho gida tana shiga ta ajiye jakanta da hijab a parlo ta wuce kitchen ta hada mai abinci ta ajiye akan table ita kuma ta dauka maltina ta bude tana sha seya dago ya kalleta se a lokacin ta tuna shigan da tayi crayz tasa se wani top me V neck seta kinkima jakanta zata gudu daki yace dawo nan taki kulashi yace wlh idan baki dawo bah zan biyoki dakin ta dawo tareda kare kirjinta da hijabin

Ya mike a haka kika fita daman,no wonder kika zunbula katon hijab toh wlh karki kara yanxin idan kika manta kika daga fah
Ta kalleshi tace kana magana kaman kana kishi na se tayi murmushi ta wuce daki

Da karfi yace meyasa zanyu kishin ki mstewww!! Se wayanshi tayi ringing yana dubawa Mommy ce suka gaisa take cemai gobe zasuzo itada safieyarh yayi murmushi yace toh se kunzo sukayi sallama yaji dadi dan a gaskiya yayi kewarsu ba wasa 

Yayi knocking dakin Ameenah "Uhmmm" kawai tace yace fito ya kuma parlo
Seda ta gama shanye maltina seta mike ta shiga closet dinta ta dauka wani jacket shara shara ta daura akai ta fito

Wetin??
Ni kike cema wetin yace
A hankali tace toh kai waye dan kaga ina ma sanyi kwana biyu ta juyarda bakinta 

Heheh zanyi maganaki Mommy da safieyarh zasuzo gobe 
Ae data daka wani tsalle tareda ihu se kuma ta daura fuska a lokaci daya tace karfe nawa dan inada class gobe

Ya kalleta yace kaji yar rainin wayo toh ban sani bah 
Ta kama hanyan daki tace kai ka sani din me halin mugaye
Taga alaman ze mike seta karasa da sauri ta kulle kofan

Shi gyara zama yayi dan yasan idan ya mike kafin yakai ta shige mutun kaman tsinke

*****

Ta ringa zumudi ta shiga gyara dakinta dukda a gyara yake ta shiga closet ta debo wasu atanfa wanda Mami tayi mata bata taba sawa ba ta debo su guda shida ta ajiyesu dan da ta turasu wani gune ta fito guest room ta shiga tadan karkade ta wanke toilet seta dawo tana rike da kukunta wai ta gaji

Wanka ta shiga ta fito tasa kayan bacci lokacin biyar ma batayi bah dan tasan ba inda za[truncated by WhatsApp]
[20:27, 3/5/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹UMARNIN IYAYEπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹



WRITTEN BY:
                      TYETYELORH

_diz page is for you guyz Mama da Baba i luv you so very mch i dn't knw how to do without you i luv you, i luv you there is no word to describe it all i knw is i can do anything just to see dat we are together forever i really can't do without you we will be here for you no matter how. One month to you guyx 37year anniversary can't wait we love you_❤


_In dedication to Aysha wakili and Aysha sayedi *ILY* guyz and more grace to your elbow_πŸ’‹


                          πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹


*114*

_Washe gari_

Karfe shida ta tashi tayi sallah dan bata samu ta tashi da asubah bah tana gamawa tayi wanka ta shirya cikin duguwan riga ta yafa gyale ta dauko handbag dinta ta ajiye a parlo ta kalla agugu sauran 20 mintues 7:00am yayi kuma bakwai daidai tanada class se 10 zata fito se kuma gobe dan haka da sauri ta hada mai sandwitch ta ajiye ta bude jakanta ta ciro ta rubata mai note cewa ta tafi makaranta dan tanada class karfe bakwai ta ajiye kusa da sandwitch din ta dauka jakan da sauri ta fita ta shiga motanta ta wuce tanata tafiya tayi nisa se hold-up ya tsayar da ita tana tsaye se taji anyi knocking windon motanta ta dayan gefan ta saukar da kadan wata tsohowa ce irin ta tsofa sosai tace sannu yarinya

Ameenah ta kare mata kallo sannan ta gaidata ta amsa da murmushi kwance a fuskanta 

Kana tace yarinya kinada baiwa wanda ban taba ganin irinta ba a duniya 

Tayi murmushi tace nagode ta bude wallet dinta ta ciro 500 ta mika mata 
Tace ni ba almajira bace kawai gayan maki nayi dan randa zaki gane baiwan nan naki zakiji dadi sosai haka ma mijinki zeyi alfahari dake dukda baku son junanku seta juya ta wuce 

Tana kallon tsohowan harta juya se kanta ya daure taya tasan bamuson juna setayi sauri ta fito ta duba tsohuwan nan sama da kasa amma ta rasa haka ta koma cikin motan ta wuce makaranta

Tana isa da sauri ta fito har lecturar ya shiga ta shiga ta sama waje ta zauna yana teaching amma hankalinshi yana kanta duk ta gama tsarguwa duk daguwan da zatayi se sun hada ido dan haka ta mike tareda cewa i cn't take it duk aka kalleta ta dauka littafin data fito dashi tareda handabag dinta ta kama hanyan fito yace Mrs. Adeel where are you heading to??

Ta kalleshi se kuma ta tsaya taje gab dashi tace "so you know am married msteww" seta fita 
Duk aka tsaya ana kallonta 
Tana fita gun motanata tayi ta shiga ta fuzga da karfi ta kama hanyan gida tanata faman bala'i ita daya a mota 

Adeel ya fito a shirye gun dining ya nufa ya bude kolan data sa sandwitch din ya cira daya seya tafi kitchen yana ci ya dauko tea cup ya dawo ya hada tea yana zama ze fara sha kenan se idonshi yakai gun paper ya dauka ya karanta se kuma ya tsaya yana kallonshi kawai can seya ajiye ya cigaba da break-fast dinshi yana gamawa ya mike ya shiga daki a gaban mirror ya tsaya seya cire holan kanshi ya sake cambing gashinshi ya maida holan yayi murmushi se kuma ya fito key din motanshi ya dauka ya fito su basu ma damuda sa key a kofan bah 

Motanshi ya shiga ya fito daga gidan

Tana karya kwanan shiga layinsu seta hango motanshi tana zuwa dab dashi harta dauke kai setaga ya tsayarda motanshi dan haka ita ta tsaida nata a tare suka sauke glass din window ta kalleshi yace meyafaru kika dawo da sauri yana magana yana kallon agogan hannushi 
Seda ta dan yamutsa fuska sannan tace kawai lecturar ne ya ban haushi 

Tahb kawai yace ya kulle glass din a tare kowa ya kama gabanshi
Tana shiga gida tayi packing ta fito ta shiga ciki dakinta ta tafi ta ajiye handbag dinta ta cire duguwan rigan jikinta tasa rigada wando ta fito kitchen ta shiga ta rike kukunta tanata faman kallon kitchen din ta rasa mezata dafa masu mommy se kawai ta daura ruwan zafi ta fito ta kunna waka a parlo ta koma tana tafiya tana rawa ta dauka bread akan fridge ta gutsura kana na akan plate ta baza ta fita waje akan motanta ta daura danya bushe

Tafashen naman kaza ta daura sannanta ta dauko semovita ta tilga kadan ta dauka ruwan zafin data daura ta sama katon ruba seta kwaba semovita da ruwan zafi tasa yist a ciki ta yanka albasa shima ta ajiyeshi akan motanta dan ya kumbura


Tana dawowa kan kujera ta haye wai ta gaji
Seda tayi kusan mintuna 20 daga baya ta mike ta koma kitchen tafasen naman saniya ta daura tana cikin yankan albasan ne seta yanke a tafin hannunta ihu tayi tayi wulli da wukan ta kalla wurin tace mayan lalle yaki fita 
Lallan bikinta bakin ya fita henna tafin hannunta ne be fitaba haryanxin

Ta fito tana kallonshi kawai ta rasa me zatayi se awch taketa faman fada 

Adeel yana isa office din be wani dadi ba ya fito ya dawo gida yana shigowa ya fito daga motanshi ya shigo ciki seya tarar da ita a tsaye seda ya karema shiganta kallo 

Dataga shigowanshi seta maida kollonta inda jini ke ziba a hannunta kawai se hawaye ya fara zubuwa kaman ruwa 
Shi bema lura da hawayen da takeyi ba harze tafi seyaji tasha majina dan haka ya kalla fuskanta yaga hawaye ya karasa gunta yace meyafaru

Nuna mashi gun yankan tayi seya juya ya shiga dakinshi first aid box ya dauko karami ya zauna tukun ya kirata ba musu tazo ta zauna a dan gefe sedaya bude kana ya mika hannunshi alaman ta daura hannunta a kai ta daura ya kalla hannun

Yace ina ciwon yake
Gashi nan kana gani ta nuna wani karamin yanka amma jini se zuba yakeyi kaman katon yanka

Ni ban ganin komai se lalle kawai
Ta janya hannunta da nufin mekewa seya kamo hannu yace toh tsaya na wanke

Haka yasaka ya fara wanke wa kawai seya tsaya yana kallon hannun can ya kara motso da hannun gun fuskanshi sosai yace wait meye wannan 

Gabanta ya fadi ta aza wani abu ne taja hannun danta gani 
Meye?? tace
Yace A & A mana
Ta sake kalla tayi wani dariya irin na rainin wayon nan tace kana tunanin zan tsaya asamin A wai da nufin sun-
Abunda bata karasa ba kenan ta ganshi 
Wtf ta fada tareda mikewa tana kara kallon gun "Am gonna kill you"

Seta shige daki tanata masifa ita daya 
Shi ko kallo ya bita dashi kana ya mike ya maida box din

Wayanta ta dauka ta kira number safieyarh dan daga gidansu Adeel aka kawo me henna
Ringing daya biyu ta daga kafin tace hello
Ameenah ta fara bilbileta da fada 

Safieyah tace toh yanxin menayi 
Nasan ke kikace me henna design tasa A & A a hannu na
Ta fashe da dariya ta ringa mata dariya hadda buga cinya

Kefa yar rainin wayo ce banda san iskanci ina maki magana kina min dariya
Toh ba dole nayi maki dariya bah yau how many weeks dayin henna abu a hannunki amma baki taba gani bah se yau

Toh ya a'ayi na lura anyi abu kana na wlh da zanga me lallen da sena shafa mata bakin lalle a fuska 
Dariya safieyarh ta kara sakewa tace toh Mami ce tasata shiyasa itama tayi 

Se masifan ya kuma kan Mami wai taya zatayi min haka 
Daga baya koma setace wai kuna hanya ne

Safieyarh tace yanxin zamu fito muna jiran yaya Hakeem ne danshi ze kawo mu 
Ihu ta saki tana murna hadda hakeem za'azu daga baya sukayi sallaman bayan sun danyi gulma

Fitowa tayi tana saka wani karamin bandage agun ta shiga kitchen din ta sake yanka wani albasan tasa a cikin tafashen tayi mai hadi
Fitowa waje tayi ta dauka bread din ta farfasashi ya kuma kaman gari ta sauke tafashen naman kazan da ta daura ta fasa kwai tana soya kaza da bread da kuma kwai tana gamawa ta dauko kullin waina ta daura tanda ta fara soyawa 

A xuciyanta tana gode ma Mami da Auntie dan sune suka sakata a gaba suka koya mata girki amma da dan itane toh a barshi gashi yau yana mata amfani

Tana gamawa ta saka a kulan Adeel sauran ta zuba a wani kula shima kazan haka tayi 
Gun miyan ta kuma ta hada miyan alaiyahu shima tana gamawa ta gerasu akan table ta saka drinks a fridge daga nan ta gyara kitchen din tas dan ita akwai tsabta parlo ta dawo ta kunna turaren wuta nan da nan gidan ya kama kanshi 

Gun kulan kazan taje ta dauka yanka daya tana ci ta shiga dakinta


                              πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[21:57, 3/5/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: Yana kwance a daki duk kanshi ya gama cika mai ciki se juyi yakeyi akan gado daga baya de ya mike ya fito wani ajiyan zuciya yayi da wani kamshi ya sake dakan mai hanci seya saki lallausar murmushi gun dining ya nufa ya bude dukka kollolin duk wanda ya bude kamshi kawai 
Plate ya dauka ya deba naman ya sama waje ya zauna yana ci tareda kurawa da lemo

******

Wanka ta shiga ta wanke gashinta tayi wanka ta fito dring gashin tayi oiling ta shafa mai ta dan gyara fuska daga powder se eye liner sannan tasa chapet dukda batayi wani kwalliya bah tayi kyau sosai 
Wani riga da skirt ta dauko red na atanfa tasaka ta feshe jikinta da turare sannan tayi zama na musamman ta fara daura dankwalinta 2yard  
Tana gamawa ta kalla mirror ita kanta tasan ta fito phone dinta ta dauka ta ringa selfie tayi iya yinta ta fito tana kallon wayan 
Adeel kowa kaman ance ya daga kai seya ganta kawai seya kware 
Abunda ya dago da ita kenan ta kalleshi
Wani dariya ne yazo mata tana kokarin tarewa amma ta kasa shi kuma yana mata alaman ta kawo mai ruwa ta gane sarai amma tana tambayanshi meyake so 

Daga baya ta bude fridge ta mika mai ruwa seya fuzga ta kalleshi tace gobe ranace ae ta sama waje ta zauna ta cigaba da sana'arta wato hoto

Yana dawowa daidai yace dan mugunda na kware amma seda kika gadama kika ban ruwa 
Nunawa tayi kaman bataga wani halitta agun gah 
Abun ya kular dashi ya zagayo ta gabanta ya amshe wayan se a lokacin ta dago tace give it back
Yasaka a aljihunshi yace zaki iya kwata idan kinada karfi seya juya ya kama hanyan fita waje

Da sauri ta kai hannunta zata dauka ya chafke hannun yace lallai kina ganin hakori na kwana biyu

Ae wlh Mommy na zuwa zan tafi da ita dan na gaji da zama dakai kullum na tashi wannan fuskan nake gani kaman na mayo idan zan kwanta ma shine karshen abunda zan gani its annoying seriously 

Really haka kikace idan haka ya faru i will be so glad dan nima na gaji and idan tazo dakina zaki dawo dan karsu gane wani abu
Tace chab ae nafison ta gane ni kuma bazan taba kwana dakai a daki bah da wani dimple dinka kaman a hankali tace zomo

Wani murmushi ya sake yace yanade burgeki 
Ta rike west dinta tace are you kidding me ba abunda ze burgeni anan gara manade voice dinki

Awwwn finally ya cigaba da tafiya 
Ta sake biyoshi tace ka bani phone dina haka ka daukemin laptop dina and an bani assignment wlh mommy tana zuwa duk zan gayan mata ta wuce 
Shima ya wuce 
Se kuma ta dawo da sauri tace ka bani mana 
I thought kinyi zuciya ne kice please kawai sena baki

Tahb ka rike ta wuce dakinta da karfi ta bugo kofa 
Yace kede kika sani shima ya fito gun garden ya nufa ya sama waje ya zauna seya ciro wayan ya fara nata bincike gun gallery ya fara zuwa shirme ne
Daga hoto na kylie sena Ariana da kuma screamshots din lipstick din kylie da kuma handbags kala kala 
Gun camera kuma hotanta ne baja baja kaman hauka 

Tsaki yayi ya maida aljihu yadan kwantar dakanshi a jikin kujeran ya rufe ido
☆☆☆

Duk abun haushi ya gama ishanta se kunkuni taketa faman yi 

_30 mins later_

Duk ta gaji da jiransu ta kunna tv dakinta tana kallo kawai setaji bell din parlo yayi ringing se kuma karan horn daga waje ae batasan sanda tayi wani super ba ta fito daga dakin a guje hadda tuntube ta fito waje se gasu suna shigowa da motan dan Adeel yana garden din har yanxin

Se tsalle takeyi ita daya duk ta kusa su tsayar da motan 
Ae kowa motan na tsayuwa tayi gun aguje safieyarh ce ta fara fitowa a tare sukayi ihu suka rungume juna 

Hakeem ne yazo wucewa da kaya a hannunshi yace zaku fasama mutane dudan kunn-
Kawai ta dane jikinshi tana ihu seta fara hawaye dan a gaskiya tayi kewarsu d[truncated by WhatsApp]
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹UMARNIN IYAYEπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹


WRITTEN BY:
    
                    TYETYELORH



                          πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

*115*

Mommy tace toh mena kukan kawai seta sakeshi ta kuma kanta se kukan ya karo
Seda sukayi kusan mintuna 5 a haka se mommy tayi murmushi ta dagota tace toh ya isa but still bata dena kukan bah se hawaye takeyi

Adeel se galla mata harara yakeyi ta gefan ido dan taki sake mashi mamanshi shima ya dan rungumeta 
Ya kalla safieyarh se tayi sauri ta juya yace haba baby sis are you still angry 
Am sorry okeyy??
Riketa yayi yanata lallashinta harta sauko

Haka suka dinduma suka shiga gidan mommy tasa hannunta ta dafa bayan Ameenah suna tafiya tare suka shiga 

Hakeem ya ajiye kayan a parlo se Adeel ya deba yakai dakin Ameenah 
Duk suka zauna Addel da Ameenah a kasa suka xauna suka gaidata ta amsa da fara'a sosai a fuskanta dan taji dadi yadda ta gansu sunyi haske gabadayansu ga Ameenah ta danyi kiba ba laifi
Bayan dan gaisuwa da hira 
Kiran sallah akayi Adeel da Hakeem suka mike suka tafi masallaci while su kuma suka shiga daki sukayi nasu 
Da suka gama Ameenah kanta a kasa ita duk kunyanta takeji safieyarh data gane haka ta ringa mata dariya mommy ta bugeta 

Parlo suka dawo sannan su Adeel suma sun dawo aka fara hira duk Hakeem ne me surutun se dariya sukeyi
Ameenah da safieyarh suka mike suka shirya dining safieyarh ta gayan masu cewa azo aci abinci
Ita kuma Ameenah kitchen ta shiga ta dauko ma kowa drink ta ajiye seta koma ta dauko ma Adeel aya da kwakwa data hada saboda Mommy tayi dan karta kawo komai zuciyanta ta ajiye mai a gabanshi da cup
Hakeem iyayen surutu yace "lallai na mijinki daban ne toh nima shi zansha"
Akayi dariya batayi maganaba ta dauka cup ta zuba mai shima harzata zauna kusa da safieyarh se taga Mommy tana kallonta tana murmushi dan haka seta koma kujeran kusa dana Adeel

Hakeem ya fara deban nasa safieyarh ta mike itama ta zuba tasama Mommy  
Adeel ya motso dede kunnanta yace what about me
Tayi banza dashi tana shan ruwa
Ya sake cewa idan bakison tayi suspecting wani abu dole ki zuba kin

A hankali itama tace wlh saboda mommy zanyi ba dan kai bah
Smilling yayi sannan yace bade yadda kika iya
Kafanta ta daga da karfi ta take kafanshi yace awchhhh
Duk suka dago amma banda mommy safieyarh murmushi kawai tayi dan ta gansu suna magana a hankali

Badan taso ba ta zuba mai dan mugunta ta ringa zubawa kuma tasan yayi mai yawa seda yaja plate din ta dena ta zuba miya seta kuma ta zauna
Ta gefe yayi mata gwalo yace ba yadda kika iya 
Dan haushi mikewa kawai tayi 

Mommy tace Ameenah bazaki ci abincin bah
Tsayawa tayi chahk sannan ta juyo tayi murmushi tace na koshine na rigada naci

Adeel yace karyane bataci komai bah ita kwata-kwata bata son cin abinci wata rana ma sena mata dure takeci
Murmushi tayi tace yauma duren ya kamata kayi mata

Wani wawan murmushin mugunta ya sake tareda kallon Ameenah 
Ae tana jin haka ta dawo taja plate tasa guda biyu ta ringa turawa 

Duk dariya suka saki
Suna gama ci safieyarh takai dishes din kitchen suka dawo parlo aka ringa hira itade ta kasa sake jiki  

Wuraren karfe 9 bayan sun gama dinner suna zaune a parlo suna kallo se Mommy itada safieyarh suka mike zasuje su kwanta se itama Ameenah ta bisu mommy wai ita alankatafar bazata kwana a dakin Ameenah bah se'a guest room se safieyarh ta kwana a dakin ba yadda ta iya haka suka deba kayanta suka shigan mata dashi safieyarh itama taje ta kwanta a dakin Ameenah Hakeem shima a dayan guest room din ze kwana 

Ta dawo parlo ta cigaba da kallo se aka gama film dinda suke kalla daman _twilight_ suke kalla aka saka wani horror film _The ring_ duk jikinta rawa yakeyi kuma gata tason horror dan haka ta ringa kalla 

Dayake a three siter suke zaune itada Adeel yana can gefan itama tana dayan gefan while Hakeem yana zaune a sitter daya shine kusa da tv

Se dukun kunewa takeyi duk ta gama takurewa gu daya kaman dole seta kalla 
Hakeem shima duk a tsorace yake dan yama fi Ameenah 
Gara-garade Adeel ya natsu yana kallo

Yarinyan film din ta fito daga rigiya gashinta ya rufe fuskanta tana zuwa toward the camera
Kawai se sukaji dubbbbb
An dauje NEPA

Duk sukayi shiru Hakeem kam still idonshi yana kure da tv kaman yana ganin alaman yarinyan 
Wani wawan ihu ya saki kaman karamin yaro
Ae Ameenah tana jin ihun nan daman a tsorace take wani tsalle tayi se akan cinyan Adeel ta rungumeshi

Alaman mutum dayaji a jikinshi ta mugun tsoratashi da sauri ya mike amma still tana rike dashi toh abunda yasashi ihu kenan shima
Hakeena yana jin ihun Adeel seya kara kain wani kaman mata

Duk abun nan befi a cikin 3mins ba ya faru
 
Kawai se solar ya kunnu
Haske na zuwa Hakeem ya kallesu Ameenah tana kankame dashi still idonta a rufe 
Wani dariya ya saki se suka bude ido a tare da sauri Ameenah ta sakeshi tayi hanyan dakinta dan tasa pajamas dinta da sauri take tafiya

Adeel kam gun Hakeem yaje ya ringa lausa kaman an aikoshi still Hakeem bebar dariyan bah
Tana shiga dakin closet ta shiga ta changa kaya seta saka sucks dinta da katon hijab ta fito hadda sa hannu ta gansu gun tv ta nufa ta kashe dan tsokana seta kashe wutan parlon gaba daya 

Hakeem da sauri ya mike ya shige daki ya kwanta 
Se kuma ta kunna wutan ya kalleta seya shige dakinshi ta dade a tsaye agun daga baya ta kashe wutan kitchen tazo ta kashe na parlon a hankali ta shiga dakinshi kaman dagaske

Baya dakin da alama ko ya shiga closet koh toilet ta tsaya ta karema dakin kallo tace ba lefi a zuciyanta
Se gashi ya fito daga toilet dagashi se three quters koh riga babu ita kuma kaman ance mata ta kalle gun se ta ganshi idonta akan packs dinshi yayi masauki seda tayi 2mins tana kallonshi seta dauke kai

Shi yama manta cewa ana zata kwana dan haka closet ya shige da sauri ya zura jallabiya ya fito
still tana tsayen kaman statue yace se ki shigo dakin mutum babu sallama kam-
Ta katseshi da cewa am glad to live seta juya xata fita da sauri yasha gabanta yasa lock akofan yace baki isa bah wlh baki isa ran mommy ya baci sboda ni bah

Batayi magana bah ta wuce gun gado tana cewa am only doing this to her
Da sauri ya dakatar da ita yace what do you think you are doing nida gadona sena fake da kwana akan cauch 

You expect me to sleep where???
Seya nuna mata kujera 
Murmusawa tayi kawai ta haye kan gado taja pillo ta kwanata akai hadda juyamai baya

Yayi mugun kuluwa ya dauka dayan pillo ya wulla mata 
Whatever kawai tace ta rufe ido ya dade a tseye yana ta sake-sake ta ya
Yadda ze kwana shi kuma kwana akan kujera yana sa mai tsamin jikin
And baze iya kwana a kasa bah

Kawai seya debo pillos dayawa ya jerasu yayi kaman ya rabasu kenan ya kashe wuta ya haye gado shima 

Duk motsinshi tana jinshi harseda taji shiru tayi addu'a ta tufa bacci ya dauketa


           [truncated by WhatsApp]
[17:52, 3/11/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹UMARNIN IYAYEπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

WRITTEN BY:
                       TYETYELORH

                        πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

_Nasan last page was too short am so sryy for that zanyi replacing a wannan page din_πŸ’‹
_In dedication to lawizas_


*116*

Da asubah kaman hadin baki a tare suka tashi toilet dinshi ya shiga yayi alwala ya fita suka wuce masjid da Hakeem ita kuma mikewa tayi ta shiga dakinta ta tada safieyarh sukayi sallah tare ta kuma dakin Adeel dan tasan be dawo bah seta ga laptop dinta ya daura wayan akai ta kinkima da sauri ta kuma dakinta ta kwanta kafin gari yayi haske

Suna dawowa shima baccin ya kuma da beganta a dakinba be wani damu ba sema pillo daya gyara ya saka a tsakiyan gadon ya wanta

Wuraren bakwai ta tashi ta sake tada safieyarh wai tazo ta tayata aiki dan rashin mutunci se tace ni wlh bacci be isheni bah ta kuma tareda kulle fuskanta da bargo 
Wani wawan duka ta buga mata tace wlh idan baki tashi ba Mommy zan gayan mawa kefa ya kamata kimin gyaran gidan

Ta kalleta tace kaman nazo gidan Auntie nah
Ameenah tace toh gidan wa kikazo idan ba na Auntie naki bah ki tashi baf

Badan taso ba ta mike suka shiga kitchen  
Dishes din tasa a dishwasher se suka fara hada breakfast suna hira  
Suna gamawa Ameenah ta gera akan dining ita kuma safieyarh ta gyara kitchen din da parlo
Dakinta ta shiga tayi wanka atamfa ta sake sawa riga da skirt dan kwalin nan ya dauro ta feshe jikinta da turare 
Black handbag ta dauko tasa laptop dinta a ciki da bakin takalmi ta yafa gyale ta fito 

Safieyarh tace inyeee amarso kinyi kyau fah
Murmushi kawa tayi sega Adeel ya fito daga dakinshi kallonta yayi lokaci daya koma ya dauke kai

Safieyarh kowa shigewa daki tayi 
Ita kuma gun kofa ta nufa zata fita
Yana kokarin zama kan kujeran dining yace ina zaki
Ta juyo tace school ofcorse 
Toh jirani nayi dropping naki kallonshi tayi se kuma tace mommy ofcorse ta dawo tareda zunbura baki 
Kan table din ta nufa ta dauka dankali guda daya tasa a baki seta dauka ketchup ta matsa a bakinta haka ta ringa yi kaman sau uku shi tsayawa yayi yana kallon ikon Allah 
Kaman ance ta kalleshi se taga yana kallonta tace what!!
Girgiza kai yayi yace "you are so weird"

Gun fridge ta nufa ba tareda tayi mai magana bah ta dauko malt ta sama waje tana sha shi kuma yana cin abinci kaman mace yana yanga kallonshi kawai takeyi duk ta kusa ya gama su tafi yadda yake tauna abinci kawai yayi mata kyau lips din na natso tana kalla they are so pink 
Sega Hakeem ya fito a shirye ya kalla Ameenah inda ta natso tana kallon Adeel yayi dariya ta tabata 
Da sauri ta kalleshi tace kaban tsoro
Ba dole kiji tsoro ba kin tsaya kina kallon mijinki yana magana inda Adeel baze ji bah  

Kame kame ta fara tace me zan kalla ajikinshi se kuma tayi tsaki ta cigaba da shan malt dinta 

Murmushi yayi ya zauna a hannun kujeran da take yace kalla na fara tara gemo
Kollon gun tayi babu komai kaman fuskan jinjiri tace hala ka bada ajiya ne a fuskan wani ta mike
Kallonta yayi ya hada fuska
Adeel kowa wani dariya ya saki yana mikewa 
Harara ya aika mai fuskanshi a daure

Hanya fita sukayi da Ameenah se kuma Adeel ya juyo ya kalla Hakeem yace idan Mommy ta tashi kace mata na tafi gun aiki
Yace ae kun ajiyeni ne 

Ameenah tayi murmuahi tace wai ina zaka kayi wannan shirin 
Sakin fuska yayi yana gyaran wuyan rigan dake jikinshi yace neman aure

Kaman an gefo safieyarh se gata ta fito daga daki ta kalleshi 
Yana ganin ta fito seya juya 
Su Ameenah kowa fita sukayi suna mai dariya 
Motan Adeel suka shiga suka fito ba wanda ke magana 
Bayan sun danyi nisa se ta kalleshi tace wai yaushe ka fara zuwa gun aiki
Kaman baze amsata bah se kuma yace meye ruwanka

Kanka akeji ta murmuda mai baki
Maimakon taga sun nufa makarantansu setaga sabanin haka
Taso tayi magana amma se kuma tayi shiru dan tasan "ina ruwanki" zece
Sunata tafiya tana kallon window gefenta se suka tsaya a wani katon building a saman ansa *Lawizas* phone dinshi ya ciro yayi dialing wani number seya sa a kunne can sega wata budurwa ta fito da file a hannunta tayi knocking window ta gefan Adeel seya sauke a lokaci daya kuma seya changa fuskanshi

Gaidashi tayi ya amsa ciki ciki sannana ta gaida Ameenah da murmushi ta amsa 

Se budurwan wato Assistant din shi kenan tace "sir bakada apointment yau se gobe kakede meeting"
Tana magana tana wani fari da ido 
Shi kuma phone dinshi kawai yake kalla tana gamawa yace "okeyy" koh kallonta beyi bah yaja motanshi

Gyara zamanta tayi tana facing dinshi tace waye ita?
Ba tareda ya kalleta ba yace "if you most know everthing Assistant dina ce"
Dariya tayi tace she is seriously into you
"Well good for her"

Seriously kaga wani yangan da take maka
Yace she's not my type

Kara kallonshi tayi tace then who's your type
"Wai ina ruwanki ne wait mema kike karantawa?"
Fuska a daure tace _Law_
Kallonta yayi yace "no wonder it fits you "

Ba wanda ya sake magana har suka isa makarantan fitowa tayi daga motan har zata wuce se kuma ta juyo tayi knocking glass din ya sauke 
"By 12 zan gama class dina gabadaya"
Then kije ki fadan ma driver ki garama tun wuri ki sama me keke napep

"Haka kace koh toh wlh Mommy zan kira in gayan mata kaki zuwa daukana ae daman iyayinka ne ya saka ka kawoni tin farko "

Zanga da wani wayan zaki kirata ae kawai seya ja motan ya wuce 
Tsayawa tayi ta duba jakanta ae kowa ta daura akan dash-board din motan kaman tayi kuka tace mugu kawai ta wuce

Yana cikin tafiya phone dinshi tayi ringing Manager shine ya daga suka gaisa yace mai nan da 5 days ne match din saboda haka ana sauran 4 days zakazo zan shirya maka komai
Sukayi sallama

Gidan wani frnd dinshi yaje sunsha hira se 12 dai-dai suka rabo ya kama hanyan dauko ta
Ita kuma tana gama class dinta ta fito ta sama wani kujera ta zauna sega wani saurayi yazo shima ya zauna kusa da ita dan corse mate dinta ne suna dan gaisawa amma besan matan aure bace hira dukeyi sama sama shine ma de me magana ita daga mai kai kawai takeyi se faman kallon agogan hannunta takeyi.

_Some minutes later_

Se gashi yazo yayi packing ya hangosu amma ita hankalinta gabaya begon tanata murmushu fitowa yayi daga motan yana wani takon kasaita hannunshi a aljihunshi dayan koma yana shafa gashin kanshi har gabansu yaje se a lokacin ta ganshi murmushi tayi jakanta dake kan laps dinta ya sa left hand dinshi ya dauka dayan hannun kuma ya kamo hannunta ta mike tafiya suke a hankali se kallonsu akeyi still yana rike da hannun nata

Suna isa gun motan dayan jefan ya bude ta shiga ya wulla mata jakanta akan cinyanta ya shiga gun driver ya fuzga motan da karfi besan dalilin haushin da yajiba da yaganta da wani suna zaune tare

Bayan sunyi nisa seta kalleshi tace "whats with the bad mood?"
Shareta yayi beyi magana ba se wani gudun da yakeyi sosai 

"Easy am not ready to die kayi dropping dina ni kam idan yaso kai kadai ne a motan kayi iy-"

Bata karasa ba ya daka mata wani tsawa da seda ta furgita
"Shout up"

Murguda bakinta tayi tace anje can an bata maka rai kazo ka sauke min 
Wayanta ta hango seta dauka ae kowa sega missed calls.

Suna isa yayi packing motan ta fito shima ya fito tana tafiya kawai yazoya wuceta ya shige tsaki tayi ta cigaba da tafiyanta 
Yana shiga parlon Hakeem ne da safieyarh suna zaune suna hira ya wucesu koh magana beyi masu bah dakinshi ya shige yayi locking kofan

Itama ta shigo fuskanta a daure Hakeem yace meyafaru da mijinki
"Oho" tace itama ta shige nata dakin
Kallon juna sukayi suka cigaba da hiransu.


                            πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[19:50, 3/11/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: _Three days later_

A lokacin su Mommy sun kuma kaduna dan kwanansu hudu suka koma taci kuka sazasu tafi.
Tana kwance a dakinta se taji ta gaji da kwanciyan dan haka ta mike ta fito a parlo ta tarar dashi seta wuce kitchen burger da suka sayo jiya a _zufeey bakery_ ta saka tana warming dinshi seta zauna kusa da inda take jira plate dinta tana chating tana gamawa ta saka a plate dayake guda biyu ne ta fito a parlon ta zauna 
Adeel kowa yadan kishingida da remote a hannunshi ya kalleta shi baci yake ba amma dan tsokana seya kai hannunshi ya dauka daya ya gutsora seya maida mata 

Kallonshi tayi tace "kaji dadi koh wlh bansanme kakejiba idan kayi tsokana baci zakayi ba kawai-"
Shiru tayi dantaga alaman hankalinshi be kanta ta cigaba da ci tana kallon wayanta 

Gyara zama yayi yace gobe zanyi tafiya
Da sauri ta dago da murmushi a fuska zatayi magana ya katseta da cewa "Nop bazan kaiki kaduna bah, so ki tsaya kiji me zance"

Shiru tayi ya cigaba cewa zanyi 5 days probably one week dan haka idan kinada bukatan wani abu ki gayan min
Girgiza kai tayi tace banson komai amma nikadai zaka bari a gidan
"Yah why not" 

Tace ni wlh tsoro nakeji
Mikewa yayi yace tazo ta gani itama ta mike tabi bayanshi gun kofan shigowa ya tsaya wani red Alarm ya nuna mata yace idan kikaga wani abu weird a gidan shi zaki danna 

Toh idan na danna mezeyi
Za kigani ae ya wuce ya zauna 
Dakinta ta shige tayi wanka tayi shirin kwanciya.

_Washe gari_

Wuraren karfe 10 ya gama shirinshi se wayanshi yayi kara wanda zezo daukanshi ne ze kaishi kaduna dan an kulle airport din Abuja so ta kaduna zebi 
Ya kira number Daddy ya gayan mashi zasu tafi amma yace mai mota aka turo masu dan haka baxe sama biyowa ta gida bay 
Addu'a yayi mashi yabama Mommy itama tayi mashi sukayi sallama
Ameenah ya kira ta fito ya mika mata kudi yan duba daya daya
Bata amsa ba tace for what 
Idan zaki amsa ki amsa banson iyayin seda ta murguda mai baki ta amsa

Wlh kika sake murguda min baki zakiyi mamakin abunda zan maki 
Shiru tayi ta ajiye akan hannun kujera ya kama hanyan fita kaman abun arziki tabi bayanshi harsun kai bakin kofa ya kalleta yace idan kuma zaki fita ki tabbata jin gayan min

Hadda school din
Yace a mana
Toh ni inama da phone number kane 
Yace ae ni inada naki idan muka isa zan kiraki 
Toh kawai tace 
Har ya cigaba da tafiya ya sake juyowa 
A zuciyanta tace "god" dan ta kusa ya tafi.

Duk wanda yayi knocking a dakina akwai camera na gate ki fara dubawa first kafin ki bude 
"Toh"
Karfa ki fita sekin gayan min ya sake repeating mata 
Tace toh zan fara zuwa exerise da safe fah farkon layin nan zuwa karfe dan gaskiya i have gain more ponds kwanan nan

Noh ban yarda bah idan na dawo semu fara zuwa tare
Murguda baki tayi a zuciyanta tace toh babana 
Kafin ta ankara yakai lips dinshi zuwa nata a lokaci daya ta dauke nunfashinta kuma ta kasa janye kanta kusan 3mins seya saketa da sauri ta shige ciki
Shi kuma murmushi yayi yace ae na gayan maki ya fita shima yana fita ya shiga motan suka tafi.

Dakinta ta shige ta fada kan gado tana shafa lips dinta ta dade a haka har bacci ya dauketa.
 
_Some hours later_
Sun isa kaduna lokacin har ya shiga girji suna isa UNITED STATE ya fito daga girgin da glass a idonshi yana jan akwatinshi sega wata yar budurwa kaman Ameenah yana ganinta Ameenah kawai ya tuno tazo gunshi tace can she plx take a selfie with him buturiyace yarinyan
Yace why not

Ta ciro wayanta jikinta na rawa ta dauka guda biyu ta mai godiya ya cigaba da tafiya dayake an aiko da motan daze daukeshi se kawai ya shiga suka tafi hotel dinda ake ajiyesu 

Yana shiga dakin shawer ya sakan ma kanshi ya saka three quater koh riga babu ga abs dinshi manya manya guda takwas (so sexy) gado ya haye se bacci koh abinci be nema bah

Ita kuwa tana tashi tama manta abunda ya faru alwala ta dauro tayi sallah se kuma ta fito parlo lokacin 1:00pm tv ta kunna tana kallon wild child. 
Yana tashi daga bacci yayi sallah ya bude fridge din dakin cookers ya gani ya dauka da madara yaci seya saka riga ya fito waje da glass a idonshi 

Dakin wani frnd dinshi yaje shima yana cikin players din amma bature ne suka zauna suna hira.

Mikewa tayi tayi shirin zuwa makaranta dan 2:30 takeda lectures yau duguwan riga tasa ta yafa veil din ta fito koh handbag bata dauka bah wayanta kawai ta dauka se laptop dinta tayi shiga motanta ta kama hanyan makaranta.



IG.Tyetyelorh
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
        (admin
   Arewa hausa novels 
       Novels villa
     Duniyan novels 
   Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
          And 
Cool novel, makeup and cooking) 

      WHATSAPP NO:
    +2347039625239

[19:55, 3/14/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹UMARNIN IYAYEπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹


WRITTEN BY:
                        TYETYELORH

EDITED BY:
                    AMEENATOU
              
                             πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

_in dedication to lawizas_


*117*

_Washe gari_

Wuraren karfe uku tana zaune duk ta gaji da zaman gidan gashi ita kadai mikewa tayi tasa takalmi ta fita tsakar gidan yau two months da zuwanta gidan amma bata taba zaga gidan bah

Gun garden tafara zuwa can gefe taga suke suke daban-daban zuwa tayi gun hadda mint wato (na'ana'a )n gasu carrot amma kaman basu nuna bah mint din ta tsinka ta rike a hannunta ta cigaba da zaga gidan can bayan gidan ta shiga tana tafiya tana waka tayi kusan rabin se taji bell din gate ana dannawa komawa gun gate din tayi har zata bude seta tuna batada mayafi seta kuma ciki a guje dakin Adeel ta fara shiga gun cameran gate din ta nufa ta kunna wani kyakkyawan saurayi ta gani yana tsaye hannunshi aljihunshi se faman danna bell din yakeyi da daya hannun

Dakinta ta tafi da sauri ta dauko hijab din sallah ta kuma parlo remote din gate din ta dauka se wani zuciya ya hanata kawai seta maida ta ajiye ta cigaba da harkanta shi kuma ya danna har ya gaji dan haka ya tafi.


Adeel ne ke kwance akan kujera dagashi se gajeran wando yunwa yakeji amma yasan baze iya cin abincin ba kawai coffe ya hada ya sha seya dauka wayanshi Hakeem ya kira ringing na biyu ya daga dan shi Hakeem din yanada numbershi na US din 

Suna gama gaisawa yace mai dan Allah yadan mai sending number Ameenah dan numberta yana daya sim dinshi kuma ya barshi a nigeria ya sharara mai karya
Toh barin turo maka se yayi hanging up

Ba'a dade bah ya mai snding kallan number yayi kusan for 5mins can kawai seya kira lokacin tana sallah dan haka bata dauka bah shi kuma maimakon ya sake kira se ya ajiye wayan ya mike dan girman kai Tana kan sallaya ta idar da sallah tana jin ringing wayan amma bata daga ba seda ta gama addu'anta ta shafa seta mike ta dauka wayan number ta gani kuma ba irinta Nigeria bah tsaki tayi ta ajiye wayan itama ta cire hijab kwata-kwata bata kawa a ranta cewa shi bane infact tama manta cewa yana can kasan

_After like 30mins_

Kasa hakura yayi ya sake kiran number wannan karan tana kusa da wayan amma yana ringing seda ya kusan katsewa seta daga ta kara a kunne amma batayi magana bah
Shima shiru yayi se can yace "Hello"

Can karkashi ta amsa 
Masifa ya fara mata yace dazin na kiraki baki dauka ba kuma nasan kinga missed call baki kira bah
"Wait wai waye daga kira ka fara ma mutum masifa"
Sarai tasan waye iskanci ne kawai irin nata 

Cewa yayi bansani bah se yayi hanging up  
Wani dariya ta saki tace dan rainin wayo kawai 

Shi kuma magana zuci ya fara wai meya kaishi ma kiranta in the first place gashi ae abunda ka jama kanka tsaki ya saki 
Mikewa yayi ya sake wanka dan lokacin match dinsu ya kusa 

Text tayi mai tace ita zata fita danta gaji da zaman gidan ita daya bata jira reply nashi bah ta mike dayake three quater wando ne a jikinta da vest kawai tasa hijab me hannu ta dauka car keys nata da credit card se wayanta ta fita.
Harta kunna mota seta tuna da kudin daya bata kumawa tayi ta dauka dan tanason ta biya ta bank tasa ta gwammace ta ringa yawo da credit card abinta

Yana fitowa wayan ya dauka seya messege dinta da sauri yayi replying mata wai karta fita ashe iskanci ne ta ganeshi ne
Saloon taje aka gyara mata gashinta sega messege dinshi ya shigo sake replying tayi itama tace "too late dan yanxin ma zan kuma gida"

Shareta yayi ya dauka sport bag dinshi ya fita
Tana gamawa bank taje data saka kudin ta kamo hanyan gida.
Haka rayuwanta ya cigaba da tafiya ita daya kwallin kwal gashi makarantansu an tafi strike kullum tana gida 

Adeel kuma yayi match biyu sauran daya yana gama dayan se yaje wani meeting daga nan ya dawo gida kuma tun tafiyanshi kwana uku kenan har yau be zauna yaci abincin kirki bah shima ya kasa gane dalili kawai daga ya yanka wannan yaci yasha coffe se drink haka yakeyi
Ranan da zeyi match dinshi na karshe tana zaune seta dauka remote kawai takai sport channel ae kowa se gashu Adeel sunayi live ajiye wa tayi tana kallo 


2-0 akaci su Adeel sune masu 0 dariya tayi tace losers seta mike ta shiga dakinta ta kwanta 
Daga baya duka fara ci har 4-2 na karshene Adeel yaci aka ringa ihu yan team dinsu se ihu akeyi.

_Washe gari_

Tunda safe data tashi ta gyara gidan ta goge ko ina gidan yashaturaren wuta se kamshi yakeyi wanka ta shiga bayan ta fito 
Bom-shorts tasa da wani half top ansa MSFTSrep a jikinta baka head-phone ta saka a kunnenta ta shiga kitchen tana girki lokacin karfe 2:00pm
Ta gama hadawa kenan ta fito parlo tana tsaye tana kallon tv juyawan da zatayi kawai taga mutum a tsaye yana kallonta shidewa tayi kaman na 3mins daga baya ta saka wani kara seta kuma kitchen din a guje tasa key bata bar ihun bah har lokacin

Fashewa yayi da dariya se ya shige dakinshi ya shiga wanka 
Gabadayanta a tsorace take tana manne da kofan ta dade a wurin se taji abincin na kauri kashe gas din tayi seta dauka wuka ta bude kofan a hankali taga babu kowa a gun dakinta ta shige da sauri tasa key zama tayi bakin gado tana maida numfashi se kawai alarm dinda ya fadan mata ya fado mata wukan ta sake dauka ta bude kofan a hankali taje ta danna alarm din a sittin ta dawo dakin

Ya fito daga birthroom din kenan towel ne a waist dinshi da kuma wani a hannunshi yana goge gashin kanshi yaji karan alarm din 
Sake towel din dake hannunshi yayi da sauri ya fito daga dakin gun alarm din ya jufa ya kashe seyayi knocking dakinta

A bakin gadon take taji ana buga kofan da karfin gaske wani wawan fitsari taji yazo mata toilet ta nufa tana rike da maranta seda tasa key sannan tayi fitsari

Buga kofan yakeyi da karfi sosai amma bata bude bah kiran sunanta ya farayi bata amsa ba seya cigaba da knocking din
Fitowa tayi closet dinta ta shiga ta rasa me zata dauka seta hango takalminta hill ne daukowa tayi ta fito kofan ta nufa kirjinta na dukan uku-uku tana bude kofan idonta ta kulle tana ihu wajan hill din ts buga mai a kanshi tana kukarin sake bugawa se yayi sauri ya riketa ya kwace hill din 

Amma still bata bude idon ba sema wani ihu da take karayi sunanta ya kira da karfin gaske a zuciye
Furgita tayi ta bude idon ta kalleshi sun hada ido goshinshi kuma ga jini yana zuba 
Jada baya tayi tace yaushe ka dawo 
Ban sani bah yayi wulli da hill din gun kafanta yayi hanyan dakinshi
Da sauri ta bishi tace am really sorry seriously i thought-

Bata karasa ba yace i don't care
Yana shiga dakin ze turo kofan kenan tayi sauri ta shige kallonta yayi 
"Dan Allah kayi hakuri wlh bansan kai bane"
Toh naji fita 

"Toh ka tsaya nayi treating dinka" 
"Banaso ki fita zanyi dakaina"
Shareshi tayi ta nufa inda yake ajiye first aid box din ta dauko bakin gadon ta zauna tana budewa tace kazomana i promise ina gamawa zan fita.
Tsayawa yayi yana kallon shiganta ita tama manta abunda ke jikinta
Bakin gadon yaje ya zaune 

Dan matsowa tayi kadan
Tana dagowa takalla wurin fashewa tayi da dariya 
"Wlh na samoka sosai"
Kin gani ko tashi ki tafi zan iya gogewa dakaina kuma sena rama in fadan maki kokarin amsan box din ya farayi

Tana kokarin gintse dariyan tace toh tsaya yahakuri 
Mikewa yayi nace banso koh ana dole 

"Allah tunda nayi niya sena goge koh danneka zanyi sena goge"
Haka kikace koh toh ma gani 
Tana mikewa idonta akan abs dinshi suka sauka tsayawa tayi tana kalla so sexy ji take kaman taje tayita shafa har seta gaji

Da yaji tayi shiru seya kalla fuskanta ya gane inda take kallo se yace zo ki fita kona wullaki waje

Se a lokacin ta dawo duniyan data tafi 
Kumawa tayi ta zauna "wlh ina gamawa zan fita kalla inda jinika yake zuba"
Dakyar ta lallameshi ya dawo ya zauna gogewa ta farayi tana gamawa ta dauka plasta zata samai ya matsar da fuskan yace bansonshi 

"Taya zakace bakasonshi jams fa zasu shiga ka tsaya mana na saka maka"
Jikina ne koh toh banaso bani box din ki fita 
Kokarin jan box din ya farayi ita kuma taki sakewa 
Wannan karan dukka karfinshi ya hada yaja da karfi seya janyo hadda ita ta fado jikinshi se suka kanta a atare shi kuma first aid box din ya wuntsile gefe ya baje 

Tsayawa sukayi suna kallon idon juna fadunwan da tayi se hannunta ya tsaya akan packs dinshi dukka biyun
Sun kai 9mins a haka suna shakar nishin juna se tayi sauri ta mike ta gayara riganta se a lokacin ta tuna dressing dinda tayi kallonshi tayi yana kallonta da sauri ta kare cibiyanta dake a waje ta fita da sauri 

Shi kuma yafi 30min yana kwance inda ta barshi kaman statue daga baya ya mike yana jin kanshinta a jikinshi murmushi yayi ya shafa gashinshi seya mike ya shafa mai yayi combing gashinshi yasha turare suman nan dan duk jikinshi daga abs nashi se gashinshi yake kula dashi sosai

Data shiga dakinta tsaki taja seta saka streght shirt ta cire rigan tasaka vest a ciki ta maida kitchen ta shiga warming abincin tayi ta juye a flask akan dining ta ajiye kitchen din ta kuma zubu ta hada wanda tayi blanding pinapple daya a ciki dan haka yayi kauri sosai tasa ice na cube a ciki ta ajiye shime deban nata tayi seta kuma dakinta 



                          πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[20:35, 3/14/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: Yana fitowa da gajeran wando a jikinshi se shirt zama yayi ya fara cin abincin yaci sosai dan tun tafiyanshi beci abinci bah zoban ya diba ya shiga cikin parlon ya zauna da wayanshi a hannu 

Fitowa tayi da plate a hannunta tana ganinshi a zaune seta dauke kanta daga wurin ta shiga kitchen 
Tana fitowa gun dining ta nufa tana kwashe plate dinda yayi using seta kalleshi tace wai meyasa ka dawo yanxin bakace one week ba kuma four days kawai kayi

Banza da ita yayi ya cigaba da shan zobanshi da alama yana mai dadi dan hadda wani lumshe ido yakeyi kare mashi kallo tayi 
A hankali tace losers kawai

Kallonta yayi yace canceling meeting dina nayi and for your information mu mukaci
Fashewa tayi da dariya hadda shewa 
"Kaman ban kalla bah live na kalla fah so don't pretend"

Smiling yayi ya dauka remote yakai channel din cikin sa'a an saka seya mike ze tafi dakinshi 
"Ki sama glass kisaka kafin ki kalla"
Ya wuce dakinshi dan yayi alwala dan an fara kiran la'asar
Harara ta galla mai kaika sani kai plate din tayi tana dawowa shi kuma ya wuce masjid dan haka seta sama wuri ta zauna tana sake kallon match din.

_Two days later_

Tana kwance a parlo ne akan three sitter tana rikeda maranta saboda wani radadi da yakeyi mata gashi Adeel ya tafi office 
Mikewa tayi dakyar ta debo zam-zam da Mommy ta kawo mata sanda sukazo karamar jarka a cike
zama tayi ta tufa addu'a a ciki tasha seta kuma ta kwanta ba'a dade ba wani wahalallan bacci ya dauketa amma still hannun yana rikeda maranta 

                        KADUNA

Hakeem ne gaban Mami ya sata gaba waishi wlh aure yakeso ita kuma dariya taketa mashi
Daure fuska yayi yace haba Mami ina maki magana amma kina min dariya wlh dagaske nake ni aure nakeson ayimin

Kallonshi tayi tace kanada aiki ne 
Girgiza mata kai yayi 
"Toh taya zaka rike iyayi?"
Mami ae sena fara aikin 

"Daga baya kenan ba yadda bamuyi dakai bah Abbah ya saman maka aiki a Katsina wai kai yayi maki nisa gashin nan ae"
Wlh Mami yanxin zanje koh maiduguri nema zani i promise

Ae kowa akwai wani aiki a maiduguri-
Da sauri ya katseta "Mami ke bakisan wasa bane a neman min na katsinan kawai"

Wai dagaske kake zakayi aure wai ma wazaka aura
"Safieyarh mana Mami"
"And iyayenta zasu baka kayi yaro ae"

Haba Umma Adeel fa mate dina ne amma shi bakuce yayi yaro bane kuka bashi yarku seni
"Saboda shi yasan abunda ya kamata yayi da wanda be kamata bah"

Yace toh nifa Mami yawancin mate dina fa sunyi aure amma ni kice nayi yaro Allah Mami idan bakuyi min aure bah zan shiga duniya seya mike yayi ficewanshi

Dariya ta ringa yi tace ae ga alaman yarintan nan namiji dakai zaka shiga duniya ta ringa mai dariya.

********
Bata dade a baccin bah seta tashi kuma sena kasa kikewa zaune dan rikewan dayayi wani kuka ta saki dan kaman ana suka mata abu me tsini

Tana jin alaman shigowan mutum shiru tayi amma hawaye na zuba a idonta na azaba
Haryazo wucewa dakinshi ya juyo ya kalla parlo se yaganta tana kwance tana hawaye ga hannunta rike da maranta 
Karasowa yayi da sauri yana tambayanta mike damunta take hawaye 
"Marana ze fashe"
Kawai ta fada ta cigaba da kukan 
Dagota yayi yace tashi mu tafi hospital toh

"Noh please idan mukaje karamin ruwa zasuyi ka barni kawai anjima ze dena"
Ae kowa ya tuna abunda doctor ya fadan mashi se yaji tausayinta 

Mikewa yayi ya shiga dakinshi wani karamin leda ya dauko ya bude frigde ruwan gora ya dauko ya saka itacen (ararrabi) a ciki ya girgiza yadan ajiye danya jiko

Can seya dauko ya zuba a cikin cup seda ya tufa mata addu'a seya dagota ya bata batayi musu ba ta amsa tasha 
Tana sha kaman tsafi yana sauka a hankali

Zama yayi akan kujeran kanta na kan laps nashi tana sha harta gama ta kalleshi meyeshi wai 
"Oho nima bansan sunanshi ba Mommy ta bani nima"

Shiru kawai tayi can tace "sometimes you are nice"
Cire kanta yayi daga cinyanshi seya shige daki
Murmushi tayi ta gyara kwanciyanta bacci ya dauketa.



IG.Tyetyelorh
[16:47, 3/16/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹UMARNIN IYAYEπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

WRITTEN BY:
                       TYETYELORH

EDITED BY:
                   AMEENATOU

                          πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

*118*

Abbah daya dawo daga office yana zaune shida Mami da Hakeem tace "Yawwa danka yace aure yakeso kuma idan ba'ayi mashi bah ze shiga duniya"

Dariya ya saki "toh gaskiya ya fito da mata tun kafin yaja mana abun kunya"
Ya fada yana dariya
Hakeem yace Allah Abbah dagaske nake aure nakeso 

Dafa mashi kai yayi yace toh an gama wace tayi sa'an samunka
Murmushi yayi yace safieyarh
"Safieyarh dana sani"

Daga kanshi yayi 
Toh ae daka fada tun wuri da mun hada dana Ameenah kawai
Wani dadi yaji yace amma yanzin za'ayi din koh
"Da zaran ka fara sana'a naga kuma kana kukari sosai za'a daura"
Mikewa yayi ya rungumeshi yana jin dadi

Mommy tace kaga irinta koh a haka za'a maka aure 
Kumawa yayi ya dake ya gyara wuyan riganshi yace "Toh yaushe zan fara zuwa office din"
Dariya Abbah ya saki yace haka akeso ranka ya dade 
Yanzin ran monday zamu je na kaika
Dadi yaji sosai ya mike dakinshi ya shiga yana murna

_Two weeks later_

Adeel yayi wata sabowan mota shima kia ce but wannan glass din motan is bulletproof ta ku wannan window kuma is black yasha tint 

Sunata shirye shiryen zuwa kaduna zasu kwana biyu acan Ameenah se duki takeyi randa ya gayan mata bata san sanda ta rungumeshi bah
Suna gama shiryawa da sassafe bayan sun karya suka fito kuma ya hanata gayan masu 
Tunda suka shiga suketa faman fada kaman kishiyoyi data gaji baya ta kuma seya tsayar da motan yace kaman wani driver ki ae wlh baki isa bah fito ko kuma fito dake

Shareshi tayi ta kulla idonta
Bude kofanshi yayi ya fito zagayawa yayi da karfi da yaji ya kinkimota tana ihu yasata a gaba suka cigaba da tafiya
Se surutai takeyi ita daya
Tsayawa yayi a wani store ya sayan masu tsaraba kala-kala se suka cigab da tafiya

Suna isa gidansu Ameenah suka fara zuwa dan shine a kusa tayi hauka data shiga gidan se ihu takeyi kwanansu daya amma basu gayan ma su safieyarh bah Mami se ji da ita ake duk abunda tace zataci shi ake bata danta ganta tayi wani kiba ga haske
Ameenah bata gane abunda take nufi bah se wani kwanciya take a jikinta kaman mage

Washe gari suka wuce gidansu Adeel sukaje lokacin safieyarh bata gida dan ta fara zuwa school daddy ya hanata zuwa Abujan Mommy jiki na rawa take tambayan Ameenah me zataci Adeel yace ni baza'a tambayeni bah
"Gafara can ae ita tanada nalura ne"

A tare suka hada ido seya fashe da dariya mikewa tayi a guje ta shige dakin safieyarh 
Duka takai mai toh mena dariyan gashi kasata ta gudu
"Wai Mommy kunyi tsammanin tanada ciki ne batada komai fah"

Ban gane batada komai ka sani bansan hauka fah
Shiru yayi kawai yana murmushi 
Da safieyarh ta dawo rungume Adeel tayi seta tambayeshi Ameenah dakinta ya nuna mata wucewa dakin tayi tana ihu
Rungume juna sukayi suna ihu take ce mata wai kinsan wani abu 
Mommy fa da Mami sun aza inada ciki ne
"Toh bakida shine"

Ke wlh banza ce yaza'ayi kice inada ciki
"Ya ko za'ayi bazan ce bah ji yadda kika kara wani haske gashi kin danyi kiba abunki"
Seta kai hannunta gun cikinta tace kuma fa ya fara girma
Bege mata hannu tayi ta mike tace ke kika sani

Washe gari wuraren karfe 3pm sukayi sallama dasu Mommy 
Gidansu Ameenah sukaje suma sukayi sallama dasu akan zasu koma kuka ta fara dakyar aka rabata da Mami danta riketa wai ita bazata koma bah 
Suna hanya se shan majina takeyi tana kuka a hankali 
branch din office dinsu yaje dan zekai ayi mai signing wasu documents toh basu tashi barin kaduna bah se ana kiran magrib tace mai kawai su koma se gobe da safe su kama hanya amma ya shareshi ta ya cigaba da tukin 
Sunyi nisa sosai dan har sun shiga Abujan lokacin har anyi isha an gama 
Suna cikin tafiya se sukaga motoci sunata juyowa wasu suna masu nuni da hannu suma su juya ga yan-fashi a gaba 

Zare ido Ameenah tayi tace mai su juya mana 
Yaki kawai se sukaji harbin bindiga wani ne ya gudu shine suke harbin motanshi har seda suka samoshi
Ihu Ameenah keyi ta tushe kunnanta gabadaya ta burkice se kuka
Sit belt dinta ya cire mata ya dafa mata kafada yace kalleni
Ta dago jajayen idanunta still ta tushe kunnanta da hannunta 
_"its okey babu abunda ze faru window motan nan is bullet-proof babu abunda ze faru kinji"_

Still ae zasu iya harbin tires din please kawai mu juya
Saketa yayi ya bude wani abu a cikin motan bindiga ya ciro a ciki
Tana gani ihu ta sake yi ta juyarda kanta tana kallon jefe

"Saka sit belt dinki"
Yace mata nan take ta juyo tace me zakayi 
Wucewa mana
Rike mashi hannu tayi tace "i beg of you kawai mu juya kowa juyawa yakeyi"
Murmushi yayi dan duk tabi ta tsorata
Juyarda motan zeyi amma motoci sun cika a bayansu kowa nasan guduwa amma an kasa saboda wannan ya shiga gaban wancan

Daga kanda zatayi kawai barayin sukayo kansu da bindigoji a hanunsu koma motansu shine na biyu
Kawai harbin bindiga suka karaji se sukaji ihun mace aka kara harbawa se shiru koma

Yana jin haka ya maida gun din sit belt dinshi ya cire itama ya cire mata nata dan shock dinda ta sama 

Fita yayi daga motan ya zagaya ta gefanta ya fito da ita security yasa a motan kawai yajata suka shige daji
Gudu kawai sukeyi se kuma harbin bindiga se duhu da sukeji sosai 

Barayin da sukaje gun motan kokarin budewa suka fara amma sun kasa kuma sun haska duhu kawai suke gani dan haka suka shiga harbin windows din amma be fashe ba se bullet dinda ke manne a jiki
Daga baya duka hakura

Cigaba da gudu sukeyi yana rike da hannunta se bayan sunyi nisa sosai seta tsaya tana maida numfashi tace ta gaji dakyar take magana
Shafa aljihunshi yayi seya ji waya da sauri ya fito dashi ya kunna haske daga ita se dankwali dan atanfane a jikinta toh tabar gyalen ma a cikin motan 
Tausayinta yaji sosai network din wayan ya duba yaga babo ku daya 
Haska gefansu yayi se kuma ya dawo da hasken gunta zaunar da ita yayi shime seya zauna
Kuka ta farayi tace toh yaza'ayi mu kuma gida yanxin gashi dare yayi
Shiru yayi 
Can bayan tadan huta se suka cigaba da tafiya koh zasu sama gida su kwana a ciki se da safe su kama hanya 
Sunyi nisa seta rikeshi suka tsaya kawai yankan jiki tayi ta zube 
Kamota yayi da sauri kiran sunata ya shiga yi amma shiru 

Daukanta yayi kaman baby ya cigaba da tafiyan 
Wani dan runfa ya gani seya karasa wurin da dabara ya ciro wayanshi ya haska zama yayi seya kwantar da ita akan laps nashi 
Fuskanta kawai yake haskawa 
Inda yaga dare haka yaga safe dan kwata kwata beyi bacci bah koh rufe ido ya kasa fuskan Ameenah ya kwana yana kalla she looks very innocent 

Da gari ya fara haske har yakaiga yana shafa fuskanta bude ido ta farayi a hankali seya cire hannunshi da sauri
Da fuskanshi ta fara sallama da sauri ta mike zaune gefe ta fara kalla ta tabbatar da ba mafarki takeyi bah 
Hawaye ta fara seta kalleshi mikewa yayi yana karkade kayanshi yace toh tashi mu kuma

Babu musu ta mike suka fara tafiya seta zo ta rike hannunshi 
Tana rike mai hannun wani abu yaji jirrrr ya tsireshi dakewa kawai yayi suka cigaba da tafiyan 
Sunyi nisa se kuma ya tsaya danya manta hanyan da sukabi saboda jiya hanya daya kawai ya gani amma yanzin seyaga biyu
Kallonshi tayi tace meyafaru
"Babu" kawai yace mata 
Hanya daya kawai yabi tafiya kawai suke amma shide besan inda suka nufa bah
Sunyi nisa sosai kawai se sukaga katon rafi a gabansu shi kuma ya tabbata jiya bega wannan rafin bah

Kalloshi ta sakeyi tace hala mun bata 
Daga mata kai yayi alaman hakane
"Toh wayanka fah ka duba map nama"
Cirowa yayi yana unlocking nashi seya mutu tsaki yayi ya maidashi
Juyawa yayi yace mu kuma semu bi ta dayan hanyan haka akayi sun koma amma basuga hanyan bah sun kara bata haka suka ringa yawo a dajin nan har kusan karfe 3pm 
Waje ta sama ta zauna wai ita wlh ta gaji gashi kuma tanajin yunwa

Toh hala namana zan yankan maki na baki
"Its not a bad idea zaka iya yanka ae wlh duk laifinkane daka bari mun sake kwana da duk haka be faru bah"

"Haka kikace koh ae seki kuma gidan da kanki"
Seya juya ya fara tafiya mikewa tayi ta bishi da sauri
Tafiya sukeyi idan sunyi nisa sesu huta se kuma a cigaba duk ta gaji se dingishi takeyi har muryanta ya dashe dan kuka
Juyawa yayi seya ganta tana tafita a hankali tana dingishi tsayawa yayi harta iso gun da yake 
Kawai daukanta yayi kaman baby gashi daman batada nauyi batayi musu ba dantasan ta gaji haka ya ringa tafiya da ita tafiya suke amma basu san inda suka nufa ba dan they are totally lost 
Ya gaji sosai shima seya sauketa suka zauna

Har gari ya fara duhu basu bar dajin nan bah kuma through out basu ci abinci ba talkless of sallah 
Suna tafiya ne akwai dan haske kadan kawai suka fito titi wani ihu tayi danjin dadi 
Tafiya sukeyi a titin duk motan dayazo wucewa seya saka hannu yana tsayar wa amma dan tsoro ana zuwa kusa dasu se kaga an kara gudu shi abun har dariya yake bashi.



                        πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[18:57, 3/16/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: Can sega wata mota tazo wucewa seta fara tafiya kaman zombie danta tsoratar dasu suna isowa kusa dasu wata mace ce a ciki tana ganinta kuwa seta kara gudu sosai
Dariya ta saki 
Shima dariya yakeyi yace idan kika ba kowa tsoro ae se muga inda zamu koma gida.
"Toh yan rainin hankalin sunki tsayawa"
Hannu ya kara sawa amma ba'a tsaya bah

Wani haddan mota ya kara zuwa kallonshi tayi tace karka sa hannu "watch and learn" 
Kallonta ya tsaya yi 
Wani dan iskan tsayuwa tayi hadda harde kafanta wuri daya seta saka hannu
Ae kowa ba tareda bata lokaci bah ya tsayar da motanshi
Kallon Adeel tayi ta sakar mashi da murmushi 
Shi ya kasa motsi ma mamakin abunda tayi kawai yakeyi

Gun motan ta nufa ta gaidashi saurayin ya amsa da fara'a shi yaga yan mata
"Daman lift muke so dan Allah motan mu yana gaba yan fashine suka taremu jiya da daddare shine muka bar motan a dajin nan muka kwana so please ka taimaka mana nida brother nane"

Tana magana tana wani fari da ido inda tasan ze yarda kuma tace yayanta ne saboda ta tabbata idan tace mijinta ne baze yarda bah

Murmushi yayi yace Allah sarki babu komai ko shigo
Godiya tayi mai seta kira Adeel wanda ya sankare yana kallonta kawai 
Jawo hannunshi tayi ya shiga gaba saurayin ya bashi hannu suka gaisa ita kuma ta shiga baya suka fara tafiya

Chager ya gani a cikin motan seya fito da wayanshi ya hada 5% yana shiga ya kunna seya kunna GPS dinshi yana anfani dashi wurin neman direction din motan

Sunata tafiya babu me magana a cikin motan Adeel se duban motan yakeyi
Ba'a dade ba sega motoci dayawa a wajan anyi fata fata dasu amma an matsar dasu gefe da alama sujoji sunzo wurin 
Cigaba da tafiya sukayi se suka hango motansu da sauri Ameenah tace gashi nan tsayar da motan yayi suka fito glass din motan yadan tsage kadan kadan alaman bullet din bude security na motan yayi 

Ameenah godiya tayi ma saurayin yace ze iya samin number ta murmushi tayi charap a kunnan Adeel juyowa yayi yace Mallam da aurenta saboda haka ka wuce kawai 

Beyi magana bah yaja motan ya wuce 
Shiga motan sukayi wayanta ta fara dauka tayi unlocking missed calls ne baja-baja a ciki
Hadda naso Mami 

Kunna motan yayi ya fara tafiya gudu kawai yakeyi dan kar su sake haduwa dasu 
Basufi 30mins ba suka shiga gari a wani bakery ya tsaya dan cikinshi har wani kara yakeyi,shi ya shiga ya sayo masu burger da lemo se ruwa 
Yana dawowa a tsakinyansu ya ajiye kafin ya tada motan harta kai hannu ta dauka guda daya

Kallonta yayi yace i thought yana saki kiba
"Ina ruwanka yunwa nakeji yini daya banci abinci bah wasane"
Murmushi kawai yayi 
Kafin ya fara tafiya ta dauka ruwa kuskure bakinta tayi ta fara cin burger nan shima haka yana tafiya suna ci 
Seda ta cinye guda biyu ta kura da ruwa se tayi ajiyan zuciya shi kuma guda daya yaci 

Suna isa gida yayi packing koh kayansu na cikin motan basu fito dashi bah suka shige tare duk sun manta dashi ita hatta wayanta ma a cikin motan ta barshi da gyalenta
Suna shiga ciki kowa dakinshi ya wuce
Wanka ya shiga yana fitowa sallolinshi ya biya yana gamawa gado ya haye wani wawan bacci ya daukeshi

Itama haka shower ta sakan ma kanta ta dade seta dauro alwala sallah itama tayi daga nan koh hijab bata cire bah bacci ya dauketa 

Su Mami kowa duk hankalinsu yaki kwanciya dan sun kira number Ameenah so nawa bata dauka ba na Adeel kuwa a kashe 

Basu suka tashi ba se washe gari shima se wuraren karfe 11am Ameenah ta tashi tayi sallah Asubah seta sake wanka ta fito kitchen ta shiga ta fara hada masu break-fast
Adeel kowa har lokacin be tashi bah se sharan bacci yakeyi se bayan ta gama tana gyara gyaran kan dining din ya fito koh wanka beyi bah da gajeran wando se riga a jikinshi
Tana daga kai ta kalleshi seta tintsire da dariya 

Kallonta yayi yace dadinta de tare muka sha wahala
Dariya take sosai hadda zama akan kujera 
Haushi dariyan ya fara bashi 
"Wlh idan baki dena min dariya bah zan gefeki"
Toshe baki tayi tana kokarin rike dariyan tace yahakuri- seta sake fashewa da dariya

Mikewa yayi yayo kanta da sauri ta mike tayi waje a guje shima ya bita gudu suka ringayi a tsakar gidan tanata dariya shima dariya yakeyi

Wajan pipe na ruwa taje kunnawa tayi yana yowa kanta fesa mashi ruwan ta ringayi jikashi yayi shakaf 
Zuwa yayi ya amshe itama ya fara jikata se dariya sukeyi.


IG.Tyetyelorh
[21:46, 3/17/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹UMARNIN IYAYEπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

WRITTEN BY:
                       TYETYELORH

EDITED BY:
                    AMEENATOU

                           πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

*119*

Sake pipe din tayi ta shige ciki a guje shima ya biyota dakinta ta shige tana dariya 
Changa kayanta tayi seta dauko drier tayi drying gashin 
Shan majina ta farayi alaman mura ze kamata fitowa tayi ta shiga kitchen tea ta hada da na'ana'a yasa ginger a ciki cup biyu ta hada tana fitowa a parlo ta sameshi yana zaune shima ya changa kaya mika mashi cup daya tayi itama ta zauna a dan gefe tana sha amma se tari takeyi shima haka gashi daman lokacin sanyi ne 

Mikewa yayi ya kunna hitter parlo ya dawo ya zauna 
Still bata bar tarin bah kallonta yayi yace kinason ki dene tari daga mai kai tayi seya ajiye cup din yace toh matso 
Daga gira tayi alaman tambaya 
"What ba abunda zan maki ki matso mana"

Mikewa tayi ta dawo kusa dashi ta zauna hannunshi ya daga yasa a kafadanta se tayi sauri ta matsa
Murmushi yayi yace serioualy ba abunda zan maki
Jikinshi ya matso da ita tareda saka hannu ya yagaya zuwa bayanta dan kwantawa tayi kadan a jikinshi setaji dumi tea din ta cigaba da sha 
"This so weird"Ameenah tace 
"Why do i feel close to you in a very short time?"
Adeel shiru kawai yayi a zuciyanshi yace "you have no idea"

Cup din ta ajiye tayi lamo a jikinshi wani dadi takeji dan zatayi iya bacci a jikinshi for the rest of her life 
Dagowa yayi ya kalle fuskanta yaga idon a kulle ta fara bacci smilling yayi yana shafa gashin ta a hankali har bacci shima ya daukeshi

Bacci suka ringayi har se wuraren karfe biyu suka tashi 
Abinci ta daura seta kuma dakinta danta dauka wayanta ta tuna da missed calls dinda ta gani dubawa tayi sama da saka amma ta rasa seta tuna bata dauko daga motan bah
Tana fitowa taga Adeel shima ze je gun motan dan haka seta bishi yana budewa trunk din ta fara ciro kayanta ta dauka wayanta da veil din seta kuma ciki
Mami ta fara kira suna gaisawa ta tambayeta sun isa gida lafiya tace lafiya kalaw 
Toh meyasa baki dauka call dina bah tun shekaran jiya naketa faman kira
Taso ta bata labarin abunda ya faru amma tasan zasu tada hankalinsu shiyasa tace mata wayan was silent ta nema ta rasa ashe ya fada karkashin kujera a motane ta zabga mata karya
"Toh shikenan ya Adeel din"
Lafiya klww
Yawwa toh ki gaida minshi se anjima 
Zeji ina gaida Abbah da Hakeem 
Ta katse wayan 
Wani call din ya shigo wayan smilling tayi seta dauka

Afra ce yarinyan sister Abbah amma tun suna yara suke paris acan aka haifesu kuma acan suka girma se suyi shekara biyu basuzo nigeria ba amma haka be hanasu zumunci ta waya ba yaransu biyu ne Afra da Afreen twins ne
Afran ce babba 
Yaran kyawawane dan mamansu a paris din tayi karatu so acan ta hadu da babansu 
Saboda haka sun dauko haskenshi da gashinshi sosai kuma sun iya hausa dan mamansu hausa take masu

Tana dauka tace Afra ae nayi fushi dake tun yaushe kikace zakizo min hutun amma har yau
"Habah babe yanxin kira nayi na gayan maki in two months time nida Afreen zamuzo maki hoto hadda Mama"
Ihu tayi wlh da kin gama min komai toh ya kuke

"Lafiya kalw ya Adeel dasu Hakeem"
"Wlh lafiyansu kalw wai anya baki crushing ma Hakeem din nan last post dinki na snapchat was his picture"

Dariya tayi tace kaman kinyi reading mind dina tun karshen zuwan mu nake crushing mai
Wani dariya Ameenah ta saki tace ae kowa yarinya you are too late dan yanxin yana dating safieyarh

"Ohh my goodness meyasa kika gayan min karkisa na fara kishi da ita"
Hira sukayi tayi daga baya tace tabama Adeel su gaisa 
Mikewa tayi tace toh barin kai mashi
Knocking tayi seta shiga dakinshi a gaban laptop ta sameshi yana zaune mikamai wayan tayi tace gashi Afran ce

Amsa yayi ya kara a kunne "Hello" 
"Hello Ya Adeel ina wuni"
Lafiya klw Afran ya kuke ya school
Wlh lafiya kalaw
"Ji yadda kike hausa kaman kina 9ja"
Smilling tayi tace ba dole bah Mama bata mana turanci koh french kwata-kwata idan muka mata magana bada hausa bah bata amsawa

Dariya yayi yace ae haka ya kamata toh ya Afreen 
"Wlh gatanan har tayi bacci"
Hira suke sosai har Ameenah ta gaji tayi wucewanta

_2 hours later_

Mura ne ya kamasu sosai suna zaune se shan majina suke dukda hitter dake parlo 
Wayanshi ne yayi kara alaman messege ya shigo dan haka seya duba alert ne yana dubawa 3million ya gani anyi mai snding a account dinshi ware ido yayi da mamaki ya tabbata hakan ne seya kira number manager shi

Yana dagawa suka gaisa yace yaga alert ne kudin meye
"Toh nima de ban sani bah captain dinku ya turo na tambayeshi na meye yace inde tura maka"

Toh shikenan barin kirashi se yayi hanging up
Yana kiran captain din yace mai babu wani dalili kawai turo mai yayi

"Dan ba yau ya fara bah tun aurensu da Ameenah kawai seyaga alert ya tambaya dalili seyace kawai turo mashi yayi amma be taba kaiwa millian uku bah se yau"
Godiya yayi mashi sukayi sallama 
Se yayi using wayanshi daga bank dinshi ya turama Daddynshi 1millon hakama Abbah shima ya tura mashi 1millon

Ba'a dade bah se Abbah ya kirashi mikewa yayi ya shiga daki ya daga call din 
Gaidashi yayi sosai ya amsa yace ya iyali
Lafiya kalaw
"Naga alert ne na meye"
Dan shiru yayi yana susa kiye kaman yana gabanshi can yace daban captain dinmu ya turomin dazin shine na tura maka kaida Daddy

Dukda Abbah shima yanada rufin asirinshi sosai amma yayi mashi godiya ya saka mashi albarka sosai sannan yayi ta mashi addu'a daga baya sokayi sallama
Kafin ya ajiye wayan sega Daddy shima ya kirashi shima yace mashi yaga kudi
Bayani yayi mashi shima yayi ta mashi addu'a sosai yaba Mommy tayita sa mashi albarka da fatan kuma Allah ya bashi yara masu bin umarninshi kamar yadda yabi UMARNIN IYAYENshi shima godiya yai sukayi sallama

Abbah yana cikin office dinshi seya kira number Daddy suna gama gaisawa yake cemai yanxin yaga alert Adeel ya turo mai millan daya Daddy yace shima ya turo mai addu'a suka ringa mai da kuma fatan Allah ya barsu tare Ameen

Dawowa yayi ya zauna se faman shan majina Ameenah keyi gashi saman hancinta yayi jajir abunka da faran fata 
Cewa yayi maganin ki kenan ae 
Murguda mai baki tayi tace duk ba laifinka bane da baka biyoni ba ae bazan taba ruwan ba gashi kaja min mura
"Kede kika sa-" se yayi atishawa
Dariya tayi "ni karka karamin da wanda ke damuna nawama ya isheni"

Mikewa yayi ya shiga kitchen ginger,garlic,lemon tsami se tom tom ya hada su waje da ya nikasu sannan yasa honey(zuma)
A wani karamin bowl ya saka ya daura spoon akai ya fito  

Zama yayi ya sha spoon daya kaman ya maida cikin bowl din dakyar ya hadiye haka yasake kai wani shima dakyar ya hadiye tana kallonshi se yamutsa fuska takeyi wane ita kesha
Kallonta yayi ya mika mata "gashi kisha"

"Ewww no thanks" tace seta juya dan ko warin amai ze sata
"Wlh dure zan maki idan baki sha bah"

Ae idan ana dole se muga yadda zaka dura min 
Mikewa yayi kujeran da take zaune akai ya zauna yace bude baki kallonshi tayi seta kalla bowl din tayi dariya "Do you really expect me to take that"
Seta nuna abun tana wani yamutse fuska wane taga kashi

"Seriously idan baki amsa ba zan maki karfi da yaji"
Dariya tayi toh ae semu gani sena zauna kaman gunki kana-
Bata karasa ba ya kamo lallausar hannunta dukka biyun ya hadasu gu daya kuma da hannu daya ya rike
Ihu ta farayi 
"Zaki tsaya kisha da kanki ko sena danneki na baki"

Wlh zansha, Zansha Allah Dan Allah ka sakeni
Murmushi yayi seya saketa kallan wajan tayi har yayi ja 
Mikewa tayi niyanyi ta gudu amma seyayi sauri ya rikota ya maidata ta zauna tareta yayi inda bazata iya sauka daga kujeran bah

"Kiyi two spoons dakanki ko kuma na dura maki five spoons"
Toh bani nasha ta mika hannunta
Mika mata yayi ta deba cokali daya seta toshe hancinta ta kai baki harcenta ta matsar dashi gefe inda baxe taba maganin ba balle taji taste dinshi seta zazzaga a cikin bakin 
Lokaci daya koma seta damke idonta tana hadiyewa seyi tayi kaman zatayi amai da sauri yasa hannunshi akan bakinta ya tare 

Wani spoon din ta kara kaiwa kaman zatayi kuka tana hadiyewa ya mika mata ruwa tasha setayi niyan mikewa 

Tareta yayi yace se nanda seya kalla agogon hannunshi ya cigaba nan da 20mins seki tashi lokacin ya gangaka
A hanakali tace "mugu kawai"
Murmushi yayi yace kice duk abunda zakice kinde sha

Harara ta galla mai ta gefe

_20 mins later_

Mikewa tayi da sauri tayi dakinta toilet ta wuce tayi2 tayi amai amma ta kasa haka ta hakura ta kwanta akan gadonta harta fara baccin dole


                              πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[22:31, 3/17/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: Life moved on wani sa'in kaman abun arxiki suyi shiri amma anjima kadan se suyi fada
Har yau kowa school din nasu basu bar strike bah

Har wata rana Manager shi ya kirashi yake gayan mashi in two days time yanada wani match din amma idan yaje two weeks zeyi 
Badan yaso bah ya amince 

Ameenah ya fadan mawa amma dan hauka irin nata setayi murna dajin haka shi kuma besan dalili bah amma se yaji ba dadi da yaganta tana murna

Dakinshi ya shiga ya kulle be sake fitowa ba se washe gari koh dinner beyi bah hatta masallaci beje bah a dakinshi ya zauna kawai 
Data fito daga dakinta taga se taga dinner shi be ciba bah bataji dadi bah amma seta kuma dakin

washe gari ma haka da safe ma be fito bah beyi breakfast ba kuma ita ta ajiye mai a dining tazo kwashe dishes din se taga bema taba bah 
Dakinshi ta nufa danta aza beyada lafiya ne 
Knocking ta shigayi amma be amsa ba balle ya bude 
Murda handle din tayi setaji shi a bude a hankali ta shiga tareda sallama 
Akan gado ta sameshi yana kwance da alama bacci yakeyi karasawa tayi bakin gadon ta kalleshi babu riga a jikishi ga abs dinshi manya manya 
Wani murmushi ne ya kwace mata a fuskan ta 

Tsayawa tayi tana kallonshi sosai batasan sanda ta zauna a bakin gadon bah kawai murmushi takeyi fuskanshi ta kalla he looks so very cute idan yana bacci 
A hankali takai hannunta kan packs nashi se kuma ta cire da sauri sake sakin murmushi tayi wannan karon hannu biyu takai wurin a hankali ta shafa 

Wani dadi takeji wane anyi mata kyautan daki a aljanna se murmushi takeyi she's really enjoying it dan a rayuwanta bata taba shafa packs ba se yau binshi takeyi kaman tana zanawa 
Ji takeyi kaman tayita yi harseta gaji dukda tasan ba gajiya zatayi bah 
Juyawa yayi kafin ta cire hannun harya danne mata hannu daya kokarin ja takeyi amma ta kasa har hannun ya fara sagewa wani zuciya yace mata kawai ta kwanta itama 
Cigaba da jan hannun takeyi but tasan bazata iya ba 
Tapping hannunshi ta farayi a hankali danya tashi amma kaman ba tabashi takeyi bah baccinshi yake hankali kwance 

Har wani murmushi yakeyi ta tabbata yana enjoying baccin dan haka seta dena tadashi ta cigaba da kallon fuskanshi dayan hannun kuma yana kan cikinshi haryanxin murmushi takeyi
Juyin da zeyi seya jawota daman abunka da mutum me kiba (Lmao)
Rabin jikinta yana kan gadon while rabin na waje 
A zuciyanta tace na kawo kaina yau
Kallonshi taketa yi har yanxin bata sani bah bacci ya dauketa itama din haka suka ringa tikan baccinsu ita tanada wani abu kuma ta gane ne lokacin da ya kwantar da ita a jikinshi sanda sukayi wasan ruwa abun shine idan tana kusa dashi bacci na saurin daukanta kuma tana dadewa tana bacci.

Basu suka tashi daga baccin nan ba se ana kiran la'asar shima shine ya tashi mika yakeyi amma idonshi a kulle yake yana salati kawai se yaji ya tabo mutum da sauri ya bude idon tareda matsawa baya kadan 

Abunda ya bashi mamaki kawai seyaga Ameenah tana bacci kusa dashi hankali kwance mamaki yayi sosai 
"Toh meya kawota dakina"abunda ya tambaya kanshi kenan 
Wata zuciya tace kilan aljana ce da sauri ya mike fita yayi dakinta ya shiga bata nan ya leka kitchen thesame answer infacts gidan gaba daya seda ya duba bata nan seya koma dakin har a lokacin tana bacci hannunshi yakai a hankali dan ya taba yaji ko itace da gaske 
Yana tabawa ya tabbata itace murmushi yayi se yayi pecking goshinta toilet ya shiga yayo alwala seya wuce masjid..



IG.Tyetyelorh
[05:55, 3/22/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹UMARNIN IYAYEπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

WRITTEN BY:
                      TYETYELORH

EDITED BY:
                   AMEENATOU

                                πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

_Ina gaisuwa Naja'atou salisu jahun jigawa state dis page is highly dedicated to you Tyetyelorh loves yuh_❣

*121*

Fitowa tayi bayan gidan ta zagaya harcan karashe tana zuwa setaga wani kofa murda handle din tayi danta bude but it's locked tsaki tayi har zata juyo seta tuna da keys dinda ya fadan mata da sauri ta kuma cikin gidan dakinshi ta shiga bunch of keys ta dauko ta kuma gun kofan trying keys din ta shigayi har daga baya tayi dace wani ya shiga daidai bude kofan tayi a hankali seta taja da baya 

Da taji shiru seta shiga kunna wutan dakin tayi sake baki tayi kawai setayi wani tsalle na murna shiga ciki tayi sosai tana shafa kayan wani dadi takeji

Dakin Adeel ne na gym so akwai kayan training dinshi kala-kala a ciki
A fili tace ashe nan kake zuwa idan ka dawo daga sallah asubah dan mugunta baka fadan min bah
Ba tareda bata lokaci bah ta fara excising itama ta dade sosai a ciki daga baya ta kulle ta fito duk tayi zufa 
Ajiye keys din tayi akan tv stand seta wuce dakinta wanka tayi ta saka riga da wando parlo ta dawo tayi zamanta 

A zuciya ta cewa tayi _"Allah yasan am missing you alot the house is so boring without you"_
Dan guntun tsaki ta saki seta kwanta kan kujeran

Shima haka ta gefanshi yana kwance se faman juyi yake ji yake kaman yayi tsalle ya ganshi gabanta he's missing her like crazy wayanshi ya dauka ze kirata har yakai kan number seya maida wayan a ajiye wani mugun yunwa yakeji amma shi baze iya cin wani abinci bah idan ba nata bah tun zuwanshi beci abin arziki bah 
Sake daukan wayan yayi kawai yana kallan kan screen din tunani barkate yakeyi a zuciyanshi

Wayanta ta dauka babu second thought tayi dailing numbershi seta saka a kunne
Kallon screen din yakeyi kawai yaga numberta akan wayan alaman kira da sauri ya mike zauna seya dan tsaya wai shi jan aji

Can seya dauka "Hello" yace itama ta amsa seta gaidashi 
Mamaki yayi sosai dan bata taba gaisheshi bah
Amsawa yayi a hankali se duk sukayi shiru kuma 
Can se tace daman akwai gym a gidan nan baka fadan min bah
Murmushi yayi yace a mana shiyasa na gayan maki inda keys din gidan yake dan nasan wata rana if you get bored zaki zaga

Ae kowa daga nan nake yanxin
Yanxin ma shiru sukayi se tace yaushe zaka dawo ne 
Dariya yayi "Someone is missing mee"
"Seriously to be frank i missed you ni kadai a gidan kaman mayya"

Yaji abunda tace kuma yaji dadi sosai seya basar yace toh meyasa baki fita ki dan ringa shiga makuta mana
Da muryan shagwaba tace "ni na gwammace nayita zamana a gida a kan na shiga makuta dan mata sun fiye gulma

"Toh school fah?"
"Ae ba kullum nakeda lectures bah"
Tahb kawai yace 
Akwai wani frnd dina zan kirashi ya kawo maki matarshi gobe da safe seta maki yini

Dadi taji sosai "yeey thank you"
"You are welcome"
Toh seda safe ni zan kwanta yanxin
"Sweet dreamx" se yayi hanging up

Wani murmushi ya saki dan har cikin ranshi yaji dadin wayan da sukayi and the best part is da tace she missed him pecking gaban wayan yayi yana murmushi seya mike training ya farayi dan yau basuda wani match se nan da two days

Da daddare ta kasa bacci se famam juyi takeyi mikewa tayi alwala tayi ta ringa gero sallah ta kusan 30mins tanayi tayi addu'anta seta kuma kan gado dukda hakan ta kasa bacci parlo ta dawo ta kunna tv ta ringa kallo but still koh gyan-gyadi ta kasayi kuma gashi dare yayi sosai dan har 1am tayi

Mikewa tayi dakin Adeel ta shige karkade gado tayi ta haye seta kashe lamp din kusa da gadon tana kwance kan pillo amma tana jin kanshin turarenshi sosai koh 10mins batayi bah bacci yayi awon gaba da ita baccin da tun randa ya tafi batayi irinshi bah dan bacci rabi da rabi takeyi kullum batasan dalili bah

Mafarki takeyi wai gatanan tanata shafa packs dinshi tana murmushi ita daya haka ta ringa baccinta

_Washe gari_

Karfe takwas na safiyan ranan tana cikin baccinta se taji bell na gate yana kara a firgice ta mike kallon cameran gate din takeyi tana mika tareda salati 

Mota ta gani zooming fuskan tayi se taga mace da namiji ne a cikin motan wanda tanada tabbacin cewa bata taba ganinsu bah

Komawa tayi ta kwanta kawai se abunda Adeel ya gayan mata cewa gobe da safe ze aiko abokinshi ya kawo mata matanshi
Da sauri ta mike fitowa tayi parlo seta bude masu gate din dakinta ta wuce ta zunbula katon hijab na sallanta seta fito a bakin kofan parlo ta tsaya tana kallonsu

Yana gama packing shiya fara fitowa seya zagaya gunta ya bude mata ya mika mata hannu seta fito 
Sun burgeta sosai inama itace abunda tace kenan a fili
Dusowa sukayi gunta suna murmushi se a lokacin ta gane shi shine wanda ya taba zuwa yanata danna bell din gate amma bata bude bah

Murmushi ta sakar masu lokacin da suka karaso inda take 
"Sannunku da zuwa" tace seta koma cikin parlon suna biye da ita

Seda suka zauna seta fara gaidashi amsawa yayi da fara'a kwance kan fuskanshi itama haka suka gaisa 
Mikewa tayi tace bari ta kawo mai ruwa tunda shi yanxin ze koma

Dakatar da ita yayi yace ta barshi kawai jiranshi akeyi idan yazo daukanta yasha

Murmushi tayi seta kuma ta zauna 
Mikewa yayi yayi mata sallama akan bayan magrib zezo daukanta se ta fito ta rakashi ita kuma Ameenah tana kallonsu sun mugun bata sha'awa

Muhseen kenan abokin Adeel ne sosai dansun dade tare da matanshi me suna Fauziyya

Yana tafiya Fauziyya ta dawo parlon anan suka sake gaisawa
Shiru sukayi can se Ameenah ta mike kunna tv tayi tace ina zuwa dakinta ta shiga watsa ruwa tayi tana fitowa shafa mai kawai tayi ta taje gashinta seta saka duguwan riga na atamfa ta fito haka gashinta a waje 

Kallon fauziyya tayi seta sakar mata murmushi seta zauna can mikewa tayi tace barin hada mana breakfast koh
Itama fauziyya mikewa tayi tana cire gyalen jikinta tace muje na tayaki babu musu suka shiga kitchen din Ameenah na gaba 

Dankali ta debo suka shiga barewa tare suna dan hira sama-sama har suka gama 
Soyawa suka shigayi dankali da kwai sukayi seda suka gyara kitchen din se suka fito kan dining suka zauna kayan tea Ameenah ta tura mata tace ta hada tea ba musu ta amsa ta fara hadawa
Ita kowa dankalin kawai take ci
Tambayanta tayi ke bazaki sha tea bah

Girgiza kanta tayi tace Aa banshan madara
Murmushi tayi halan munada Baby ne toh Allah saukar lafiya
"Banida komai fah " Ameenah tace

Shiru tayi kawai suka cigaba da cin abincin suna gamawa tare suka shiga da dishes din kitchen 
Parlo suka dawo suna dan hira

Wuraren karfe 2pm by now sun dan saba dan ita Fauziyya ta gane cewa ba wani son juna sukeyi ba dan haka tace zata koya mata rike miji da kuma girki daban-daban 

Kallonta kawai takeyi 
Shiga kitchen sukayi dan fara koyan girkin
 yanxin abinci kala biyu sukayi na yan gayu 
Ameenah taji dadin zuwan Fauziyya dan ta koya mata abu kala-kala banda ma girki hadda yadda zata gyara jikinta yadda zatayi tattalin kanta a matsayin ya mace da kuma rike mijinda

Da yamma Muhseen yazo ya dauka matanshi seda suka sashi ya zauna yaci abincin da suka hada 
Ameenah tayi mata godiya sannan ta tambayashi akan dan Allah gobe ya kawota
Murmushi yayi yace insha Allah
**********

Wayanta ne ke ringing tana dubawa taga Adeel ba tareda bata lokaci bah ta daga 
Gaisawa sukayi se yake tambayanta Muhseen ya kawo matan nashi kowa

"Ya kawota tunda safe harse yamma yazo ya dauketa tanada kirki wlh ta koya min abubuwa kala-kala hadda girki"
"Allah sarki, girki dame ta koya maki?"

"Abu mana"
"Abun nakeson naji ae"
Wai ina ruwanka tsakanin mata ne.
"Kide fadi gaskiya hadda rime miji ta koya maki koh"
Katse wayan tayi da sauri dan wani kunyanshi ne yazo mata 

Da yaji ta kashe wayan dariya yayi yana kallon kan wayan dan ya gane kunya taji
Ya rasa gane dalili tun barinshi garin idan yana waya da ita yana samun nishadi sosai ku meyasa ohu

Ta gefanta kowa itama dariya takeyi hadda rufe fuska wane tana gabanshi ne 
"She's really crushing on him cus she admit it he's handsome his lips are killing her he have this big brown sexy eyes that duk lokacin da take kalla she's feeling like thousanda butterflies in her stomach and he have this romantic voice wanda tasan ko shi besan yanadashi bah ga wani tafiya da yakeyi kaman yana cat walking ga wasu jijiya a hannunshi wanda tun suna school itada Ameerah da fatye idan kaman class-mate dinsu masu jijiya a hannu ne suna burgesu and the best part is his packs thats her weak point dan lokacin kafin tayi aure wayanta hotonan shirtless maza ne dayawa ga account dinta na instagram packs ne baja-baja Mami ce ta sata a gaba gabadaya ta goge su dukka

A kwance take wannan tunanin a dakin Adeel
Har bacci gwanin sata ya sace ta 
Ta gefan Adeel shima haka yaketa tunanin nan yasan he have already falling for her dukda besan ya *so* yake bah 
Saboda idan tana magana abu biyu kawai yake sakashi tsayawa kallonta na farko lips dinta suna kasheshi dan idan za'a bashi dama ace yata shafa lips dinta harseya gaji ze iya kuma yasan ba gajiyan zeyi bah na biyu kuma voice dinta dan akwai wasu lokaci da take cewa yana banza da ita shi beman san abunda take cewa ba lokacin dan idan tana magana ji yake tana mashi waka a kunne
"He knows it he have feelings for her but he have no idea taya ze fara gayan mata dan a rayuwanshi be taba tunanin ze fada tarkon soyayya ba balle harya gayan ma ya mace yana sonta but Ameenah deserve it she deserve more"

Tunani barkate kawai yakeyi shima har bacci ya daukeshi 
*************

Tun daga ranan idan Muhseen zeje office ze kawo Fauziyya gun Ameenah ta yini mata dansu basuda yara har tsahon kwana biyar haka yake kawota

Rana na biyar ya kama ranan saturday kenan shiyasa be kawota bah 
Ranan Monday kowa
A lokacin Ameenah tasan komai gameda zaman aure da kuma gyaran jiki( bawai da bata sni bane Noh amma yanxin ta kara ganewa)
 Ameenah ta cigaba da zuwa makaranta abunta idan kuma batada class toh zatayi zamanta a gida ta ringa koyan girki da littafin koyan girkin da Fauziyya ta bata 


                             πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[06:28, 3/22/2017] 1D-Tyetyelorh-❣: . KADUNA

Mami ce ke zaune ita kadai da glass a idonta tana danna wayanta se Hakeem ya shigo dakinshi ya shige ba'ayi koh minti 10 bah sega Abah ya shigo mikewa tayi da sauri ta amsa jakanshi tana tambayanshi lafiya ya dawo ba lokacin daya saba dawowa bah

Samun waje yayi ya zauna yana mikar da kafa se yace wlh dan zazzabi ne ke damuna shiyasa 

"Subhanallah toh ka tasu muje doctor ya dubaka mana"
"Aa lafiyana kalawa fah hutawa zanyi kawai zan dawo daidai"
"Habah Allah ya zaka ce haka toh barin kirashi yazo kawai" tayi magana tana niyan dauko wayanta

Hannunta ya rike "calm down nace maki lafiya na kalaw fah ki barshi kawai"
Badan taso ba ta hakura seta dauko mashi maganin zazzabi ta mika mashi da ruwa a cikin glass cup ba musu ya amsa yasha
Zama tayi a kusa dashi 

_30 minutes later_

Mikewa yayi yace barin dan watsa ruwa sena-
Maganan dabe karasa ba kenan ya zube a kasa sumamme
Salati Mami ta farayi tana hada hannunta waje daya tayo kanshi jijjigashi ta farayi tana cewa Alhaji!! Alhaji!!!  
Amma shiru
Kwallama Hakeem suna ta shigayi Allah ya taimaketa yana nan dukda weekdays ne 

Kiran sunan Hakeem take sosai tana hawaye 
A guje ya fito daga dakinshi a durkushe ya sameta ga Abbah a gabanta kaman mamaci kansu yayo shima ya shiga tadashi yana cewa Abbah!! Abbah!!!

Amma shiru mikewa yayi aguje yayi waje gate-man ya kira danya tayashi sa Abbah a mota suje asibiti
Shigowa yayi shima da sauri a kafada kowa ya saka hannun Abbah suka sauko dashi a hankali

Mami na binsu a baya tana salati da kuka dukka
A sit din baya suka sakashi 
Mayafi ta ganyo ta shiga itama bude masu gate megadi yayi a guje suka fita

Share this

WhatsApp
Email ThisBlogThis!Share to TwitterShare to Facebook
Newer Post Older Post Home

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts

  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 11 to 20
    Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima.     Casuke A...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 31 to 40
    Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gado...
  • RAINA KAMA Book 1 Page 1 to 10
    RAINA KAMA......!!♦_*                _{Kaga gayya}_          *_Bilyn Abdull ceπŸ€™πŸ»_* *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!._* πŸ‘‰πŸ»1⃣      *Matsanan ...
  • RAINA KAMA BOOK 2 Page 21 to 30
    Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”.         Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, murya...
  • BARIKI AUREN SOJA Page 51 to 60
    Motocine guda shida aka ajiye musu sababbi dal suna sheki ta tsakiyar tasha Adon balloon kana gani Kasan motar AMARYA ce ta fito tareda su ...
  • KASUWANCI NA Page 61 to 70
    Ameer kasa jurewa yayi gaba daya jikinsa ya fara rawa,tunawa Meenat tayi ba Muharraminta bane sai ta dan matsa kamar zata fada kasa ta wayan...
  • KASUWANCI NA Page 31 to 40
       A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, d...
  • UMURNIN IYAYE Page 51 to 60
    Suna isa asibitin emergency ward aka shiga dashi  Wani kujera suka zauna akai Hakeem yana shafa bayan Mami a hanakali yana bata hakuri shim...
  • UMMU AYMANA Part 6
      *UMMU AYMANA PART 6* Suna isa Asibitin likitoci suka rufu akanta,wanda da taimakon Allah bata jimaba ta farfaΙ—o se kuka takeyi,prince kasa...
  • MIWASMITI Page 31 to 40
    Kuka ta Kuma saki gamida kamo hannushi ta matse a tsakiyar qirjinta Dan jin wani irin suka da yake mata Ga jiri da takeji gaba daya bata gan...

Categories

  • 'YA'YA DA KUDI 1-END (8)
  • 'YA'YA MATA 1-END (9)
  • 'YAR BOKO 1-END (6)
  • 'YAR FULANI 1-END (14)
  • 'YAR GIDAN TSOHUWA 1-END (6)
  • 'YAR JAMI'A (9)
  • 'YAR MAFIYA 1-END (6)
  • 'YAR TALAKAWA 1-END (7)
  • AGOLA 1-END (17)
  • AKIDATA BOOK 2 Page 45 -End (11)
  • ANAL 1-END (12)
  • ANTIN YARA 1-END (6)
  • AUREN JARI 1-END (9)
  • BAKAR MACE 1-END (3)
  • BARIKI AUREN SOJA 1-End (8)
  • BINTU 1-END (7)
  • CIN AMANA KO FANSA 1-END (10)
  • CIWON IDANUNA 1-END (7)
  • CIWON IDANUNA AUDIO (2)
  • DAGA TAIMAKO 1-END (5)
  • DAKON SO 1-END (4)
  • DAMA TA BIYU 1-END (13)
  • DR BOBBY 1-END (11)
  • DUBU CIKAR MAI CARBI 1-END (7)
  • FULANI 1-END (11)
  • GURBIN IDO 1-END (1)
  • HADIN ALLAH 1-END (8)
  • HIBBAH 1-END (4)
  • INA ZAN GANSHI 1-END (7)
  • INAYA 1-END (9)
  • JIDDARTIL KHAIR 1-End (1)
  • JIHADI 1-END (10)
  • JUWAIRIYYA 1-END (7)
  • JUYAYI PAGE 1-END (6)
  • KASUWANCI NA Page 1-End (1)
  • MACIJINE SHI 1-END (1)
  • MAH NOOR 1-END (5)
  • MAIMOON 1-END (10)
  • MAKARANTAR KWANA 1-END (5)
  • MAKAUNIYAR KADDARA 1-END (10)
  • MATAR ALI 1-END (10)
  • MIWASMITI 1-END (8)
  • MOTAR KWADAYI 1-END (4)
  • NAMIJI BAYA KADAN 1-END (16)
  • NI AYS NAKE SO 1-END (16)
  • RAINA KAMA 1-END (1)
  • RAYUWATA 1-END (6)
  • SHIMFIDAR MIJINA 1-END (3)
  • SONE AJALINA 1-END (5)
  • SURBAJO 1-END (14)
  • TUDUN DAFAWA 1-END (4)
  • TUZURU 1-END (6)
  • UMAR KO FARUUQ 1-END (5)
  • UMMU AYMANA 1-END (8)
  • UMURNIN IYAYE 1-END (7)
  • WAMINAL HOOB 1-END (9)
  • YAN MATAN ZAMANI 1-END (6)
  • ZAYN MALIK 1-END (10)
  • ZUCIYA KOWA DA IRIN TASA 1 (10)
  • ZUMA SAI DA WUTA PAGE 1-END (7)

Social Plugin

  • facebook
  • twitter
  • instagram
  • youtube

Hausa novels 2023

Search This Blog

Powered by Blogger.

Blog Archive

  • July 2023 (7)
  • June 2023 (65)
  • April 2023 (33)
  • March 2023 (132)
  • January 2020 (10)
  • December 2017 (62)
  • November 2017 (33)
  • October 2017 (38)
  • September 2017 (39)
  • August 2017 (75)

Report Abuse

Total Pageviews

Copyright © 2023 To Hausa novels 2023 | Powered By WwW.aysnovel.com.ng
Design By Aysha Adam | Theme By WwW.aysnovel.com.ng | Distributed By Aysha Adam